-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

KISAN GILLA Hausa Novel

KISAN GILLA Hausa Novel

 KISAN GILLA Hausa Novel

Littafi na Daya (1)

Complete 

E-book Suleiman Zidane Kd 

Whatsapp 08161272634

.


Marubucin Littafin

Abdul Aziz Sani M/Gini

Typing AA Misau

Ke Magana

.

Labari ya isowa AA Misau cewa...

MARUBUCIN YA RARA DA CEWA,

A wani zamani can baya mai tsawo da ya

shude anyi

wani babban birni mai suna madinatul

haswar

a cikin daular larabawa

birnin madinatul haswar ya bunkasa a kan

karfin

arziki girman kasa, karfin mayaka da yawan

al umma

sarkin dake mulkin birnin madinatul haswar

ya kasance adali mai tausayi da jin kan

talakawa ana kiransa da suna HISHAM IBN

UBAIDA

.

SARKI HISHAM yana da matar aure guda daya

jal mai suna

shamilat wadda ta kasance yar wani babban

sarki mai

mulkin wata kasa da ake kira da hushush

ana kiran wannan

sarki da SAHIBUL HILAYAT

sai da sarki hisham ya auri shamilat da

shekaru goma sha daya sannan Allah ya

albarkace su da samun juna biyu nan fa

sarki hisham da shamilat suka cika da

tsananin farin ciki

domin

a duniya basu da wani buri wanda yafi

ganin sun sami haihuwa saboda a shekarun

baya babu abin da basuyi ba, domin su sami

haihuwar amma abu ya gagara,

lokacin da mahaifin

shamilat ya samu labarin cewa 'yarsa ta

sami juna

biyu sai ya kamu da tsananin farin ciki fiye

da ita

kanta shamilat din da mijinta saboda shi

kuma bashi da burin da yafi yaga jikansa

kafin ajali ya riske shi kasancewar tsufa ya

riske shi

a ko yaushe ta Allah zata iya kasancewa

Al amin Ahmed Misau, Guyson nake magana,

bisa wannan dalili ne sarki sahibul hilayat ya

tashi manzanni da dukiya mai yawa ya aiko

su izuwa ga sarki

hisham yace ga wannan ayi

renon ciki kuma idan haihuwa tazo daf yana

son

shamilat ta je gida ta haihu, yayin da

wannan sako ya isa ga

sarki hisham sai hankalinsa ya dugunzuma

domin

baya son ya rabu da matarsa dai dai da

dakika daya

amma kuma yana matukar jin nauyin

surukin nasa don haka

sai ya amince da hakan ita kuwa shamilat

sai ta kamu

da matukar farin ciki saboda a rayuwarta

babu abinda

take so sama da ta kasance tare da

mahaifinta a ko yaushe

saboda ita kadaice 'yarsa a duniya

sarki Hisham yana da dan uwa yarima

ZAMARU wanda

ya kasance azzalumi kuma mara imani mai

tsananin son duniya

uwa daya

uba daya suke dashi da hisham, a zahiri

yarima zamaru

yana nuna cewa yana matukar kaunar dan

uwansa

sarki hisham amma a karkashin zuciyarsa

babu

abinda ya tsana sama da shi ba wani bane

ya haddasa

wannan gaba ba a tsakaninsu face kawai

hassada da

kyashi da kuma tsananin son KARAGAR

MULKI

TUN mahaifin su sarki hisham na raye ya

futa cewa hisham

ne zai gaje shi daga

wannan lokaci ne yarima zamaru yaji ya

tsani

dan uwansa sarki hisham ya fara tunanin

hanyar

da zaibi ya kawar dashi daga doron kasa

sau bakwai

yarima zamaru yana bayar da kwangilar a

kashe

hisham amma yana kubuta kasancewarsa

sadauki mai

dakawa maza gumba a hannu

Guyson nake magana Al amin Kenan

Lokacin da yarima zamaru yaga ya kasa

ganin bayan

sarki Hisham sai ya

zuba ido izuwa lokacin da tsufa zasu

riskeshi har

rai yayi halinsa

saboda ya tabbatar da cewa indai babu

sarki hisham

dole shine zai hau karagar mulki, ana cikin

wannan hali ne

na jiran lokaci kwatsam sai shamilat ta sami

juna biyu

hm Al amarin da ya kara dugunzuma

hankalin yarima zamaru kenan saboda ya

san cewa idan matar hisham ta haihu to fa

sarautar ta kara yi masa nisa, a ranar da

zamaru ya sami labarin cewa shamilat

ta samu juna biyu sai ya kasa zaune ya kasa

tsaye

har dare ya raba bai rintsa ba

Babban abinda ya kara jefa

shi cikin bakin ciki shine shima matarsa ba

ta taba

haihuwa ba don haka duk ranar da ya mutu

shi

kenan bashi da magajin mulki, cikin tsakar

dare yarima

zamaru na kai kawo a cikin turakarsa ya

kasa barci sai matarsa sarima ta farka

daga barci koda taganshi a tsaye yana kai

kawo saita dube shi

cikin tsananin damuwa ta mike da sauri

tasha gabansa

tana mai rike kafadunsa, tace yakai mijina

menene

ya tayar maka da hankali a yau har ka kasa

bacci?

Koda jin wannan tambaya sai yarima

zamaru ya yi ajiyar zuciya sannan yace

baki da labarin cewa matar sarki ta samu

juna biyu ne?

Sarina tayi ajiyar zuciya tace haba maigida

yanzu

a kan haka ne ka tayar da hankalinka har ka

kasa bacci koda jin haka

sai zamaru ya rufe sarina da fada yana cewa

bata da

hankali bata da kishin rayuwarta,

sarina ta bushe da dariya sannan ta ce ka

kwantar da hankalinka mijina ina so ka

sani cewa ni na san abinda ba ka sani ba

idan har kana so ka san abinda na sani

yanzu ka

tashi mu tafi izuwa can bayan gari wajan

wani bakon boka da yazo

cikin alamun karayar zuciya yarima

zamaru ya dubi sarina yace ke nifa na gaji

da maganganun bokayan nan

tunda an dade ana ruwa kasa na tsotsewa

kuma na gaji da gafara sa har

yanzu banga kaho ba

Guyson nake magana, sarina tayi murmushi

tace aiko bokaye

suna suka tara wannan bokan ya wuce

yadda duk kake

tsammani duk wani bayani da zan yi maka

ba zaka

gamsu ba don haka gani ya kori ji kawai

kazo muje wajansa

yanzu a cikin wannan daren cikin sirri

koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya

cika

da farin ciki kawai sai ya mike zumbur ya

kama shiri

yayi badda kama itama sarina yasa ta ta

batar da kamanninta sannan sukayi

hawa suka fice daga cikin birnin madinatul

haswar a sirrance ba tare da kowa ya

shaida su ba

sai da suka yi tafiyar kusan rabin

Sa a sannan suka iso gaban wani katon

dutse

wanda a kansa akwai wata yar karamar

bukka

abinda ya daurewa yarima zamaru kai shine

ganin matattakalar bene a kan dutsen

tamkar sassake dutsen akayi

aka samar da ita shi dai

zamaru ya san wannan dutse sama da

shekaru

talatin baya amma bai taba ganin wannan

matattakala

a jikinsa

ba tabbas wannan matattakala aikin aljanu

ne

bana mutum ba abinda zamaru ya ayyana

kenan a cikin

zuciyarsa

bayan zamaru da sarina sun tsaida

dokunansu a gaban dutsen sun sauka

sai suka daure dawakan nasu a jikin wata

bishiya sannan suka taka

wannan matattakala suka hau kan dutsen

suna isa gaban wannan bukka sai sukaga

bokan tsulum ya

bayyana a gabansu yana kyakyata dariya al

amarin da ya dan razana yarima zamaru

kenan ya dan ja da baya kadan , shi dai

wannan boka

ya kasance dogon mutum garjeje mai kirar

mutanan

farko jikinsa gaba daya a murde yake alamar

karfi ta bayyana karara a tare da shi yana da

yar

faffadar fuska kyakkyawa cike da kasumba

da gajeran gemu

babu riga a jikinsa face wata fatar damisa

wacce ya yafata bisa kirjinsa ta zagayo

izuwa bayansa

daga cikinsa zuwa gwiwoyinsa a rufe suke

da bante irin na fatar damisar da ya yafa

kuma

takalmin dake kafarsa ma anyi shine da

wannan fatar damisa

gaba dayan damatsansa na hagu dana

dama a cike

suke da gurayen tsafi , tabbas wannan boka

yana da kwarjini da cika ido kai da

ganinsa kasan cewa murucin kan dutse ne

wato bai fito ba

sai da ya shirya

bokan ya dubi yarima zamaru yayi

murmushi yace

kada kaji tsoro ya shugabana ni mai

taimako ne a gareka

ko ince zamu yiwa juna taimako ku biyoni

izuwa cikin bukkata mu zauna domin mu

tattauna sosai

koda gama fadin haka sai bokan ya juya ya

shiga

cikin bukkar nan take yarima zamaru da

sarina

suka bishi a baya ba tare da fargabar komai

ba

da shigarsu cikin bukkar sai yarima zamaru

ya sake cika

da tsananin mamaki domin kansa ne ma ya

kusan juyewa

saboda ya tsinci kansa ne a cikin wata

makekiyar fada wacce

ta kawatu ainun ninkin

fadar sarki hisham sau uku wadansu

kuyangin aljanu sunata hidima da kai kawo

bokan yaci gaba da tafiya a tsakiyar fadar ya

nufi inda karagar mulki take

su zamaru na biye dashi amma basu isa

inda karagar mulkin take ba sai

da suka yi taku dari da arba in, da zuwa sai

bokan ya zauna akan karagar mulki yarima

zamaru da sarina kuwa sai kuyangin aljanun

suka kama hannayansu suka kaisu izuwa

kan wadansu

kujeru dake daf da karagar mulkin suka

zaunar

dasu

nan da nan aka kawowa yarima zamaru da

sarina

ruwan inibi a cikin tambulan na zinare da

kofuna suka fara jika makoshinsu a sannan

ne bokan ya dubi yarima zamaru a karo na

biyu yace lale maraba

da yarima zamaru dan uwan hisham sarkin

gobe

Al amin Ahmed Misau

Guyson Sunana Kenan

koda jin wannan batu zamaru ya natsu

sosai

bokan ya ci gaba da bayani yana mai cewa

ka kwantar da hankalinka ya kai wannan

dan sarki

kayi sani cewa matarka tazo nan kafin kai

kuma

mune mukace ta kawo ka

mun san duk abin dake damunka da kuma

burin dake

zuciyarka

tabbas mune zamu magance maka dukkan

matsalarka muddin muma zaka bi umarnin

mu shin ka amince da wannan sharadi?

Koda jin wannan batu sai yarima zamaru ya

dubi bokan cikin alamun rashin

fahimta sannan yace menene sharadin da

kake so ka gindaya mun

bokan yayi murmushi yace ina so ka dauki

alkawari cewar idan bukata ta biya zaka

raba birninka

biyu ka bani kaso guda na mallakeshi haka

kuma zaka bani rabin dukkan

dukiyarka

lokacin da yarima zamaru yaji wannan batu

sai

hankalinsa ya dugunzuma ainun ya rasa

abin dake masa dadi yayi shiru yana tunani

bokan ya tuntsure da dariya alamun da ya

janyo katsewar

tunanin yarima zamaru kenan ya dago kai a

firgice

ya dubeshi yace ni ne Hizainu ibin Markasi

masanin sirrin gobe,

yakai wannan dan sarki ina so ka sani cewa

babu wani

abu da mutum ke samu a saukake kuma a

banza face

ya rasa wani abu

ina mai shawartarka daka dauki sharadina

ni kuma na

taimaka maka na sanar dakai duk abinda

zaka yi ka

samu biyan bukatarka kuma

yanzu ne kadai damarka

idan ka bari wannan dama ta wuce ka har

abada ba zaka samu wata ba

sa adda yarima zamaru jai wannan batu sai

ya kawo gwauron numfashi ya ajiye gami

da ajiyar zuciya ya sake yin dan guntun

tunani

sannan ya dubi boka

hizainu yace na yarda idan ka taimakeni

burina ya cika zan raba mulkina da dukiyata

gida biyu na baka rabi amma bisa shardi

guda

sharadin kuwa shine sai dai kayi rantsuwa

da girman

tsafi da kuma darajar iyayenka cewar a gaba

ba zaka yi yunkurin

rabani da mulkina ba

domin ka mallaki kasar gaba daya kuma ba

zaka taba cutar

dani ba ko wani nawa

koda jin wannan batu

sai idanun boka hizainu suka zazzaro ya

kamu da tsananin

mamaki saboda bai taba zaton cewa yarima

zamaru zai daureshi ba da jijiyarsa haka, al

amarin da ya jefa

shi cikin shakku da wasu wasi kenan ya

kama muzurai yana

kallon kuyanginsa dake kai kawo a cikin

fadar suna hidama

sai da yayi dan tunani da nazari sannan ya

bushe da dariya

nan take yayi rantsuwa da girman tsafi gami

da darajar iyayansa bisa kan cewa ba zai

taba neman

wani abuba daban a wajan yarima

Zamaru a nan gaba kuma ba zai cutar dashi

ba koda jin haka

sai farin ciki

ya lullube yarima zamaru yace shima ya

amince da bukatar

boka hizaunu

boka hizainu ya kyalkyala da dariyar murna

yace

gobe da safe idan kaje fada zaka iske dan

uwanka sarki hisha,

a kwance cikin cutar ajali kuma ba zai wuce

kwana bakwai ba a kwance rai zaiyi halinsa

abu na biyu da nake so dakai shine a yanzu

haka

matar sarki hisham ta haifi da namiji kuma

har ta

gama wankan jego ta baro can birnin

darul hushush ta taho izuwa nan birnin

madinatul

haswar tare da jaririnta da kuma dakaru

dubu biyar masu tsaron

lafiyarta

wadanda suka kasance zakwakuran mayaka

fasa taro lallai ka shirya

wadansu zakwakuran dakarun da suka fisu

jarumtaka wadanda zasu je su yake su su

kashe matar

sarki ya zamana cewa baka da wata

barazana a mulkinka ina mai

tabbatar maka da cewa a daren da dan

uwanka sarki hisham

zai mutu ne shamilat da jaririnta

zasu iso cikin garin nan

don haka duk yadda zakuyi kusa a tare su a

can cikin daji

kafin su iso kusa da wuri, kuma kada ka

kuskura ka shiga

cikin mayakan da zasu je yin wannan aiki

kuma ka

tabbatar da cewar anyi wannan aiki a cikin

sirri

ba tare da wani ya sani ba lokacin da yarima

zamaru

yaji wannan batu sai hankalinsa ya kara

dugunzuma fiye da ko yaushe ma ya dubi

boka hizainu cikin alamun tsananin

tsoro da damuwa yace yakai wannan boka

mai daraja

yanzu a ina zan samo dakarun da zasu iya

kashe

dakarun da sarki sahibul hilayat masu yiwa

shamilat da

jaririnta rakiya izuwa nan birninmu? Ka sani

cewa dakarun birnin darul hushush mayaka

ne na asali kada su ba wasa bane

boka hizainu ya sake bushewa da dariya

lokaci guda

kuma ya turbune fuskarsa yace babu wanda

zai iya

yi maka wannan aiki face sarkin yakinka

amzadu ibn karlyas

koda jin haka sai yarima zamaru ya cika da

tsananin mamaki gami da tsoro yace

to yaya amzadu zai amince yayi min wannan

aiki alhalin kasan cewa ya kasance

babban aminin sarki hisham wanda a shirye

yake ya

sallama rayuwarsa domin kare ta sarki da

iyalansa

koda jin haka sai boka hizainu ya sake

bushewa da dariya

sannan yace

da zarar sarki hisham ya mutu kaine sarki

komai

ya dawo karkashin ikonka da mulkinka

a wannan lokaci kana da ikon sarrafa komai

da kowa da karfin karagarka

a daren da sarki

hisham ya mutu ka tura akamo sarkin yaki

amzadu da iyalansa a matsayin kana

zarginsa

da laifin sawa sarki wannan ciwon ajali

tunda kowa ya

san cewa dare da rana yana tare da sarkin

bayan an tsare su a kurkuku shida iyalan

nasa sai

kasa a fito dashi shi kadai azo dashi har

cikin

turakarka ka kadaita dashi a sannan ne zaka

gaya masa

bukatarka ta son ya

debi zakwakuran yaransa suyi

bada da kama suje su kashe matar sarki

shamilat da jaririnta

da duk dakarun da sukayi musu rakiya

izuwa nan birnin madinatul hashwar idan

kuma yaki koyayi wani abu ba dai dai ba

sabanin umarnin da ka bashi

zakasa a kashe iyalansa idan kuma yayi aikin

daidai

bisa nasara zaka bashi babban matsayi a

fadarka fiye

da wanda yake da shi a yanzu...

Suleiman Zidane Kd 

08161272634

KISAN GILLA

Littafi Na Daya (1)

Part B.

.

.

Marubucin Littafin

Abdul Aziz Sani M/Gini

Typing AA Misau

Ke Magana

.

Labari ya isowa AA Misau cewa...

Fiye da wanda yake dashi a yanzu.

lokacin da boka hizaunu yazo nan a

zancensa

sai yarima zamaru ya kamu da tsananin

farin ciki

nan take ya kama kyalkyala dariya saboda

murna sannan ya dubi boka huzainu yace

yakai wannan boka mai daraja hakika ka

cika makiru uban masharranta na duniya

Hm

babu makawa wannan dabara taka saita yi

nasara

shin yanzu ka tabbatar mini da cewa idan

na koma gari zan iske sarki ya kwanta cutar

ajali

koda jin wannan tambaya sai boka huzainu

yayi murmushi yace yau fa

shekara bakwai kenan ina shiri da jiran

zuwan wannan

rana saboda me ma zaka rinka shakku bisa

furucina ku koma

gida kuje ku sha barcinku a cikin wannan

dare lallai gobe da safe za a yi kiranka izuwa

fada kaga zahiri

nan take yarima zamaru da sarina matarsa

suka yi wa boka

hizaunu sallama suka fito daga cikin gidan

nasa suka hau dawakansu suka koma

cikin birnin madinatul hashwar ba tare da

wani ya shaida suba akan hanya

.hakika masu iya magana sunyi dai dai da

sukace

tsafi gaskiyar mai shi kuma maso abinka

yafika dabara

Kashe gari kuwa da sassafe aka tashi manzo

daga gidan sarki ya ruga izuwa gidan

yarima zamaru ya sanar

dashi cewar ya rugo izuwa gidan sarauta

ana nemansa yanzu yanzu

a majalisa koda jin wannan batu sai yarima

zamaru

ya dubi manzon cikin alamun tsananin

mamaki

da tsoro yace lafiya ake namana a fada

da sassafen nan haka

Manzon ya risina yace ai sarki ne ya kamu da

wani irin ciwo

farat daya ko mikewa zaune ma ya kasa,

koda jin

haka sai yarima zamaru ya dimauce ya ruga

da gudu izuwa cikin turakar matarsa

sarina

da shigarsa ya iske sarina a kwance tana

shirin tashi

kenan

nan take ya labarta mata labarin da manzo

yazo dashi

dajin haka sai sarina ta mike zumbur daga

kan gado ta daka tsalle ta rungume

zamaru

tana mai kyalkyala dariyar murna tana cewa

shi kenan

bukatar mu ta biya

nan dai zamaru yayi sauri ya kintsa sannan

ya

bi manzo suka wuce izuwa gidan sarauta

da isar su ya wuce kai tsaye izuwa cikin

turakar

sarki inda ya iske sarki hisham a kwance

bisa gado fuskarsa ta cika

da wadansu irin kuraje babu kyan gani

ga likitoci da manyan bokayan garin nan

sun taru a tsaitsaye a gefen gadon

a daya bangaren kuwa gaba dayan yan

majalisar

sarkine a zazzaune suma sunyi jigun jigun

cikin alamun tashin hankali

koda shigowar yarima zamaru sai sarki

hisham ya

dubi yan majalisarsa da dukkan likitocin sa

da bokayan

nasa har dama duk hadimansa

dake cikin turakar yace kowa ya fita ya

barsu yana son

ya gana da dan uwansa zamaru

a wannan lokaci sarkin yaki amzadu na

zaune daf da sarki ya rike hannayan

sarki yana ta zubar da hawaye kuma ya

kurawa

sarki hisham idanu kodajin umarnin da

sarki ya bayar sai

kowa ya fice daga cikin fadar amma shi

sarkin yaki amzadu saiya kasa mikewa

ya fita har saida sarki ya dubeshi ya budi

baki yace yakai babban masoyina ka

sani cewa a rayuwata ban taba boye maka

wani al amarina ba saboda

kauna da yardar dake tsakaninmu amma

yau kuma bana son ka san wani babban

sirri dake tsakaninmu da dan uwana

zamaru

saboda uwa daya uba daya ya wuce wasa

don haka ina son ka fita ka bamu wuri

koda jin wannan batu sai mamaki ya

turnuke sarkin

yaki amzadu domin irin haka bata taba

faruwa ba

tsakaninsa da sarki

cikin sanyin jiki ya mike tsaye yana waigen

sarki yana

zubda hawaye ya fice daga cikin turakar

kuma ya janyo musu kofa ya rufe

ta

faruwar hakan keda wuya sai sarki hisham

ya dubi yarima

zamaru ya yafito shi da hannu ya sake budar

baki da kyar

yace

matso nan kusa dani ya kai dan uwana

rabin jikina

cikin nuna alamun tsananin damuwa har

idanun

na zubar da hawaye zamaru ya je ya zauna

agefen

gadon sarki daf dashi suka kurawa juna

idanu

har izuwa tsawon yan dakiku

sannan sarki ya dubeshi yace

yakai dan uwana kayi sani cewa a daren jiya

na kamu da wannan cuta farat daya

kuma likitocina da bokayena sunyi iya bakin

kokarinsu akan

su gano abinda ya haddasa wannan cuta da

maganinta sun kasa, tabbas jikina

ya bani cewa

mutuwa zanyia cikin yan kwanaki kalilan

ka sani cewa bani da wani makusanci

wanda yafika sai kuma matata shamilat da

abinda ta haifa

tuni mahaifin shamilat sarki sahibul hilayat

na birnin darul hushash ya aiko da manzo

cewar shamilat da jaririnta data haifa sun

taho nan birnin bisa

rakiyar dakarunsa kuma zasu iso a daren

kwanaki bakwai masu

zuwa

koda sarki hisham yazo nan a zancensa sai

hawaye ya zubo masa yaci

gaba da cewa

a duniya bani da wani buri wanda yafi naga

dana na cikina

wanda ban same shi ba sai bayan na shafe

shekaru

goma sha daya dayin aure amma gashi

burina ba zai cika ba

domin ina ji

a jikina cewar kafin shamilat ta iso garinnan

ajali ya riskeni

Al amin Ahmed Misau, guyson nake magana

koda jin haka sai yarima zamaru ya

rungume

sarki hisham yana mai fashewa da kuka

yace yakai

dan uwana kayi sani cewa dukka mai rai

baya

fidda tsammani rabo kuma babu wata cuta

wadda bata

da magani a doron kasa don haka ni yanzu

ina so ka bani dama na

garzaya izuwa makotan kasashenmu na

nemo maka magani

koda jin wannnan batu sai sarki hisham ya

busheda

dariya cikin

Matukar karfin hali da juriya, al amarin da

yayi

matukar baiwa

yarima zamaru mamaki da tsoro kenan yaji

a ransa

kamar sarki ya gane cewa yana da masaniya

a kan

wannan ciwo da ya same shi, lokaci guda

kuma sai yaga sarki hisham ya fashe da

matsanancin

kuka na bakin ciki

da kyar zamaru ya rarrasheshi yayi shiriu

sannan ya dube shi yace yakai dan uwana

tunda na hau

kan karagar mulki ban taba kamuwa da

ciwon da ya kaini

ga kwanciya ba sai jiya fruwar hakan ce ta

tabbatar mini da cewar nesa ta

matso kusa ina so ka sani cewa ba wani abu

bane ya sa na sallami

kowa daga cikin dakin nan ba sai domin

muyi wani sirri

guda daya wannan sirri ba komai bane face

ina son na roke ka wata alfarma guda daya

ka sani cewa rayuwa ban taba tauye wani

hakki naka ba

a matsayinka na kanina kuma baka taba

neman wani abu a wajena ba wanda banyi

maka shi ba tun daga kuruciyarmu

kawo izuwa girmanmu a lokacin da

mahaifinmu ya ke raye da kuma ya mutu

koba haka bane?

Yarima zamaru ya gyada kai a lokacin da

hawaye na gaskiya ya zubo masa

domin take yaji tausayin sarki hisham ya

ratsa jikinsa

saboda sanin cewar gaskiyar ya fada sai

yace

hakika ka fadi iyakar gaskiya yakai dan

uwana

sarki hisham yayi dan guntun murmushi

sannan yace

ni kuwa ban taba neman wani abu ba a

wajanka kuma ka taba saka mini da kwara

zarra ba koda karfin jikinka

bisa duk irin abubuwan alherin da nayi

maka a rayyuwa

zamaru ya gyada kai yana mai nuna alamar

haka ne

sarki hisham yaja dogon numfashi sannan

yace alfarmar da nake nama a wajanka itace

idan har matata ta iso birnin nan a raye ita

da jaririnta

kada ka sa a kashesu ko a boyesu a wani

wuri bisa

tsoron nan gaba zasu iya rabaka da

mulkinka

idan har ba zaka iya zama tare dasu ba

kamar yadda na zauna tare dakai tsawon

shekaru talatin alhalin na san

cewa baka kaunata ka tsaneni kamar yadda

ka tsani mutuwarka

saboda karagar mulki

ina son ka tura su izuwa can kauyen limras

su karasa sauran rayuwarsu a can a

matsayin talakawan gari

kawai koda ba zaka taimaka musu da komai

ba

na san wacece matata shamilat macece mai

zuciyar maza ko

babu aure zata iya rike kanta kuma tare da

abinda ta haifa

Guyson Sunana

Koda sarki hisham yazo nan a zancensa sai

hawaye ya sake zubo masa a lokacin da ya

kurawa

yarima zamaru idanu

nan take yarima zamaru yaji ya kamu da

tsananin kunyar sarki hisham gami da

matukar tausayinsa har shima hawaye ya

sake zubo masa

kawai sai yarima zamaru ya mike tsaye ya

juyawa sarki hisham baya yace nayi alkawar

idan har matarka da abinda

ta haifa sun shigo cikin garinan a raye lallai

zan zamo mai rike su da amana kamar

yadda ka

rikeni har izuwa sa adda mutuwa zata

rabani dasu

koda

gama fadin hakan sai yarima zamaru ya fice

daga cikin turakar yana kuka da fitowarsa

yana kuka yayi arba da sarkin yaki amzadu

a tsaye shi kadai a kofar dakin nan fa sukayi

wani irin kallo kallo na rashin yarda kawai

sai

yarima zamaru ya yiwa amzadu dan guntun

murmushi yyi tafiyarsa shi kuma sai ya bude

kofar turakar

da sauri a dimauce ya shiga ciki

da shigarsa yayi arba da sarki

a kwance kamar yadda ya fita ya barshi

dazu

cikin hanzari sarkin yaki amzadu yaje ya

sake zama daf da sarki ya dubeshi a

firgice yace

ya shugabana me ya faru tsakaninka da dan

uwanka na ga shima ya

fita yana kuka

koda jin wannan tambaya sai sarki hisham

yayi dan guntum murmushi cikin

matukar karfin hali sannan yace Alhini ne na

rabuwa

da juna ya sakaga duk muna kuka

domin mutuwa zata shammace

mu a lokacin da bamu taba zato ba tafi na

sallame ka

wasiyata ta karshe a gareka ita ce ka tuna

da duk

irin abubuwan alherin da nayi maka a

rayuwa

a duk sa adda wata masifa ta taso kada ka

kasance mai

yin butulci a bayana

sa adda sarkin yaki amzad yaji wannan batu

daga bakin sarki sai ya kamu

da tsananin

mamaki kuma ya kasa fahimtar abinda yake

nufi har ya budi baki da nufin ya sake

tambayarsa sai ya kasa

nan dai ya juya ya fice daga cikin turakar

cikin tsananin

damuwa da tashin hankali wanda bai taba

tsintar

kansa ba

.

Daga wannan rana sarki hisham ya ci gaba

da ciwo wanda

ba sauki kuma babu alamar za a sami saukin

har saida ta kai cewa ko motsi da baki baya

iya yi

abinci ma da ruwa idan aka dura masa baya

shiga cikinsa

a ranar kwana na bakwai ne ciwon ya

tsananta

ainun

hankalin kowa ya dugunzuma a tsawon

kwanaki bakwan da sarki hisham ke

kwance

cikin jinya yarima zamaru bai sake zuwa ya

duba shiba

amma sarkin yaki Amzad kuwa dare da rana

yana tare dashi

a ranar kwana na bakwan da magariba rai

yayi

halinsa nan fa labari ya bazu a ko ina cikin

kasar mutane

suka kama koke koke sai a wannan

lokacinne aka

ga yarima zamaru ya shigo cikin fadar a

lokacin da aka fara shirye shiryen binne

sarki ana ganin yarima zamaru hankalin

kowa ya tashi

domin an san cewa dolene yanzu komai ya

sauya a birnin duk irin adalcin da ake yiwa

talakawa

an daina kuma za a matsa musu a kan biyan

haraji mai yawa za a rinka zaluntarsu

babu sauran masu jin dadi da kwanciyar

hankali

face sarakai da attajirai wadanda zasuyi

biyayya ga sabon sarki Yarima zamaru

nine dai Al amin Ahmed misau

Guyson nake

Bayan an gama jana izar sarki hisham an

binne shi a cikin dakin da aka binne

sarakuna arba in da uku na

kasar sai yarima zamaru ya tara gaba dayan

yan

majalisar kasa a dakin taro ya tabbatarmusu

da cewa

gobene za ayi bikin nadin sarautarsa

sannan kuma ya umarci sarkin yaki da ya

tabbatar da tsaro a ko ina

a cikin birni da kewaye kuma ya sanar da

dakarun dake tsaron

kofofin gari cewa ba shiga kuma ba fita

daga yanzu har izuwa gobe sa adda za a

kammala bikin nadin

sarautar tasa

koda jin wannan umarni sai kowa ya cika da

tsananin mamaki

amma sai gaba daya yan majalisar sukayi

shiru suna masu sunkuyar da kansu kasa

saboda

tsoron yarima zamaru aka rasa wanda zaice

kala sai sarkin yaki amzadu

ne ya dubeshi yace yakai sarkin gobe kayi

sani

cewa wannan hukunci da ka yanke baiyi dai

dai ba domin tsarin mulki bai yarda da

hakan ba saboda bai dace ba ka

hana mutane zuwa cikin gari nan ba koda

ka hanasu

fita a wannan lokaci da ake ciki na babban

rashin da akayi na dan uwanka

ka sani cewa mutane da yawa zasu zo ne

domin

su ziyarci kabarin sarki su nemi tabarrakinsa

kuma suyi masa addu a wasu kuma zasu

kawo ziyara ne izuwa

kallon bikin nadin sarautarka,

sarakuna da yawa daga makwabtan

kasashe ma zasu zo wannan gagarumin biki

kafin sarkin yaki amzad ya gama rufe

bakinsa tuni yarima zamaru ya tari

numfashinsa

yana mai daaka masa tsawa yace wanene

kai harda zaka gaya mini abinda zanyi

ka sani cewa in banda kana da matukar

muhimmanci

da amfani da yanzu take zan sauke ka daga

kan mukaminka

na sallameku kowa ya kama gabansa nan

take kowa

ya kama gabansa jikinsa a sanyaye ya fice

daga cikin dakin taron

aka bar yarima zamaru a zaune shi kadai

Al amin Guyson, lokacin da sarkin yaki

amzad ya isa

kofar gidansa sai ya hango kofar gidan

wayam babu dakarun

da suke yi masa gadi kuma kofar gidan a

bude take wanwar al amarin da yayi

matukar razana shi kenan yayi wuf ya sauko

daga kan dokinsa yana mai zare takobinsa

kawai sai ya ruga da

gudu izuwa cikin

gidan yana mai kiran sunan matarsa

da danta himar wanda ya kasance yaro dan

shekara

hudu amma shiru baiji sun amsa ba kuma

baiji duriyarsu ba

,,,

Al amin Guyson Kenan

Anan Zan dakata

amma Kafinnan

Nidinne dai

AL AMIN AHMED MISAU

guyson inkiya

Admin Na zauran Labarai

08161272634

KISAN GILLA

Littafi Na Daya (1)

Part C.

.

.

Marubucin Littafin

Abdul Aziz Sani M/Gini

Typing AA Misau

Ke Magana

.

Labari ya isowa AA Misau cewa...

Yana isa falo yayi turus saboda

tsananin kaduwa

da mamaki bisa abinda yayi arba

dashi ba wani abu ya gani ba face

yarima zamaru zaune akan

kujera cikin shigar yaki ya harde

kafafu daya kan daya yana kallonsa

cikin murmushi abuna farko da ya

daure masa kai shine

yaya akayi zamaru ya riga shi zuwa

nan alhalin a can gidan sarauta

ya barshi kuma yaushe ma ya canja

kayansa har yazo nan din kawai sai

amzad ya baiwa kansa amsa

yace tabbas wannan al amari ne na

tsafi cikin alamun

fushi sarkin yaki ya dubi yarima

zamaru yace ina iyalina

tuni

jikina ya bani cewar wani abu

makamancin wannan sai ya

faru kuma yanzune na tabbatar da

cewar kana da hannu

a kan ciwon da sarki ya samu

wanda ya zama sanadiyar

ajalinsa

lokacin da yarima zamaru yaji

wannan batu sai ya bushe da

mahaukaciyar dariya

lokaci guda kuma ya turbune fuska

yace ina son mutum mai

kaifin kwakwalw

da hasashe irinka

tabbas duk abinda ka fada haka

yake gaskiya ne nine na

kashe sarki domin na sami wannan

karagar mulki

wacce ta gagareni tsawon shekaru

ban zo nan domin muyi doguwar

magana nazo ne domin na sanar

dakai

cewar iyalinka suna hannunmu

kuma mun boye su a inda babu

wanda ya isa

ya gansu ko ya dauko su face mu

da kanmu ina son

yanzu take ka debi dakaru dubu

dari shida a cikin shigar badda

kamanni ku nufi

jeji na bayan gari ku tari gimbia

shaliat tare da dakarun mahaifinta

wadanda sukayi mata rakiya izuwa

nan birnin

ina son duk yadda za ayi ka kashe

su gaba dayansu

ban son mutum daya ya tsira

da jaririn da ta haifa ku tabbatar da

cewa kun kashe shi idan kuka yi

wannan aiki

dai dai zan dawo maka da iyalinka

gobe da safe idan kuma ka ki bin

umarnina gawar iyalanka zamu

kawo maka

idan kunne yaji gamgar jiki ya tsira

kuma shawara ta rage ga mai shiga

rijiya

Koda gama fadin hakan sai yarima

zamaru yayi

girgiza ya bace bata daga cikin

dakin yana mai

kyalkyala dariya tamkar bai taba

wanzuwa ba a ajan

Al amin Guyson nake

nan fa sarkin yaki amzad ya

dimauce

kuma ya fusata ainun bai san sa

adda ya kurma uban ihu ba kuma

ya fashe da matsanancin kuka

saboda tsananin bakin ciki da

takaici daga can sai ya juyada sauri

a guje ya koma

kofar gida ya kama dokinsa ya hau

ya zabureshi da gudun tsiya

A can daji kuwa Gimbia shamilat na

zaune a cikin keken

doki

rungume da jaririnta dakaru sun

kewayeta gaba da baya

dama da hagu ana tafiya saboda

kwarjinin wadannan dakaru da irin

kayan yakin da suke dauke dasu

babu abinda zai gansu bai yi

shakkarsu

ba , da yake duhu yayi gaba dayan

dakarun sun kunna fitilun itace don

haka hanya sai tayi haske

sai sauri ake

tayi saboda an san cewa saura baifi

tafiyar rabin sa a ba

a iso cikin birnin madinatul

hashwar

a wannan lokacinne shamilat na

cikin tsananin farin ciki

sai yawan kallon

jaririnta take yi tana murmushi

saboda tunanin cewa a yau ne sarki

hisham zai ga dan cikinsa da idonsa

abinda ya shafe shekara da shekaru

yana burin gani

bai gani ba

saboda zakuwar da tayi taga an isa

cikin garin har umarni take

bayarwa a kan a karawa dawakai

kaimi

nan fa aka ci gaba da gudu kai kace

hari za a kai

kaico rashin sani yafi dare duhu

ashe

wadannan zuga ba su san cewa

mahallaka suke kai kansu ba

lokacin da tawagar

gimbiya shamilat suka iso

dai dai wani fili mai fadi wanda

tsakaninsa da karshen dajin bai

wuce zira i arba in ba

sai kawai sukaji ana yi musu ruwan

kibiyoyi ta gabas da yamma kudu

da arewa wayyo Ajali idan yayi kira

sai an amsa

babu makawa

Nan fa dakarun da dawakai suka

rinka ihu da haniniya suna zubewa

kasa matattu kafin su ankara an

kashe kaso daya a cikin kaso uku

ita kanta gimbiya shamilat taga

matukar tashin hankali domin ta

gefen idanunta da kunnuwanta

kibiyoyi

suka rinka giftawa da kyar aka

sami wasu zakwakuran mayaka

suka rinka kade kibiyoyin

da ake harbo mata da takubbansu

A sannan ne kuma dakarun suka yi

wata dabara

wadanda keda

garkuwoyi sai suka yi kawanya a

tsakiya suka kare sama da kasansu

aka sanya gimbiya shamilat da

sauran dakarun a tsakiyar da irar

duk da haka sai aka ci gaba da

harbo kibiyoyin

har zuwa tsawon lokaci

a wannan lokaci jaririn shamilat na

ta faman kuka itama gimbiya tana

kukan sai da aka saina harbo

kibiyoyin

sannan shugaban dakarun ya dubi

gimbiya shamilat yace

ranki ya dade yanzu me ye abinyi

ba muga wadanda suka kawo mna

wannan hari ba

har yanzu domin sun boye ne a

cikin duhuwar bishiyoyi

shin zamu ci gaba da tunkarar

birnin madinatul hashwar ne

wanda tazararmu da shi a yanzu

bata wuce zira i arba in ba ko

zamuyi kokarin komawa da baya

ne

domin mu tserar da rayuwarki data

wannan yaron naki

sa adda shugaban dakarun yazo

nan a zancensa sai hawaye ya

zubowa gimbiya a lokacin da

zuciyarta ta buga da karfi

kuma tsoro ya shigeta kawai sai ta

dubi shugaban

dakarun ta ce sarki Hisham ya fadi ''

cikin kaduwa shugaban dakarun ya

cubeta yace

ranki ya dade ya akayi kika sani?

Shamilat ta fara zubar da hawaye

ta ce inda

mijina yana raye babu yadda za ayi

a taremu a kan iyakarsa

domin a hallakamu

abu ne mai hadarin gaske muci

gaba da tunkarar

cikin birninnan yanzu kawai muyi

Kokarin komawa da baya in munyi

sa a mu tsira da ranmu

kafin gimbiya ta gama rufe bakinta

sai kawai

sukaji sukuwar dawakai an

durfafosu kafinsuyi wani

yunkuri dakarun masu yawan

gaske ninkinsu uku sunyi musu

kawanay

gimbiya shamilat ta fito daaga cikin

keken dokinta a fusace

rike da jaririnta domin taga ko

suwaye ne wadannan dakaru da

suka kawo musu hari

kawai sai taga ashe dakarun sunyi

shiga ne irin ta

bakaken kaya ba shigar kayan

yakin dakarun birnin madinatul

hashwar ba kuma duk

sun rufe fuskokinsu da bakin kyalle

idanunsu kadai ake gani

a dai dai wannan lokaci ne

shugabam dakarun gimbiya ya

rugo gareta ya dubeta

cikin alamun tsananin tsoro da

damuwa yace

haba ya shugabata yaya zaki fito

fili haka gaban wadannan makiya

alhalin muna kare rayuwarki da ta

jaririnki

shamilat tayi ajiyar zuciya tace ai

zancen kare ni da

jaririna ya kare ka dubi wadannan

dakaru ka gani ai sarkin yawa yafi

sarkin karfi kuma ba zamu iya guje

musu ba

duk mutuwa zamuyi ni kawai

yanzu ina son na san wanda ya

turo a kasheni kafin na mutu

Al amin Guyson Sunana

don bana son na mutu cikin wasu

wasi

koda gama fadin hakan sai gimbiya

shamilta ta dubi wadannan dakaru

masu bakaken tufafi

ta daka musu tsawa tace ku su

waye kuma waye ya turoku ku

kasheni

mtar sarkin birnin madinatul

hashwas

dajin wannan tambaya sai bakaken

dakarun suka dare

shugabansu ya ratso ta tsakiyarsu

ya matso kusa da ita ya tsaya

duk da cewar fuskarsa a rufe take

idanunsa kadai ake gani saida

gimbiya shamilat ta shaida ko

wanene shi nan take hawaye ya

zubo daga cikin idanunta

ta dubeshi tace yakai Amzad yanzu

dakai za a hada baki aci amanar

mijina

Yanzu ashe dama zaka iya yiwa

sarki butulci aashe zaka iya

mancewa da duk

irin halaccin da yayi maka a rayuwa

sa adda shamilat tazo nan a

zancenta sai sarkin

yaki Amzad ya kwaye fuskarsa sai

ga hawaye na zuba masa a lokacin

da suka kurawa juna idanu shi da

ita

tsawon yan dakiku dayansu baice

uffan ba sannan Amzad yace ki

gafarceni ni ya shugabata idan ban

bi umarni ba nima zan rasa matata

da dana

Koda jin haka sai shamilat ta fashe

da kuka tace

haka ne rai baifi raiba amma kafin

ku kashe mu

ina son ku fada mun iyakar

gaskiyar menene ya faru ga mijina

dajin wannan tambaya sai hawaye

ya sake zubowa sarkin yaki amzad

ya ce mijinki ya mutu

koda jin haka sai jiri ya debi

shamilat ta yanke jiki zata fadi kasa

cikin zafin nama amzad ya daka

tsalle ya dira a gabanta ya tallafeta

tare da jaririnta yana mai baiwa

dakarunsa umarnin su hallaka

dakarun gimbia

kaico Ajali ba a sa ma rana nan da

nan dakarun amzad suka kama

ragargazar dakarun shamilat

wuri ya hargitse banda ihun

mazaje babu abinda mutum ke ji

duk da cewar sarkin yawa yafi

sarkin karfi sai da aka jima ana

gumurzu a karshe dai ragas aka yi

aka karar da gaba dayan daakarun

kowanne bangare ya zamana cewa

babu daya da ya rage a raye face

sarkin yaki Amzad a dai dai

wannan lokaci ne gimbia ta farfado

daga dogon suman da tayi

idanunta suka bude tana mai gani

dishi dishi idanunta na washewa

tayi arba

da sarkin yaki amzad a zaune daf

da ita rungume da jaririnta

gaba dayan dakarun dake wajan na

kwance a kasa sun zama gawa

shamilat ta mike tsaye zumbur ta

rugo iduwa wajan amzad ta miko

hannayanta

da nufin ta karbe jaririnta amma sai

ya tokare da kotar takobinsa a

kirjinta yace ya shugabata

kiyi sani cewa yarima zamaru ya

umarceni da na kashe ku keda

jaririnki in ba haka ba kuwa sai ya

kashe matata da dana ba zan iya

kashe ku ba

domin idan nayi haka naci amana

Koda yazo nan a zancensa sai ya

durkusa bisa gwiyoyinsa agaban

shamilat a lokacin da idanunsa

suka

ciko da kwalla yace ina rokonki

daki bar garin nan kuma karki

koma birnin darul hashbush ki

sanar da mahaifinki abinda ya faru

domin kina gaya masa zaice zai

yaki sarki zamaru kuma kin

sani cewa mayakan mu sun ninka

nasa sau goma a yawa da karfin

makamai

cikin tsananin bakin ciki shamilat ta

fashe da kuka

kamar ba zata daina ba daga can

saita dago kai idanunta sunyi

sharkaf da hawaye tace shi kenan

ka bani dana nayi alkawarin

zan tafi izuwa wata nahiyar daban

na reni dana a can har

abada ba zan dawo nan ba kuma

ba zan taba gayawa dana

matsayinsa ba

koda jin wannan batu sai hawaye

ya zubowa sarkin yaki amzad ya

dubeta yace

ba zan iya baki yarima ki tafi dashi

ba

cikin razana shamilat tace yanzu

kana nufin zaka rabani

da dana kenan wanda shi kadai ne

abinda ya rage mini a duniya

amzad yace

kawar kuwa domin barinsa

awajanki ba karamin hadari bane

nayi miki

akkawari zan reni wannan yaro a

cikin birnin madinatul

hashwar

kusa da karagar mulkinsa ba tare

da ya san ko shi wanene ba

kuma komai dare dadewa in dai

kina raye yana raye nima ina raye

saina sadaku

zan tsare lafiyarsa da ransa kamar

yadda na tsare na mahaifinsa

wannan shine kadai

gatan da zamu iya yiwa kanmu da

wannan jariri

naki idan har muna son mu tsira da

rayukanmu

sa adda sarkin yaki amzad yazo

nan a zancensa sai shamilat ta sake

fashewa da kuka daga can sai ta

matso daf da amzad ta shafa kan

jaririn ta sumbaci goshinsa sannan

kuma ta ciro wata laya dake

wuyanta ta

Daurata a wuyan jaririn ta dubi

amzad tace

ina da laya irin wannan sak don

haka ka gayawa dana

cewar duk ranar da yaga mai irin

wannan laya ba wata ba

ce face mahaifiyarsa

koda gama fadin hakan sai ta karbi

jaririnta ta rungumeshi

a kirjinta ta sake fashewa da kuka

al amarin da ya karyar da zuciyar

sarkin yaki kenan ya ji ya kamu da

tausayinta fiye da ko yaushe

sai da ta jima a kankame da jaririn

sannan sarkin

yaki ya karbeshi ta tafi izuwa inda

keken dokinta yake tana waigen

jaririn nata

tana zubar da hawaye

Wow nIma Al amin Guyson na

tayata haka dai taje ta zauna a kan

keken dokin

ta sakarwa dawakan linzami suka

zabura da gudu suka nausa da ita

cikin

daji suka nufi wani bangare daban

wanda bai shafi nahiyar ba gaba

daya

a sannan ne shima sarkin yaki

Amzad ya tafi da jaririn izuwa inda

dokinsa yake ya kama ya hau ya

nufi

hanyar da zata kai shi cikin

madinatul hashwar

a lokacin da yake bacewa a cikin

duhun daren

tun kafin sarkin yaki ya iso kofar

shiga gari ya boye jaririn a bayansa

tamkar baya dauke da komai kawai

ya wuce gaba masu gadin kofar

garin

ba tare da jaririn yayi kuka ba

ai kuwa yana isowa bakin kofar sai

masu gadin suka tare shi saboda

basu gane shiba

sakamakon yana sanye ne da

bakaken kaya kuma basu ga sa

adda ya fice daga cikin garin ba

tare da dubun nan daakarunsa

saboda ta wata barauniyar hanya

suka fice

masu gadin na tare shi sai yayi

sauri ya bude

fuskarsa don kada su bata masa

lokaci koda suka dallare fuskarsa da

madubi

sukaga shine sai suka yi sauri suka

bude masa kofa ya shigo suna

masu binsa da kallo cikin alamun

tsananin mamaki domin su dai

basu ga lokacin da ya fita daga

cikin garin ba kuma tunda suka

ganshi a cikin shiga ta

bakaken kaya lallai sun san cewa

wani aiki ne na sirri yaje ya gabatar

amzad na shiga cikin gari bai zame

ko ina ba sai gindin wata karuwa

wacce ake kira kimaratu

a wannan lokaci dare ya fara

nisawa kuma sawu ya dauke ba a

jin sautin komai face haushin

karnuka amzad ya kama buga

kofar gidan da karfi

a fusace kimaratu tazo ta bude

kofar tace wanene nan yake neman

fasa mini kofar gida ka kama

gabanka

ina da abokin kwana a ciki

koda jin haka sai amzad ya daka

mata tsawa yace bude kofar na

shigo nine

sarkin Yaki Amzad

jikin kimaratu na karkarwa tayi

sauri ta bude kofar nan take amzad

ya mika mata

jaririn sannan ya danka mata jakar

kudi

cike da dinare yace wannan kudine

dinare dubu dari uku ki rike su ki

reni wannan jariri har izuwa

lokacin da na bukaceshi

idan wani abu ya tafa lafiyarsa a

bakacin ranki

.

SHIN SARKI ZAMARU ZAI CIKA

ALKAWARIN DAKE TSAKANINSA DA

BOKA HIZAINU.??

.

YAUSHENE SHAMILAT ZATA SAKE

GANIN DANTA???

.

ME ZAI FARU IDAN DAN SHAMILAT YA

GIRMA ???

.

MU HADU A LITTAFI NA BIYU

DON JIN CI GABAN WANNAN LABARI

DAGA MARUBUCIN LITTAFIN

ABDUL AZIZ SANI MADAKIN GINI

KANO

WANDA NI AL AMIN AHMED MISAU

INKIYA GUYSON

NAYI TYPINGDINSHI

NAKE CEWA SAI MUN HADU A NA

BIYUN

Whatsapp 08161272634

0 Response to "KISAN GILLA Hausa Novel"

Post a Comment