-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Adalilin Link Hausa Novel

Adalilin Link Hausa Novel

 [02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK 😭

  


  WRITTEN BY 

UMMEEN YUSRAH 


     EDITOR: QUEEN MEEMI 

     

     

DUKKAN YABO DA GODIYA SUNTABBATA GA ALLAH MAD'AUKAKIN SARKI ,TSIRA DA AMINCI SU TABBATA GA FIYAYYEN HALITTA ANNABI MUHAMMAD (S. A. W). 


BISMILLAHIRRAHMANIRRAM 


Wannan Labarin k'irkirarshi nayi, don nunama 'yan'uwa illar dake cikin wasu *Link*

Allah ya karemu da Imaninmu. 




page 1


*******

Kwance take kan Gado hannunta d'auke da waya da alama tanajin dad'in hirar da suke a wani group mai Suna( MATAN AURE GROUP ) wata ke kwararomusu bayanin wani Maganin mata datasha yadda Oga ya gama Rikicewa jiya akata.


Inda 'yan group kowa ke tofa Albarkaci bakinta. Hafsat dake kwance tanajin Dad'in hirar tasu don ita  A duniya indai zataji irin wannan zancen zata iya bata Lokacinta, don yadda zata samu k'warin Gwiwar gara oga wajen harka. 


Sallama akayi tareda shigowa dakin da Gudu yaranta suka haura Gadon. Babban maisuna

Ahmad(sabeer) yace "Umma mun dawo",k'aramar maisuna Asma'u (sabeerah) tace "Umma yunwa nakeji."


 Abbansu na tsaye k'ofa bai Idda shigowa ba. yazubo Mata ido yana kallonta, don yasan bata d'aura Girkiba. Saukowa tayi tace "barin had'a muku tea, kafin na gama abincin."

 

Sai sannan yayi Magana Ranshi a b'ace "habba Hafsat ace kullum sai yara sundawo sannan kice zaki d'aura abinci! wannan wani irin Rayuwace? idan zasu tafi ba wani karyawar kirki sukeba, sannan sundawo ba abinci, kin d'auki dukkan Lokacinki kinbama Waya, wannan wani irin Rayuwace? fisabilillah! bakida Lokacin Gyaran Gidanki, bakida Lokacin yaranki, ace  Kullum kina kan waya. Gaskiya ki gyara nafara gajiya."


Wani kallon Raini tamai tace "uhmmmm saikayi kuma dad'in abin bakai kasaimin wayarba, balle kamin Gori."

Ta Murgud'a mai Baki tayi ficewarta, tabarshi wajen, Shigewa yayi ya cirema yaran kayan Makaranta ,sannan ya masu wanka ya shiryasu  ya sake fita dasu.


Tana zauna a Pallor ya wuce ta. Gidansu yakai yaran bayan sungaida Ummanshi yq kira k'anwarshi Rahma taba yarn Abinci.

Umma tace "ina ummar tasu?"

 "Tana Gida batajin dad'ine."

 "Ayyah Allah ya  bata lafiya Ameen."

 "Ummah nizan wuce sai yamma zanzo in d'aukesu."

  "Toh Allah yabada sa'a."

  

***

Bayan fitarsu saida tagama hirarta kafin ta tattara wanke-wanke  ta gyara Gidan.Asannan k'arfe Uku tayi gashi ko sallar azahar bataiba saidata d'aura Girki kafinnan ta jetai sallar azahar da La'asar Alokaci d'aya.

 Bayan ta gama Girki ta yiwanka kwalliya sosai tayi wanda tasan zai Janyo hankali Abban Sabeer, bayan tagama Girki ta zuba cikin Cooler, ta dib'i nata taci ta koma Sana'arta ta. 


Bashi yadawo da Yaranba sai wajen 8:00MP 

Yana shigowa yayi Arbada ita zaune a Pallor da Shigarta mai tada Hankali. Da Sallama Yashiga ta Amsa kallo D'aya yayi mata ya kauda kai don yasan wannan Shigar da Viyu ne. Amsa Sallamar tayi sannan tamai sannu da zuwa ya Amsa chan k'asan Mak'oshi.


Tunda taji haka tasan Mutumin ya shaka Gashi yau so take su mori juna. Karb'ar Sabeerah tayi takaita D'aki, sannan ta dawo ta kawo mai Abinci kad'an yaci ya tashi ya kama Sabeer ya nufi D'akinshi .Tana zaune taji yama k'ofar Key. Ai take tayi Mutuwar zaune. 



   Kubiyomu don jin yadda zata kasance


   ✍🏻✍🏻UMMEEN YUSRAH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK 😭




WRITTEN BY:

      UMMN YSRH 


        EDITOR BY:QUEEN MEEMI 



GODIYA MAI TARIN YAWA GAREKU 


AUNTY RUMA 

HAMEBRAH 

MOM SULTAN (UWAR ALKHAIRI) 

JAMEELAH K MASHI

AMIESTY

ANTY FARY NOVEL GROUP 

MERMUE NOVEL GROUP 

LABARINA GROUP 

SIST FAREEDAH MUSA

 DA DUKKAN MASOYA WANNAN NOVEL 

INA MIKO GODIYA 👏🏻


         6⃣TO 10 🔟



          12:30MP 


Haseeb ya d'aukosu daga Makarant yauma gida ya wuce dasu dake basuda nisa da School din, Sannan ya koma wajen Aikin shi. 


Hafsace zaune a falo tana Sana'arta ta yau Anyi sa'a tagama komai Amma har yanzun wajen 1:30MP bai dawo da yaranba Tunda taga haka tasan ya wuce dasu Gidan kakarsu, ita kad'ai ke magana tace "uhmmmm shi yasani kuma nikam hutuna." 


     Gidan Bilki

     

Abbansu Salmane ya shigo d'auke da kayan Abinci daya sayo musu.

Saidai abun haushi Matar tashi bata gida sai yaran ta bari da gadin Gida.

Salma ina Mamanku ta fita ? "Abbah tun yaushe! Tajima da fita tace zata shiga Gidan Maman Nana wai an kawo kaya har yanzun bata dawoba.

"kunci Abincine?"


"Aah zabbah kad'a kai yayi tsabar takaici 

"wai yaushe Bilki zata daina wannan shegen yawon natane? kullum akazo Gidan batanan Sai dai tabar yara k'anana da Gadin Gida ta tafi bin Gidan Mak'ota, Allah ya shiryeta.ke jeki ce tazo" 


 "Tam Abbah" 


Saidata zaga kusan Gidaje Biyar kafin ta samota tasamu sai kwasar Girki take tama mantada tabar yara a Gida. 


"Umma kizo Abbanmu ya dawo"

 

Ai take d'unbun tsakin datakai Lomarshi bakinta ya shak'eta ta zaro Ido "Abbanku ya dawo?'

 

"Eh yace inkira woki"


 "Toh Muje sallama tama Mutan Gidan tasa kai da yar kwanon danbun ta. Gidan kusa dasu ta shiga tace subata abu zata d'ebi Garwashin wuta, Bayan ta d'iba tashige Gid da sallamarta tama Abban yaran barka da zuwa. 

Sannan ta kama kame2 "Ai Nashiga dibar Gaushi nasami Matar Mak(ocinmu tana kan Gwiwa shine muka taimaka mata har yanzu bata saukaba". 



Binta kawai yayi da ido yatashi yayi Gaba. Don yarasa kalmar dazai mata magan tunda kullum cikinta yake fatanshi Allah yaye mata wannan yawon nata. 



*ABUBAKAR TAFAWA BALEWA TEACHIN HOSPITAL BAUCHI *


DR.Haseeb ne shida Babban Abokinshi Dr. Khamees suna tattaunawa akan Aikinsu, su

Aminai ne sosai.

$

Dr haseeb Mutumne mai k'wazo wajen Aikinshi k'wararren Lokitan Matane. Mutumne Maisaukin kai da son Mutane, Sai dai sam baiyi sa'ar Abokiyar zamaba. 


Bayan tashinsu daga asibiti 4:00MP Gidan Dr Khamees suka wuce can yaci Abinci yayi sallar Magrib da Isha'i kafin ya wuce Gidansu d'aukar su Sabeer. 


Bayan sun gaisa da Umman tashi tace 'ya mai jikin dazu ka sauke Yaran baka shigoba"

 "Da sauki Ummah na kawosune don karsu koma sudameta da Hayaniya".

 

  "Eyyah Allah kara sauki gobe insha Allah zanje indubata yace ai dakinyi zamanki gobe ma gida zan wuce dasu tunda jikin nata da sauki sosai."

   

"Toh ai shikenan idan ka koma ina gaisheta"

 "Tih Umma mun wuce saida safe."CITY STORE ya tsaya yasai musu ice cream  da abunda zasuyi B Break sannan suka wuce Gida


Falon shuru ba kowa D'akinshi suka wuce yaba Sabeera wani Ledar takaima Ummanta saida sanda taje ta tura kofar tajita Rufe ta buga k'ofar taji shuru ta dawo ta sanarma Abbanta karb'ar Ledar yayi ya ajiye ya shiga bayi ya hada musu ruwan wanka ya musu sannan yayi nashi yazo ya kwanta. 


Gimbiya Hafsat tana d'aki tagama cika tayi fam saura kiris ta fashe ta gaji da jiran dawowarsu shine ta kule daki ta rufe tanajin dawowarsu taki budewa. 


    6:00am 

Bayan dawowarshi daga Massallaci ya tashi Yaran yamusu wanka sannan sukai Alwala sukai sallah sukayi Break yashiryasu sukad'au Hanyar School.

 

Yauma kamar kullum a Makare ta tashi tayi Sallah ta ta had'a abun kaiwa dai2 Bakinta don tasan sun riga suntafi School.


Abinci data ajiyemusu haka tazo tasamu ta dada kulewa da haushi, komawa tayi tai Break sannan tashiga Sana'artata wato Chattin ba Gyaran Gida ba wanke2 ba Gyaran Jiki ba komai ita damuwarta waya kawai. 



         HOSPITAL


Dr. Haseeb ne zaune da Abokinshi suna hira yake bashi Labrn halin da suke ciki da hafsat. 

 

"Habba Dr Amma bai kamata ka biye mata ba  kama tta yayi kacigaba da Hakuri da kuma mata nasiha wala Allah kozata nutsu yanzun kai kahau itama ta hau hakanfa kabata damar tacigaba da abunda takeyi kenan! Gaskiya ka sake tunani karfa ka manta Mace k'aramin k'wak'walwa gareta sai Anyi ana tarota (kuyi hak'r yan'uwa mata) sabida fadawa wata hanyar."

 

Sai sannan Dr Haseeb ya gane kurenshi na fushin da yake Tabbas Maganar Dr. Khamees Gaskiya ne don yaga kamar kara bata dama yayi, akan taci gaba da abun da take yi, yayi niyyar in Allah ya yadda ya koma Gida zasuyi magana. 

   


✍🏻UMMIN YUSRAH.

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . . 😭ADALILIN LINK😭



    WRITTEN BY:

           UMMN YSRH 


     EDITOR BY:QUEEN MEEMI 




INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U

Waishin wannan rayuwar wacce irice bakomai zuciyar dan adam sai cin zali dason ganin bayan al'umma domin biyan bukatunshi da neman duniya, lallai mutum mugun iccene, mugu baida kama, makashinka na gidinka. UMMU ABIHA Allah miki RAHMAN ALLAH GAFARTAMIKI zunubanki Allah Albarkaci rayuwar abunda kika bari. Kukuma gaku ga duniyar ku tabbata cikinta Karku barta😭


             1⃣1⃣TO 1⃣3⃣


Yau gida ya wuce dasu bayan ya d'aukosu daga Makarant, a kofar Gate ya saukesu ya juya wajen Aikin shi. 




         8:00MP 

Haseeb ne yashigo Gida falo yasameta zaune tamai sannu dawawo ta karbi kayan hannunshi ta kaimar daki sannan ta dawo tace ga abincifa akawo mane.

Saidai mamakinta yake amma kuma yasan indai tana bukatar wani abun gareshi Ladabinta dabanne. 


Abinci ta zubamai yaci sannan ta hadamai ruwan wanka, bayan fitowarshi yake tambayarta ina yaran sunyi bacci tun dazu. Dakinta ta wuce


Bayan yagama shirin kwanciya lokacin yana shirin zuwa dakinta domin Tattaunawa kan Matsalarsu sai gata tashigo da shirin Bacci

Ina shirin zuwa sai gaki Dariya tai tace "Eh nazo tayaka kwanane" yace "kin kyauta dama inaso Magana dake." 

"Toh Allah yasa lafiya!?

"Lafiya lau. 

Kizauna mana". 

 Bayan sun zana yafara mata Magana. "Gaskiya Hafsat baikamata ace kindauki dukkan lokacin kin ba wayaba bakida lokacin Yaranki, ibadarki, Gidanki, bakida Lokacin komai sai chattin bai kamata kibari wata tayi rinjaye kan komai na rayuwarkiba amma ga dukkan alamu kina neman jefa kanki hanyar da baida ceba ibadarki tayi Rauni idan Allah yadauki Rayuwarki mezaki cema Ubangiji?"


 "Bakida Lokacin yaranki kisani yaranmu amanace akanmu Allah zai tambayemu akansu mezakicema ubangiji akansu?" 


"Zaman aure ibadane shin kina yin ibadar aurenki yadda Addini ya koyar?" 


"A kullum nakanyi kokarin ganardake hanyar da ya dace Amma Saidai kisa k'afa kishure Allah ya gani ina iya bakin kokarina wajen nuna miki hanyar data dace bakuma zan gajiya da fadi mikiba, da sannu wataran zai miki amfani."

Nasiha sosai yamata maishiga Jiki, su Hafsy harda k'walla 


"Kayi Hakuri insha Allah zan Gyara komai zai dawo dai-dai." Allah yasa tace Ameen gaba daya sukayi Dariya daganan salon ya sauya

Kofar najamusu na kara wuta. 

   


    ✍🏾UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: 😭ADALILIN LINK 😭


WRITTEN BY:

 UMMN YSRH 


EDITOR BY:

 QUEEN MEEMI 

 

    HBD SIST MARYAM S BELLO ALLAH ALBARKACI RAYUWARKI Y KARO SHEKARU MASU ALBARKA👏🏻


     2⃣to 5⃣


Tagama zaman jiran Tsammani taji shuru ta tashi ta nufi dakin ta. Takoma sana'ar data saba. 

Sai wajen 12:00MP Tasauka sannan tayi sallar isha ta kwanta. 

  

    WASHE GARI

 

Bayan tashinsa Alwala yayi ya wuce Masallaci Daya dawo ya Jona Ruwa a Kettle ya tada Sabeer yayi Sallah sannan yamai wanka ya turashi a kira Sabeerah sannan ya taho da kayan School nasu, d'akin ummansu ya nufa har ya shiga ya tada Sabeerah ya d'aukar musu kayan Makaranta ya fita bata saniba ta baje tanata kwasar bacci.


Ad'akinshi ya shiryasu ya had'amusu Tea suka sha  ya kwashesu zuwa Makaranta.


  

  *AL_YUSRAH INTERNATIONAL ACADEMY MAKAMA JAHUN BAUCHI* 

  

 Anan suke karatu Makarantane na masu k'aramin k'arfi akwai koyarwa sosai ga kula da Yara. 

 

Kafin yakaisu saida ya tsaya yasa musu Hadd'iyar Masar Bauchi wajen HAJIYA FARIDA (GWANACE SOSAI WAJEN IYA MASA MAI INGANCI DUK WANDA YACI SAI YA MANTA HANYAR GIDANSU). 


Bayan ya saukesu ya wuce wajen nasa Aikin.




     7:00am

 Hafsa kuwa tana D'aki sai bacci take sadidan hankalinta a kwance Juyi tayi zata gyara kwanciyarta taga D'akin yayi Haske tashi tayi da sauri ta juya zata tashi Sabeerah taga wayam!.

 

Band'aki ta Lek'a taga bata ciki fita Falo tayi batanan Juyawarta daki tayi tasan suna gun Abbansu.

Ita adole fushi take dashi don yamata wulakanci. 


*CIKIN GARIN BAUCHI 

  UNGUWAR NASSARAWA*

 

Unguwace mai tarin Jama'a.Bilkisu ce ta shigo gidan da saurinta tana tambayar Yaranta "Babanku ya dawo kuwa?"Babbar mai suna Salma 'yar Shekara 7 tace baidawoba.


 "Yawwa inata sauri indawo"  sai bimata Aisha 'yar Shekara 5 tace "Mama tun d'azu kika fitafa kince zaki dawo da wuri kinje kin zauna gashi munatajin Yunwa."

  "Kuyi hkr ga Abinci na kawo muku kuci kafin na D'aura Abinci."

  Bilkisu Macece mai shegen son bin Gidan Mak'ota idan ta sabi Mayafi saita gama karad'e Gidajen Unguwar taci tayi k'at kafin ta dawo Gidan Mijinta.

  

  Malam sani Ma'akacin Gidan Block ne yana iya k'ok'arinshi wajen Rufa musu Asiri Amma hakan bashi ya hana Bilkisu bin Gidan Mak'ota ba wani Lokacin taje da yaran wani lokacin tabarsu Gida. Yaransu Uku duk Mata k'aramar Asiya 'yar Shekara 3 wani Lokacin Gida take barinta ta tafi gararinta. 



   ✍🏻UMMIN YUSRA.

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . . 😭ADALILIN LINK😭


      WRITTEN BY:

                UMMN YSRH 

       EDITOR BY: 

             QUEEN MEEMI 


   THIS PAGE IS 4 U SISTO UMMY ABDOUL (AWANI MASARAUTA)

NAGODE DA KAUNA ALLAH BAR ZUMUNCI 😘



        1⃣4⃣TO 1⃣5⃣


Ba Laifi Hafsat kwana 2 tadan chanza, 


Dattijuwa ce tsaye kofar Gia da yar jakar kaya da wani buhu agefe tana tunanin ina Bilky taje awannan lokacin ta deb'o hanya ga Gajiya abun Haushi tazo Gida rufe. 

Bayan ta gama tunane tayanke shawarar shiga mak'wabtansu ko sun san inda taje. 



Da sallama ta shiga bayan sun gaisa da Maman Maryam ta tambayeta ko Bilky tayi nisane tace "Aiko bansan inda tajeba, ki shigo mana sai indubo miki ita hala Maman tane?" "eh wallahi" 

"Barin dubota don nasan bata wuce cikin Unguwarnan Duk yawonta" wajen zama ta bata sannan ta d'au Mayafi don yaran duk sun tafi School.


Gida kusan biyar ta shiga bata sametaba haka ta hak'ura ta dawo ta sanar da Maman Bilky bata nan. 


"Toh nagd Allah yayi Albarka, narasa gane Bilky wani irin yawo gareta Mutane da yawa idan sunzo sun koma sai suce sunzo basu sametaba. Shin Aiki takeyi ?kodai zaman Gidan ya gagreta ne? Amma ace in d'auko Hanya tun daga Azare ace bakowa A gidan wannan hali sam bai ba." 



"Ki hak'uri Mama sam Bilky ban san wani irin hali ta d'aurama kantaba indai Garin Allah ya waye saita gama karad'e Gidajen Unguwa kaf.! 

Har fad'a mukayi don inamata Maganar ta daina yanzu haka ko Magana ba tamin.".                                              "Humm Allah ya kyauta ya shiryeta." 

"Ameen Mama"

Maman Maryam ta gama Abinci ta zubo mata taci anan tayi Sallar Azahar da Al'asar. 



      4:00MP 

Bilky ta dawo Gida Yaran na biye da ita bud'e Gidan tayi suka shiga suna shiga da sauri Murhu ta nufa tana k'ok'arin had'a wuta taga yara suna shigowa da kaya Mamanta na biye dasu.                                                          


Da Murnarta ta tafi yima Maman nata Barka da zuwa yadda wani kallo ta bita dashi take tasha Jinin Jikinta.                                                                                                               


                                                                                       

  Kayan ta karb'a takai D'aki sannan ta d'eboma Mama ruwa tace "koshe nake najima da zuwa tun shabiyun rmRana na shigo Gari naga Gidan arufe nace hala kintafi wajen Aiki." kallon mama tayi tace "Aiki kuma!" tashi tayi ta barta da Jikokinta ta tafi d'aura Girki. 



       8:00MP 

Mamace da Bilky da Abbansu salma suna zaune suna hira. Gyaran Murya Mama tayi tace "yanzu kai 

Sani haka zaka zubama Bilki ido tana wannan yawon dabai da Amfani ace kullum kina Bibiyar Gidan Mak'otan, haka sauran Makotan kika ga sukeyi?  

Idan kwad'ayi ke kai ki me Mijinki ya tsare miki yana k'ok'arinshi iya k'arfinshi kamata yayi ace yanzu Salma da Aisha suna Makarant Amma kun barsu daga Gadin Gida saiki kwashesu yawon Gulma da kwad'ayi Gidan Mutane. Baki tunanin Lalacewar zamani kifita kibar yara k'anana kuma mata sukad'ai.A gida wani ya shigo ya Lalata miki Rayuwar yara yanzu ka killace yaranma baka tsiraba balle kuma kayi watsi dasu, wallahi duk Randa na sakejin Makamancin haka Sai dai ki fita kibarmai Gida ni kuma nama Alk'awarin Sadakin Aure da akwati kije kici gaba karki fasa yara uku baki hankali kinba kanki shawara mai kyauba sai wa kikeso yazo ya baki? Nasan halin Sani yana iya k'ok'arinshi kece dai shed'an ke yawo akan ki Allah yashiryeki damasu Hali irin naki." 


Kuka take Sosai "Mama ki hakuri wallahi ban k'arawa." 


"!Ah kici gaba kin daiji hukuncin dana yanke." 


Malam Sani Bawan Allah hakuri yayita ba Mama"insha Allah komai zai dawo dai2, yara suna Makarant ita ke hanasu zuwa yayi Maganr har ya gaji 



   ✍🏻UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . . 😭ADALILIN LINK 😭



      WRITTEN BY:

              UMMN YSRH 


      EDITOR BY:

            QUEEN MEEMI 


   THIS PAGE IS 4 U  SIST LUV 

          YESMEEN TAFEESU ALLAH BAR ZUMUNCI DA SO DA KAUNAR JUNA 😘


       1⃣6⃣TO 2⃣0⃣

       

       


Humm mai halidai bai fasa halinshi.Hafsat dai takoma Sana'arta Sai dai muce Allah kyauta. 



Kwanan Mama 2 ta tattara takoma Azare 

Bilki kamar jira take ta tafi don kwana 2 dinnan atakure take yau jitake tamkar Sallah. 


Abbansu Salma na fita ta shirya su Salma suka wuce Makaranta dake basuda nisa sosai da Makarantr ta gyara Gidan tsaf sannan ta Goya yarta taja k'ofar tayi gaba. 



FARKON AL'AMARIN 


Kwance take kan Gado tana chattin a wayarta taga anturo wani GROUP LINK mai suna (GIDAN DADI) kodaga icon na jikin Grouprp d'in kasan bana Mutanen kirki bane Macece keshan Nonon yar'uwarta.

🙊

Wasu sai Allah wadai suke ma LINK din wasu da shedan ya bugamusu Ganga take suka hau Join d'in LINK din acikinsu harda Hafsat. 


Bayan shigarsu kowa ta fara Gabatar da kanta, daya daga cikin Members tace "toh bak'i kowa ta turo Pic dinta ko zan sami Sabuwar kawa." 


Pic suka fara turowa wasu Sanye da Hijab wasu da Gyale wasu ba Mayafi. 


Wata mai suna Ayna tace                                                                                                           "habba wannan wane irin iskancine Pic mukace kuturo muga komai bawai kalan Mayafinkuba." 


"Hauwa tace habba dad'ina dake Rashin hakuri ki Musu uzuri kinsan sabbin shigane meyuwa basu san komai ba ahankali zasu gane komai." 


Aynah tace "uhmmmm Allah yasa donni kinsanni dason sabon zuma."


"Sorphy tace "hhhhhhhhhhhhhh nasanki Ayna ba damane wajen harka abisu asannu zasu fahimci komai."



Shamcy Hot girl:

"Munama baki Barka da zuwa. 

    GIDAN DADI 


   GIDAN MATA MASU 'YANCI 


GIDAN MATAN DA SUKASAN KANSU


GIDAN MANYAN MATA 



   NIDAI GEFE NAKOMA INA TUNANIN WANNAN WANI IRIN GIDANE?"



✍🏻UMMIN YUSRAH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK😭



      WRITTEN BY

             UMMN YSRH 


        EDITOR BY:

             QUEEN MEEMI 

             

             

     FATAN ALKHAIRI GAREKI HAUWA KELE (ADMIN ADALILIN LINK) NAGODE DA KAUNA ALLAH YARAYA ZURI'A NASADAUKAR MIKI DA WANNAN PAGE ALLAH BAR ZUMUNCI👏🏻 



       2⃣1⃣TO 3⃣0⃣


ZEE:


 Sai Admin wannan kirari haka ke Allah dai yaja daranki


Shamcy: 


Gadiya nake Matan masu dadi. 



Ummi:


kutaimaka yau banda lafiya


Zully:


Maiya faru


Ummi:


Yau ban Abokiyar Rayuwa


Shamcy:


hhhhhhhhh!

Ummi Dadina dake ba wasa yau ina Mutuniyar taki? 


Ummi:


Munsami matsala ta gujene abani wata don ban iya rayuwa idan ba harka. 


Hafsat:


Assalamu alaikum 

Barkanku da wannan Lokcn ni bak'uwace ina garin Bauchi ina zaune a Gombe road Fatan zamu karu da juna. 


Shamcy:


   Muna miki barka da zuwa muna bukatar Pic dinki 


Hafsat:


Amin afwa zuwa anjima zan turo. 


Zully:


Muna jira


Shamcy:


Ummi kizo ga yar garinku kinsami Sabuwa. 


Ummi:gani aguje Fatan tasan harka ba Dunkum baceba



Shamcy:


Inbata saniba saiki sanarmata. 


Ummi:


Angama shugaba


        12:30MP 


      GIDAN BILKY 


Salmace da aisha suna a zaune k'ofar gida sundawo Makaranta gidan arufe nan suka yada Zango sunata wasa don inda Sabon sun saba da yunwa. 


Wani Matashin Saurayine yazo wucewa ya gansu zaune awaje da ganinshi kasan abuge yake "kai me kukeyi anan?" 


"Mundawo daga makarantn kuma gidan arufe Mamanmu batanan!" 


Duk Magar da suke idonshi nakan Salma. Naira Hamsin ya mik'ama Salma yace "kuje kusayi abu kuci Maza kafin Mamanku ta dawo." 

Karba sukayi suka sa gudu shi kuma ya kama gabanshi.



     GIDAN HAFCY


Dr. Haseeb ne da yaranshi sun dawo daga Makrnt 

Hannunshi dauke da ledar Abinci, da sallama suka shiga falon ba kowa cikin. Ya Leka d'akinta bai gantaba k'arar ruwa yaji abayi. Juyowa yayi ya cire musu kayan Makarta yace su chanza kaya sannan suci Abinci, Idan Ummansu ta fito suce ya wuce ana Jiranshi.


Tana jin tashinl Motonshi ta fito bakomai take  Abayinba Maganane kawai bataso yasa ta shigewa tayi zamanta. 


      10:00MP 


Kwance take kan gado tana Chat a Sabon group d'insu (GIDAN DADI) tanajin Dadin hirar da sukeyi abu d'aya ya daure matakai yadda sukata Labarin Dad'in da suke kwasa gun 'yan'uwasu mata, itadai Hafcy abun ya d'aure mata kai. 


     Tace don "Allah inada tambaya"


Muna Jinki 


"Naji ku nace idan "Mace da Mace suna harka ya fi Dadi fiye da yadda na Miji da Mace sukejin Dad'i, Amma dai ba Matan Aure cikinku?" 


   Gidan gaba d'aya ya kaure da Dariya


Ummi:

      Akwai Matan Aure cikin mu Akwai 'yan Mata, Tabbas harkar Mace da Mace yafi komai Dad'i Namiji agunmu ya fita ya nemo ya bamu shine Burinmu." 


Hafcy: 

           "Kumin Bayanin group d'in sosai don ban fahimtaba har yanzun" 


Shamcy:

              "Kamar yadda kikaga sunan wannan Gida asama Tabbas haka yake muna d'ebe ma Junanmu kewa muna Jiyar da Junanmu dad'i muna taimakon Junanmu idan hakan ya taso

Kowane Gari muna da k'ungiyarmu Babban Reshenmu yana Abuja muna Meeting Gari- Gari duk k'arshen wata kuma wajibi ne kowacce ta shugaban kungiya ta zoda Members dinta akwai matan manya da masu kananan karfi cikinmu amma duk bamai gane matsayin kowa cikinmu, muna Fatan kema zaki zama daya daga cikinmu." 


Hafcy:

          "Na fahimta, Amma tayaye kuke jiyarda junanku dadi? Ko kuna tara kud'a dene duk Meeting kurinka rabama Junanku wanda yake da bukata?" 


Zully:

        "Kewai dallah bakida fahimtane?" 



Zeee:hhhhhh! 

"Kawai kamata bayanin yadda zata gane sabuwace sai ahankali"


Ummi:


"Muna jiyarda Junanmu dadine tamkar yadda mace da miji sukeyi

Wannan group din na yan LESBIAN NE (MADIGO") 

 


INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U


   Tsabar Razana sai da wayata ta tarwatse

Kuyi hkr idan na hada zanci gaba😉



    ✍🏻UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK😭


        WRITTEN BY:

               UMMN YSRH 


       EDITOR BY:

             QUEEN MEEMI


 YABO DA JINJINA TAKICE KINYIMIN DUKKAN ALKHAIRI GODIYA YAYI KADAN AGAREKI SAIDAI ADDU'A DA FATAN ALKHAIRI A GAREKI ALLAH Y RAYA ZURIA YA ALBARKACI RAYUWARKU ALLAH KARAMIKI BASEERAH DA HAZAKA ALLAH BAR ZUMUNCI DA SO DA KAUNAR JUNA 

      QUEEN MEEMI 

         QUEEN MEEMI 



     3⃣1⃣TO 4⃣0⃣


Ummice tacigaba da bayani ta. 


"idan Mutum ya Burgemu mukayi k'ok'arin sanyashi cikinmu idan yazo munada mai Janyo mana da Ra'ayinshi kota halin k'ak'a." 



Ahaka suka ta mata bayanin Group din 


Zuciyar Hafsat ta Rabu Gida Biyu d'aya nabata shawarar ta yadda daya na mata hani da hakan. 



     3:00pm 

     

Bilky ta dawo Gida tunda taga basu Salma tasan suna Mak'ota tayi shigewarta Gida don tasan inbtashiga Gidan yanzu zata isheta da Surutun ta cika yawo. 



*Hafsat*


Hafsat ta Gama tunanin itama zata Gwada wannan Rayuwar taji yadda akeji. 


Wayarta ta D'auko ta hau Online tana bud'e Group taga anturo Pic da Video na Mata yadda suke Shek'e ayarsu take taji tana Sha'awar Irin Rayuwar, hira suke tasha kowacce tana yaba yadda k'ok'arin Abokiyar bad'alarta. 


Hafcy:


     "Sannunku"


Ruky:


     "Yawwa sannu dai"


Ayna:


     "Amma ke Bak'uwace ko?" 


Hafcy:

   

      "Eh"


Aynah:

         "Ayyah Barka da zuwa wani Gari kike? "


Hafcy:

       "Bauchi nake


Aynah:

      "Kice Garinmu kike nima Bauchi nike, Unguwar mai kafi dai2 Jikin Gidanshi inada Aure da yara hudd'u


Hafcy:

     "Ayyah ni kuma yarana 2"



Aynah:

    "Fatan zamu k'ulla Zumunci" 


Hafcy:

      "Insha Allah" 


Aynah:

     "Muje prvt kituromin Pic naki don na fara kishinki"


Hafcy:hhhhhhhh! 

"Amma ngd"


 Tun dagan suka k'ulla Gurb'atacciyar Alak'a

Ayna Gwanace sosai wajen harkar shiyasa bata sha wuya wajen koyama Hafsat harkar ba, sukan d'auki tsawon Lokaci Awaya ko chattin suna d'ebe ma Juna kewa tare da turama Junansu Pic na tsirai cinsu. 


ALLAH KA TSAREMU KA KAREMU DA IMANINMU 



YAU TAKE ALHAMIS


Yauma kamar kullum Salma Sundawo daga Makaranta suka shige Gidan ba kowa. Bayan sun cire kayansu suka fito waje suka zauna suna wasa, chan Matashin Saurayin nan yazo don tunda ya fuskanci Yaran kullum akebari Gida kullum sai yazo ya basu Naira 50 susai abu idan Ummansu ta dawo suka fad'i mata tayita Murna tanamai Godiya taimakon da yake Mata. 


Bayan yazo ya ciro Naira 100 yaba Aisha 


"Maza kije gun mai saida warar Bakin hanya ta baku na Narai tamanin, sannan ki sayo muku Zobo na Ishirin ma zaki kawo kuci, ke Salma shiga ki D'ebo min Ruwa insha." Aisha ta tafi da gudu tana Murnar yau zasuci dadi ko nisan tafiyar bata gani don akwai dan tafiya daga Gidans zuwa bakin Titi. 


Bayan tafiyarta Saida ya duba Gabas da Yamma kudu da Arewa baiga kuwaba yashige Gida ya Jawo k'ofar ya rufe nayi ,kokarin Bude k'ofar na kasa ina tsaye k'ofar Gidan, Ihun Salma kawai nakeji ko me yake Mata Ohh🤔🤔. 



✍🏻UMMEEN YUSRAH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK😭




     WRITTEN BY:

           S. S. AL_EEMAN 



      EDITOR BY:

            QUEEN MEEMI 



 WANNAN PAGE NAKINE SIST FAREEDAH MUSA

 (YAUDARAR ZICIYA DA NI'IMATULLAH) 

  YSRH DA LABEEB SUN SAMI LFY NGD SOSAI DA ADDU'A ALLAH BAR ZUMUNCI ALLAH KARA

 BASEERAH DA HAZAKA ALLAH KARA KARFIN IDO DA ZAKIN HANNU👏🏻



        5⃣1⃣TO 6⃣0⃣

Bayan rabin awa zsalma ta farfado Alhamdulillah yanzu kam bata razana sai kukan datake na ciwon da takeji akasanta. 


Tunda ta dawo daidai sukayi shirin komawa Gida 


           8:00pm 


Da sallama suka shiga Gidn yaya faty tana dauke da Salma, Bilky ta fito daga daki daukeda wani Takarda da guntun kifin dayasha Maganin Bera zata kai shara taga yaya Faty rike da Salma ita tama manta da wata Salma


(kunji uwar kwarai) 


"Lahh yaya Faty sannu da zuwa yaushe kika zo? 

Tun rana nazo kushiga toh sannu da zuwa." 

Bayan ta zubar da sharar tazo suka Gaisada yaya Fatyn tare dayima Juna ta'aziyar Rasuwar Aisha. 


Nan Bilky ke gayamata "Ashe kifin data sama B'eraye Magani Jiya basu ciba shita dauka taci" yaya Faty cikin bacin rai tace "hummm koma me ke kika jawo kece silar komai dama Mamace ta turoni in dubaku sannan inga halin naku Nanan ko kin dai na nayi wayama Abbansu Salma yazo ya d'aukeni a tashi muna isowa muka tararda Bakin Al'amari Burinki ya cika Bilky kin kuma kyauta kin kasa zaman Gidan Aurenki kin kasa kulada tarbiyar yaranki yau an wayi gari wani Azzalumin mara imani mara tausayi yama Diyarki fyade yamata Mummunan illar da har abada bazamu taba Manta shiba duk Adalilin rashin zamanki sai kishirya tarar Hukuncin daga wajen Mama don nasan Abban su Salma bazai taba D'aukar hannu ya Rubuta miki takardan saki ba don kun mana hallacin da bazamu taba mantawa ba." 

Tunda tafara mgnr Bilki ke kuka sai yau take dana sanin irin Rayuwar data jefa kanta ciki. 



GIDAN DR HASEEB 



Hafcy ce kwance suna waya da Aynah yanzu kam tagama Gogewa a harkar don har ziyara sukema Junansu. 


Da sauri ta tashi tahau Gyaran Gida tayi Girki sannan ta D'au Gayu don Aynah tace mata 4:pm tana zuwa Gidanta yau su shana



Cikin dare Zazzabi mai zafi ya rufe Salma numfashin ta Sai sama2 ya keyi kafin da Futo Yaya Faty ta kira Abbansu Salma a dakinshi yazo ya ga yadda ta keyi kafin su iso D'akin sukaji Bilky ta kurma wani uban ihu tana shikenan itama tabita wayyo Allah kutaima kamin" 

Atare suka shigo d'akin don Ganin meke faruwa Dagota sukayi Atare suna Jijjigata Amma inah Rai yayi halinshi, Sai dai muce Allah Jikan Salma yasa mai cetone



Aynah tazo sun gama sheke ayarsu Lokacin yara na Islamiyya sai wajen 6:pm sukayi sallama Badon sun oba



Hafcy ta goge ta zama gwana sosai kullum suna bin Gidn kawayen harka irin tasu harta kaiga yanzu ko kula Dr Haseeb ba tayi balle taji wani Sha'awarshi abun yana Mugun damun shi gashi yafara Jin Jita2 wajen Mutane halin da Matarshi take ciki, shidai kam bai yaddaba tunda bai gani Azahiriba, yadai bar abun A ranshi yakuma kudurama Ranshin insha Allah zaiyi Gogon Bincike.




Haka suka kwana da Gawan Salma da Asuba bayan idarda Sallah Abban Salma ya sanar A masallaci Anyi Rasuwa A Gidanshi zuwa karfe takwas insha Allah za'a mata sutura. akaita Sakamakon Maganin Berar da sukaci a abinci shiyayi Ajalin yaran nashi Gaba daya. Anmai ta'aziya da Alkhairin insha Allah zasuzo akwaita Makwancinta.



Mak'ota duk sunji lbrn Mutuwar Salma itama Dalilin cin kifi mai Dauke da Maganin Bera 



Maman Bilky da 'yan Uwanta dake Azare duk sunzo Sai dai suma ance Musu kifi sukaci da Magan ajiki don Abban Salma ya Roki yaya Faty dasu Boye Gaskiyar Al'amarin domin Maman Bilki uwace Agaresu basuda kowa bayan ita idan taji Gaskiyar Lamarin Tabbas zata iya Tsinema Bilky. 



    WAIWAYE ADON TAFIYA


Asalin yaya faty da sani(abbansu salma) yan jos ne cikin garin mongu wani fadar kabila da akayi akasama gidansu wuta cikin dare gaba dayan al'ummar gdn suka kone yaya faty da kaninta kawai suka tsira tsirarun mutanen da suka rage kowa ya kama hanyar neman tsira duk suka watsu cikin jeji hakan har Allah ya kawosu cikin garin Bauchi bakin tasha suka zauna lkcn mama Hadiza takawoma kanwarta ziyara datake garin bauchi zata koma tazo wucewa yaya faty tace don Allah mama ki taimakamana da abunda zamuci yau kwnananmu uku bamuci komaiba nan take taji tausayinsu tace daga ina kuke ? Ina iyayenku aikam nan take suka fara kuka yaya faty ta sanar mata daga inda suka fito da abunda ya faru da danginsu ta tausayamusu matuka tagayamusu itama ba nan garin takeba daga azare take idan sun yadda zasu bita zata rikesu ba musu suka amince Mmn Hadiza tasai musu abinci ta biyamusu kudin mota sai azare 



Ahaka sukaci gaba da rayuwarsu cikin rufin asiri Mmn Hadiza mijinta y rasu tana zaune da yaranta uku biyu maza daya mace Bilky yar auta 


Haka sukaci gaba da rayuwarsu sani dama bamai yawan magna bane komai akayi baice eh balle aah 



Cikin rufin asiri mama hadiza ta aurar da faty anan azaren lkcn sani yana zuwa bauchi kawo kayan gwanjo duk Ran jumma'a kasuwar C&C yana samun budi sosai anan suka hadu da wani bawan Allah mai gdn block yace idan ba damuwa yadawo bauchi da zama zai bashi wajen zama sai yarinaka aiki a wajen don ya yaba da hankalinshi 


Tundaga sannan yadawo cikin bauchi da zama har yasamu yayi gininshi yar madaidaici yaso mm hadiza ta dawo amma sam taki tace batason rabuwa da abokan arziki saidai yasamo mata ayi mgnr aure in yaso ya sata gdn. 

Yace shibaida kowa yabar ma mama zabi ahannunta taji dadi sosai tace idan sunyi shawara da faty zata nemashi 



Bayan tasami faty da zancen ko da wacce ta yaba da hankalinta tace mama ai basai ansha wahalar neman mataba matanshi tana gidan ga Bilky mezai hana ahadasu

Anya faty kinaga hadin zaiyi kuwa kinsan halin kanwartaku akwai tsiwa da rawarkai kar azo ana dana sani, insha Allah hakan bazai faruba.




Ansha shagalin biki akakai amarya gidan tareda gargadi da nasiha mai shiga jiki sai Fatan Allah yabaku zaman lfy 




✍🏻

      UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: 😭ADALILIN LINK 😭




WRITTEN BY :

     UMMN YSRH 


EDITOR BY:

       QUEEN MEEMI 



WANNAN PAGE NAKINE


 DR ZALIHA(MOM FATY) 

INA ALFAHARI DAKE SIST DA KWARIN GWUYWA DA SHAWARWARINKI FATAN ALKHAIRI GAREKI DA AHALINKI ALLAH KARA MIKI DAUKAKA ALLAH RAYAMANA BBY FATY YAKAWO WASU MASU ALBARKA NAGODE KWARAI ALLAH BAR ZUMUNCI SO DA KAUNAR JUNA 😘




   8⃣1⃣TO 9⃣0⃣


Anyi neman duniyar nan ba'asami Hafcy ba k'arshedai aka hakura aka barma Allah komai.



Da kyar aka samu Dr yadawo dai2 amma kullum ya kalli Sabeer da Sabeerah saiya zubarda kwallah don tausayinsu da kuma halinda Mahaifiyarsu ta jefa kanta. 



Mama Hadiza ta dage sosai wajen ba Bilky mugun2 da Umma lami ta hada mata 


Ranar farko da aka bata amai tarinka zubowa da wani irin bakaken abubuwa, ranar wuni tayi agalabaice sanda taje wanka da ruwar Maganin tana zubawa wani bakin hayakine ya rinka fita ajikin ta. 



Nikaina danake tsaye kofar bayan gidan saida na tsorita(😉) 



Kwana uku tayi tana wanka da ruwan Maganin zallah tunda ta fara amfani dashi sai taji kamar an sauke mata wani Dutse mai dan karan nauyi taji jikinta ya mata sayau 

   

 

(Allah shiga tsakan na gari da mugu) 




    BAYAN WATA SHIDA



Abubuwa da dama sun faru Sai dai Fatan Allah kyauta



Tun ana saran dawowar Hafcy har an gaji da jiran tsammani



Dr.haseeb har yagaji da korafin umma kan ya kamata ya manta komai yanzun yasamo ma ya'ya'nshi uwa, don zamanshi ba mace baiyi tsariba. 



Tun faruwar abun yaran suke gidan Umman tun kwana biyu da kawosu suka fara kukan akaisu wajen ummansu .


Sai akace musu tayi tafiya ta tafi wani gari mai nisa karatu da fari sun hakura amma daga baya suka rikice sai da aka kawosu gidan suka tabbar sannan suka hakura dama bawani sabawa sukayi da itaba shiyasa suka manta da ita don sunfi jin Dadin gidan Umma da gidans



Yawan zan cen ya sake Aure yasa yanzu sai ya yi kwana 2 ko 3 baije gdnb donshi yanzu mace tagama fita arayuwarshi baida ra'ayin aure garaya kare rayuwarshi ahakan. 




   ATBTH BAUCHI 


Dr. Haseeb ne zaune cikin office dinshi yana duba mata masu matsala yaukam akwai mutane sosai ga tun 8:00am yake fama da mutane gashi har yanzun kusan 12 ba alamar zasu ragu. 



Mafi yawancinsu masu matsalar Infection Sai 

Masu family planning 

Wasu sunyi amfanida kwayoyi Wasu Allurai 


Wasu kuma sunsa robar hannu gashi ya jawo musu matsalar zubar jini 


Wasu kuma wata matsalar ta daban


Wata kyakkyawar budurwace ta shigo cikin nutsuwa sallama naji tayi dawani sassanyar murya tamkar sarewa ta busa, da sauri dr ya dago yana kallonta har ta iso gabanshi bai saniba saida tace


 "Barka da Aiki Dr"


"Barka dai" 


Tami kamai katinta tana mai bayanin daga G. O. P. D

Akaturoni nan 

Yace ok "meye damuwar?" 


Sunanta ya duba yaga YESMEEN TAFEESU MUHAMMAD 


A Zuciyarshi yace lallai kinci sunanki TAFEESU 


Tace dama, dama kanta na kasa sai in ina take 


"Dr. Nanfa asibiti kikazo don samun lafiyarki ya bada kyau ki saki jikinki kiyi kyakkyawar bayani idan ba kiba ba yadda za'ayi musan Matsalarki ki ajiye kunyarki agefe idan kin gama bayani sai ki maicda abunki, akwai kyakkyawar fahimta da kulawa tsakanin likita da mai jinya, inaji bayanin ki."


"Dama duk lokacin da zanyi period ina yawan ciwon mara sosai wani lokacin har suma nakeyi ga shi yana zuwa da yawa."


Kintaba zuwa ganin likita Tunda kika fara jin hakan? 


Eh ina zuwa Saidai konasha magani baya dainawa Saidai indaji saukin kadan 


Ina gefe ina dariya TAFEESU don tana bayani tana kuka, daga dukkan alamu tanajin ciwon abun sosai 


Ki shuru yanzu zan baki scaning kije kiyi gobe in Allah ya kaimu saiki kawomin amsar inga me matsalarko 


Toh dr. Ngd


Ruce2 na likitoci yy sannan ya mika mata katin tayi gdy ta tafi. 


Wunin ranar dr. Da tunanin kyakkyawar fuska da zazzakar murya da kuma shagwabarta ya wuni. 


Nidai nace anya Dr. TAFEESU basa fara chanza ra'ayiba kuwa 


Muje zuwa don jin yazata kasance 

  

Taku har kullum mai kaunarku 


   YAR MUTAN 


BAUCHI KEMUKU FATAN ALKHAIRI 





✍🏻UMMEEN YUSRAH 

      UMMEEN LABEEB

    UMMEEN SADEEQ


UMMEEN KOWA😛

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . . 😭ADALILIN LINK😭



    WRITTEN BY:

        S. S. AL_EEMAN


  

     EDITOR BY:

           QUEEN MEEMI 

  

   nasadaukar da wannan page gareku dukkan masoyan wannan wannan novel din ngd😘


   

       4⃣1⃣TO 5⃣0⃣



Yakai kusan rabin awa aciki da gudu naga ya fito yana gyara wando, 


Nidai tsoron shiga nake don bansan a halin dazan sami Salma Yarinya mai shekara 7 ba. 


Can na Hango Aisha tana tahowa da gani taci kuka koshi tunkafin ta karaso na isa gareta "meyafaru kike kuka?" 

"Wani yarone ya k'wacemin Naira darina dazan siyo mana awara." 

"Ayyah ki hak'uri Allah zai saka miki, shiga Gida ki duba Salma" toh Aunty, tsaye nake ina jiran fitowarta da Gudu ta fito arazane kafin in k'araso gareta na Hango Abbansu tare da wata mata sunnufo hanyar Gidan gefe na koma naji Aisha tana cemai "Abbah sauri kazo kaga Addah Salma kwance duk ta Jikinta jini tana kwance."


 Ai kafin ta karisa bayani ya shige Gidn da gudu wacce suke tare ta rufamar baya. 



Abunda yagani yasashi Mutuwar tsaye.  

Wacce sukazo tare ita tayi k'okarin dago ta ba komai Jikinta k'asanta kam ba ko kyan gani. 

Dakinsu ta shiga ta samo Doguwar riga tasa mata sannan ta dauke ta, tace "muje akaita Asibitin nan dake kusa, don ko Numfashi batayi"


Taji shuru dagowa tayi taganshi tsaye Hawayen bakin cikine kawai ke zuba idonshi, sai data tabashi sannan ya dawo hayyacinsa "muje akaita asibiti don sanin halin datake ciki. "


      ASIBITIN UMAR ISAH YUGUDA 


Sanda suka isa Doctors sun tashi Aiki sai guda daya itama shirin tashin takeyi  sukai mata bayani, Aikam take ta balbalesu da Masifa da irin sakacin da sukeda yaransu, tace "ina mahaifiyarta? "


"Batanan nima zuwana Gidan kenan na riske hakan ga Mahaifinta awaje ni yar Mahaifintane don Allah ki taimaka."


"Gaskiya wannan case din sai an hada da hukuma sannan ayi Bincike wanda ya mata wannan Mummunar aikin".


"Don Allah ki taimakamin ki rufaman Asiri komawa ya mata hakan mun barshi da Allah mudai yanzu burinmu musan halinda Yarinyar take ciki".da k'yar ta yarda zata musu Aiki sannan bata bukatar Asani don zai iya shafa Aikinta. 



Dr. Khady Gwanace wajen Aikinta wata Ma'akaciya ta kira ta dauki yar suka nufi dakin da zasuyima Salma aiki. 


Yaya faty ta leko gunda D'an'uwanta yake tsaye. Hakuri tayi ta bashi da Nasihar yadda da k'addara sannan tace ya koma wajen Aikinshi idan angama komai zatamai waya, da k'yar ya yarda ya tafi badon ranshi ya soba, ya koma wajen Block dinsu tunda ya koma ya kasa komai Abokan Aikinsa sai tambayarshi suke ko lafiya yace ba komai don sun sanshi Mutum ne mai k'ok'ari waje Aikinshi Amma yanzu ya dawo ya kasa Aikata komai da suka dameshi da tambayar yace baijin dadin Jikin shine. 


Yaya faty zaune tana jiran fitowar Dr da Salma amma shiru. 



Sun shafe wajen awa daya da mintoci kafin suka fito wani Daki daban akakai Salma aka kwantar, Sannan ta bukaci yaya Faty ta biyota zasuyi magana. 



"Gaskiya duk wanda ya mata wannan Mummunar Aikin ba Mutane mai cikakken Hankaliba, yanzu haka sai da muka mata d'inki sosai ya riga ya mata kaca2 Sai dai kuringa kula da ita sosai yanzu an mata Allurar bacci zuwa Anjima zata Farfad'o insha Allah akwai Magun-gunan da za'asiya san nan kurink'a mata tsarki da Ruwan dumi da Gishiri insha Allah zata Sami Lafiyay Allah yakare na gaba."


"Mungode sosai da taimakonki Allah biyaki ya karemiki zuri'a." Ameen ngd. "Zaku koma Gidan idan ta Farfad'o sai kimin kwatancen Gidanki zan Rinka dubata acan, tunda kinga taimaka mata nayi bai Shiga Record na Asibitiba." 

 "Toh Dr Mungode da taimako" nan tamata kwatancen Gidan sannan ta wuce Gurin Salma. 


   

   5:00pm

    

Bilky ta dawo Gida tsakar Gida taga Aisha kwance wani Farin kumfa na fita Bakinta tana rike da ciki da Gudu ta isa gareta tana Jijjigata Amma ina ba Numfashi, da Gudu ta fita ta shiga Mak'wab tansu don Allah Maman Abbah zaki dubamin Aisha na dawo na sameta kwance ko matsi batayi. 


Mayafi ta dauka suka fito zuwa Gidan tana dubawa tasan rai yayi halinshi. 

"Umman Salma Sai dai kiyi hakuri Aisha Rai yayi halinshi. 


Wani Uban Ihu Bilky ta zuba take Mak'ota suka fito ana tambayar ko lafiy? 

Maman Abbah ke gaya musu abunda ya faru sun tausayama yarinyar yayincda wasu kecewa ta huta wasu kuma kecewa Laifin Uwar sune Allah kadai yasan me taci 

 

" hakuri zakiyi Balki Allah Jikan Aisha yasa ta huta ko wannan kinga ya isheki ishara." 


"Ki kirawo Mahaifinta ki sanar mai don ayi Gaggawar kaita Makwancin ta kar Magrib tayi."


Bakin zaninta ta Lalubo wayar tasa number Abban Salma tamikama Maman abbah tamai magan Bayan ya d'au Wayar tace mai "don Allah yayi kokarin dawowa Gida Aisha Allah ya mata Rasuwa" 


"INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U "

Kawai yake fadi. 


Bayan kashe wayar ya sanarda Abokin Aikinshi suka mai gaisuwace Allah Jikanta wasu kuma suka bishi domin yimata Sallah akaita Makwancinta. 


An kai Aisha Makwanci ta sai Fatan Allah Gafartamata yasa mai Cetone.


Asibiti ya wuce Bayan dawo wansu daga kaita nan yasamu Salma ta farka Amma kuma sai Razana takeyi Addu'a ya yita tofa mata sannan tad'an sami nutsuwa, nan take ya Gaya ma  Faty Labrn rasuwar Aisha yan zuma daga kaita suke duk dauriyarta wannan karon saida tayi kuka.


"Tabbas Bilki ta Cucemu komai ya faru itace Sila, wannan Jarabawa Lokaci guda Mungode ma Allah. 

Allah yabamu ikon Cinye dukkan jarabawar mu 


      Ameen 


✍🏻UMMIN YUSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK😭




     WRITTEN BY:

            UMMN YSRH 



      EDITOR BY:

         QUEEN MEEMI 



  1⃣0⃣1⃣ TO 1⃣1⃣0⃣



YESMEEN TAFEESU 


Yau sammako tayi don kawoma Dr. Result don tun jiya yake mata gizo shiyasa ta bugo sammako yau Mutum ukune gabanta bayan sun shiga lfy yazo kanta shiga da sallama cikin nutsuwa ta zauna ta gaida Dr. 



Bayan ya gama duba Result ya tambayeta "kinada Uurene?" 


Dagowa tayi arazane "Aure kuma?" 

"Eh!" 

"Nikam banda aure." 

"Kina yawan ciwon ciki?" 

"eh inayi"

"Ayadda Result dinki ya nuna gaskiya kina bukatar abokin Rayuwa ta hakane zaki samu saukin Matsalarki da yaddar Allah."

 

"Dr. Abokin rayuwa kuma? 

Eh! Kina bukatar Aure don shine kawai zai sa kisami sauk'in ciwon cikinki da kuma ta mara."


Hawaye yaga na fita idon cikin damuwa yace "lafy kuwa?" 

"Bakomai" 


Yace yazakice "ba komai bayan fuskarki ta nuna alamun damuwa."

 

"Tunanin nake yaushe zan samu Maganin ciwona ansamin rana da wani ana saura kwana 2 Auren yace ya fasa tun daga lokacn ba wanda ya kuma zuwa kusan shekara kenan" 



Wani Dadi Dr yaji "yace shine abun kukan karki damu  ai komai da lokacin sa Allah bai yi shine Mijinki ba yanzu da lokacin yayi kinga Allah yakawoki wajen Mijinki."


 "Miji kuma Dr?"


 "waye shi?" 

"Kuma ina yake?"

 

"Wani bawan Allah ne gaki kuma zaune gabanshi. 

Dagowa tayi ta kuramai manya idonta zuciyarta na rayamata anya wannan ba tsokanarta yakeba? 

Muryarshi taji yanace idan kingama kallon nawa saiki gayamin ko namiki, da sauri ta sinkuyar da kai tana murmushi


Kije kiyi tunani sannan kiban number ki kinga mutane suna lfy idan kin gama tunanin sa inji ra'ayinki, ga number na kisa ki kirani inga number ki

Wayarta ta ciro tanasa number shi mamaki yake dayaga wayar dake hannunta yanzu ace budurwa kamar wannan tana rike karamar waya haka lallai akwai abun mamaki don irin rawarkai da dogon bari na y'an matan yanzu ba abunda zaisa surike irin wannan wayarda ko chat batayi, lallai abun da mamaki. 


Ringing yaji awayanshi yaga number, 

Yayi svn sannan sukayi sallama. 



*BAYAN WATA UKU* 


hafcy na hango ta cika ta batse kirjinnan ya gama cikowa kamar zai fasa riga ga mazauna masha Allah kamar na kawata (hamebra🙊) 

Duk wacce ta kalleta saita kara tayi kyau sosai na gaban kwatance, 


Sukankaima junansu ziyara aduk garinda suke suma ana kawo musu, kudikam suntara suna fachakarsu son ransu da nera. 



Bilky na hango a kitchen tanata kokarin daura girki tayi kyau ta kara kiba yanzun kam Alhamdulillah 

Komai ya daidaita zama suke naso da kaunar juna. 



Nima inamusu Fatan alkhairi da samun wasu zuri'a masu albarka 



Gidan zeenah na shigo inata zuba sallama amma shuru, kai tsaye daki na nufa tundaga kofa nakejin wani nishi da numfarfashi sama2 ga k'ofa rufe. nace ko lfy? Baradai in leka inga kome kefaruwa ta kasar kofar na hango zeenah zaune kan kujera ta ban kare kamar wata gasassar kaza(😂) 


Hafcy tsugunne sai tsotse gabanta take da harshe tana tura harshenta chan ciki idan ta yi ta sake chanza salo tasa ya tsun hannunta cikin Hq din tana sarrafashi irin tasu ta gwanaye, ita idan tayi ta gaji itama ta koma kujerar zeenah ta jagwal gwalata son ranta, anyi ana tsotse nonuwa ana tsotse bakin juna. 



Idona naga ya fara rufewa da sauri na tashi nayi gaba inata mamaki wai bakinda ke karanta *ALQUR'ANI MAI GIRMAN YAKE ZIKIRI YAKE SALATI GA FIYAYYEN HALITTA YAKE KIRAN TSARKAKAN ABU AMMA YAU SHINE WAJENDA KE FIDDA NAJASA MAI DATTA YA FIDDA FITSARI YA FIDDA JININ AL'ADA YA FIDDA MANIYYI DA SAURAN NAJASA AMMA WAI YAU SHINE AWANNAN WAJE WA'IYAZU BILLAHI

ALLAH MUN TUBA BADON HALINMUBA*


nidai nan nabarsu nayi gaba



Dr. Haseeb dai sun aminta da junansu bayan gama bincike daku bangaren manya sun shiga zancen har ansa ranar aure. 



Ina musu fatan Allah yasa tazame masa sauyi mafi alkhairi 



Zeenah ce rungume da hafcy bayan sun gama tsotse bakin juna ta saketa "tace wallahi zumata jinake kamar kar inje meeting dinnan don dai kawai ba yadda zan yine amma sam banason zuwa 

Hafcy tace kidaure kije kinsan taron jahohine kuma duk shara sau daya akayi idan ba'aga ko daya cikinmuba zasu karbi tara sosai hannunta, 

Inda da isashen lfy ai kinsan ba abunda zai zaunar dani. 

Hakane Allah yabaki lfy kiyi kokarin zuwa ganin dr plss kafin nadawo ki kularmin da kanki barinje kar afara kirana.

Toh sai munyi waya Allah tsare hanya. 




Bayan rabuwarsu

 Hafcy tayi ciki don shiryawa zuwa ganin likita



Zeenah kuma tayi gdn shugabarsu na y'an les dake KADUNA don dukansu anan zasu hadu da katuwar bus dinsu na kun giya da suke tafiya gari gari meeting yau kuma ABUJA suka nufa sai muce Allah kyauta. 



Bayan Hafcy taje asibiti tama dr bayanin damuwarta fatar bakintane yake fidda wasu kananan kuraje ga HQ dinta na mata kaikayi da fidda wani irin ruwa mai wari sannan ga yawan ciwon ciki. 

Test aka bata da kuma scanin taje tayi ta kawomai amsar


Nace Allah yasa ba wata matsalar bace



 *KUDUNDUMO VILLAGE ABUJA*



Wani tamgamemen gd na gani mai kyan gaske manyan motoci sai shiga suke 

Taron matane sosai daga kowace jaha sunzo don gabatar da taronsu


Anci ansha an batse ankuma masu shafe2 juna ana kai, suna tsaka da meeting sukaji wajen nata kairi kafin su ankara hayaki ya gauraye wajen saukuma wuta ya tashi ganga2 kafin su ankara wutar takimmusu kafin kira yan'kwana2 wuta ya cinye wajen tas wani ikon Allah bai tabo gidajen dake kusa dasuba. 


*ALLAH AKBAR*



Labari ya karade kasa gaba daya, Hafcy zaune tana kallon labaran karfe tara a NTA ABUJA aka nuno ajen aikam ba karamin razana tayiba ta kira wayar zeenah shuru kuka take sosai tana Allah jikanku danasani na biku muka tafi tare lallai munyi rashi sosai 


*BAYAN WATANNI UKU*


Hafcy tana zaune abun duniya ya dameta ga ciwon sai damunta yake wani babbar tashin hankalinma allurar datayi na karin hips da breast yanaso ya jamata matsala gaba daya nononta da mazaunanta sun jaruwa sai kumbura suke kamar balo balo haka tasake zuwa taga likita a scanin dinta ya gwada ta kamu da kansar ma haifa sanadiyar yawan wasa da yatsa Cikin HQ



KOGA MACE MAI AURE IDAN MIJINKI NA WASA DA HQ NAKI YANA HAIFAR DA CANCER MAHAIFA YANA DA KYAU KAFIN KU KASANCE TARE YA WANKE HANNUN DA GISHIRI KODAI WANI ABUN MAI KASHE KWAYOYIN CUTA 


MUKULA MATA MUKARE KANMU 

ALLAH KAREMU DA LFYRMU



Bakintama ya kamu da kwayoyin cutar cancer idan ta dage da magani insha Allah za'asamu waraka 

Amma mahaifarta sai an yanke ranar kwana tayi kuka tana dana sanin da baida amfani, gidan da take ciki ta sayar da moto daya ta tattara sauran shirginta tayi gida wato BAUCHI YAKUBU


Tabbas wanda yabar gd gd yabarshi gaba daya garin taga ya chanza mata ta rasa inama zata nufa don tasan bamai karbarta koda cikin dangin tane lallai tayi babban kuskuren, hotel ta kama kafin tasamu gd ta saya kwanta uku tasamu gdn shayarwa ta siya a sabon unguwa bayan filin jirgi bayan ta huta ta nufi gdn tsohuwar kawar harkarta Ummy bayan zuwanta aka sanarmata ai mijin ya saketa sakamakon kamasu suna aikata alfasha da wata kawarta tana gdns yanzun haka tace amta kwnatance

Bayan zuwanta gdnsu Ummy tayi mamakin ganin sauyawarta nan Hafcy ta bata lbrn banyan barinta gd harda ciwon datake fama dashi Ummy T tausaya mata tace itama tayi wannan ciwon saida aka ciremata mahaifa yanzu hakama tanatashan magani amma akwai kashe kudi tace yanzu ta tuba tanata neman gafarar ubangiji yanzu haka akwai wani islamiya datake zuwa hakan nandai suka rabu akan Hafcy zatazo suje gun dr. Dayamata aikin idan yaso itama ayanke mahaifar ta huta




 ✍🏻UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: 😭ADALILIN LINK😭




   WRITTEN BY:

           UMMN YSRH 


EDITOR BY:

       QUEEN MEEMI 


   

     9⃣1⃣TO 1⃣0⃣0⃣


    *GARIN KADUNA*


Wasu y'an mata biyu nagani cikin wata hadaddiyar moto, mai tuka Moton kamar nasanta Sai dai wacce na sani batakai wannan Haskeba. 


Binsu nayi abaya donjin ko suwaye wannan zaratan Matan 


Kofar wani chemist naga sun tsaya duk suka fito suka nufi cikin chemist din, 


Nidai tunani nake duk cikinsu ba wacce tayi kama da Mara lafy amma na gansu dakin Magani kodai Aikensu akayine baradai na kutsa kar ayi bani. 




Wani san k'amemen kato nagani cikin chemist din daga duk kan alamu shike sai da Maganin, daya daga cikinsu tace "oga James kawata na kawo agyaramin ita sunanta Hafsat."


Ido na zaro nakuma kallon wacce aka kira da Hafsat nace dama Hafcyn Haseeb ce ta dawo haka? 

Uhmmmm lallai harka taci uban tada. 



"Tanaso Amata Allurar da kamin na karin hips da breast" 

"angama zeenah indai da kudi komai mai saukine." 



Bayan fitowansu gida suka nufa wani dan madaidaici gida 


idan kashigo daga Gate akwai wajen ajiye Motoci guda biyu sai harabar Gidan dake d'auke da fulawoyi sai kofar shiga Gidan. 


Kana shiga wani falone Madaidaici yasha gyara ga kamshi na tashi ba wani tarkace cikin shi, sai Dakunan kwana 2 ko wanne daukevda bayan Gida cikin shi, sai kitchen da kuma store gidan ya tsaru ba Laifi ga ko ina atsaftace kasancewar mai Gidan Zeenah akwai son tsafta gason kamshi. 



*WAIWAYE ADON TAFIYA*


Bayan barin Hafcy Gida jos ta nufa gdn wata kawar Lalatarta sunkai wata hudu suna tare daga baya suka hadu da zeenah awani grp nasu na y'an les mai suna AJI DADI 


Zeenah karshece wajen les tayi sanadiyar tsunduma mutane da dama, tana harka da matan manyan kasarnan har gd da motoci biyu ta mallaka yar kwalisace ta karshe. 


Tun haduwarsu da hafcy a grp suka kulla  abota har takai hafcy ta kawo mata ziyara akan kwana 2 zatayi gdn zeenah dake kaduna ta koma jos.


Amma sai gata har sati biyu suna morar juna ba lbrn komawa daga baya take sanarda zeenah ta gudu daga gdn mijinta yanzu intabar nan batasan inda zataba.


Tace indai ba matsala tayi zamanta anan tunga lkcn zamanta ya dawo KD anan suke tsula tsiyarsu suke sha'ani da sha'anonuwansu


Nidai inamusu Fatan Allah shirya



✍🏻UMMEEN YUSRAH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: 😭ADALILIN LINK 😭



    WRITTEN BY:

              UMMN YSRH. 


    EDITOR BY:

           QUEEN MEEMI 



       6⃣1⃣TO 7⃣0⃣

Bayan kai Bilky gdnt zaman lfy suke da kaunar juna har Allah ya azurtasuda yara biyu salma da aisha 



Tundaga wannan lokacin kuma halayen Bilky ya sauya ta tsiri yawo gidajen makota wanda hakan ya haifarda mummunan al'amari. 


          

        11:00am  


Dr. Haseeb ne ya shigo gd cikin sauri yadawo daukar mantuwar da yy dakinshi ya shiga ya dauko wasu files da dakardu yafito yaga jaka da takalmi da alama bakuwa sukayi agidan Saidai kuma gdn shuru kamar gdn mutuwa dakin hafsat ya nufa ya murda k'ofar ya shiga


Dasauri naga ya dawo da baya cikin mummunan  yana fadin

 INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U 


Da gudu nima na leka don ganin abunda yasashi rikicewa lokaci daya

Tsabar rudewa har ina  buge dr narasa ina zan dosa harnakai bakin kofa zan fita najuyo naga dr zaune kan kujera nima dawowa nayi na zauna 


        DAKIN HAFCY


Gaba daya hafcy ta gama razana ita kuwa Ummy haushine ya gama kamata don tana tsaka dajin dadi sukaji shigowar mutum gaskiya ya cuceta, juyowa tayi tana kallon hafcy "meye kiketa wani karkarwa kamar mazari don kawai miji ya ganki saiki rude haka Amma Allah sauwake ni mikomin kayana kawai ya ragen jin dadi. 



Idan ya koroki kizo gdn ina maraba dake. 


Falo ta fito ta dauki jakarta da takalminta saidatazo daidai gun dr zata wuce taja wani dogon tsaki kawai kawani ragema mutum jin dadi tasakai tayi waje 



Wayarshi ya dauka ya kira mahaifiyarshi 


Assalamu alaikum 


Umma


Wa'alaikumussalam 


Yanaji muryarka wani iri lfy daiko


Haseeb 


  Ummah ba lfy gani zuwa gidan 


Umma


   Saikazo ka kula da hanya


Tashi yy ya nufi motarshi dagudu nabishi kafin na isa haryaja motarshi, yatsa kawai nake ciza don nasan za'ayi bani. 



Dakin hafcy nasake lekawa naga tanata hada kaya cikin akwati ko ina zata ohho? 


Bayan ta fito wani takarda naga ta ajiye kan kujera tayi hanyar fita saikuma ta tsaya ta karema falon kallo idonta na zubar da hawaye sannan ta juya ta fice bako waiwai


Ko ina hafcy zata Allah masani. 



    GIDAN UMMAN HASEEB 


Haseeb da ummah na gani cikin daki yana kuka yana sanarmata mummunan al'amarin dayagani cikin gdnshi sallalami umma ketayi tana kumawa wannan wacce irin rayuwa hafsat tajefa kanta har tsawon wani lkc ta dauka tana aikata wannan mummunan aikin da ubangiji yayi hani dashi lallai wannan tashin hankali Yakai matuka tayaya hakan ta faru? Yaushe ta jefa rayuwarta cikin sabon ubangiji haka? 

Tabbas umma wannan illar wayace kullum nasiha nakemata kan nacema waya amma bata daukar maganata inajin jita2 hakan a unguwa wasuma har wajen aiki suke samuna suke sanarmin Saidai nakasa daukar mataki akan hakan Tabbas umma nayi sake, magana yake yana kuka 


Katashi muje chan gdn naka 

Barinsa rahma ta dauko su sabeer daga mkrnt 



Bayan isarsu gdn falo umma ta zauna tace ya shiga ya kirota 


Tunda ya nufi kofarta gabanshi ke faduwa yanaga kamar zai kuma karo da abunda yagani d'azun, tundaga kofa ya fara karo da kaya gaba daya dakin ahar gitse bakowa ciki ya leka bayi ba kowa ciki da karfi yace ummmmmma! 


Haf haf haf kawai yazube kasa da gudu umma tashigo warwas taganshi akasa da alamar dakin ba kowa gashi kaca2 isa tayi gashi tana jijjigashi innah ba alamar numfashi da sauri ta koma falo ta dau wayarta ta danna kiran khamees abokin haseeb yana dagawa tace kazo gdn abokinka yanzu2 bako jiran amsa ta katse wayar ruwa ta dauko mai sanyi ta yayyafamar amma ko motsi baiba



Khamees da sauri ya fito daga office nashi ga tarin mutane suna layi amma haka ya wuce don baisan dalilin kiran da akamaiba cikin gaggawa haka bayan ko awa basuyiba da rabuwa da amininshi 

Allah dai yasa lfy 


Bayan isowarshi kai tsaye ya wuce cikin gdn Saidai kamar ba mutane sallama yy daga ciki umma tace ya shigo kwance yaga amininshi ba alamar numfashi atare dashi da sauri ya isa gareshi yana tambayar umma ko lfy 

Umma na kuka tanacewa ba lfy khamees dubamin abokinka 


Nan yashiga aikinsu na likitoti kusan minti 20 kafin yasamu ya dawo allurar bcc yamai sannan suka koma falo shida umma 

Umma lfy kuwa naga haseeb cikin wannan munnanan yanayi bayan lfy muka rabu yazo gida daukar wasu files sai kuma inzo ingashi haka, Sannan kuma ina hafsat? 


Khamees inafa lfy hafsat ta gudu bayan tabka mummunan aiki 


Take gabanshi yafara bugawa kardai yau sunyi karo da mummunan aikinda matar amininshi ke akatawa? 


Ummah don Allah sanar dani maiyafaru kardai yau haseeb yaci karo da abunda matarshi take aikatawa


Juyowa umma tayi tana kallonshi 


Dama kasanine? 


Eh umma munyi mgnr ko jiya da haseeb 

Akwai wata mata unguwar mu kowa yasan kazamin aikin da take aikatawa sunanta Ummy tayi sanadiyar lalacewar mutane da dama sai kuma naga hafsat ta fara mu'amala da matar sau uku ina ganinta tana zuwa tunda nakamata na ukun na nacemata saina sanarda mujinta sai tace ba wani abu tsakaninsu kaya kawai take saya wajenta 

Munyi mgn da haseeb akan duk sanda na kuma ganinta in kirashi awaya zaizo har wajen ya tabbatarda gaskiyar lamarin. 


Umma tace ikon Allah ashe ta dade cikin lamarin Allah ya shiyeta da duk y'an uwanta masu wannan hali gari guda Allah ya halakar saboda irin wannan zunubin sai kuma gashi yanzun yazamo mana tamkar abun arziki Allah yabarmu da halinmu muyi dukkan abunda mukaso 

Shiyasa dole zamuyita karo da jarabawar rayuwa iri iri tunda bamu maida sabon Allah kimaiba 


ALLAH MUNTUBA BADON HALAYENMUBA


ALLAH KATSAREMU KA TSAREMANA IMANINMU ALLAH KARKABARMU DA IYAWARU


ALLAH KAMANA JAGORA ARAYUWARMU KA KAREMU DA FADAWA HANYAR SABA MAKA



nan umma ta kwashe komai ta fadamishi


Umma toh yanzu ina zamu nemota 


Babu tunda rayuwar data zaba kenan Saidai mumata Fatan shiriya ai ba korarta mukayiba ita ta kori kanta don haka taje duniyace wanda baizobama tana jiranshi




  ✍🏻UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK😭



  WRITTEN BY:

        _UMMN YSRH_


   EDITOR BY:

      _QUEEN MIEEMI_


_masoya wannan labari ina muku Fatan alkhairi nagode sosai da adu'o'inku Allah yabar zumunci, Darasin dake ciki Allah bamu ikon ammafi dashi👏🏻_



    1⃣1⃣1⃣TO1⃣2⃣0⃣


ALHAMDULILLAH 


 Anyi auren tafisu fa Dr. Hasseb Sabeer da Sabeerah sundawo Gidan sun, sosai take basu kulawa. 


Soyayya mai tsafta da mutunta juna suke ita da Dr.  Allah bada zaman lfy da zuri'a masu albarka 




Yautake suna Allah ya azurtaki Bilky  da samun da namiji yaci sunan Babbn Abbansu Salma Abdullahi (abul khair) 

Allah raya Abul da imani




_Bayan kwana biyu_


Ummy tazo Gidann Hafsat don tafiya Asibiti, sanda taga Hafcy ta mugun tausayamata ayadda taganta.


Gaba daya Nonon ta da mazaunanta (duwai) sun kara kumbura ga Nonon ta wani gefen ya dan bule har wani ruwa yana zuba. 


(Allah sarki Hafcy taban tausayi) 



"Nikam wani Asibiti zamunee? 


_TEACHING HOSPITAL_

zamuje

 

Wani Mummunan Fad'uwar gaba taji da aka Ambaci sunan bata Fatan ta had'u da wanda ta sani a wajen. 

Bayan isarsu sun bud'e File sunga Dr. Sanda yaga yadda Nonuwanta da duwais dinta suka kumbura sukaja ruwa Masifa ya rinka mata, 


"waiku mata meke damunku har yanzun ba zaku rinka kare kanku da Lafiyar kuba? Kun san Allurar nan nada illah sosai takan Jawo Cancer da zai sa ayanke wa Mutum wasu sassa na Jikinshi.


 Idan kuma hakan ta faru zaiyi wuya ya rayu." 


Yabata Magunguna na sati guda tasha ta dawo acire mahaifar bakin kuma idan kin kula dashan magani insha Allahu zai warke. 


_kalubale garemu mata masu amfani da allura ko maganin karin mazaune, kusani kuna siyan cuta ma kanku da hannunku, dukfa abun don maza muke inda tunani_


_Meyasa su mazan basayi?_


_Mudin bamason Mugansu da kyakkyawar sura?_


_Meyasa bama hakuri da halittar da Allah ya mana?_


_Wai maza dama don surar jikinmu suke sonmu ko don Allah?_


      _Amsa gareku_



      _BAYAN SATI DAYA_



Magani yayi amfani don ruwan duk ya tsiyaye sai kadan ya rage shima ana Fatan Tsotse warshi gaba d'aya bayan zuwanta Asibiti Likita yaga anyi Nasara zuwa Gobe Talata insha Allah za'a mata aiki


Anyi aiki cikin nasara kwananta uku aka sallameta 


Tana ta Godiya da Allah baisa ta haduda Abbansu Sabeer ba. 



Shiko yana gida yadau Hutu. 


Bayan Sallamanta Dr yabata sati biyu ta sake dawowa adubata.



Yanzu kam Alhamdulilla Hafcy tasami lfy Sai dai wani abun mamaki sanda naganta nakasa tantace war macece ko Namiji don kirjinnan kamar Lamusha shshen silifas bayan nan kuwa kamar an shafe. 


_ikon Allah kamar ba hafcy mai cikakkiyar halittaba_


Yanzu kam gaba d'aya hankalinta ya koma gida tana bukatar neman gafarar iyayenta ga uwa uba m/Mijinta. 



_BAYAN SATI BIYU_


Ta dawo ganin Likita 

suna layi likitan ya fito da sauri ya basu hakurin yau bazai sami ganin suba anmar waya yanzu Mahaifiyarshi ta rasu suyi hakuri yama abokin Aikinshi waya insha Allah yanzu zai karaso ya dubasu, sun mai ta'aziya tareda adu'ar Allah gafarta mata. 


_bayan minti shabiyar_

Haka kawai hafcy taji gabanta yanata faduwa tarasa ko meye dalilin, 

DR. Hasseeb ne ya iso tare da wasu ma'akata biye abayanshi, jitayi mata suna yawwa ga likita ya iso d'agowa tayi don ganin waye Likita don daga duk-kan alamu k'warrarene  kuma Mata sunajin dadin aikin shi don naga duk sun rud'e da murna, dagowar da zatayi taga DR. HASSEEB yakara kiba ya kara haske kamar bashiba daga duk-kan alamu yana cikin kwanciyar hankali sauri tayi ta sunkuyar da idantayi don karma ya ganta. 


Bayan ya wucesu taji matan dake jefe wata tace "kai nifa likitannan ba karamin Burgeni yakeba, da zai auren ai dana huta Sai dai nasan yafi karfina. 


" hhhhhhhhhhhhhh! Tab mezai dake watan data wuce yayi aure idan kinga Matarshi karshece wajen kyau 


Wata agefe tace"aini uwargidashi tayi Babbar asara irin wannan mazan yaushe zan Samesu in gujeka aiko dukana kake zan zauna wallahi." 


"saketa yayine? 


"Aah guduwa tayi daga gida sabida tabiyema rudin shaidan yasa ta jefa kanta cikin kazamin harka adalilin waya ta fada harkar lesbian(madigo) ADALILIN LINK .

Ta jefa kanta Mummunan rayuwa ."


Gaba daya wajen sukace "WAYA!" 


Lallai taga illar waya Allah karemu ya tsaremu da dukkan musulmai baki daya sukuma Allah shiryesu yasa sugane gaskiya, 


Gaba daya taji zaman wajen ya gagareta ga file dinta yana ciki haka ta tashi ta gudu ta hakura da ganin likitan


Cikin kwarewa na manyan likitoci masana aikinsu ya duba mutan file din mutum daya yarage anyita kira batanan harsun gaji gashi yanason komawa gun amarya.

yacewa mai kiran sunan yarabuda ita maiyuwa bata damu bane. 

Har  ya ajiye file din yace ya mikimai ya gani, ko sunan bai dubaba yafar duba matsalar ciki ya tausaya wa mai ciwon ya duba sunan ai take gabanshi ya fadi ya mai 2 ta sunan hafsat

 INNALILLAHIWA'INNA'ILAIHIRRAJI'U 

Lallai kinga saka mako tun aduniya 


Tun bayan komawanta gida kuka tawuni tanayi na nadama da nasani tayi alkawain da safe zataje gdns ta nemi gafarar iyayenta da kuma mijinta


_nace adakenan yan zukam na tafeesune_


Tana kwance cikin dare barayi suka kawo mata farmaki saida suka yasheta tas sukayi gaba 


_dama kudin haramne_


Gari na wayewa ta nufi gidansu gabanta sai fadi yake sallama tayi tashiga matar babanta tagane tsakar gdn kasancewar uwarta tun tana karama ta rasu.

Salati take tare da hamdala tana kiran malam kazo yau Allah ya amshi addu'armu ga diyata ta dawo, yana zaune daki yana lazimi bai tasoba hannunta tazo taja sukayi dakin. 

Bako dago idoba balle ya kalleta duk da azuciyarashi sai hamdala yake da Allah yadawo da ita gd 


Har gabanshi ta iso tana kuka tana neman gafararshi


"ai kobance komaiba hafsatu nasan duniya ta horaki Tunda ga yadda kika dawo, tabbas DUNIYA TAFI GABARUWA IYA JIMA 


DUNIYA MAKARANTANE 


kinshigeta kinga yadda take kinkuma koyi darasi nayafe miki saura yarage gareki da ubangiji 


Nasiha yayita mata yace idan ankwana biyu zasuje dashi ta nemi gafarar tsohon mijinta don da kanshi yasa ya rubuta takardan sakinta ya bashi. 


Ranar asabar bban hafsat yasata gaba sai gdn umman Haseeb 

Umma tayi mamakin ganin hafsat yadda ta koma akayima Haseeb waya yataho da iyalanshi duka


Bayan haduwarsu baban hafsat yace ya kawotane tana neman gafararsu musamman mijinta

Tana kuka tana neman gafararsu saidata basu tausayi duk sun yafe mata umma ta mata fada sosai da nasiha sunyi gdy suka koma gd haka rayuwarta ta kasance ganta aka saida akabada sadakar kudin 

Duk sati ana kawo mata yaranta sunakuma zumunci da TAFEESU 

Saimuce Allah kara shiryar damu yasa mufi karfin zuciyar mu 


_gareku masu hali irin na hafsat yanzun dai basai kamutuba kake ganin sakamako tun aduniya Allah take fara nuna mana_


ALHAMDULILLAH 

_nan nakawo karshe wannan takaitaccen labari_


_kuskuren danayi Allah yafeni_


  _godiya ga dukkan masoyan wannan novel din ina alfahari daku_


_GODIYA GAREKU_


_UMMN YSRH HAUSA NOVEL GROUP 1&2_


_YESMEEN TAFEESU NOVEL'S GROUP_


_MERMUE NOVEL GROUP_


_QUEEN MIEEMI NOVEL GROUP_


_RASH KARDAM NOVEL GROUP_


_FHAREEDAT MUSA NOVEL GROUP_


_MUSADA ZUMUNCI MATAN BAUCHI_


_DUK DANAKE CIKI INA GDY DON YAWANKU YAFI KARFIN LISSAFI SAI GDY DA FATAN ALKHAIRI GAREKU ALLAH BAR ZUMUNCI ALLAH HADAMU FUSKOKINMU GDN ALJANNAH_


_INA ALFAHARI DAKU MARUBUTANMU NA BAUCHI ALLAH KARA MUKU BASEERAH DA HAZAKA DA KWARIN IDO DA ZAKIN HANNU_


_RASH KARDAM_

_AISHA GANA_

_FHAREEDAT MUSA_

_BINAXIR OMAR_

_SAKEENAH SALIS AL_EEMAM_


_FATAN ALKHAIRI GA DUKKAN MARUBUTANMU ALLAH KARA DAUKAKAMANAKU_


_ALLAH BAKU HAKURI DA JURIYA_


_ALLAH KARAMUKU ILMI MAI AMFANI_


_ALLAH KARA BASEERAH DA HAZAKA DA KWARIN IDO DA ZAKIN HANNU_


_BISSALAM_


              _NABARKU CIKIN AMINCI DA KAUNAR JUNA 

  

 ✍🏻UMMN YSRH

[02/05, 6:00 a.m.] Zeee Bello: . 😭ADALILIN LINK 😭



     WRITTEN BY:

             UMMN YSRH 


      

 EDITOR BY:  

          QUEEN MEEMI 

        

         7⃣1⃣ TO 8⃣0⃣


Wanjen k'arfe hudu Haseeb ya farka Sai dai harya fad'a Lokc guda, wanka yayi Sallah kadan ya iya cin Abinci shima don Umma ta Matsamai ne. 


Hakuri tayi ta bashi da kuma Nasiha san nnan ya tayima Hafsat Addu'ar Alkhairi da fatan Allah shiryar da ita ya dawo da ita lfy."


Khamees yaje gidan Ummy ko gidan taje ba'asa metaba anje 

Gidansu nan ma batanan,



 Sallama suka ji daga waje bayan sun amsa suka bada izinin A shigo.

Wani dattijone ya shigo da Ganinshi akwai dattako da Nagarta tare dashi, yana shigowa  Naga Haseeb ya sauka y koma kasa. 



Bayan yasami waje ya zauna suka gaisa da Umma sannan Haseeb ya Gaida shi, 


Malam Usman kenan Mahaifi ga Hafsat 

"Yace dazu na dawo gida ake sanar min da wani Mummunan Al'amari 

Shine nazo don inji Gaskiyar Lamarin." 


Ummace tabashi lbrn komai 


Hakuri yata basu tareda nasiha sosai ma Haseeb insha Allah zansa ayi cigiyarta Gidajen 'yan uwa, yanzu ka haifi Mutum ne baka Haifi halinshi ba k"arshen Duniyace tazo Masifu iri_iri an maida 

Zina, Luwadi, tamkar abun Burgewa ba komai bane yanzu don Mutum ya kashe d'an'uwanshi ya cire sassan Jikinshi yayi wasu sidda barun, ba komai bane Agaremu mun riga mun d'au son Duniya mun d'aurama kan mu ko kad'an mun mata da Ranar Hisabi, mun d'orama Ranmu zamu raya idan munso zakuma mu kashe idan Nunso mun manta da Allah Mun maida wasu kas kantattun bayi sune masu biya mana bukatunmu Matanmu da Mazanmu mun maida Bokaye tamkar sune abun biyan bukatunmu."


Shin wai akwai abunda wani bawa zai ma wanda yafi kanema gurin Mahaliccin kane?" Inda suna Azurtawa meyasa koda yaushe suke acikin k'as k'anci duk randa muka taka kafa wajen wani Boka munyi Babban shirkane Sallarmu na kwana 40 babu karb'ar shi."


kullum fad'akar damu ake Amma shedan sai buga Gangarsa yake akan mu Allah kuma ya barmu da iyawarmu ya barmu da halinmu Gamu ga Duniyar muyi duk abunda mukeso karshenta kasa zamu koma zakuma muje mu tararda ubangijimu Allah ka yafemu." 


Hakuri yata basu da nasiha sannan ya musu sallama ya tafi, 



Duk inda ake zaton samun hafcy anduba ba ita ba lbrnt, wayartama bata shiga haka aka hakura. 



Yau kwana ukun salma, mama suna zaune da wata y'ar uwansu ta kalli Bilky tace cabdin! 

Lallai hadiza yarki Allah ya kareta, akwai sihiri atare da ita, 

Gaba daya dakin aka dau salati. 


Da anso akadata ta shiga duniya saikuma Allah ya takaita insha Allah zan bata magani komai zai dai2 indai tamaida hankali kan maganin, 

Mama hadiza tace magani ai yazama dole. 


Mama hadiza da umma lami da abbansu salma suna zaune daki ana bashi labarin abunda yake faruwa, mama lami tace akwai wacce kuka taba nema da ita sama da shekara uku ko? 

Dogon tunani yayi sannan yace tabbas akwai wata mai kawo abinci gidan block dinmu taso na aureta amma naki nace mata  banda bukatar karin mata tundaga lokacin ta fita harkata daga bayama tabar kawo abinci wajen mu andau lkc mai tsawo wani rana da yamma tazo ta kawo mana katin aurenta, cikin katin databan naga wani guntun takarda ciki ta rubuta in Allah ya yadda shida zaman lfy da matata sai alahira lkcn bandau zancen da muhimmaciba ashe rashin zaman lfyr kenan. 


Umma lami tace da sunso haukatar da itane saikuma abun yazo da sauki ta tsani zaman gidan, amma insha Allah za'asami waraka muna sake da addu'o'in neman tsari da kariya daga dukkan abunki muna sake da yawan ibada da yawan sadaka, Allah kara karemu 


      Ameen 👏🏻



✍🏻UMMEEN YUSRAH

0 Response to "Adalilin Link Hausa Novel"

Post a Comment