-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Za'a fita neman jinjirin watan gobe Juma'a

Za'a fita neman jinjirin watan gobe Juma'a

Za'a fita neman jinjirin watan gobe Juma'a



Za'a fita neman jinjirin watan Zhul-Hijja a kasar Saudiyya ranar Juma'a, 29 ga Dhul Qa'adah 1442 bisa kalandan Ummul Qura, wanda yayi daidai da ranar 9 ga Yuli, 2021, rahoton Haramain Sharifain.

Duba watan Zhul-Hajji ne zai bayyana ranakun Hajji ga Mahajjata da kuma Sallar Layya ga sauran al'ummar Musulmai a fadin duniya.

Za'a yi duban watan na farko ne a jami'ar Al Majmah dake Sudair, yayinda za'a sake dubawa a Tumair da kuma sauran wurare.

Kotun Kolin Saudiyya ce zata sanar da sakamakon gani ko rashin ganin watan da yammacin ranar Juma'a

Source: Legit

0 Response to "Za'a fita neman jinjirin watan gobe Juma'a"

Post a Comment