-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

WACECE ITA Hausa Novel

WACECE ITA Hausa Novel

 



WACE CE ITA MARUBUCIYA HAUWA

M.JABO

By Hauwa jabo 15:44 3 comments

[3:43AM, 4/25/2015] .: WAC CE ITA..?? 1 1⃣

Na Hauwa M. Jabo

Kiyi sauri ki sauko maigadi ya kusa zuwafa,

Daga saman icen wata siriyiyar yarinya kamar

bulala da qarfi tace mangoro nawa na tsinko?

Daga gefen wata yar lukutar yarinya tace guda 8

ne Amma uku basu nunaba. Yarinyar da take

saman ice tace yauwa.. haka naga ta diro

kaman biri daga saman iccen ni jabo da naje

gano muke WACE CE ITA? saida na firgita mace

haka ba tsoro na kalli bishiyar naga tsawonta

abinda yafi bani mamaki ya akayi ta hau bishiyar

ba tsani.? Kamin in waigo sai kawai na hangota

saman dayan bishiyar har ta Dane bishiyar, ta

fara tsunko gwaiba tana wurgowa qasa

qawayenta suna cabewa, da gani wayannan

yaran taqdiraine waima ya take hawan bishiyar

ba tsani?? Yau sai na kakkaryaku Dan

ubanninku! Matsiyata..!! Muryar wani dan tsoho

naji da alama shine mai gadin wurin Iffatu sauko

baba shehu.!! baba Shehu!! Haka suke fada

suna ihu, Timmm naji Abu siririyar yarinyar ta

fado na tsorata Dan na dauka ta karye Amma

inaaaa tana fadowa qasa ta dauki dayar gwaibar

ta basu daukaba ta filfila har ta wucesu koda ta

iso bakin qofar gonar taga baba Shehu ya kulle

qofa tashin hankali..... Kunsan baba Shehu ya

kulle qofa dole zamu tsallaka ne kamin yazo,

tana fada jikinsu na rawa, ke dijee kulllum ke

kike bamu matsala wallahi bazaki qara biyomuba

gashi ke baki iya gudu sabida shegun duwawun

nan naki. Mtswwww... Kuzo mubi ta chan ginin

yafi gajarta. Suka kwasa a guje suka samu suka

tsallakar da dije da yake ita rukayya irin ippatu

CE ba auki da kanta ta tsallaka duk da haka sai

da iffatu ta taimakamata. Juyowan da ippatu

zatayo ta hango baba shehu da gudunsa ya

kusa kawowa gurinta, ya wurgo mata sandarshi

amma bai sametaba, da yake gurgune sai ta

yanka a guje kamar fanka fil fil da ita, gurin ginin

yafi tsawo dama, na yanda ta iya baba Shehu

zai iya kamata, tana nisa dashi,taja baya sosai

tazo a guje sai kawai ta dane ginin saida ta hau

ta waigo tayiwa baba shehu gwalooo sannan ta

dira a qasa......

WACE CE ITA..?? 22⃣

Na Hauwa M. Jabo

Tana dirowq dijee rukayya kozo nan ta basu

umurni. Sukazo ina mangurona da gwaibata ?

Taki ko tamu inji dijee, ta wani harereta itama

dijee ta harereta ta jajayen idonta gasu qanana

itadai rukayya batace dasu komaiba tayi tsaye

dama sune hatsabiban dije da ippatu.

Ippatu ta rufe ido cikin tsiwa, abani kayana

kamin in lissafa uku. Ta fara lissafi daya biyu

uku itadai rukayya ta miqaa mata kayanta dijee

ko ta sakasu a Dan kwali ta gulle taci damara

da Dan kwalin. Bude idon ippatu ta kwashe dije

da mari dama sun saba. Suka fara danbe aka

tima dije a qasa dama batada qarfi sai rashin

kunya, dagyar rukayya ta rabasu Amma duk

manguron da gwaibar sun turmuje a qasa sai

guda biyu da gwaiba hudu suka rage. Ko

wannen su na fitarda numfashi daddaya. Amma

fa dije anji ji jiki kusan kullum sai sunyi dambe

da dijee Dan dukansu basuda kunya kuma

basuda haqurin juna gashi basu iya rabuwa da

juna.! Gamon jini da hali ita rukayya batada fada

biye take dasu kamar raqumi da akala duk yanda

akayi da ita chan takeyi. Ippatu ta baiwa

rukayya mangoro daya gwaiba daya ta riqe

mangoro daya gwaiba uku kaji adalci irin na

ippatu dije kuwa tahau tsini Dan bata bata

komaiba. Ta daure fuska muninta ya qara fitowa,

Sunkama hanya ana gaba da juna kowacce tabi

hanyarta ippatu na tafe tana shan magoro da

gwaibarta, Bala'eeeee wallahi ga bello mai kifi

chan, inji rukayya, Habawa baima hangosuba

Amma tuni sun yanki ticket suka fara gudu ba

tsayawa basu tsayaba saida suka daina

hangoshi suka fara dariya. Kamar basune sukayi

danbeba har sun shirya. Ippatu tana dariya tace

dijee kin tuna faduwar da bello mai kifi yayi suka

qara kwashewa da dariya suka tafa ai ranar

saida ya bani tausayi habadai, wallahi baibani

tausayiba kifinsa bala'en tsada sai shegen dadi

inji dijee, Dan yaga ana saye yake yiwa mutane

yanga. Shegiyarda sukamai saida ya qare suyar

kifi ya jera akan tire zaije talla kawai sukayo

tsokana aka biyosu suka zo a guje suka barar

mai da kifi kuma sukabi takai suka wuce ko

waigowa basuyiba shiko bello mai kifi dan jaraba

maimakon ya tsaya kwashe Dan kifinsa sai

kawai ya biyosu a guje, garin binsu ya fadi a

qasa ya huge bakinsa, sukam tuni suka bace

mai ko mai lafiya baya iya kamasu idan suna

gudu bare bello mai kifi daya tsufa. Dan ko dijee

bai mangalar duwawu idan ta saki qafa ba dama

bare rukayya mai kamar bulala, Nidai Jabo

bantaba ganin gyauyawa kuma Yan iskan yara,

marasa kunya ga tsokana da rashin tsoro irin

wayannan yaranba dije da ippatu ba, Dan ita

rukayya yar kallo ce sai zugasu da takeyi idan

sun samo su sammata ko ta musu gadi suyi

abinda zasuyi.

Suna dariya suna tafawa abinsu har suka iso

gida sai lokacin ippatu ta tuna da aikenta akayi

sayen daddawa da manja, ko shakka babu ta

xubar da kudin, ta kwance Dan kwalinta data

daure kudin amma ina tuni sun fadi, zakuwa

tashi qaniyarta idan ta koma ba daddawar nan

da manja ga uban shiririritan da tayi..

Maimakon ta shiga gida sai kawai ta kama

hanya tana tafe tana tunanin yanda zatayi da

saqon googo, kicibis taci karo da wasu yara

suna fada ta tsaya kallo suma aikensu akayi sai

taga sun yarda kidi naira ashirin da biyar ta

dauke ta qulle a habar zaninta. Yau wace rana

ippatu taga fada bata tsaya sayen fadanba da

walakin. Taje ta siyo manjanta na goma

daddawan biyar ta siyo kan kifi na biyar tana

tafe tanaci har taje ta dawo suna fada fadan

yanzu kuma na an sace kudin dayane ta

kyalkyale da dariya iron ta mugunta ta wuce

abinta.....

WACE CE ITA..?? 3 3⃣

Na Hauwa M. Jabo.

Ta wuce abinta koda taje gida ta rasa yanda

zatayi ta shiga Gidan ta fara labe labe. Ubanme

kikeyi anan ??muryar babanta taji ya mata

tsawa saida hanjin cikinta suka juya duk duniya

babanta kawai take tsoro ta fara kame kame,

bakomai baba sannu da zuwa. To wuce gida

munafukar banza ya tasa qeyarta suka shiga.

Malam ina ka tsintomin ippatu? wallahi tun

qarfe biyu na aiketa Dan nasan halinta

batadawoba sai yanxu, kaga har na qare tuwo!

Dan ubanki ina kikaje? Ta fashe da kuka wallahi

baba sai bayan la'asar ta aikeni ko minti uku

banyiba na dawo. LA ilaha illallahu Muhammadu

rasulillahi... Ihhatu "haka take kiranta Dan bata

iya sunan ba" kina nufin qarya zan miki? Kinma

saba bani kayana ta qwace manjanta da

daddawarta, baba ya juyo ya kalleta ina kika

samu kifi sai qarnin kifi kikeyi. Ta fuske kamar

gaske gidan su kulu mai daddawa suka

sammini.! Na dauka kin qara tsokano bello mai

kifine. Aah wallahi baba.!! Idan ta tashi zama ta

Allah sai ki rantse da Allah ba ita bace take

taqdiranci a hanyaba kamar wata waliyiya har

ma dai gaban babanta.....

*********************

Ippatu yarinyace yar kimanin shekara 11 duk

yanda zan muku bayanin ta idan dai ba ta muku

taqdiranci nata kungani da idonkuba ba zaku

gane WACE CE ITA ba, Sabida batada kunya,

batada tsoro ba tada ladabi ba tada mantuwa ba

yafiya haka take wata hargitsatsiyar yarinya da

ita. Gata qazama taqin qarawa, batasan

tsabtaba ko kadan haka batasan wankaba bare

wanki farace Amma yanxu tafi zainb khalifa baqi,

haqoranta Dan rashin wankewa har sunyi tsatsa

daga sama, daga qasa kuwa kamar an kwaba

laka an shafa mata idonta kuwa gasu Manya

Manya Amma sunyi jaa kamar na sister khade

qafar nan kuwa duk tayi wani iri Allah ne ya

tsareta qafar bata Faso da tuni ta farfashe Dan

su dijee tuni qafafunsu sun yayyage da Faso,

bata yawo da takalmi, a cewarta takalmi basa

barinta gudu. Mahaifiyarta sun rabu da

mahaifinta tun tanada shekara 6 tanada yayye

guda biyu maza duk mamansu daya, suna gurin

mamansu, itama babansu yaje gun mamar ne

akan dai ta bashi yayanshi, ta hana, dazai dawo

ippatu ta maqalemasa ya dauketa ba da son ran

mamarba, tana zaune gun kishiyar mamanta

gwagwo rabi, gwagwo batason ippatu ko kadan

ita kuwa ippatu ba abinda ya dameta harkar

gabanta take bata damu da asotaba kuma

gwagwo rabi duk abinda zata mata saita rama

cox bata mantuwa bata yafiya.! Shiyasa

hankalinta kwance bata tsoron kowa duk

qauyensu sai babanta kuma bata ragawa kowa

duk qauyen nan. An sakata makarantar boko har

uku ana korota sabida uban yara da takeci, a

makarantar allo ma Dan yana maqocinsune da

tini ya korota ippatu kenan....

WACE CE ITA..?? 4 4⃣

Na Hauwa M. Jabo

************

Ta dauki allo na tafi makaranta, gwaggo ko

kallonta batayiba Dan tasan ba makaranta

zatajeba wacce batason makaranta zata fita tun

qarfe biyu, za'a gurin jarabadai, allonta har

rubutun ya goge dan tsabar rashin zuwa

makaranta da takeyi tana fita taje bayan qyaure

ta boye allon ta sa mai bata tsayaba sai gidan

su dijee da yake dijee da rukayya gida daya suke

dagyar suka samu suka sulalo suka fito. Suna

tafe suna tadi duk yaran garin har Manya

tsoronsu suke dan basu bar kowaba, idan

babbane ya daki daya taron dangi sukemai ko

suyita jifarsa da duwatsu, basu tsaya ko inaba

sai rafi suna zuwa suka tube dagasu sai qajeren

wando rukayya dai ta fara girgar dangi dija ma

ya kunmo kai Amma basu kunyar kowa suka

fada ruwa sukayi iyo sosai kaman kifaye sun iya

ruwa kaman me suna ruwa suka hango baba

shehu mai gadi shima ya hangosu sunsan kamin

su fito ya iso sai dijee tace kar mu gudu idan

yashigo kamamu mu bashi ruwa mu danneshi a

ruwa.! Sun haqamai gadan zare, Baba shehu

dayazo sai yaqi shiga kaman yasan abinda suka

fada, ya kame guri daya kamar bai gansuba,

sukayi jira har suka gaji Amma yaqi tafiya sai

kawai suka yi shawara akan su nutse su tafi

chan nesa dashi su fito. Suka nutse a ruwa,

baka ganin tafiyarsu, saida sukayi tafiya mai

nisa sannan suka fito suka lallabo suka zagayo

suka saka tufafin su suka nufi gona satar

mangoro shiko baba shehu yanachan yana jiran

fitowarsu daga nutsewar da sukayi yaji shiru sai

abin ya bashi tsoro kardai ya kashe yayan

mutane!!! Tuni ya fada ruwan ya shiga lalube

Amma basu ba labarin su chan ya hangosu suna

gudu sun ciko zaninsu da mangoro da gwaiba

yau hadda lemu da basu cika diva ba sun debo.

Tsoro ya kama baba maigadi daganan baba

shehu mai gadi ya sallama cewa ba mutane

bane aljanun dajine ko Yan ruwa suke

addabarshi, dole ya nemo tsari karsu hallakashi.

Da sauri ya fito ruwan saida sukaxo Dan kusa

dashi suka kwashe da dariya sannan suka mai

gwalo suka gudu. Kaji hatsabibai....

*****

Tun daga ranar baba maigadi bai qara binsuba,

hasali ko kallonsu baiyayi idan suna abinsu, da

suka gane ya saka musu Idone sai suka maida

abin Sana'a kullum zasuje su debo sai suje su

wanke suje talla da sukaga basa ciniki sabida

baqin halinsu sai suka riqa daurawa rukayya

tallar rukayya kuwa akwai farin jinin talla, talla

ta karbeta nan danan suke saidawa gurin rabon

kudi suyita bala'e da danbe. Ba ranar da basa

fada kuma aranar suke shiryawa,.....

[4:50PM, 4/26/2015] .: CHI GABA....

WACE CE ITA..?? 5

Na Hauwa M. Jabo

********************

Yauma kamar kullum yan matan uku dije ippatu

da rukayya suna tafe suna labari suna shewa da

dariya da gani dai kasan basu da kamun kai

bare uwa uba tarbiya, laaaaaaaa dije kalli

malan garba da ya dakemu ranar.! suka waiga

gaba dayansu suka kalleshi, ippatu tayi tsaki

share shi mugun banza, dijee ta kalli ippatu

bazamu share shi ba,yakamata mu rama, mi

zamu masa mu rama kalli fa har yanxu tabon

bulalanshi, ta nuna hannunta, kawai mu

ramako ? Eh mu rama, Suka fara shawara

sharrin da zasuyiwa Dan saurayin malamin

makarantar allonsu, yayo wankansa na juma'a

zashi masallaci sallar juma'a baima kula

dasuba. har sun hada sharrin da zasuyi tunda

nanne hanyar sa kamin ya dawo daga masallaci,

sun nemi toka ta murhu sukaje Gidan da ake

daka taba gari irin wannan da tsofafi suke

sakawa a qasan lebonsu, suka siyo ta ashirin

suka siyo garin barkono na goma suka hada guri

daya suka ijiye suka samo bokoti daya suka

debo ruwan kwata mai shegen wari suka je

suka samo kashin shahu sabo suka kwaba da

kwatar nan suka labe gefen hanya, ippatu ta

dane bishiya kamar biranya, da bokitin kwatar ta

da suka dama da ruwan kashi, malam garba na

bullowa shida dije ta watso mai garin tokar

daidai fuskarshi, da suka yiwa hadi ita, ita kuma

ippatu ta watsomai ruwan kwatar daga saman

bishiya, daga kansa har qasa ta diro gasa suka

waske, idon malami sun cika da yaji ya sai ihu

yake yana Neman dauki,yana murxawa ga ruwan

wari a saman kanshi kamin mutane suji ihunsa

tuni sun gudu gidajensu. Kuma ba Wanda ya

gansu Amma sabida hatsabibancinsu duk Wanda

ya sami labari sai yace hatman aikinsu ne sun

koma gida duk ranar ba Wanda ya fita cikinsu,

wayanda tun safe idan sun fita gantali basa

dawowa sai guraren yamma shima Dan sunsan

idan sunyi dare akwai samarin da zasu

hallakasune shiyasa duk la'anarsu da dibar

albarkarsu basa fita gida da dare.

Ina ippatu? tana daki, Malam lafiya kashigo a

hargitse?? Inafa lafiya yarinya tana son tasa

xaman qauye nan ya gagareni..

Ke ippatu.!! Na'am baba, zonan mara kunya

yarinya, ku ne kuka jiqe Malam garba da ruwan

kwata kuma kuka zuba masa barkono a Ido ko??

LA ilaha illallahu Muhammad rasullullahi wallahi

tana taba hannu tana salati kaman gaske,

wallahi baba ka tambayi gwagwo yau duk ban

fita koda zaureba, Dan banida lafiya, ko goggo,??

to ubanwa zai masa wannan ta'addancin idan

bakuba gashichan ido sai Allah, kuma yace bazai

barwa Allah ba.

Salamu alaikum. Daga waje sukaji sallama koda

baba ya fito saiga yan sanda biyu an kamo dije

da rukayya akazo a tafi dani, ina kuka ina kiran

baba, amma saida yan sanda suka tafi damu

police station..

************

Kun Dade kuna addabar mutane a garinnan, ba

makhluqin da bai kawo qararkuba a qauyennan,

kun zama annoba jaraba a gari to zamu kulleku

har sai likita ya tabbatar mana da samun idon

malam garba, DPO yake wannan bayani wasu

ippatu, iyayensu sunyi sunyi abasu belin su

amma sunqi badasu aka kullesu suna kuka suna

basu bane!

DPO yasa an musu Dan karen duka tunda ba

wata sheida da take tabbatar da cewa su suka

aikata wannan laifin, kawai sanin hali yasa aka

tsaresu, sunji wuya matuqa, amma dukda haka

sunqi fada gaskiyane, rukayya ta gaji ta tona

asiri tace sune dije da ippatu duk wahalar da

suka sha sun qi aminta hasalima sun qaryata

rukayya ne, Dpo dayaga ba nasara kuma likita

yace malam garba ya samu sauqin idon sai aka

sakesu, aka musu kashedi mai tsanani, sunyi

wujiga wujiga dasu, tun suna police station suka

fara shirya sharrin da zasu yiwa dpo insun fito

kaji hatsabibai dpo ne next target dinsu.......

WACE CE ITA..??6

Na Hauwa M. Jabo

*********

Bayan sun fito da sati biyu sundan yi lafiya dan

iyayensu sun manna musu mari a qafafu basa

zuwa ko ina hatta makarantar allo, gari ya samu

lafiya two days,

bayan sati biyu kamar sun shiryu sun zama na

kirki, aka kwance musu marinda aka saka musu,

ranar da suka hadu da juna suka fara dariya

suna bada labarin yanda iyayensu suka musu,

bayan sun qare labari suka fara shirrin yanda

zasu yiwa Dpo su dau fansar dukanda yasa aka

musu da marinda ya riqa tsinka musu lokacin,

bayan iyayen su ba Wanda ya taba marinsu

saishi.!!

Sun shirya zuwa har gidanshi su fasa mai glss

din akwalar motarsa. Amma basusan yanda

zasuyiba, sun gargadi rukayya akan idan ta

kuskura ta qara tona musu asiri basu ba ita ta

amince, matsalar su daya kada a ganesu, sun

yanke shawarar fita da dare Amma suna tsoron

samarin garin.

Yauwaaaaaa ina yan matannan da muke tsokana

masu saka baqiin Abu da hijabi su kulle

fuskarsu?? Eh nagane inji dijee naji ana ce musu

wani Abu namanta sunan, yauwa mu samo irin

wannan abin da suke sakawa mu rufe fuskar mu

sai a dauka sune zasu makaranta sai muje mu

fashe mu dawo, kaji hatsabibai marasa tsoro.!!

Suka saka dariya sun sami wani tuggu da zasu

qulla, Matsalar su daya basu da niqab din nan

dijee akwai gyallen tatan gasara na Maman su

zata dauko sai su yagashi suyi niqab tunda

gyallen baqine haka kuwa akayi, suka tare yar

makaranta ita ta dauka dukanta zasuyi, sai taga

kawai sun karbi niqab dinta suna kalloyanda

yake, suka sa allura suka hada irinsa, kaji

shegun yara...

da dare suka fita sai unguwar su dpo suka shiga

har chikin gidansa batareda shakkun komaiba,

da qarafunansu da suka samo gun kanikawa,

suka ma glss din motar tamas tamas, da yake

dpo yana gurin aiki, matarshi tana islamiyya

yarane kawai suke Gidan wataqil suna bacci

sukayi operation din ranar har suka gudu ba

Wanda ya gansu,har suka iso gida!!

Labari ya chika qari, ya yadu a kowa yace da

dai da rana ne da sai muce su ihhatu da dijee

ne, Amma yanzu duk qauyen an yarda basu bane

barayine kawai suka masa wannan karen

aikin... uku bala'e kenan!! suna nasara aduk

aikinda sukasa gaba koda zasusha wahalane..

*******************

Yauda gobe ba wuya a gurin Allah abubuwa da

yawa sun faru a dan qaramin qauyen nan ciki

kuwa harda rasuwar mahaifin ippatu sanadiyar

hatsarin mota, yajee birni siyo kayan shagonsa

anan babbar mota ta bi saman motar su Allah

yayi mai cikawa.! Su ippatu an Dan natsu kadan

an rasa mahaifi, mahaifiya kuma dama batasan

duniyar da takeba coz ba rabuwar allah sukayi

da babantaba duk sharrin goggone, tunda tayi

wayo bayan babanta ya kwatota a hannun

mahaifiyarta bata qara saka mahaifiyarta a idoba

haka ma yayyenta..

Tun farko farko zaman haquri goggo takeyi da

ippatu, bare yanxu da ba mahaifin ippatu, sabida

haka ta yanke shawarar miqata birni wanke

wanke ko ta moreta....

[4:50PM, 4/26/2015] .: WACE CE ITA..?? 7

Na Hauwa M. Jabo

Tashin hankali ni kaina Jabo na tausaya

wayanda zasu dauki ippatu aiki gidansu kamin

su korota nasan zataci ubansu.!

Goggo kullum gori take mata har ta fara girgar

dangi a gida, amma ba mashinshini bare a aurar

da ita. Wazai kwasar ma kanshi jaraba. ippatu

da yar birni ce da sai anyi haddadiyar mace dan

komai Allah ya bata sak mamanta ta dauko

fulani gaba da baya sai ta hada da da duhun

babanta sai tayi Dan duhu farinta mai haske ne

da duhu gata qirar kalangu ga gashinan kamar

yakasheta amma ba gyara idan akayi kitson

sallah qarama sai babbar sallah ake tsefeshi,

tayi baqi Dan na tabbatar da tafi zainb khalifa

baqi sabida tsabar rashin wanka, qafafu duk sun

jeme haqora sunyi tsatsa da wata laka laka a

ciki idonnan sunyi ja duk jikinta tabone sabida

fadowa saman bishiya da akeyi a jijji ciwo, ko

saman Garu da ake dirowa ko a na gudu a fadi a

ji ciwo haka dai take masha Allah.....

*********

Goggo tayi magana da altine akan tanason a kai

ippatu birni aiki amma inaaaaaa altine taqi

aminta Dan tasan halin ippatu sama da qasa,

gaba da baya, altine taqi yarda har goggo ta gaji

da zuwa gidanta neman alfarma ta haqura,

ranar goggo taje suna maqotansu taga wata

mata daga birni tana maganar a nemo mata yar

aiki yarinya qarama mai qoqari da kuzari goggo

batace komaiba, Dan tasan idan ma tayi magana

anan mutane zasu fadi mugun halin ippatu.

Saida aka watse matar na fita goggo ta faki ido

ta bi bayanta, tajata gida tace tanada ya amma

batason kowa yasan zata kaita aikine zatace

takaita gun yar uwartane goggo tace yarinyar

marainiyace, tanason ta dan riqa samun abinda

zasu chi su rufawa kansu asiri, Amma batason

kowa ya sani, hakadai goggo yayita tsara matar,

ana haka saiga ippatu an dawo daga kogi tun

safe dataje sai yanxu tayi shudi daya, Koda

matar taga ippatu taga uban bokitin data dauko

saman kanta chike da ruwa ta tabbatar da cewa

ippatu Nada kuzari, kamar gaske ippatu ta gaida

matar ta wuce abinta matar kuwa ta amince da

ganin ippatu kuma tace baxata fadawa kowaba.

Matar da yake gidan biki tayi sanarwar anata

kawo mata yara yan mata amma Duk wacce aka

aiko sai tace musu ai ta samu bata fadawa

kowa cewa ippatu CE ta samuba har ta koma

birni,.!!

Bayan kusa sati uku da magana matar tazo ta

tafi da ippatu birni ta mata dinki kala biyu Dan

kar taje Gidan daga shigarta a koresu , aka hada

da yan kayan sallarta. Ippatu tayi kukan rabuwa

da qauyensu Dan batason zuwa aikin da

za'akaita sun rabu da dijee da rukayya sunata

kuka sai birni......

WACE CE ITA..?? 8

Na Hauwa M. Jabo

*******************

Bayan sun isa birni matar da nikaina Jabo

bansan sunantaba takaita gidanta, tasa tayi

wanka ta saka kayan da ta dinka mata, suka

kwashi hanya takaita gidan da zatayi aiki, ippatu

tunda ta shigo birnin sokoto take qauyanci ganin

sabuwar duniya ya hanata kula da fadan da

matar take mata bare ta mata rashin kunya,

data shigo gidan Alhaji Habib nan kallo ya koma

sama, gidane da idan na tsaya muku bayaninsa

zan bata lokacine, duk unguwar ba gidan da

yakaishi girma, ga lambu a gidan shuke shuke

manyan itatuwa swimming pool ne, gurin ijiye

motoci ga abubuwa nan kala kala, ataqaice dai

Gidan dai ya hadu, ippatu tana shiga palon

santsin tayis ya kwasheta ta xube qasa tiiiiim..!!

Wata Yar budurwa da matar gidan suka saka

dariya, taji haushin dariyar da aka mata ta daure

fuska abinta, badan yau tazoba da sai ta tsula

musu rashin mutunci su har sun isa su mata

dariya.!!?

Matar data kawota ta riqa hannunta suka

qarasa palon suka zauna, sanyin ac tuni ya fara

shigarta ta fara rawar dari sai qarar haqoranta

kikeji kakaf. kakaf, alhaji yace a kashe ac din

baquwarsu tanajin sanyi.! haba Abba wallahi

zafi akeyifa wani Dan saurayi ya fada yana

yatsina fuska alamar zafi! Alhajin dakanshi

yatashi ya kashe ac ya dawo ya xauna. Wacce

ta kawoni ta fara musu bayanina kamar yanda

goggo ta mata bayani, taji qaryarda goggo ta

zuba tayi yawa ta kasa haquri Dan ita ba'aqarya

gabanta, tayi charb ta chabke ta fara zuba,

goggo ba itace mahaifiyataba mahaifiyata sun

rabu da mahaifina tun ina qarama mahaifina ya

rasu shekara kusan biyu da suka wuce kum.....

Keeee, keep quiet mana ya fada yana mata

kallon wulaqanci, chikin tsawa ya fadi maganar

ta gane keep quiet dan lokacinda tana boko

kamin a korota Malaminsu yana yawan fadar

haka idan ana surutu kuma daya fada sai kowa

yayi shiru, shima malaminsu da qarfi yake fada

kamar yanda wannan ya fada, ta dallamai

harara hadi da yimai kallon banxa ta zubar.

Kaiiiii abba u see? Kaga yanda take kallona

kuwa,?

Farhaan yakamata ka riqa haquri mana, da

zuwan baquwa zaka tsaneta haka, kada ka

manta da ita zaka zauna.. farhaan ya juyar da

kai gefe gaskiya dady bana tunanin xan iya

zama da wannan, kalletafa!! wata kyakyawar

dattijuwa ta kalleshi wallahi kayi kadan wannan

itace ta qarshe ba chanji. Duk maganar. da

suke da englsh suke yinta, Ya bata fuska ya

tashi yabar musu guri yar qanwarshima ta bi

bayanshi suna gunagunai da turanci,

Matar data kawoni ta basu haquri tace kuma

kada in qara magana, ganin maganata kamar

itace ta haifarda rigima sai nayi shiru bawai dan

raina yasoba, taci gaba da musu bayani inajin

tana qarya amma ba halin magana......

Mujeee zuwa muji yanda iffat za'azauna a gidan

aiki, da wannan hali nata......M jabo

.......

[4:00PM, 4/27/2015] .: WAYE ITA..?? 9

Na Hauwa M. Jabo

Wacce ta kawoni Ta qare bayananta na qarya

dana gaskiya da goggo ta kitsa mata....

Kyakyawar matar tace Allah ya bamu ikon riqeta

yar marainiya da ita, dama yaron mune muka

nemowa mai aiki, duk wacce aka kawo sai su

sami sabani dashi kusan mai aiki 13 ana

kawowa suna samun sabani, shine yanxu yace

asamo mai qaramar yarinya tunda aikin nashi

bashida yawa yace bayason Yar cikin qari sabida

sauran daga qazamai sai barayi sai yan iska sai

marasa kunya da sauransu, shi kuma baya iya

zama dasu amma wannan yarinyar ni tamini

sosai, ammafa sai ta zama mai haquri Dan

farhaan akwai fadin rai da fushin bala'e sai kina

haquri kinji yan mata? Ta amsa da to kamar da

gaske, ya sunanki da sauri nace ippatu. Matar ta

maimaita iffaah suna mai dadi! Sai naji tafi kowa

iya sunana yanda ta fada ta wani juya baki,

"kunsan bahaushe baya banbanta "P""F" duk

daya yake kiransu" Maman farhan ta mini nasiha

ta kira yarta farahnax amma shiru bataxob,

dakanta tace muje in nuna mini dakinki da zaki

zauna, tashin hankali koni Jabo dakin ya burgeni

bare wata yar qauye irin iffaaah...

An gaya mata aikin da zatanayi, zata gyaramai

dakinsa tattara mai kaya takai ma mai wanki ya

wanke, ta wanke bayi, ita zata riqa tashinsa da

safe yaje skull. Hummm iffaat kam sarkin bacci

wa zata iya tayarwa daga bacci, Naji matar

gidan ta burgeni cox batada gyama kuma ba

wulaqanci haka mai gidan amma su hatsabiban

yayan yan wulaqanci ne tasan ma korarta zaiyi

Dan bazai iya zama da itaba.

********

Kwanan hajiya Fati hudu da iffaaat anyi sa'a ba

wanda ya tsokaneta bare ta rama, yau zasu bar

naija su koma UK da yarsu farahnax, akabar

farhan da iffaaat a gidan. Da gani jininsu ko

kadan bai haduba amma ba yanda ya iya

mamarshi harda rantsuwa akan cewa bazai

chanza taba, dole yayi haquri koda na shekara

dayane, ya fahimchi yarinyar batada kunya dole

ya saitata.!!

Bayan tafiyar su hajiya ya dawo daga rakiyansu

da yayi a airport ya shigo gidan,

Keeee come here, taxo gabanshi tamai qiqam

kamar ice ta tsaya, Oyaaaa get seat tazauna

bawai ta gane mi ya fada bane kawai a

makarantar boko kamin a korota taji maliminsu

na cewa seat down ta gane cewa acikin biyun

daya na nufin zamame tunda yana fada kowa

yake xaunawa, haka yana cewa come here sai

taga anje gun malami. sai itama tayi hakan,

akayi Sa'a ta gane farhaan ya dauka tanajin

English ganin ya mata Dan biyu ta gane sai ya

fara bayani Hausa da turanci saida yayi yayi

yace have u get me.? Yaga ko motsi batayiba,

ya qara tambaya shiru kakeji yagane aikin banxa

yayi, keee ya daka mata tsawa. Kina jina?? eh

inaji. to mi nace?? Ta harareshi mi kace kuwa?

Duk maganar da nayi bakiji abinda naceba. Ta

tabe baki ai ban dauka dani kakeba to da uban

wa nake, zanci ubanki fa.! ta miqe zunbur ta

nunashi da yatsa kada ka qara zagar min baba

sabida ya rasu idan ka qara zagin babana zan

rama masa kaji na fada maka. Ta murguda baki

ta maka mai harara... Farhaan kam gaskiya

tamai yawa ya tsaya yana kallon baqauya tazo

tanamai rashin kunya har gida wai kuma Yar

aikinsa, anya kuwa tasan WACE CE ITA anan

gidan? ba shakka batasan WACE CE ITA ba nine

xan Sanar da ita WACE CE ITA a gidannan, baice

mata komaiba yaci gaba da kallonsa....

[4:00PM, 4/27/2015] .: WAYE ITA..?? 10

Na Hauwa M. Jabo.

Ta kalleshi in tafi?? Yayi banza da ita, ta qara

tambayar sa yayi mata banxa, ta kama hanya

zata tafi ya daka mata tsawa, ki dawo ki tsaya

nan, taja ta tsaya kusan 30mnt tana tsaye, ta

gaji zata zauna ya hanata Idan kika zauna sai

na kakkaryaki, tayi tsaki, ta kauda kai, ya qare

abinda yakeyi ina miki magana zakice baki dauka

dake nakeba ko?? To waye a dakin da zanyi

magana dashi? Ta kalleshi a wulaqance da chan

dakake maganar dawa kakeyi?? sau nawa ina

ganinka kana daura hannu a kunne kanata

magana ko kuma kayi yare kana dariya, wani

lokaci ai wata waya kake sakawa a kunnenka

kayita magana kai kadai duk da uban wa kake

magana?

Kaga yanzuma na dauka da ubanda kake

magana farko dashi kakeyi yanxu .

Zunbur ya miqe yayi niyyar mammaketa sai ya

tuna da abinda ummanshi ta fada mai "ban

amince ka daki yar mutaneba marainiyace duk

abin da ta maka kamin waya zan mata magana"

sai ya koma ya zauna ya dun qule hannu itako

tana tsaye ta riqe kunkuminta kamar mai jiran

danbe, ya kalleta wata mummuna qazama da

ita, ya rasa abinda zai fada mata ta gane WACE

CE ITA. ya harareta yaja dogon tsaki, to ki

zauna, ta zauna ya maimata bayanin da ya mata

da dazu, shima dai iskancine yazai ijiye baqauya

kamar wannan yana mata English to amma ai da

yayi na farko ta gane, ya akayi ta gane? Koma

yane ya rage nata..

Yace Inada abokai mata da maxa, kuma ko

wanne yana zuwa nan gidan suna kwana wasu

suna wata daya wasu suna sati biyu idan sunzo

suma duk abinda kike min suma zaki musu

hadda girki idan suna buqata zaki musu. Ni ban

iya girkibafa Malam.! Gidanku basu koya miki

girkiba ? Eh basu koyamin ba, ta fada cike da

tsiwa,sai yayi banxa da ita ya fahimci yarinta na

damunta amma zai gyarata a hankali, ya nuna

mata WACE CE ITA a gidannan, OK ya rage naki,

haka zaki girka musu in sun buqata, tayi banza

dashi Dan tunda take bata taba yiwa goggo

girkiba cox batama zauna gidaba bare tasan

yanda ake girka abinci. Ko girkin murhu bata

iyaba bare na gas, ya qara jaddada mata abinda

umma tace bata ba fita waje, ba wasa da masu

gadi, ba ruwanta da kowa aikinta kawai. za'ayi

shegiya kuwa.!

Yaqare fada mata abinda zai fada mata ta tashi

ta shige dakinta.

Tunda tazo gidan a Leda take kashi sai ta saka

bola idan yayi yawa ta fitar dashi sabida duk

dube dubenta bataga masai a gidan ba, shi yasa

dakinta yake wari Dan bata damu da gyara

komaiba, gurinda kawai akace ta gyara dakin

farhaan take gyarawa....

[4:00PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 11

Na Hauwa M. Jabo

********

Ranar farko da farhaan yayi baqo wani abokinsa

da sukayi karatu a UK. Tare sunyi missing din

juna, farhaan yanata addu'a kada wannan

kucakar ta fito ta kwafsa mishi Dan ya lura

kanta rawa yakeyi ba kadanba, suna tsaka da

gaisawa sai gata ta fito. Kamar an korota daga

daki, Ku tashi zan goge nan gurin! Ta fada ba

tareda ta kallesuba, Tafara share palon, meene

kebakiga inada baqo bane,? maza ki bacemin da

gani har ta fara shara tajiyo tsawan da ya daka

mata ta miqe tsaye, tana yatsina fuska kai

bakasan lokacin aiki na bane da zaka kwaso

tarkacen abokanka kazo dasu Ku hanani aiki..!

Habawa Ya wanke ta da mari tashin hankali..!

ta dauki bokitinta na ruwan dattin data goge

sauran guraren dasu, ta watsawa abokinsaA

fuska, tunda shine silar adaketa, ta matsa daga

nesa tana jiran hukuncin da za'amata da Wanda

itama zatayi Dan bata yafiya, dukansu sun rasa

abinyi abokinsa ya fara bala'e ya zaka zauna da

mahaukaciya farhaaah, bakasan hadarin

hakabane? Wannan wata rana zata iya kasheka

wallahi, tana shigowa palon nagane batada

hankali, Kaine Mara hankali baniba tana zazzare

ido kamar lecturer ya titsiye jabo a clss bata iya

karatuba, farhaan zaije gunta abokinsa yariqe

hannunsa, cool down my man. Akwai banbanci

tsakanin mai hankali da mahaukaci nasan da

tanada hankali bazata taba yimin hakaba, muje

daga ciki inyi wanka in chanja kaya kawai.

Baqin ciki ya hana farhaan magana ya rasa

yanda zaiyi, Dole ya nuna mata WACE CE ITA a

gidannan. Abokinsa yaja hannunsa suka wuce

daki ita kuwa hajiyar tachi gaba da aikinta.

((Allah ya tsaremu da aikin jahili da baqauye.))

ta gyara gunda ta jiqe da ruwa kamar bata

zubarba, aikin ma fa yinsa kawai takeyi amma

ba abinda ta iya bayi ruwa kawai take sakawa

ta dauraye duk da cewa umma ta nuna mata

wasu abunuwan, gadonsa kuwa sai Wanda ya

gani da yake shima gwanine gun shiririta haka

yake kwanciya akan gadonsa shi warine kawai

bayaso.

Bayan abokinsa ya tafi ya kwala mata kira ta

fito ya nunata da yatsa wallahi yau sai kin bar

gidannan Dan ba gidan ubanki bane, ko in

hallakaki matsayaciya kawai, tofaaa ran ta ya

baci ta tsani a zagi babanta ta kebe baki, ai bani

nakawo kaina gidan na ubankaba, ubanka ya

kawoni sai ka bari idan ubanka ya dawo sai ya

maidani gidan ubana kamar yanda ya daukoni,

ta fada cike da gadara da rashin tsoro. Sai ya

saki baki yana kallonta ta juya ta koma dakinta

ya bita da kallo,

Ita kanta tasan zata iya gayawa farhaaah ko

wace irin magana amma bata taba kawo ta kulla

masa sharri ko daya a zuciyantaba, haka kawai

yake bata tausayi kajifa..

Maamanshi ya kira, umma wallahi yau sai na

babbala wannan qazamar yarinyar batada

amfanin komai, umma dai nata bashi haquri dan

tasan zai rina, nan ya kwashe duk abinda ya

faru ya gayawa umma ita kanta umma ta jinjina

wa wannan yarinyar da Karen aikinta. amma

bata nunawa dantaba ta bashi haquri da kuma

yimai kashedin ya fita hanyarta Kuma kada ya

qara sa mata hannu, tace yakaiwa iffaaat waya,

waye iffaaat umma?? Itayarinyar mana,

baimasan sunantaba sai yau, kullum da yake

kullum da keee yake kiranta ya kwala mata kira

ta fito ya bata waya yaga dai batasan wayaba

bata Masan yanda ake amfani da wayarba sai

kawai ya sa speaker, taji ana kiran sunanta a

ciki, farko ta dauka radio ne yake magana sai

taji ana kiran sunanta habawa.... Ta wugar da

wayar Da gudu ta koma daki jikinta na rawa abin

ya bashi dariya sosai, sai ya bita dakin yana

shiga wani qarni da wari ya tarbeshi ya kasa

numfashi ya dawo Palo ya qara kiranta dagyar

tafito, ni kaina Jabo abin ya bani mamaki Dan

kuwa iffaaat ko lokacinda aka kaisu police

station bataji tsoronda taji yanxuba Ashe Akwai

abinda take tsoro.......

Mujeee zuwa muji ta'addancin da zatamai kamin

tafara..

[4:52PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 12

Na Hauwa M. Jabo

Ta samu guri ta rakube nesa dashi, ya daure

fuska ki karba umma zatayi magana dake, ina

ummar? Magana take kuka kuka Ya zanyi

magana da ita? Ki karba nace jiki na rawa duk

ta rude ta karbi waya, ki daura a kunne takuwa

danna waya a kunne,tayi mutuwar tsaye, Tana

tsoron kar ta jata, wayar ma a juye ta daurata

sai ya shareta, to kiyi magana, kamin tayi

magana sai taji an sake kiran sunanta har zata

wurgar da wayar sai kawai ta daure ta amsa, jiki

na rawa, sundan gaisa, nan dai umma ta mata

magana akan ta daina yiwa yayanta rashin

kunya duk abinda yakeso ta mishi, ta amsa da

to zata daina, amma hajiya kice ya daina

dukana,!! gaban abokansa yake dukana kamar

jakar gidansu, duka.!? Eh, kuma kullum saiya

zagi margayi babana bayan na fada mishi

babana ya rasu yadaina, amma kullum saiya

zageni, kwallata ta cika mata ido batason a zagi

babant ko kadan. umma taji haushi sosai ta bata

haquri tace zatamai magana,daganan tadan

bata labari har tana dariya, tama manta da

tsoronda takeji,, haushi ya kama farhaan ya kira

amata fada, ta bige dakai qaranshi, har tanata

dariya, tana dariya shiko ya qura mata I do yana

kallon haqoranta da sukayi wani tsatsa, ta qare

ta kawo mai tana dariya ya kalleta ke wai laka

kikeci hala,kinga yanda haqoranki sukayi tsatsa

kuwa? Ta harareshi, ba laka naciba kashi

nakecii, tayi tsaki ta wuce dakinta, ya bita da ido

cike da takaicinta to waima miye amfanin kiran

umma da nayi? Gashi ba abinda ya chanza! Kalli

ko second goma ba'ayiba ta qara yimin rashin

kunya, shima yayi tsaki lallai an hadashi da

qaddara kuma umma tace sai ta dawo

za'achanzamai ita, nanda shekara daya kenan

lallai zaici uban yarinyar nan kuwa, dole ya nuna

mata WACE CE ITA, a duniya ya rasa horon da

zaimata taji haushi ko zata Dan natsu, ya kira

kukunsu yace daga yau kada ya qara yin girki da

ita, okay sir,

******

Da yamma mutuniyar taku ta tashi daga bacci

ta nufi kitchen taga wayam ba abinci da Rana

ma batachi komaiba yanxuma bataci komaiba,

tana tsaye saiga farhaan ya shigo, abincin sa a

shirye kamar yanda aka saba hadamai amma ba

nata ta kalleshi fuska a yatsine, Ina abincina?

Nine mai miki girki? Ko ni nasaba girka miki?

Karki manta kema yar aikinace so ki kula kisan

abinda kikeyi a gidannan ya bone. Ta kalleshi

rai a bace to dan ina Yar aikinka sai akayi mine?

Sai kada in nemi abincinda zanci? Ta kalleshi Ni

yanxu mixanchi ? Yana kai spoon a baki ya

tauna ba tare daya kalletaba Kici halinki ko ki

girka da kanki idan kin matsu,.! Tofa yau

za'aqure iffaaat yan mata......

[5:00PM, 4/27/2015] .: WACE CE ITA..?? 13

Na Hauwa M. Jabo

Ta kalli kitchen din ko za'akasheta ba abinda

zata iyayi a bayan buda fridge ba abinda ta iya,

kuma ga wasu abubuwa kamar fridge akai taga

ana girki. Za'ayi shegiya kuwa.ta kalleshi taga

yana kai loma hankalinsa kwance., tayi tunanin

ko ta barar mai da abincin da yake ci a jikinsa

sai kuma ya bata tausayi, kawai saita rakube

saida ya kammala Wanda ya rage shi tacinye....

****

Tafiya ta kama farhaan zuwa Lagos, ya tafi

satinsa daya baidawoba. tun ranar da ya tafi

batachin abinci saidai tabuda fridge duk abinda

taga nacine ta dauko ta chinye, cikenta ya

lallace kullum tana hanyar bayi, to anachin

abinda ba'asaba Chiba wasu kuma ba bisa

Qa'ida ake cinsuba duk wani abu da tagani mai

Dan gishiri gishiri da zaqi zaqi ta gama dashi.

Kaihar saida ta qare chiye chiyen takai batada

abincin da zatachi yau.

kwananta biyu bataci komaiba yunwa na

Neman ta hallakata.. tunda tazo gidan bata

taba koda fita wajen Palonba daga daki sai Palo

sai kitchen, batamasan qofar da ake fitaba...

Aranta taji ta fita haka ta biyo hanya tabi nan ta

leqa chan har tayi karo da qofar fita, ta baya ta

fita, Habawa, tayi murmushi taga S pool aranta

tace wato gidan nan hadda qaramin kogi sukeda,

ta waiga ta hango lanbu komai yaji fruit duk sun

nuna wasu sun fado a qasa Habawa tayi ciki da

sauri taci ayaba son ranta saida ta qoshi,

sannan ta kwance Dan kwalinta tayo guxuri ta

fito har zata wuce taga yanda ruwan nan sukayi

sky colour sai suka bata sha'a ta tu6e ta fada

tayi wanka sosai gata gwanar iya ruwa, gashi,an

Dade ba'ahaduba ta Dade a ruwan sannan ta

fito, dama tunda umman su farhaan ta tafi

batayi wankaba kwana goma kenan, ta fito cike

da nishadi an samu banxa, dagyar ta gane

hangar komawa daki taje ta chanxa tufafi tunda

wayannan sun jiqe, tana zaune Palo a qasa ta

miqe qafafu ta saka fruits dinta tsakiyar qafafu,

tanashan mangoro abin sai Wanda ya gani,taji

qamshin turare hadi da dariya koda ta duba

farhaan da wata mata yar gayu da qananan jaya

a jikinta tasha attach fuskannan tasha fenti

bakinnan yaji janbaki, ta rurungumo farhaan,

tana mai shagwaba suna ta dariya, sun bata

haushi haka kawai, ta miqe da dariyanta

tagaishesu a tunaninta matarsace, matar ta

mata kallon tsana da gyama ta kalleta a

wulaqance ta zubar, hooney miya kawo almajirai

a gidannan bayan kace min ba kowa dagakai sai

masu aiki biyu. Wai itama mai aikinace, .matar

ta wani jaa da baya honey wannan din?? Aiko

hanyar databi bana son nabi tana magana

ayangace tana wani rungumoshi, ran iffaaat ya

bace tuni tasha magani aranta tace Dan an

samu an gaishesu suke yiwa mutane wulaqanci

ba matar shi bace ko uwarshice tamin iskanci

zanci zan rama, taja wani dogon tsaki,ta

murguda baki ta wucesu, hooney kana kallo mai

aikin gidanku abinda ta mini...??

[2:48PM, 4/28/2015] .: WACE CEE ITA..?? 14

Na Hauwa M.Jabo

Kiyi haquri tanada matsalar gwagwalwane, ta

wani zare ido kana nufin mahaukaciya kake

rayuwa,?? Haba Hoooney wannan ai gangancine

ta fada da qarfi, har saida iffat tajiyota, ta waigo

ta zare ido gasu masha Allah idonta, ido cikin

ido tace; waye mahaukaciya?? Rufee ta rungume

farhaan da qarfi kiyi haquri badake nakeba, rufee

dai taji tsoro, hankalinta ya tashi qarshe taqi

zama gidan tace sai dai ya kaita hotel Dan

bazata zauna da mahaukaciyaba ta hallakata.!

Haka dai rufee ta hana farhaan zama gida duk

gajiyar daya kwaso saida yakaita hotol, kuma ta

hanashi dawowa kar mahaukaciya tamai illa sai

gobe da dare ya lallabata ya dawo gida, iffaaat

dai fruits dinta takeci dare da rana amma taji jiki

ba kadan ba har ta chanxa kala, kullum tana

hanyar bayi tana gudawa.

Dan ma Allah yasa ba irin zainb khalifa bace mai

shegen ci da ba haka ba..

********

Yana isowa ta fashe mai da kuka wallahi saika

maidani gida!! angayamaka banida gata zata

ijiyeni ba abinci wallahi saika maidani gidanmu

ta riqe mai gefen riga tana kuka, anyi arziki

bataci kwalarshibama. sai yanxu ya kula da ta

Dan chanza kamar ta tame ta qara duhu ya tuna

da cewa ya hana abata abinci.! Girjinsane ya

buga to me takeci tsawon kwana 9?? Ya kalleta

sai kuka take sai ta bashi dariya kuma, Ashe

kawai abinda zaisaa wannan shu'umar kuka, yaji

dadi aransa ko banxa ya rage baqin cikin ta

kuma dama Dan ya bata wahala ya mata

hakan..

Sorry iffaaahh, na manta dana hana abaki

abinci, to mi kikeci kullum,?? bansaniba ta fada

a yatsine wato kai ka yahana a bani abinci,

wallahi Dana sani da ban mai kukaba duk a zuci

take maganar.!!

Kiyi haquri kinji, tana kallo ya kira kukunsa yace

a riqa girki da ita,tace bazanciba gida zaka

maidani, bai kulataba ya wuce abinsa.

Bayan kwana biyar farhaan ya sallami rufee,

Kwana na shida yazo da wata matar,

Itama yar gayuce irin rufee saidai wannan tafi

kyau, koda suka shigo iffat na goge Palo,

yarinyar ta kalleta ke kawo min ruwa mai sanyi.!

Ta fada a gajiye tafada kan kujera ta zauna iffat

ko kamar batajitaba, aranta tace dama matansa

biyu yaro dashi sai mata, baijira amsar iffat ba

Dan yasan halinta sarai batada kirki, yanda ya

gaji bazai iya fita nemawa ramsy hotel ba, ya

dauko mata ruwan ya kawo mata kixo mushiga

daga ciki kinga ana aiki anan ka shiga idan na

huta zan shigo ta fada alalace,

Ya wuce yabarta tana danna waya amma ranshi

baiso barintaba, kee mai aiki idan kin gama kizo

ki matsamin qafafuwana....

[3:00PM, 4/28/2015] .: WACE CE ITA.?? 15.

Na Hauwa M Jabo

Nan ma Tayi banxa da ita har ta qare aikinta,

tana neman ficewa palon, ta kalli iffat kizo ki

danna min hadda bayana kiyi min a hankali Na

gaji sosai, tana magana a wahalce irin ta gaji

dinnan, iffat nan ma ko ta mata banza ta fara

waqar ta badi ba rai soyayyar jigon rayuwa da

amana...... kusan kullum sai iffaat ta yi wannan

waqar Dan tana bala'en Sonta kuma baiti biyu

ta iya tun aqauyensu, ramcy taji shiru, ke kodai

kurmace ke? Kurmane kuma zaiyi waqa,! Kee

Ana magana kinyi banza da mutane, iffaat

Tamata kallon wulaqanci, shi mijin naki yace

miki aikina kenan danne dannen matansa??

Aikina biyune zuwa uku hajiya batace in ma

matansa tausaba.! ta miqe zaune Ke marar

kunyar yarinya, kina kallon mutane kamar kina

kallon kashi, wai ma Waye matar tasa? Zan miki

display a gidannan kuwa, iffat kam bata ko

kalletaba taja tsaki ta wuce dakinta, ramcy a

fusace ta tashi taje dakin farhaan, har ya fara

bacci ihunta ya tayar dashi, ya zaku ijiye mai

aiki Mara kunya a cikin gida yarinya har tana

mini tsaki.! Yadanja tsaki ya rasa abinda zaice,

aransa yace ki godewa Allah data tsaya akan

tsaki, bayason ta fahamci koshi iffat ba ragawa

takeyiba, cool down baby ba girman ki bane kina

fada da mai aiki in kin kula yarinyace, xata qara

magana ya janyota ya rungemeta.... nidai jabo

danaga abin zaifi qarfina sai kawai na bar musu

daki nayo waje.

Guraren maqreeb suka farka daga bacci suka

fito yunwa ta addabesu ya nema musu snack

suci, ramcy tace indomie take so tachi, kuku

kuma bayanan, to miye amfanin wannan

yarinyar? Basai ta girkamin ba, no ki barshi xan

girkamiki farhaan ya fada yana miqewa Dan

yasan iffaat zubar mai da mutunci zatayi, ramcy

dataga dai da gaske zai mata girkinne sai tace

ta fasa amma zuciyarta fall da tunanin miye

amfanin yar aikin, suna zaune suna hiransu suna

dariya iffaat ta taso tazo gabansu ta wuce, wani

warin datti ya daki hancin ramcy tace; kai amma

wannan yatinya na wari! Ta toshe hanci, iffat ta

waigo taceni nake wari? Farhaan yace ke ki

matsa ki baiwa mutane guri,an fada kina wari

qaryane bakya warin? Shima kallon banxa ya

mata yaci gaba da hiranshi, ran iffat ya baci

matuqa, ba'ataba fada mata hakaba wai tana

wari sai yau, ko qauye su dijee da rukayya ne

ake cewa suna wari ba wanda ya taba CE mata

tana wari ta wuce fauuuuuh kamar guguwa ta

tasooo, tana zuwa daki ta fara tunanin abinda

zatama matar farhaan ta rama, cox taji haushin

abinda ta fada mata, itaf ta dauka matarshice,

batasan matan banxa bane, tayi wata dariya

mugunta an samu idea ta miqe tsaye taje

kitchen ta dauko man gyada, tayi zaune duk ta

gogo gurin da ba carpet dashi tayis sai maiqo

yake yaji oil sosai, cox ta taba zubarda man

gyada a kitchen tafadi har sau biyu sai ta gane

cewa yana fadar da mutum, ita kanta da

tsantseni take tafiya har takai wani guri ta

zauna, ba'ajimaba kuwa saiga ramcy an fito da

kayan bacci kamar tsirara, tana fitowa daki tana

yatsine yatsine, sai wayanta tayi qara

juyawanda zatayi ta dauko wayan, kikajita

teeeeem ramcy anfadi qasa ansha qasa, ta fadi

saman hannunta tayi wata qara, iffat ta

gyalgyale da dariya, tazo kanta tana kallonta

tana dariya, ramcy kuwa sai kuka takeyi tace da

bana wari Dana taimakeki Amma ina tsoron in

saka miki warina .......

[3:43PM, 4/28/2015] .: WACE CE ITA..?? 16

Na Hauwa M. Jabo

Maimakon ta dagata din amma ina sai dariya

takeyi, ramcy sai kuka take tana ki taimakeni

iffaat taci gaba da wa qarta ta badi barai, tayi

sauri ta goge duk gunda ta saka mai,ramcy nata

kiranta ta taimakamata amma iffaat kamar ma

batajiba, hankalinta kwance, ramcy ta rarrafa

taja jiki ta dauko wayanta ta kira farhaan ta

gayamai faduwan da tayi da dariyar da house

girl dinsa tamata ba'ajimaba saiga farhaan da

Dr. Sunzo Dr. ya duba ramcy akace hannunta da

qafarta sun targade, farhaan yaje dakin iffaat

batanan yaje ko ina batanan kamar daga sama

ya ganta ta chiko dan kwali da fruit lambu taje

kenan, tana qarasowa ya wanketa da mari.!saida

abinda ta debo ya watse, Ke dan ubanki Mara

tarbiyar inace ke?? Mace ta fadi Dan bakida

tausayi idan baki taimaketa kin dagataba ai

bakya mata dariyaba, Dan Kinga ina gyaleki a

gidannan kike abinda kikaga dama, karfa ki

manta ke ba kowa bace illa yar aiki, kuma

wallahi zan riqa chin ubankine, wawuya Mara

tarbiya.!! Ya fada a hasale ya wuce daki gun

ramcy, ranshi a bace yaci gaba da rarrashinta...

ran mata ya bace ga duka ga zagin chin

mutunci, ta fashe da kuka, ta fito harabar gida

ta rakube wani guri tasa kanta a cikin chinya ta

fara kuka, kuka take sosai cox ranta ya bala'en

baci ba'ataba samun nasara akantaba irin

wannan wato duk dabarar da zatayi dan ta rama

abin da ya mata ta sai taji yana bata tausayi

bazata iyaba, shegiyar matar ya kamata ta qara

yiwa wani sharrin, haka taci gaba da kuka har

farhaan ya fito zaikai ramcy asibiti ya sameta

anan ya zabga mata harara ya wuce abinshi, har

sukaje suka dawo tana kuka sai ta bashi tausayi

yaje ya ijiye ramcy ya dawo, kewai mi kikeyi

anan,? ki tashi ki shiga ciki kinzo kina ma

mutane kuka, tayi banza dashi yayi yayi tun

yana fada fada har ya dawo rarrashinta, har ya

gaji taqi daina kuka kuma taqi tashi, ya gaji ya

koma chikin gida, iffat dai ta gaji da kuka tayi

bacci anan, har gari ya waye guraren 9 farhaan

zaije skull yaganta anan kwance ya rasa yanda

zaiyi da ita sai kawai ya dauketa a hankali

yakaita Palo saman kujera ya shinfidar, ita kuma

ramcy tana Palo zaune saman keken guragun

da aka bata, tamai kallon tuhuma waye ka

dauko, sheeeeeeee, ya dora yatsansa akan

lebensa yace kada tashi, banganeba yar aikice

kake dauka, yace batada lafiya, jiya sabida

abinda na mata akan ki waje ta kwana. Ramcy

tace then so what Dan ta kwana a waje, ya bata

amsa da then so keep quiet kada ta tashi nace!

Tamai kallon tuhuma farhaan ka gaya min WACE

CE ITA??

[3:44PM, 4/28/2015] .: WACE CE ITA..?? 17

Na Hauwa M.Jabo

Ya kalli ramcy kallon bangane mi kike nufiba, ya

tambayeta WACE CE ITA?? Eh wace ce e ita.!!

Wace ce ita kuwa bayan house girl dina, yayi

guntun tsaki, ki kula kada ki tayar da ita bacci

ba tada lfy, ya bata amsa ya fita abinshi, house

girl ce hadda wani daukota,aranta tace yanda

tasan farhaan da gyangyami ba yanda za'ayi ya

kula wannan qazamiyar yarinya, yarinyar da ko

qirqar danki yanxu takeyinsa.

Ta gungura kekenta ta koma dakin farhan.

Farkawan iffaat keda wuya taganta a saman

kujera itada tayi bacci a waje taja tsaki ko wane

aljanine ya daukota ya kawota nan oho? taje

lanbu abinta ta nemi abinda zai qosar da ita taci

ta haye wata qatuwar bishiyan mangoro mai

sanyi bata dadeba ta fara gyangyadi da taga

zata fado sai ta daura Dan kwalinta tayi yanda

bazata fadoba.

Farhaan yayi baqo kuma bayason yaga ramcy

dan ba kowa yasa yana neman mataba, sai

kawai ya janyoshi lanbu dama wasu takardune

zasu cika tare, kusan awa uku sunanan suna

aiki. bayan sun qare suna tadi suna dariya, sai

kawai sukaga abu kaman ruwa saman kan baqo

amma ruwan yellow ne har dai ruwan suka jiqe

takardun da suka cija gabaki daya, takardun da

da suka sha wahala kamin su sami signed su

chika, sun miqe lokaci daya suna kallon sama

cike da mamaki da tsoro coz sun gane ba ruwa

bane fitsarine hadda diminsa... farhaan ne ya

hangota tana sharar barchi, wato fitsarin kwance

takeyi, yaja tsaki kunya da takaici suka isheshi

kawai yaja abokin sa zo muje ciki, abokin yace

minene?? wallahi wani hatsabibin MONKEY muke

dashi, shine ya mana fitsari Dan Allah kayi

haquri muje ciki kayi wanka ka chanza kaya, sai

kuma ya tuna ramcy tana ciki bayason ya

gantane shi yasa yama kawoshi nan ga wannan

sakaran abinda ta musu, yaqara jan wani tsaki,

ya zaiyi dole tasa ya bude mai dayan sashen

gidan yayi wanka yadauko mai kayan sa ya

saka, abokinsa yanata dariya abin ya bashi

dariya matuqa yace farhaan wannan monkey da

gani Dan iskane, farhaan ya murmusa ai

hatsabibancinsa yafi wannan, ta ciki na ciki

bayan ya sallami baqo yazo lanbu yaci qaniyarta

sai kawai yayi karo da ita gefen bishiya tana

wasa da qasa, abinda ya gani ya bashi tsoro

matuqa idonta sunyi suntum kamar jabo tayi

kuka.!

Tana ganin sa ta kauda kai sai ya yazo gurinta,

ya tsuguna umma tana gaisheki tace kiyi haquri

zaginda ake miki,kinji tace in baki waya kuyi

magana, cox yasan duk abinda za'amata taji

haushi baikai a zagi margayin babantaba, yayi ta

mata surutuai ko motsi batayiba bare ta bashi

amsa har ya gaji ya tafi.

Da yamma ta shiga gidan tasan farhaan

bayanan sai ramcy zaune a Yar kekenta ta

guragu tana cin Apple tana ganin iffaat tasha

mur ta toshe hanci, iffaat saida taxo daidai ita ta

wanketa da lafiyayyen mari, ta tureta saman

kujera ta fadi, ta take qafar da aka daure ta

murza sosai, koda batada nauyi saida ramcy ta

saki wata qara Dan azabar da taji, ya kalleta irin

kallon nan nata na wulaqanci, idan mijin naki ya

dawo kice ya kasheni, ta koma lanbu abinta.

Farhaan ya dawo ya tararda ramcy a qasa tana

kuka ya tambayeta tace ba komai gida kawai

takeson ya maidata tana tsoron ta fada yaqara

daku iffaat idan yafita ta kasheta haka ya maida

ramcy gida....

su iffaat sarkin gaba tun daga ranar bata qara

yiwa farhan maganaba ta daina aikin da takeyi,

burinta kawai a maidata gida, amma ina ba hali,

Ranar tana zaune a sabon dakinta wato lambu

cox yanxu kullum tana gun dare da rana ko tsoro

bataji, dama tsoro bashida muhalli a zuciyar

iffaat tana zaune ta hango wata qofa, koda taje

ta daga an sa sakata an kulle ta bude sakatar

tana budewa qofa ta wangale saiga ta taganta

waje,....

[10:15PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 18

Na Hauwa M. Jabo

Dama an hana mai gadi ya barta ta fita, itama

an hanata zuwa gurinsa ba gunda take zuwa

daga aiki sai aiki...

Sai yau cikin ikon Allah gata waje, Ta kalli gidan

da tafito kallon sosai, gidane na gani na fada,

kusan duk unguwar ba gidan dayakaishi tsari da

girma, tayi yan kalle kallenta, ta samu guri ta

zauna anan taga yan mata nakai da komowa ko

wacce kayan jikinta abin kallone fuska duk fenti

ta kalli yanda suke tafiya kamar basason taqa

qasa, aranta tace lallai birni birnine bata taba

ganin yan birniba saiyau. Amma ita iya sanin ta

karuwai ne basa yawo da gyale, amma taga

wayannan manya dasu amma basa saka gyale

kodai karuwanne?, haka dai aranta tayi ta saqe

saqe har guraren yamma sannan ta koma cikin

gida.!

Tana shiga taga farhaan da wata mata, aranta

tace matansa uku kenan, lallai suna qoqari,

Bata takansuba dama bayi tazo, wucesu tayi ta

fita abin ta bawanda ta ko kalla balls gaisuwa,

budurwar ta kalli farhaan waye wannan?? Yace

watace,! to WACE CE ITA?? Mai aikice, amma

batada ladabi shine kota gaida mutane, look

hafsa! ba ruwanki da masu aikiin gidan mu

please, ke kullum kikaxo sai kin kawo Qatar

masu aiki haba, Bawai komai bane illah bayason

rigimar iffaat yanxu sai ta zubar mai da

mutunci, ya qara da cewa kuma ma kurmace

bata iya magana Dan ki fita hanyarta, tace Allah

sarki,

Yaja budurwarsa ya wuce daki da ita, kwanan

hafsa biyu a gidan. ranar iffat ta dawo daga

kallon mutanen unguwa da takeyi da yake tun

lokacin ta daina mai magana tadaina yini gida

hatta aikin ta dainayi, ta fado ba sallama, sai

hafsa ta kalleta a yamutse ke Dan kina kurma

baki iya ishara da hannuba Ko uyayenki basu

koya miki gaisuwa bane? Kai Allah wadaran

halinki, ran iffaat ya baci amma guduwarta data

korota tafi mata tsayawa masifa Ta kalleta

kawai ta mata tsaki ta wuce bayi abinta, Dan

abinda takeji ya matseta!! ta qare ta fito tana

waqarta ta badi ba rai soyayyah jigon

rayuwa......., nan ma hafsa ta qara magana,

wallahi sai na sa farhaan ya koreki duk masu

aikin gidannan suna gaisheni amma bandake

Mara kunya kawai, waike kurmako?? da ganin

idonki nasan ba kurma kikeba iskancini kawai

kurmace ke waqa .dama farhaaan duk masu

aikin da yake mafi yawa yan matanshi suke sa

yana korarsu, wasu kuma baqin halinsu kesa ya

koresu, iffaat har zata tankata nan ma sai ta

mata kallon banxa tayi tsaki ta wuce abinta.

hafsa kamar an tsikareta dama idan kayi masifa

akayi banza dakai yafi haushi, ta janyo iffaat ta

wanketa da mari....

[10:22PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 19

Na Hauwa M. Jabo

Habawa!! iffaat bata dubu girmar matarba Dan

kobata kaiba zata kai 25yrs ita kuwa yanxu take

Shiga14, itama ta wanketa da wawan mari

daidai shigowar farhaan, kee iffaat lafiyanki?

hafsa ta riqe kumatu tana mamaki, yau yar aiki

take dukanta, tasan tafi qarfinta Dan ubanta

mashhurin mai kudine itama kawai tanason

farhaan ne take biyoshi har gida amma tafi

qarfinsa, yana zuwa daidai ita hasale a ya

wanketa da mari biyu masu kyau saida ta fadi,

ya nunata da yatsa, ina Dada jaddadamiki ke ba

kowa bace illa mai aikina kuma bazan maidaki

gidankuba anan zaki ci gaba da zama, kinamin

bauta, idan kikayi ba daidaiba am always ready

na babbalaki,dama sabida umma nake raga miki

so naga ba amfanin haka, qara in nuna miki ni

waye, stupid girl kawai ya, rungume hafsa yana

bata haquri, hafsa ranta yayi fari Sol Dan yayi

hukuncin da ya mata dadi, ta kuwa narke a

jikinsa farhaan mai farin jinin yan mata.

Ta miqe tsaye taja ta toge ta rasa abinda zatayi

ta rage haushi kuma ta bashi haushi ya

sallameta amma ina kwakwalwanta baya aiki ko

kadan hasalima tausayinsa takeji,

***

Tafita daga gidan taje waje kallon yan mata,

wata yarinya da take yawan gani tana wucewa

yarinyar ta shiga ranta har takeji ina mazata yi

qawance da ita, wata zuciyar tace a haka zatayi

qawance dake kina duqun duqun, ta kalli jikinta

ta tuna tafi wata daya a gidannan amma duka

wankanta uku, kamar yan makarantar su jabo

basa wanka daga frdy sai frdy..

Ta kalli kanta aranta ta fara imagine irin

gasunan tare da yarinyar suna driving a mota

Habawa ta gyalgyale da dariya hadda buga qafa

a qasa, har ta manta da an mammareta ita

kadai kamar zararriya, lallai idan har tayi

qawance da yarinyar chan Yar baqa ta qare

qawance a duniya, tana nan zaune taji kamar

maganar farhaan saida hanjin cikinta suka juya

dan kuwa shine, lallai kamin ta ruga ta shiga

gida zai iya hangota, kamar monkey dinda ya

kirata haka ta Dane bishiyar da take zaune

gurinta farhaan yazo daidai bishiyar ya zatsa

yana danna waya.....

[10:29PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 20

Na Hauwa M. Jabo

Yaci gaba da wayansa saida ya qare kamar zai

daga kai ya ganta amma hankalinsa na gun

budurwar da yake tsarawa a waya, bata gane mi

yake cewaba Dan da English yake magana, ya

wuce kamar da second 30 ta sauko ta shiga

gidan da sauri ta kulle qofar lanbu taje gurin

zamanta tana addu'a da Allah yasa bai gantaba,

idan ya ganta tunda yace bazai maidata gidaba

ya zatayi, zai kulle qofarne ya hanata fita ko ina

gashi tanason tayi qawance da yar baqar

yarinyar da take gani tana wucewa. Tana nan

zaune Tana Zane a qasa ya kwala mata kira taje

ta turbude fuska, yace taje hafsa na kiranta,

batamai musuba ta wuce shima yayi mamaki

sosai yanda ya wasketa da mari batace

komaiba, aransa yace kodai ya fara nasarar

natsar da itane, hafsa a Palo zaune, wai ta dan

qasa mata qafafuwanta da ruwan xafi, ( inaga ta

kusa fara period ne coz yan chinar skull dinmu

haka sukeyi kuma zakiga sun Dan sami sauqin

ciwon cikin) na watsa mata harara, banganeba,

tamin bayani shiko gogan yana tsaye ya

rungume hannuwansa, nikaina jabo nayi

mamakin iffaat data amince da aikin, ta zauna ta

riqa juya ruwan turinisu suna dukan qasar qafar

hafsa har suka huce ta zubar ta dauko wasu ta

mata daqowar da hafsa zataye ta hanbare iffaat

ta fadi xaune ruwan suka zube a jikinta duk ta

jiqe amma ruwan ba wani zafi sosai, farhaan ya

kallesu baice musu komai ba, yaci gaba da

kallon ball dinsa, karo na uku ta dauko ruwan

zafin da gangan iffaat ta juye matasu a qafafu,

hafsa ta tsallara ihu, iffaat ta miqe tsaye da qarfi

tayi gefe farhaan yazo da sauri yana duba qafar

ba abinda tayi a Zahiri amma tana zugi daga ciki

iffaat tayi tsaye tana jiran hukuncin da farhaan

zai yanke mata da sauri ya kira Dr. hafsa sai

aikin kukatakeyi, yana rungume da ita tanata

ihun, yace iffaahh. Ta watsomai idonta da gani

tadan tsorata ya akayi haka?? Ta fuske kamar

da gaske, naje zan juye ruwan sai kawai tasa

qafa zata shureni saita shure ruwan suka juye

mata a qafa, harga Allah ya yarda cox yaga

yanda ta shureta karo na farko, ya jinjina kai,

duk da baiji dadiba amma yasan iffaat batada

laifi,......

Dr yazo ya dubata ya bata

magunguna, tace zata koma gida kada yar

aikinsa ta kasheta, baiji dadiba cox duk cikin yan

matanshi hafsace kawai take iya jure jarabarshi,

cox ita sonshi takeyi so duk wahalan da zai bata

tana jurewa sauran kuma, kudi kawai sukeso,

Yakaita gida, ya dawo bai kula iffaat ba ya wuce

dakinsa sai yanxu ya kula dakin yayi kacha

kacha ya kwala mata kira, ke zaman me kike a

gidannan?? Kalli dakina kalli toilet dina! Miye

amfanin kine??

[10:33PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 21

Na Hauwa M. Jabo

Dole kiyi aikinda aka kawoki kiyi idan har

kinason amaidaki gida, so zabi ya rage naki, ko

kiyi aiki a maidaki gida ko kuma kiyi ta zama

anan har qarshen rayuwarki. taga gara tayi

aikin ya maidata gida.

***********************

Yau watan iffaat biyar a gidansu farhaan inda

sabo yaci ace ya saba da halinta ya kawo

budurensa daidai har 8 suna chin uban juna Ita

dasu, kuma ko wacce sai tayi nasarar daukar

fansar abinda suka mata ta hanya kala kala,

kuma farhaaah Sam baya ganewa, ita

Har yau ta kasa gane cewa ba matansa bane

matan banxa ne da taga sunfi hudu sai kawai

aranta tace auri saki yakeyi, irin na wani alhajin

qauyensu da akace auri saki yakeyi, kullum

sukaje Gidansa kallon TV sai suga sabuwar mata

a gidan akace auri saki yakeyi, anan ta gane

halinsu daya da farhaan...

*********

Yau dai iffaat an tashi ba lafiya zazzabi yake

damunta da wani gwauron ciwon ciki, har bacci

ya dauketa tsakar bacci ciwon ya tayar da ita

taji danshi danshi a qasanta dubanwa da zatayi

sai taga jini Habawa ta fashe da kuka koda ta

tashi ya mata kache kace a jiki Ashe ya Dade da

zuwa bata kulaba, tayi Sa'a farhaan yana palo

yana kallon ball ta fito a hargitse tana kuka, ta

nuna mai jininta fa na xuba, ya kalleta habo

kikeyi? aah ta gun fitsarinane, kunya ta

kamashi, shi wace irin yarinyace umma ta sashi

dole zama da ita wai mai aiki gashi ta zame mai

jaraba, yayi tsaki yana kall ball dinsa za'a

katseshi, to kije daki zan siyo miki magani

yanzu, yama Dr waya akawo mai pad da

maganin ciwon cikin na mata bada jimawa ba Dr

ya kawo mai, ya kirata amma ba amsa ya gaji

yayi banxa da ita, sai da ya qare kallon ball

dinsa ya miqe tsaye sai maganin ya fadi sannan

ya tuna da wata iffaat ba lafiya yaje dakinta da

yake yana mura baiji qarnin da dakin yakeyiba,

koda yajee ya ganta ta dunqule a qasa sai juyi

takeyi, duk jikinta ya baci, ya rasa yanda zaiyi

idan ya dauketa zata bata mai jiki ya waya da

Dr waya shiru bai daukaba, ya tsaya gabanta

ganin numfashinta na hawa da sauka kamar

zata mutu yaji tsoron tamutu a gida da zamo

mai aiki, yaqara yima Dr. dinsu waya yace mai

normal ne na farkone ya bata maganin da ya

kawo zata warke kada ya damu, ya dagata

chak ya yakaita bayinsa ya wanke mata jiki ya

rasa yanda zai chire mata tufafi tunda duk sun

jiqe yaje dakinta ba kayan da zai saka mata duk

saman gadonta suke kuma duk ta batasu da jini,

yaje dakin farahnax qanwarshi ya memo wata

jallabiya baqa yazo ya rufe idonsa Dan kada ya

ganta ya chanxa mata kayan jikinta ya....

[10:38PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 22

Na Hauwa M. Jabo

Ya bata magani dagyar tasha ta amaryar ya

qara bata wani, yace ta daure ta saka wannan

abin pad tace bata iyaba, ya kalli bayan ledar

yaga yanda ake sakawa ya hada mata ya bata

ta saka, pant ma a kayan farahnax ya daukoshi,

yace ta kwanta dakinsa dakinta ya harqitse

tunda batada lafiya, tanashan magani tuni tayi

bacci,

Bata farkaba sai bayan la'asar tafito Palo tana

dingishi zata tafi dakinsa ya kirata zonan, ya

jikin ta amsa a kasalance, naji sauqi da gani

hajiya iffaat anji jiki Dan har idonta sun fada, tayi

wani iri da ita, ya kir Dr. ya miqa mata waya Dr

ya mata bayanin yanda xatayi komai kuma kada

ta damu duk mace mai lafiya tana wannan abin

sabida haka ta godewa Allah ya fada mata zata

iyayin kwana bakwai tana xubarwa, likita jinina

bazai qareba?? No wannan ba jini bane ciwone

yake fita idan bai fitaba idan kinyi Aure bazaki

haihuba ko bakyason haihuwa?? inaso mana,

him wayaga iffaat da ciki, yadai mata bayanin

komai sukayi sallama, ta bashi wayarsa, ta wuce

daki koda taje duk an tattara kayanta gabi daya

da zanin gado duk babu, an saka wani, sai

yanzu ta tuna yanda tayi kacha kacha da ko

ina...

Iffaat saida tayi kwana biyar sannan ta

kammala, farhaan ne yasa aka kai mata kayanta

wanki.

Wannan ciwon shine mafarin fara shirin iffaat da

farhaaah..

Tunda ta fara ciwo sai yau ta fita waje kamar

yanda ta saba, tana zaune sai ga black girl

dinnan ta wuce qamshinta ya doki hanchinta

aranta tace anyi yar gayu anan gurin, ta qare

kalle kallenta ta shiga cikin gida bayan ta koma

gida tana dakinta zaune tunaninta daya ya zata

zama yar gayu irin na yar baqar yarinyar nan,

taje bayi ta kalli madubi, sosai ta bude

haqoranta taga yanda sukayi laka laka a qasa ga

wata tsatsa da sukayi tofa bata wankewa fiye da

haka ma sai tayi, batasan yanda zatayi dasuba

suyi haske irin na tsohuwar matar farhaan

ramcyba, cox ramcy akwai wushirya kuma da

fararen haqora Tass dasu, tayi tsaki ta qara

gaba...

Ranar ta fito Palo, karo na farko da ta taba

tsayawa kallon TV tunda tazo gidan nan sabida

farhaan kullum ball yake kallo itako batason ball

a rayuwarta, tafison indiya an qare ball ne Anje

talla sai kawai ga tallar signal, mouth Clean ne

mai kyau, taga yanda ake wanke baki sai ta tuna

ta tabaa ganin farhaan yana wankewa har ta

tsaya kallonsa, taje bayin dakin ta nemi mouth

clean din koda ta duba sai taga exactly irin

Wanda aka nuna a TV ne, tayi murmushi Ashe

haqoranta zasuyi fari irin na matar Tv ta Dan

barashi a brush tana wankewa yana jini duk da

ya mata xafi ta daure cox tanason ta zama yar

gayu irin na yar baqa sunanda ta sanyawa

yarinyar kenan, iffaat dai haka tajuri yi brush

kullum ko nace duk lokacin da abin ya motsa sai

tayi cox.......

[10:45PM, 4/29/2015] .: WACE CE ITA..?? 23

Na Hauwa M. Jabo

Cox a rana sai tayi brush Sau biyar ba'ayi

kwana sati day ba suka fara cire wannan lakar,

kuma tsatsar ta fara bacewa,

Ranar tana zaune tana charafke sai ga farhaan,

dama bata gaidashi idan yazo ya zauna yace

yau kuma TV ake kallo da charafke, ta juyo ta

kalleshi tayi dariya, tace eh so nake in zama yar

gayu irin na matan Tv ya kalleta sosai sai yau

ya kula tana da wushirya,idan ba idonsa suke

masa gixo ba yaga haqoranta sun cire wannan

laka lakar na da,.

Yace gashi kuwa su Umma zasu dawo anan

zasuyi azumi, Dan murna batasan lokacinda ta

tashi tsayeba Ashe nayi kusa tafiya gida,? Naga

su dije da rukayya da goggo, tanata dariya, lallai

gaskiya ya hango, haqoranta sunyi haske, kinga

idan kin tafi kin huta dani ko, ta kyalktale da

dariya saida kumatunta ya lotsa, ai zama da

mugu irinka sai An shirya kamaci arzikin ina

tausayinka, shi yasa duk matanka suke guduwa

duk matar daka aura sai ta gudu, kalli fa cikin

wata biyar saida kayi Aure 8 lallai yarinyar nan

batada wayo,! ita ta dauka duk matanane kena,

hahaha nine mugu iffaat?? babba ma kuwa. Ta

fada ba tareda shakkar komaiba bakya kunyar

fadamin haka a gabana? lallai kin girma, ta

kalleshi ta tabe baki, ai gaskiya na fada, nima

yanzu zan shirya suna dawowa sai in tafi

gidako? Taci gaba to yanxu kai zaka mini

dunkin sallah ko hajiya??

Yagyara zama ni xan miki ai ni kike yiwa aiki ko?

Eh Kaine maigiana, ta juyo tana fuskantarshi

kasan wani abu,?? Saikin fada, naga aminar

baba sule idan ta dawo aikibirnib sai ta dawo da

kayan gayu, tufafi sabbi qanzon shinkafa sabulai,

abubuwa dai da yawa na birni, ni ina zan

samu?? yayi murmushi dama tanada surutu

haka? Yace kema da kina min aiki da kyau da

duk zan siya miki abubuwan da kika lissafa

hadda qari ma zan miki, amma ke bayan tsiwa

da rashin kunya da zubar min da mutunci ba

abinda kika iya LA ilaha illallahu, yanzu duk

aikinda na maka haka zakace? kallifa baka taba

dukana na ramaba, au da ramawa kikeyi?

Taaaab wallahi a qauyen mu komi girman qato

idan ya dakemu sai mun rama, kai hadda

shugaban yan sandan garinmu ya dakemu

mukaje gidan sa da dare muka fasa mai mota,

ya fito da I do da gaske kikeye??

Ta qara gyalgyalewa da dariya sai tamai kyau,

wallahi da gaske nakeyi, kicemi ke yar

ta'addace...!

[11:13PM, 4/30/2015] .: WACE CE ITA..?? 24

Na Hauwa M. Jabo

Nan ma dariya tayi ai baka sannibane, ta fara

bashi labarin ta'addancin da takeyi a qauye, ya

jinjina mata sosai kuma ta bala'en burgeshi Dan

yanason yaga mace mai kamar maza, anan ya

gane duk abinda yan matansa suke fada akanta

gaskiya ne,

Abinda yaxo mishi gona hafsa da tayi da ruwan

zafi yace Kena da gangan kika xubawa hafsa

ruwan zafi? Ta kalleshi ta kanne mai ido ai

muguwace, kuma ita tafara xubamin ruwan kana

kallo bakace komaiba, sannan akanta kamin

mari biyu ita ma tamin daya shiyasa duk cikin

matanka nafi tsanarta, kuma da gangan na zuba

mata ruwan,? Ke yanxu data qonefa??

Aaaaaaaa miya dameni badai na rama ba!! Ya

kalleta da kyau yarinyace sosai kuma lallai

batada wayo ko kadan ga shegen surutu...

To yanxu dai ki riqa aiki da kyau zan siya miki

duk abinda kikace waccan qawar taki tana tafiya

dashi qauye idan zaki tafi gida, yatashi ya wuce

dakinsa, yabarta tanata zuba, aranshi yace lallai

da yana kula yarinyar nan da ta debe mishi

kewar qanwarshi farahnax Dan ya kula akwaita

da shegen surutu ga saurin sabo saidai sabon

baya hana tama mutum rashin kirki Dan yaji

yanda take danbe da qawarta dijeee !!!

Kamar kullum bayan fitar farhaan taje S pool tayi

wanka da yake shi yake debe mata kewar kogin

garinsu, tayi wanka abinta ta qare tabi ta lanbu

taci abinda xataci ta fita doguwar rigar da

farhaan ya bata lokacinda batada lafiya ta saka

sai ta mata kyau sosai, tana zaune tana wasa

da qasa sai ga yar baqarta tazo tayi kwalliya

baqinta sai kyalli yake tayi kyau tsab tsab da ita

da takalminta masu tsokane duniya, ba abinda

yake burgeta irin yanda take wani Dan tuntu

saman kanta ( acucu maza take nufi) yana

burgeta matuqa amma batasan yanda

zatayishiba ta qare zamanta, ta koma gida da

tunanin yanda zatayi wannan abin na saman kan

yar baqarta, tayi tunanin Idan ma gashintane

zaiyi irin na Yar baqa, tinda gashinta yanada

tsawo sosai tunda tazo gidan da kitso bata

tsefeshiba.

[11:23PM, 4/30/2015] .: WACE CE ITA..?? 25

Na Hauwa M. Jabo

Tashiga dakinta ta zauna ta tsefe amma saida

tayi kuka dan zafi kuma gashi ba kibiya duk ya

harhade ko gida kullum sai tayi kuka idan ana

mata tsifa, yauma saida tayi taje ta wanke da

man da taga anyi hoton qashi jiki haka datti ta

riqa zuba kamar an kwaba qasa, haka tayi ta

xubarda daddi har yayi fess dashi kamar bana

iffaat ba, matsalar daya ba tada mataji kuma ba

tasan yanda zatayi irin na yar baqaba, sai ta fito

Palo tana goge gashin farhaan ya kalli gashinta

aransa dama tanada gashi haka, ya zauna yace

dama kinada gashi shine baki kyarawa, tace

wallahi parhuun zafi yake min.! Ya kalleta tanata

kiciniya da gashi yace ya sunana? Tace Parhuun

mana haka naji kowa yana fada, ya kwashe da

dariya saida yayi kwalla wai PURHUUN yarinya

katki bata min suna sai nanatawa yake

PURHUUN lallai wato kusan shima bata iyaba

gaskiya anyi baqauya anan yace to ba haka

bane farhaan ne, ta dago kai tace Parhan, yace

aah farhaan, parha, ke kalli bakina, kice far, tace,

par, kalli ki haqoranki akan lebenki zaki Dora sai

kice far, takuwa yi tace far yayi dariya yauwa

kinyi daidai, sunana farhaan,ta fada daidai tace

Dan gayu ko sunan ka sai ka koyamin. Ta bashi

dariya wai Dan gayu, so funny, tace to yanxu

gayamin yanda ake wannan abin a saman kai

yayi sama sosai, yace ni ban iyabafa banmasan

mi kike nufina, LA ilaha illallahu, ta to saki

gashin ta toshe baki babba na qarya, wallahi ko

wasu a matanka kamin ka sakesu nagansu dashi

kace baka sanshiba, yayi dariya lallai yarinyar

nan case ce, ni nake qarya?? Waima waya gaya

miki matanane?? Ta zunburo ta kama gashinta

ita burinta a mata irin na yar baqa ta hanya,tace

to miye naka? Abokainane ko ban fada miki

inada abokai mataba, ta saki gashin kanta ta

qara rufe baki da hannu, shine kake tabasu?

Hmmm!! Ta tabe baki Mudai garinmu duk namiji

mai taba mata Dan iskane, ko wasa bamayi da

maza duk iskancine garinmu, kaga da garinmu

kake da nace maka Dan iska, keeeee, nine dan

iska,?? ta zaro ido ai ban fadaba. nace da garin

mu kake.. aranshi yace ko inane wannan

iskancine, yace to a birni wayewace ba

iskancineba, ya fuske ya miqe zai fita, baka

gayamin yanda akeyiba, sai na dawo zan gaya

miki...

A hanyarshi ta dawowa yayi karo da wata tayi

acucu maza sai ya tuna da alqawarin da yayi,ya

siyo mata ribbon manya da mataji da man kai

ya kawo mata.. Tanatajin dadi zata yi irin na Yar

baqa, ba'anan kizo ke saqarba bata iya

sakawaba ta kuwa fara hadashi da Allah, ya

koya mata shi ba iyawa yayiba, yana mamakin

yanda take mai kamar wani sa'arta yanaga ta

mance WACE CE ITA.!! Yayi tsaki ke kada ki

dameni kinji, na siyo miki kuma ni zan saka

miki? duk ma yan matanshi basuda gashi irin

nata duk qarine sukeyi, ya zauna yaci gaba da

kallon ball dinsa, dama iffaat akwai naci akan

abinda takeso. tazo tana hadashi da Allah tana

mai shagwaba abin ya burgeshi.. Yayi tsaki

aranshi yace yarinyar ta fara rainani, ta kuwa

miqamai gashi ta zauna ya rasa yanda zaiyi to

ki taje mana ta fara tajewa tana gwalla Dan duk

ya sarqe tanayi yana shafa mata mai har ya

taju yayi kyau gashin yana gyalli abinka da

gashin fulwni sai Wanda ya gani,ya karbi gashin

ya kasa tattarshi yace ta tattara da kanta ya

nuna mata yanda zatayi ta tattara, to aike basai

kin saka irin nasuba tunda gashinki yana da

tsayi sosai, Allah ko? eh mana, haka ya

taimaka mata tayi parking dinsa kuma yayi irin

yanda take so, yanxu kasan mi nakeso? Yace

Aah, akwai wasu kaya da ake sakawa sai ayi

wannan abin sai ayi kyau a zama yan gayu idan

xantafi gida zaka siyomin? nama taba ganin

abokiyarka da irin su! Ke ni ban ganesuba, kuma

ki sani duk suna cikin kayan sallanki, eh na

yaddda ta amsa tana zagwadii....

[11:30PM, 4/30/2015] .: WACE CE ITA..?? 26

Na Hauwa M.Jabo

Bayan ya dawo, ita duk wautarta yau zai siyo

mata kayan taga wayam hannunsa ba komai,

laaa farhaaah Yaushe zaka siyomin kayan

gayuna? irin na abokanka,? Ya harereta bakida

kunyako kina kiran sunana. Ko bangirmekiba. yi

haquri Mixance makato? ta fada irin ta matsu

dinnan taji zancen kayan gayu, look ki bari zan

siyo miki kawai kamin ki tafi gida, yayi niyar yaje

da ita a aunata gun mai dinki amma ina yana

tsoron ta kwafsa mai wannan hargitsatsaiyar

wataqilama taje ta nemo magana, to kawai tace

mai amma ranta baiyi dadiba ta wuce daki ta

zauna, ta fara tunaninta na zama gayu irin na

Yar baqa iffaat yanxu batada buri irin taga ta

zama Yar gayu, Niko inason ganin iffaat da gayu,

aranta tace gayufa dole saida wanka, taaaab

yanxu kullum sai tayi wanka kenan.?? idan ba

wanka ba gayu, ta tashi ranar farko data ji tayi

wanka Dan ra'ayin kanta, ta fada wanka tayi

wanka da ruwan zafi ta wanke dattin

wafafuwanta sabida bata yawo da takalmi ko

lanmu haka take tafiya ba takalmi tana wankewa

ta tuna da qafafun hafsa lokacinda tasata gashi,

sumul sumul qafar yan gayu ba kaushi, ta

wanke iya yanda zata iya, ta fito ta saka yan

tsumma karonta.. Tayi bacci anan tayi mafarkin

ta zama Yar gayu, tayi qawance da Yar baqarta,

ta farka ta fito Palo cin abinci bata dadeba sai

gashi ya kawo mata kaya English Wear ne, ya

nuna mata wayannan kayan kike nufi?? Sauran

nakai dinki duk na sallah ne amma, Ta kallesu a

tsorace ita a qauyensu idan mace ta saka wando

za'ace mata yar iskane so bazata sakaba, data

fada mai yayi dariya sosai wato qauye bala'ee

ne, qauyanci masifa, yace ki riqa saka wannan a

gida idan zaki fita saiki saka wayanda bana yan

iskaba. OK bari in saka ka gani, anan yaga zata

cire kayan jikinta no ki shiga daga ciki mana, ta

kwashi kayan ta shiga daki da gudu ta saka

wandon yafito da ita ainihin ita sai Wanda ya

gani mazaunan suka fito hips din ma ya fito, da

yake dukiyar fulanin yanxu take fitowa yayi dan

tudu kadan sai head dinsa ake gani ya fito

saman rigar, ta fito da gudu tana dariya na fara

xama yar gayuko? farhaaah ya kalleta tashin

hankali, Ashe babyn nan ta hadu a ransa ya

fada, dukda cewa ba daidai ta saka kayan ba

amma sun mata kyau, kalli nayi kyau, sosai kin

ganki kuwa, tace kamar ba yar aikiba ko, yace

sosai kuwa, tana ta dariya ta janyo gashinta da

yake ta cire riboon garin saka tufafi wai dole sai

yayi mata yanda akeyi dinnan, no ki bari in miki

hoton tarihi kuma na turawa umma taga

yarinyarta ta fara zama gayu, nan ya sa tayi

wannan tayi wannan idan tayi wani style sai

yakai zauna Dan dariya, qarshe yace to tazo ya

dauketa ita dashi ba tare da damuwaba ta

kwanta a qirjinsa ya daukesu photo tana dariya

duka dimple dinta sun lotsa gwanin ban sh'awa,

kawai daga kan da zasuyi sukaga hafsa kamar

daga sama, ta kalli kayan jikin iffaat ta watsa

mata harara, ta riqe kunkumi wai farhan na

tambayeka waye wannan yarinyar?? kawai fada

min gaskiya, ya kalleta kallon bangane mi kike

nufiba, sau nawa ina fata miki WACE CE ITA!

Amma kina min magana wai iri, hafsa ranta ya

gama baci iffaat kuwa dama batayi ta kantaba,

murnar kayanta takeyi batama gane hafsarba

yana juyowa tace Yaya farhaaah yaushe zaka

kawo min kayan sallah? Ya kalleta ita ba abinda

ya dameta sai su umma sun dawo,

Kamin ya juyo hafsa ta fita Yabi bayan hafsa,

itakam ta dauki kayanta ta je dakinta,

Kamin ta tada mota yasha gabanta yace mai

gadi ya kulle gate, hafsa kuwa anriga anyi fushi,

ya bude motar ya janyota jikinsa, ya rungumeta

yana shafata a hankali, miye na fushi, hafsa??

Ni kawai ka fada min WACE CE ITA please!!

[11:45PM, 4/30/2015] .: WACE CE ITA..?? 27

Na Hauwa M. Jabo

Wallahi na gaya miki WACE CE ITA, ba kowa

bace illa house girl dina, house girl take saka

English Wear?? house girl kake rungumewa kana

photo da ita?? Haba farhaaah kada ka mayar

dani qaramar yarinya mana! no hafsa wallahi ba

haka bane kin gane yarinyar batada wayo ko

kadan kuma zata tafi gauyensune da umma ta

dawo shine na siyo mata tufafi, kuma wallahi

kinji na rantse umma tace in siya mata duk

abinda take so, tunda ta kusa tafiya, kiyi haquri

wallahi ba komai tsakanina da ita, mi zanyi da

mai aikina, haba aiba class dina bane, yarinyace

fa qarama ya kanne mata ido, ai dama ka gware

a sweet mouth, yayi kissing din gefen fuskarta,

muje daga ciki tana jikinsa har suka shigo,

dakinsa suka wuce nan dai yachi gaba da

rarrashi har mai afkuwa ta afku, nidai jabo idan

zasuyi labewa nake sai sun kammala inshigo

ciki, Allah ya shirya mana zuri'a kwanan hafsa

biyu a gidan amma farhaan bai bari sun hadu da

iffaat ba Dan a labarin data bashi ya gane ba

qaramar yar ta'adda bace kuma bata mantuwa

bare yafiya, daukar fansa gunta wajibine..

**********

Ayau ne su umma zasu dawo farhaaah Dan dole

ya karbo mata tufafin da ya dinka mata atamfa

biyu les uku, yace ta saka idan su umma sunzo

ya bata turaruka da sure duk ta riqa sakawa, da

yamma su umma da abbansu da farahnax suka

iso farhaan ya rungume farahnax suna tafe suna

tadi, da guduna naje gunta ina hajiya sannu da

zuwa ta kalleni, iye yarinyar hajiya an girma an

qara kyau haskene kawai bakiyiba har yanzu,

ina zatayi haske tunda bata wanka, ta gaida

Alhajin nasu ta gaida farahnax kaman batajiba ta

qara gaisheta, da dalla mata harara, kin ishi

mutane, haba naji mana, farhan ya kwashe da

dariya, yace sister ba sauqi ai iffaat akwai naci

tun xuwan iffat jininsu bai hadu dana farahnax

ba, ta tabe baki, tajoyo gun hajiya tafara surutu

batama bari su hutaba saida farahnax ta daka

mata tsawa sannan ta natsu,

Sumi sumi ta wuce dakinta bata qara fitowaba

sai gobe da safe shima hajiya ta kirata tazo aci

abinci, farahnax tana bacci lokacin da sai taga

tsiya,

*****

Bayan kwana hudu da dawowarsu, suna zaune

hajiya da Alhaji suna kallo, saiga daya daga cikin

yan matan farhaan tazo, tana zuwa taga

iyayensa saita wayance tace kuskuren gida tayi,

tana fita iffaat tacema hajiya wallahi qarya

takeyifa hajiya qawar farhaan ce nan ma take

kwana har dukana ta tabayi

TOFA ZATA TONA ASIRIN FARHAAN MUJE ZUWA

......

[12:58AM, 5/1/2015] .: WACE CE ITA..?? 28

Na Hauwa M. Jabo

Qawa kuma Alhaji ya maimaita?, eh lokacinda

tazo tayi kwana hudu anan har na taba mata

kaya ta mareni, hajiya tace amma dakinki take

kwaniko?? Aah dakin farhaaah take kwana ai ba

ita kadai bace sunada yawa, yace min duk

qawayensa ne, yace wai anan wayewane,

sabida nace mai mu qauyenmu iskancine, umma

tace hardake yake kaiwa dakin nashi?? Aah

hajiya ni kullum dukana kawai yakeyi, nan dai

madam iffaat tayita bada labarinda

ba'atambayetaba, ganin duk sunyi shiru ransu a

bace yasa tasha jinin jikinta a ranta tace koda

yaya farhaan yace aboki mace gun namiji a birni

shine wayewa so ba komai bane, taci gaba da

kallonta sukam tuni sun bar gun sunje daki

domin tattauna xancen wayo farhaan Neman

mata yakeyi.!!! Ran umma yayi matuqar sosuwa,

saida tayi hawaye, Abba yayi ta bata haquri,

Da yamma farhaan ya dawo da farahnax coz

tunda suka dawo cikin yawo suke, umma ta

turkeshi da ba zata! Tace mai dazu baka nan

daya daga cikin budurenka tazo nemanka, ya

Sosa kai budurwa umma?? Eh inaga bakuyi

waya ka gaya mata iyayenka sun dawoba hala?

Ko kuma tana sane tazo ta nuna kantane ko

qawayenka zance a yanda kake cewa kai

wayayye, nan umma ta shiga yimai fada kamar

numfashinta zai dauke Dan takaici, iffaat ce taji

magana fada fada tafito taga abin mamaki ana

yiwa farhaaah fada, farahnax ta koreta, umma

tace ta tsaya, taja ta tsaya, ai ita ta fada mana

yarinya yar albarka, farahnax ta taso a fusace

tazo gun iffaat kinyi muna funci kinji dadi

munafuka kawai, iffaat tace haba daga fadan

gaskiya saikice nayi munafunci ai ba qarya

nayiba labari na baiwa umma kuma ni bansan

fada zata masaba, kee ina magana kina magana

sakarya kawai ta wanketa da mari, kamin ta

sauke hannu tuni iffaat ta aiko mata da nata

saqon Marin,umma tace that is very good iffat,

ta gane very good coz malamansu na

makarantar boko kamin a koresu yana cewa very

good, idan aka bada amsa yaji dadi kin min

daidai gobe sai ki qara dukanta, umma ta kalli

iffat tace duk ta dakeki ki rama ran farahnax ya

gama baci koba kamai ta girmi iffaat anxo ana

siyamata raini a gunta. fau zata wuce dakinta,

kowa yayi tsit a palon Abba yace ta dawo duk

Ku zauna har umma ta zauna, ya kalli farhaan

daya sunkuyar da kanshi a qasa tunda aka fara

zancen, abba ya kalli farahnax da tasha mari

umma nacewa good, ya kalli iffaat da tayi wani

rasha rasha da ita a qasa tana kallonsu, Abba

ya fara magana yace farko dai iffaat ba gulma

takawo manaba labari ta vamu kuma da ita

yarinyar batazoba da naxamu saniba, a yanda na

fahamci labarin itama farhaan ya gaya mata, har

take cewa a garinsu maiyin haka Dan iska shi

kuma yace anan wayewace kunga ita bata

daukeshi bad thing ba cox haka ya nuna mata,

ya juyo ya kalli farahnax millions time na gaya

miki ki daina saurin fushi, ke macece Aure zakiyi

ba abinda haka zai haifar miki nan gaba sai

nadama, iffat kin burgeni da kikayi jarumta irin

haka amma ki riqa haquri kuma ki kula da

Wanda ya girmeki, tace Tau Alhaji., ba ko wanne

mutum bane zai iya yanda kikayi, kai farhaan

bayan sallar maqreeb ka sameni a daki... Abba

ya tashi umma ta bishi, farahnax ta juyo gun

iffaat ke ni zaki Mara......??

[6:05PM, 5/2/2015] .: WACE CEE ITA..?? 29

Na Hauwa M. Jabo..

Farhaan duk da baiso yin maganaba saida yayi,

lool farahnax ki fita hanyar iffaat ya fiye miki,

banason kina biye mata yarinta Yana damunta

kuma bakisan ko waye itaba, tace WACE CE ITA

bayan house girl dinmu..! Nidai na fada miki ya

miqe ya fita iffaat ma tashi tayi taje dakinta,

tana zuwa tahau hada kaya, kawai ita dole ta

koma qauye ita ba zata iya zama a gurin da

tanaji tana gani a mata bata ramaba, sabida

haka gara qauyensu, suci uban juna da yan

qauyensu

*******

Ki bari sai an kusa sallah mana, aah hajiya

inason inyi azumi gidan mu, goggo ita kadaice a

gida, kamar tayi goggo aikin takeyi, bayanda

ba'ayi da itaba, amma iffaat ta rufe ido tace

gida take so dole suka haqura suka barta..

sun shirya mata goma na arziki akace farhaan

yakaita, baisan qauyen ba amma an mai

kwatance sai ya gane ita kuma dama da an isa

garinsu zata gane gidan su.

Suna kan hanyar komawa yake gaya mata zai

tafi karatu UK bazai dawoba sai bayan shekara

uku saidai ya riqa zuwa hutu, ita kam duk daya

a gurinta, Dan ta gaji da zaman birni ba abokai,

sun Isa qauyensu yara kuwa tun daga farkon

gari suke bin motar har aka shigo ainihin qauyen,

iffaat tace ya tsaya, yace mun kawone tace

kaidak ka tsaya, ya tdaya. leqowa kawai tayi ta

kallesu batama fitoba gabaki daya yarannan

suna ganin iffaat a mota suka watse, suna ihu

wallahi ippatu ce kozo mi gudu, bawanda ya

manta da ita, cox har yanzu su dije da rukayya

ana xuba iskanci son rai a gari...

Sun Isa gidan su ta tarar anyi ginin bulo an

gyara ko ina abin ya bata mamaki, farhaan har

ciki ya shigo goggo na ganin iffaah ta Hau salati,

da mamaki Dan batasan zatazo yauba koda

matar da ta dauketa tace mata qarshen wata

zata dawo kamin azumi kenan tayi sallah gida

sannan ta koma.

Aka fara shigowa da kayan abinci kala kala, ita

kanta iffaat batasan dasuba, sannan ga kayan

sallar da umma ta mata kala uku shima farhaan

ya dinka mata guda biyar ya qara biyu daga

baya, goggo ma an kawo mata atamfa guda biyu

baki yaqi rufuwa Dan murna....

Muje zuwa muji anya iffaat zata iya rayuwa a

qauye ko yaya??

[6:11PM, 5/2/2015] .: WACE CE ITA..?? 30

Na Hauwa M. Jabo

*************

Kamin kace kobo duk qauye ya dauka da

dawowar iffaat chikin mota mai kamar jirgin

sama. Ko ina sukasan jirgin sama oho!?? kowa

zuwa yake mata sannu, wasu kuwa gulma ake

zuwayi, bawanda yasan aiki tajeyi birni sabida

goggo bata fadawa kowaba duk wanda ya

tambayeta sai tace ai tana birni gun qanwarta,

Su dijee an tafi biki chan nesa dasu, basu ji

labarin dawowar iffaat ba sai da la'asar bayan

sun dawo, suka zo ganin iffat, ganin ta ya sasu

farin ciki koda batayi wani haskeba amma tadan

chanza suka fara baiwa juna labari, iffaat natajin

haushi anyi shegiya da yawa bata, cox dijee tayi

hatsabibanci bayan tafiyar iffaat, tayi wata qawa

ummulkhairi wacce itama hatsabibiyar gaskece,

bata wasa hakadai take yanda suke, itama iffaat

ta basu labarin ta'addancin da tayi barni, amma

bata fadi cewa qawayen farhaaan bane, sunsha

dariya matuqa, anyi kewar juna,

A tunanina iffaat zata bar abinda takeyi a qauye

koba komai anje birni kuma ta fara Dan wayewa

tanason ta zama Yar gayu, Ashe ni jabo bangane

bane, iffaat iskanci da la'ana sai abinda ya qaru,

bare yanxu da suka zama su hudu, ni kaina ina

tausayawa iyayen yaran, kowa kuka yake dasu a

qauye sun gagari kowa ga iffaat an dawo.

******

Iffaat take tambayar goggo ya akayi aka gyara

gidansu, goggo ta bata labarin cewa ai

yayantane dake birni sukazo ganinta suka tarar

batanan kuma suka tarar da babanku ya rasu, to

su suka gyara gidan suka bata wata takarda wai

duk lokacinda kika dawo ki nemesu, zasuzo su

ganki, sun kawo min alkhairi kala kala daga

birni, ainikan naci arzikin yayan kishiya,

Wannan karon Goggo bata tsangwmawa iffaat

kaman daba, shi yasa suke zaman lafiya, ba

ruwanta da harkarta itama haka,

Ranar suna hira da goggo take cewa Wai ihhatu

a birni bakiyi saurayiba, ta zare ido ta dafe qirji

saurayi goggo!!! nida ko fitabanayi, nan iffaat ta

gayawa goggo aikinta goggo taji tsoro, Allah

yasa dai baya biyoki da dare, daga ke saishi a

gida ba koea. iffaat tace taaab nida ko shiri

bama bamayi, nan ta fadawa goggo ta'addancin

da tayi,goggo bataji dadiba koda dama tasan

za'ayi haka, nan goggo tadan fahimtar da iffaat

yakamata ta gane ta girma yanxu tadaina

shirme da shiririta, kina ganin idan kikaci gaba

da haka zaki sami mijin Aure,?? a qauyen nan fa

ba yarinyar da ta tabayin jini a gida, taji raaaas

ta tuna itama tayi sau daya a birni amma

bataabaiwa goggo labariba,

*******

Maganganun goggo sun dan ratsa iffaat har ta

fadawa qawayenta su daina tsokana ko su rasa

mijin Aure duk da cewa basu dainaba amma sun

rage kwarai saidak idan an musu suna ramawa,

haka kuwa akayi sunyi sauqi sosai, har takai

suna gaida mutane a hanya, amma fa idan ka

tabasu zakaga bala'ee da masifa.....

[6:17PM, 5/2/2015] .: WACE CE ITA..?? 31

Na Hauwa M.Jabo

Rayuwa tana tafiya ayanda aka sameta, Tun

bayan komawar iffat qauye takejin garin baya

mata dadi amma bata gane komaiba sai take

dauka kamar sabon da tayi da mutane birnine

suma birni sunyi kewar iffaaat sundan saba da

ganinta da tsiwarta idan sun tuna sai suyita

dariya, idan ma farahnax tana magana akan

rashin kirkin da iffaat ta mata sai su nuna mata

ai itace batada gaskiya, akan me zata

daketa,kusan duk bayan iftaar idan suka zauna

sai anyi labarin iffaat tun farahnax bataso har

abin itama ya riqa bata dariya kuma yana

burgeta, duk Wanda yaji shaqiyanchin iffaat sai

ta burgeshi, umma dai ta kula farhaan yaji dadin

zama da iffaat, ranar bayan buda baki umma

take cewa inaga bayan sallah mu tura azo

mana da iffaat, naga duk kowa yaji dadin zama

da ita, tunda yanxuma kaga bazamu komaba

kai kadai zaki tafi ka kammala karatunka , koya

kuka gani, eh umma duk sun amince,

Iffaat ma zaman qauyen baya mata dadi matuqa

kuma tanajin dadin harka da qawayenta saidai

mafi yawan lokaci takanji tayi kewar umma, duk

ta zauna takanyi labarinsu, amma bata bada

labarin farhaaah,

*************************

Yauda gobe ba wuya a gurin Allah, Ramadan ya

qare anyi sallah lafiya su iffaat yan mata sai

gantali akeyi a gari, ba mijin aure, ba

mashinshini, abin yana damun iyayensu bama

dijee ba da take yar lukuta ga manyan duwawun

da suke biye da ita, gasuda tsini idan tana tafiya

sai ta Dan duqe cox suna mata nauyi nima Jabo

Dana ganta na dauka turosu takeyi, ita rukayya

dama kamar bulala take, iffaat kuwa hips ne

kawai take dashi mazaunanta basuda tudu irin

na dijee dijee a gida tsini ake cema dijeee sabida

tsinin maxaunnan ga gafafuwan nan nata kamar

doya, qirar maxa takeda Allah ne kawai yayita

mace...

Akwai wani mai tura kura yana saida ruwa duk

qauyennan shi kadai yake saida ruwan masu

dadi, yakan sakawa ruwanshi alim idan sukayi

kyau sai ya fita saidawa yazo neman auten dijee

kuma an bashi, shima kasada yayi dan duk

qauyen nan bai samu mataba sabida tsananin

muninsa sai yazo neman Dije iyayenta suna

Neman kai da ita tuni suka sallama, rukayya

kuwa wani Dan uwanta za'a hadata dashi, su

ippatu daikam ba Kowa har yanxu.

Bayan sallah da sati biyu....

Ranar iffaat da qawayenta sunje yawo sun dawo

sukaga mota mai kyau iffaat tasa aranta kamar

tasan motar amma ta manta ina tasan motar,

tana sanye da atamfarta ta sallah da yake yanxu

gayu sukeyi an daina yawo ba takalmi duk sun

iya acuchi maxa ataqaice duk qauyen ba Wanda

yakaisu gayu da iskanci, motar ta tsaya gabansu

farhaan taga ya fito daga motar, ai da gudu taje

ta rungume shi, ba tareda damuwaba tanata

dariya, su umma suka fito ai batasan dasuba

tasaki farhaan taje gun umma ataqaice dai taji

dadin ganinsu matuqa, farhaan rungumeshin da

tayi yaji qamshin sure din daya bata yace kullum

ta riqa gogawa Rexona na aloe vera ne kuma

long lasting protection ne yace lallai yarinya ta

waye harda saka turare....

[6:24PM, 5/2/2015] .: WACE CE ITA..?? 32

Na Hauwa M. Jabo

Sun qarasa gidansu iffaat goggo tagansu ba

zata duk da batasansuba amma ta gane farhan

goggo harda tuntube Dan tsabar rudewa, baki

kuwa har kunne tasan cewa zata samu alkhairi

zuwansu, ta musu shinfida aka kawo musu fura

sabuwa aka siyo nono aka xuba a cikin furar sun

kwashi damu lafiyayye farahnax hadda santi da

yake goggo ba qazama bace su iffaat ne dai

ragajabul, mutane sai zuwa kallon su akeyi,

iffaat dai bata gaida farahnax ba, ke ko kallon

gefenta batayiba, iffaat tace wa farhaan yazo ta

kaishi yaga gari, yakuwa biyota sun zaga garin

tana nuna mai guraren da tayi hatsabibanci

sunata dariya ko ina kallonsu akeyi wasu suna

gulma ana cewa ta lalace, har yanzu ba miji

amma ba halin magana yanxu mutum yaji ba

daidaiba ba Wanda zai iya tunkararta da zancen

rashin miji, dasu dijee aka zaga garin duk gunda

ya masa kyau sai ya tsaya ya dauki photo har

sukaje bakin ruwa, suka shiga kwale kwale yayi

hotuna sosai, qarshe yayi photo da iffaat bakin

ruwa, hotunan sunyi kyau sosai iffaat tayi haske

yanxu cox kullum sai sunyi wanka tanason ta

zama yar gayuuu....

Bayan sun dawo gida umma tace miyasa bamu

tafi da farahnax ba, iffaat tayi sauri tace au

dama tare akazo da ita?? Ni banma gantaba sai

yanxu. Taci gaba umma kinsan farahnax ta

tsaneni har na baro birni batamin magana,

shiyasa nima na fita harkarta, kowa sharhin nata

ya bashi dariya. duk suka kwashe da dariya, nan

dai aka shiryasu sundaina fada,

Su umma suna son a basu iffaat taci gaba da

musu aiki, koda ba aiki takeyiba yanxu kamar

yarsu take Dan Allah yasakawa umma qaunar

yarinyar, dama ga iffaat akwai shiga rai, ran

iffaat baiso tafiyaba amma idan ta tuna abinda

goggo tace mata sai taji gara ma tabar garin

wataqila birni ta samu miji tayi Aure,

Sun tafi akan nanda sati daya za'a aiko a tafi da

iffaat

Sun ma goggo alkhairi sai washe baki takeyi,

itakam yayan kishiya sun mata rana, koda bata

haihuba ta moresu.

****

Bayan Sati daya akaxo daukar iffaat ta buga

qafa a qasa akan ita sam baxatajeba sai anyi

bikin qawayenta dijee da rukayya, goggo tasata

daki, ta mata huduba,

Yanxu idan kika zauna har bikin su wallahi

gulmarki kawai zasu riqayi ace har qawayenki

sunyi Aure ke bakiyiba kinga ba dadi haka, gara

kije birni abin ki, ki raqayin gayu kamar yar

yarinyar nan danaga sunxo da ita har ki sami

miji Dan gayu irinki kiyi aurenki a birni, idan

kuma zama zakiyi bakin mutane yakamaki to

shike nan. Maganar goggo ta shigeta , gara birni

da qauye, ta hada kayanta taje tayi sallama da

su dijee ransu baisoba tana babbar qawa ayi

bikinsu batanan amma ba yanda ta iya itama

taso ayi da ita, amma goggo ta hore mata

kunne......

[6:46PM, 5/2/2015] .: WACE CE ITA..?? 33

Na Hauwa M. Jabo

Iffaat an dawo birni system dinda Dana yanxu ba

daya bane cox yanzu aikinta yafi Nada sauqi

yanxu dakin farahnax take gyarawa Dana

umma...

Ranar iffaat ta qare aiki tana zaune ita kadai a

Palo umma da Abba duk sun tafi aiki farahnax ta

tafi skull taji sallamar mace ta amsa tashigo, wa

zata gani yar baqarta, wacce take kwaikwayon

gayu a gurinta, batasan lokacinda ta miqe

tsayeba ta washe mata baki ta gaisheta a

mutunce kamar ba itaba, yar baqa ta amsa tana

mamakin waye wannan mai fara'a haka, duk da

har yanxu da sauran qauyancinta batayi kama

da house girl ba, ta zauna tana tambayar

farahnax, tace ai ta tafi makaranta, amma ta

kusa dawowa, suna zaune ta kawo mata ruwa

da abin tabawa iffaat sai satar kallonta take,

aranta tace ita ba wata kyakyawa bace sai iya

gayu, Allah ya nuna mata ranarda zata zama Yar

gayu irin wannan. Tana chikin tunani saiga

farhaan ya fito, tana hangoshi sai naga ta sa

hannu a jaka ta dauko turare ta qara fesewa a

hankali ta mayar da sauri, batasan na gantaba,

ta gyara zama tana wani murmushi.

Farhaaah ya Iso,

Tana wani kashe murya, yanda tamin magana

daban yanda tamai daban wato akwai banbanci

tsakanin mace da namiji ko duk chikin

gayunne,?? Yaya farhaan kayi wuyar gani, ya

dan sosa qeya abubuwan ne sai a slow zainb, ya

kike yasu hajiya? Lfya lau tana wani maqe

murya, araina nace dama sunanta zainab dama

sai ita ance duk zainb haka suke da rawan kai

da kurin banxa.. yanda take masa duk sonda

nake mata sai naji lokaci daya na tsaneta, ta

bani haushi, narasa dalilin da yasa raina ya

baci.!! Kodai dan ta cika kurine yasa haka oho,

hira suke dashi tasaki jiki tana fari da ido tana

kashe murya tana Neman gindin zama,

Ihuuun farahnax naje zainb khalifa kece gidan

mu haka?

Kai I miss much wallahi tunda kikazo

bangankiba ina kika shigane? Wallahi karatunne

kinsan sai a hankali,! hahaha hadda Ku gifted

karatu na Baku wahala, chaiii dariss God

oooooo, farahnax akwaiki da zolaya,sukasa

dariya tajata suka wuce daki...

Bayan sun wuce farhaaah ya juyo kaina yan

mata yar gidan umma, har yanxu ba'a iya gayun

bane, na harareshi na zubar Dan duk na

tsaneshi duk haushi yake bani daya biyewa

wannan zainb din, ya min kallon banganeba

Mina miki kuma? namai kallon ya rage naka ni

tashi na wuce dakina, na barshi yana mamakin

mi ya faaru yarinya kamar hawainiya lokaci daya

sai ta sauya, bayan da safee sun gaisa koma

miye ya rage nata.

******************

Farhaaah yaune zai wuce Canada karatunsa,

ana tadin rabuwa naji yana cewa yakamata

asaka yarinyar chan makaranta, umma tace

itama tayi wannan tunani Dan ranar taga yanda

take sallah ban iya komaiba hatta alwula ma

bata iyaba Kowa ya aminta da shawarar

farhaaah na Sanya iffaat boko ..

Farhaaah dai ya baqunci Canada yabar iyayensa

da kewa.

Muje zuwa muji yanda su iffaat za'a fara karatun

boko idan ta waye ya style din zai koma.!!!

[9:55PM, 5/4/2015] .: WACE CE ITA..?? 34

Na Hauwa M.Jabo

**************

Tun ranarda farhaaah yabar naija gidan yake

yiwa iffaat duhu da girma tin bata baiwa abin

muhimmanci, amma tana damuwa matuqa yanxu

har taji abin yana neman ya gagareta, haka

takejin zuciyanta na wani bugawa duk lokacinda

ta tunoshi, idan aka kira sunanshi sai taji kamar

zuciyanta tafito waje, ta rasa gane yanayinda

takejin ita ba wayoba bare ta gane cewa ta

kamu.

A duniya iyayen farhaan sunada kirki kuma sun

mata halacci a rayuwarta a matsayinta na yar

aiki amma sun mayar da ita kamar yarsu An

nema mata mai lesson, haka an sakata

makaranta tana zuwa, haka tana zuwa gun

malamin hadda da farahnax suna karatu tare,

gata da saurin fahimta so gun lessen da yawa

ake mata karatun,

Duk karatunnan da take lokaci daya idan ta tuna

farhaaah sai taji ta manta komai hatta takan

manta WACE CE ITA, In short rayuwa a gidan

bata mata dadi ko kadan, umma tasha

tambayarta mi yake damunta amma saita fuske

tace ba komai idan aka matsa sai tace ta tuna

babantane!!

Sau tari zuciyanta takan mata qunci taji batason

jin komai sai taje lanbu ta haye bishiya tayi kuka

son ranta, ba Wanda yake jinta a gurin, idan ta

qare ta dawo gida idan ma idonta sun nuna

takance bacci tayi,

********

An Sami Hutun makaranta anan farahnax tasa

rigima sai an tafi Canada gun Yaya farhaaah, da

yake ita iffaat karatunta a baibai yake shi yasa

takeshan wahala a gun lesson yanxu haka ko

Hutu batada sabida anason a mata jumping to

jss3 hakan yasa karatun ya danqaremata. Sun

shirya tafiya canada Abba ya kaita gidan wani

abokinsa Ajiya har su dawo daga Canada din.

Kuma yace yarsace,

gidan sunada mutunci abinda ya bani mamaki

shine nan ne gidan su Yar baqa wato zainb

khalifa sun mutuntani coz Basusan gaskiyar

Wace ce ni ba, Dan zaman da nayi gun zainb

khalifa na koyo abubuwa ba kadan ba gata very

friendly saidai tacika rawar kai da jiji dakai sai

qaryar yaruka kala kala, gashi malama iffaat

yanxuma take koyon turanci bare wani yare,

Dan sati ukun da nayi da yake zainb akwai

surutu sai na rage jin zafinda da nakeji idan na

tuna farhaaah, Allah mai iko tanason tayi tadin

farhaan da yar baqarta idan ta tuna WACE CE

ITA sai taja bakinta ta dinke,Dan ta kula kamar

Yar baqa bunsurace Kowa so takeyi.

Satin su umma uku suka dawo, sun mini tsaraba

kamar nice yarsu, ba abin da yafi bugeni kamar

kayan da farhaan yace a kawomin, da body

spray na Rexona da sure, idan naji qamshinsu

yakansa na riqa wani tunanin da ni kaina bana

gane mi nake ciki ..

[10:02PM, 5/4/2015] .: WACE E ITA..?? 35

Na Hauwa M. Jabo

A cikin kayan da Yaya Farhaan ya siyomin

hadda waya wai mu riqa gaisawa, ranar da aka

bata kayan Dan murna ko bacci takasa yi, kuma

wannan abinda takeyi bata gane komai,

**

wayar ni ban iya komaiba hasalima nidai saidai

na gaisa dashii in miqa musu, tawa wayar

kullum tana qasan pillow karatu ya sakata gaba,

ga abinda ta daukarwa kanta tunene tunanene...

farahnax ta koya min yanda ake amfani da

waya, ta kira min yaya farhaaah munyi waya

dashi, Wanda tunda ya tafi saudaya muka gaisa

shima ina fara magana ta tsinke,

Mun gaisa sosai yanayi yana jefomin English ina

ganewa amma bana iya bashi amsa, har yan

kudin dake cikin suka qare abinka da

international call..

Bayan kaman kwana hudu ranar na dawo lesson

ina danne danne a wayar kawai tayi karo da

maganar da sukayi da Yaya farhaan, zan iya CE

muku duk yinin ranar abinda ta saurara kenan,

ta rasa mi yasa komai nashi burgeta yakeyi,

bama kamar idan taji dariyarshiba, itama saita

dara haka take zama ta miqe gafafu tayita

saurare tana dariya, wannan voice yasata

walwala ranar farahnax taso ta gane sai kawai

ta daina saurare dan bata iya delete ba,

Sai yanzu ta gane mi wannan takardar da goggo

ta bata tace yayyenta sunce ta kira take nufi,

Ta nemota a cikin kayanta ta saka amma wayar

tata ba kudi, ta je gun farahnax tace ta kira

mata wannan number, farahnax kuwa chatting

takeyi bazata iya bata wayantaba sai ta saka

mata recharge card na 1,500 ta saka mata

number tace ta kira, ta koma dakinta haka tayi

ta kira ba tareda tasan kiran yana shigaba saida

ta bar miss call 47...

Ameen bayan ya dawo yaga miss call da yawa

sai ya kira,

Tayi sallama, ya amsa yadauka mamarshi ne

Dan kusan muryarsu iri dayane, mama lafiya kira

haka ?? sai tace ba Maman shi bane ya tabbatar

da wrong number ne sai kawai yace wrong

number ya kashe, bai tsaya yaji abinda zataceba,

Itama dataga haka sai bata qara kiran number

ba,

***************

Kwanaki sun tafi iffaah ta waye iya wayewa

kamar ba Yar aikiba, wani lokaci Idan sunfita

tareda farahnax bazaka ganetaba cox tafi

farahnax kyau nesa ba kusa ba, saidai har yanxu

qauyancinta da yake nuturally ne sai bai

saketaba tana taba abinta, gata bakinta baya

shiru duk abinda ta gani saita tambaya gata a

waye a dressing amma a aikace har yanxu da

saura...

shekara ta zagayo iffat zata koma qauyensu Dan

sallah da azumi achan kamar yanda sukayi

alqawari run farko,ta rasa gane dalilin da yasa

ranta bayason komawa qauye kodan zancen

goggo ne da take cewa za'a saka mata ido a

qauye tayi zamanta birni! ko kuwa rabuwa da

iyayen farhaan da, ko mahaifiyarsa ta kalla sai

taji sanyi sabida tsabar kamarsu da farhaaah.....

[10:05PM, 5/4/2015] .: WACE CE ITA..?? 36

Na Hauwa M. Jabo

**************

Iffaah ta isa qauyensu cike da tunanin rabuwa

da da iyayen farhaaan..

Goggo tayi mamakin yanda ihhatu ta chanza tayi

kyau duk wani Abu da ake buqata a gurin mace

ihhatunta tana dashi saidai tunda iffaat taje bata

zuwa ko ina daga gida sai gida, ta natsu

matuqar natsuwa, ga yawan shiru shiru da

takeyi.

Ranar goggo ke tambayarta bata sami miji a

birniba, goggo ni har yanxu ba Wanda

yakesona,! Ta dafe qirji kardai birnin ma kin

musu halinsu kin kashe kasuwarki, zancen goggo

ya bata dariya, goggo Allah ne bai kawoba,

hakane kuma Dan yanxu naga kin tsama yan

mata, wallahi sai mai mota zaki aura kikaini

makka ko? Ta amsa da sosai kuwa ta fada tana

miqewa tashige daki, zan iya CE muku tunda

iffaah ta dawo qauye kullum sai tayi kuka, wani

Abu takeji ya tsaya mata a zuci ya tokareta ya

hanata sakat, bata iya aikin komai Idan wannan

abin ya motsa mata.. abinka da yarinta Sam

bata gane cewa soyayyah bace, bata gane kanta

Sam. sau tari takanje bayan gari ta sami bishiya

ta zauna taci kukanta har ta godewa Allah,

sannan ta dawo gida ba abinda yafi damunta illa

rashin gane takamammen abinda yake damunta.

Wayartace tayi qara, ta dauka farahnax ce.

Hello

Ta amsa tanajin dadi

Farahnax chikin dariya take maganar bayan sun

qare qaisawa, kee iffaat Yaya ya dawo dazu sai

tambayar ki yakeyi, qirjintane yayi bala'en

bugawa sai ta tsinci kanta da zubar da hawaye,

na rashin dalili ta yi shiru.

Hello hello iffo kinajina? Tanata magana amma

iffaah ta kasa bata amsa, qarshe ta tsinke

wayar, iffaat ta shige dan dakinta ta zauna ta

rasa mi yake damunta yan watannanin Miyasa

duk lokacinda take tunanin yaya farhan take

shiga wani hali??

Miyasa duk taji sunanshi sai taji faduwar gaba??

Miyasa taji tanason ta Ganinshi yanxu ??

Miyasa duk ta zauna labarin sa take sonyi??

Kai tambayoyinta sunyi yawa, batada amsar ko

daya. Tayi wani tsaki

Ba abinda yake daga mata hankali irin son ganin

farhaan da takesonyi, Wanda ji take kamar tayi

fiffike taje ta Ganshi,

Amma ba halin yin haka,

Su iffaat an fada tarkon soyayyah amma batada

labari har yanxu ba tasan miye soba..

[10:11PM, 5/4/2015] .: WACE CE ITA..?? 37

Na Hauwa M.Jabo

***********

Kwanaki sunja gaba har anyi sallah qarama,

iffaat zata koma gidan aikinta a birni, tun lokacin

da farhaaah yazo batayi waya dashiba jifa jifa

tana kiran su umma ta gaidasu, kuma farahnax

tana turo mata recharging wayanta.

Ta shirya tsab sai birni,

Su umma sunyi murnar zuwanta matuqa ko

banza umma nasonta Dan akwai bada labarin

ban dariya kamar me shi yasa daga umma har

Abba zaune sukeyi tana basu labari suna kwasar

dariya.

Wannan karo an samu chanxi iffaat ta dawo

amma ba komai tsakaninta dasu, musamman

umman farhaan kunyar su takeji! Da kuwa zaune

take tasasu gaba tana basu labari suna dariya,

gashi kullum tanada sabon labarin da zata

bayar, bata maimaici amma yanxu Dogon motsi

bata iyayi gabansu, Ashe akwai abinda zai iya

chanza wannan hatsabibiyar yarinya,?? Hmmm

sai soyayyah.. soyayyar da ita kanta batasan

tanayiba,

Kai amma ni jabo na jinjinama duk soyayyar da

tayi tasirin chanxa wannan yarinya koda ta qara

wayewa yanxu...

*******

Iffaat miyasa tunda kika dawo kika daina bamu

labari?? ta sunne kai qasa tayi murmushi ba

komai hajiya! Nidai wannan zuwa hutu baiyimin

ba yarinya duk ta susuce sai rama takeyi? Ko

wani Abu ya faru bakyason fada mana??

Laaa hajiya bakomai Abba yace ki kyaleta kinsan

fa ta qara girma hankali yana shigarta, duk aka

saka dariya,

Farahnax ce ta shigo tare da wata yarinya

kyakyawa zatakai 24yrs kyakyawace sosai, tana

shigowa tace kinganta, yarinyar mai amsa sunan

suhailah ta gaida su umma da abba a kunyace,

ta kalleni cikin fara'a tace Ashe ma qaramace

sosai gata kyakyawa kuwa saidai tafini kyau da

kike cewa munyi kama., umma tace ai kuwa

nima sai yanxu naga wannan kama da kuke

cewa sunyi, saidai yata iffaat tafi kyau, sukayi

dariya gaba daya iffaat ta gaisheda suhailah

umma tace kuje daki mana, suka wuce umma

tace na bisu mama na tashi na bisu, anan

farahnax take baiwa Suhaila labarina sunata

dariya, sai nadan saki jiki dasu dama wani lokaci

zaman kadaicine ke haifar mata da damuwa bata

saniba..

Suna tsaka da hira wayar Suhaila tayi qara, ta

dauka tana kashe murya, duk da cewa da English

suke maganar hakan bai hanani fahimtar dawa

take maganaba kuma mi suke fadaba, farahnax

tana bani labari amma hankalina Sam baya tare

da ita qirjintane ke dukan uku uku wani baqin

ciki Mara dalili takeji Wanda ya haifar mata da

rashin natsuwa lokaci daya, Daidai nan kunnenta

ya jiyo mata maganar da takasa tantance

sanadiyar rudewarta sai ganinta tayi a asibiti....!

[12:04AM, 5/5/2015] .: WACE CE ITA..?? 38

Na Hauwa M. Jabo

Tana bude ido taga Su umma sun zagayeta Yar

budurwar na zaune gefenta itada farahnax, sai

nan ta tuna da abinda kunnuwanta suka jiyo

mata, LAAA KINGA NA MANTA IFFO BANGAYA

MIKIBA, KINA QAUYE AKA YIWA YAYA FARHAAN

BAIKO DA SUHAILA..!!!! Hawaye ne suka wanke

mata fuska shaaaaar, idan bata mantaba

Wannan maganar itace qarshe maganar da taji

sai yanxu da ta farka ta ganta a asibiti, ta

motsa hannu taji yayi nauyi ta qurawa Suhaila

ido mi yasa taji tana Sonta aranta?? Amma sai

take ganin kamar ba sontane takeyiba tsanarta

takeyi,?? Tanajin Suhaila har cikin ranta amma

kuma tsanarta tayi yawa a zuciyanta. tana tsaka

da tunani umma ta dafataa ta mata sannu, ta

kalli umma tace hajiya miya faru?? Ya akayi

mukazo asibiti?

Umma ta bata amsa da kin samu sauqi dai ko?

suna haka sai ga nurse tazo ta dubata aka

tabbatarda yanxu ba abinda yake damunta, illaa

kawai ta rage tunani....

Ta tashi zaune anan farahnax ta bata labari

muna tadi dake nake gaya miki an yiwa Yaya

farhaan baiko da Suhaila sai kawai naga kin

danne kai kina juyawa kika miqe tsaye sai kuma

naga kin kika fadi sumammaiya, Suhaila ta katse

wayar mukayo kanki muka kira umma taxo aka

saka miki ruwa amma ko motsi daga qarshe sai

Abba yace a kawoki asibiti, farahnax tace miyake

damunki iffo?? Tunda kika dawo gida kika chanja

ko su sukace miki ki riqa yi mana haka? Wallahi

iffo banajin dadin ganin ki a haka, Dan zaman da

mukayi na Saba da tsokanarki da labaranki

Masu dadi, shiyasa ma na kawo Suhaila itama ki

bata labarai sai Kuma haka ta faru, please ki

saki jiki damu ke Yar uwarmuce kinji.!? Aranta

tace da nasan abinda yake damuna Dana fada

kodan samun natsuwar xuciyata..

Ta kallesu tayi murmushi ba komaifa, sai tayi

shiru hawaye suka gangaromata,umma ta matso

Ku bar min yarinta ta qarajin sauqi sannan Ku

fara mata jarida. Dukansu suka saka dariya har

iffaat din saida tadan murmusa.

Saida ta kwana daya da yini sannan aka

sallamesu.

**

sun koma gida umma da farahnax suka sa iffaat

gaba sai ta fadi abinda yake damunta. Amma ta

murje ido tace bakomai koda yake ba komai din

tunda ita kanta batasan abinda yake damunta

ba, nifa tinda ta dawo Hutu banga dariyarta sau

ukuba, umma tace nimadai banganiba umma

ranar abbanku yace a kirata ta bashi labari

amma tazo ba wani labari,

Iffaat!! Na'am hajiya! Ki mana magana zama

damune kike gajiya dashi ko kuma wani yake

quntata miki ko kuma wani Abu yake faruwa a

qauye??

Kawai sai ta fashe da kuka, kuka mai tsuma

zuciya, ita kanta batasan sanadin kukanba,

sukayita rarrashi har tayi shiru, ki fada mana

minene idan mune mu gyara muryan ta a dishe

tace wallahi Baku bane hajiya, nima wallahi

bansan abinda yake damunaba haka kawai idan

ina zaune sainaji raina ya baci ko kuma na

riqajin inason wani Abu amma bansan ko miyeba

qunci yamin yawa hajiya ta qara fashewa da

wani kuka, sukayi chirko chirko, chan iffaat tace

mamarta takeso .....

[12:04AM, 5/5/2015] .: WACE CE ITA..?? 39

Na Hauwa M. Jabo

Umma ta nunfasa tace idan wannan ne

damuwarki karki damu xamu nemo miki mamarki

duk inda take, ta danyi shiru amma jifa jifa

takan zubarda hawaye, bayan kwana biyu, muna

zaune palo nidai kamar hoto ko nace gunki

kawai cika wuri nakeyi. Suhaila ce ta shigo ina

ganinta naji qirjina ya wani buga, da Leda a

hannu, tana murmushi ta gaida umma tace nazo

dubiyar mara lafiyane suka saka dariya ai ga

tanan taji sauqi, ta zauna tamin ya jiki, na amsa

mata inata kallonta har tadan tsargu, suhaila

tace iffaat wallahi kinyi kama da qanwar

babanmu sosai saidai tafiki haske amma hatta

gashinki irin natane ke ko murmushinku iri daya

tafiyarku ma iridayace ke hatta maganarku iri

dayane ke komai naku iri daya, duk aka saka

dariya har iffaat din ganin yanda Suhaila ta

jajirce da bayani, sai kun sami lokaci kixo muje

gidan mu ki ganta a gurinta nake zaune, iffat ta

amsa da insha Allah....

*****

Iffaat dai bata gane karatu yanxu, gashi an mata

nisa sosai abubuwan da bata yisuba a lesson

take samu a namatasu, karatun ma haushi yake

bata yanxu, zaman gidan ya gundureta, idan har

aka zauna Idan ba hirar farhaan akeyiba bata

taba samun sukuni a rayuwarta, wutar sonsa

kullum Dada ruruwa take a zuciyarta amma har

yanzu bata gane cewa she is fall in love ba...

Yar baqa qawarta tayi tambayarta har ta gaji sai

tace ba komai, to batasan mi yake damunta ba

bare ta fada,

Zaman birni ya gagare iffaat, kusan kullum saita

xubar da hawaye wace irin rayuwace wannan?!

ta matsa musu akan ita sai ta koma gurin

iyayenta ta gaji da zama anan, aka buga sama

da qasa amma taqi amincewa har suka gayawa

abba,

Ranar yasa aka kirata ya tambayeta ko ana

mata wani abinne tace ba abinda ake mata,

iffaat bamu daukeki a matsayin Yar aikiba a

matsayin Yar cikinmu muka daukeki wannan

dalilin yasa har muka damuwa da damuwarki,

muka sakaki makaranta Dan kema ki sami gata

da yanci irin Wanda ko wacce yarinya take samu

a gidan mahaifinta, iffaat kamar jiran abba take

ta fara kuka kamar ranta zai fita, Abba nagode

da dawainiyar da kukayi dani Allah ya saka da

alkhairi, abba wallahi ni kaina bansan abinda

yake damunaba rayuwata bata min dadi ba

abinda yake burgeni a duniya komai haushi yake

bani, banason naci gaba da wannan hali na

damuwa kuma na sakaku akan shakkun kanku,

wallahi kun min komai a rayuwa kuma na gode,

wata qila Idan na koma qauyenmu tunda nasan

yayyena suna zuwa nemana wataqil Idan nagan

su in sami sassauci.

Amma Dan Allah Abba Ku mayar dani gida taci

gaba da kukanta......

Tofa muje zuwa muji anya zata iya rayuwar

qauye? Yama za'ayi ta gane cewa soyayyah ce

take damunta...??!

[11:44PM, 5/5/2015] .: WACE CE ITA..?? 40

Na Hauwa M.Jabo

Abba Ku taimakamin ku mayar dani gidan mu,

jikin kowa yayi sanyi yanda take kuka kamar

ranta zai fita ta basu tausayi koni Jabo ta

matuqar bani tausayi Dan saida nayimata qwalla,

tabbas So bala'eeee ne, yana zautar da mutum

ya rasa mi yake masa dadi yama rasa gane

kansa,! zaiyi loosing din control dinsa ne gaba

daya, ko manya ya suke fafatawa da soyayya

bare yarinya Yar shekara 15 irin iffaat da har

Yanxu batada wani wayo bare har ta gane wane

hali take ciki....

Abba yace To ki daina kuka iffaat za'akaiki gida

dama Dan kada ya zama mune muke shiga

haqqinki ba tare da mun saniba amma tunda

kince bakomai kin zabi hakan shikenan, dukansu

basu ji dadin tafiyar da iffaat zatayiba, amma ba

yanda suka iya dole su saka mata ido, farahnax

ma ta sameta a dakinta tana kwance bayan ta

hada kayan ta, yanxu iffo tafiya zakiyi ki

barmu?? Muka miki dan Allah da har bakya iya

zama damu?? Ta kalleta tace sister wallahi ba

haka bane bakumin komaiba, kawai rainane baya

min dadi kuma bansan dalilin hakanba, kuyi

haquri Dan Allah, anan dai sukayi hirar qarshe,

koda iffo taqi sakin jikinta...

sun mata goma na arziki suka bata kudi masu

yawa sannan akasa driver yakaita har qofar

gidansu.

Shikenan iffaat ta baro gidansu farhaan.....

********

Iffaat a qauyen su,

Ashe yanzu bala'en yake bata saniba, yanzu

take qara shiga damuwa yanzu take gane cewa

ganin iyayen farhaaan rahamane gareta, amma

kuma still bata gano hakanba, ganin su da

takeyi yana raqe mata qunci matuqa, ta

sukukuce kamar ba itaba kai duk Wanda yaga

iffaat sai yayi mamakinta bata magana, Yar gayu

kam da take burin zama ta Riga ta zama, saidai

so silent yanzu take yanxu. goggo har tana tsoro

kardai ba abin kunya tayo aka korota birnin ba!!

*******

Watan iffat biyu a qauye ba walwala kullum

fuskar nan a turnuqe kamar ta dijee dama dijee

haka take ba sakin fuska su iffaat ne masu

dariya, yanzu kam iffaat ta zama Yar baqin rai

fiye da dijee..

Ranar iffaat ta tashi da ciwon cikinta har Yanxu

goggo batasan ta fara period ba tasha magani

ciwon ya fada mata tana zaune cikin runfar

qofar dakinta da Dan tsinke a hannunta tana

tsane a qasa taji sallama ta amsa batareda ta

dago kaiba tsul goggo ta fito daki tana washe

baki na dago kai na kalleshi, ke ihhatu bakiga

yayanki yaxoba, koda na Dade ban ganshiba

hakan bai hanani ganeshiba Yaya nane! Taje

gunsa na fada jikinsa tna kuka shima dai yayi

gwalla, suka zauna saman tabarma,

Yaya Ameen yake cewa goggo kinsan kuwa ba

nan nakeda niyyar zuwa ba sai naga na biyo ta

kusa danan nace bari na shigo qauyen namu in

gaisheki, Ashe rabon naga Yar mamane kullum

zancenki take mana, nayi murmushin jin dadi

Dan uwa Rabin jiki ciwon cikinta tuni ya ware sai

murna takeyi tana xubar da yan hawayen

murna..

Nan take Ya kira Mama ya gayamata ai gani ya

sameni yanxu mama murna kamar ta kasheta

yau taji autanta munyi magana ta ita inatajin

dadi,

Anan aka kitse akan gobe Yaya zaizo ya fafi dani

daidai nan na Dan shirya, goggo ranta baisoba

don iffaat ce rufin asirinta gata ba da bare

jika.....

[11:48PM, 5/5/2015] .: WACE CE ITA 41

Na Hauwa M. Jabo

Tun da safee iffaat ta shirya kayan da take

buqata sai rawar jiki takeyi duk da har yanxu

zuciyanta a qunci take hakan bai hanata

zagwadin ganin mahaifiyarta ba, goggo ta

sakata taje tayi ban kwana da mutanen , taje

tayi bankwana dasu, wasu nata mamakin

natsuwarta kowa na fadin albarkacin bakinsa,

taje gidan qawayenta dijee da tsohon ciki abin

sai Wanda ya gani, tana tsaka da ban kwana

akace mata yayan ta yazo zasu wuce, a gurguje

tayi sallama ta dawo gida...

Ranar goggo tayi kuka kamar ranta zai fita tana

ganin kamar hanyar samunta duk ta to she

kenan... ta manta samu da rashi na Allah ne....

****************

Guraren 6 na yamma suka Isa zaria birnin

zazzau amma iffaat anyi bacci a mota so bata

gane garinba, direct unguwarsu aka wuce da ita

gyallesu, iffaat sun tararda mama tana ta gyare

gyare tarbon autarta, tana ganina taxo ta

rungumeni tana yan hawaye, nima hawayen

nakeyi Yaya Ameen kuwa yanata dariya, yace

mama murnace haka harda kuka haba miye aciki

Dan ba iffaah tunda nida Yaya Ali mumanan,

dama kullum ta damesu da zancen iffaah

autarta, mama ta harareshi ai kowa matsayinsa

daban, taja autarta suka wuce daki suna

marmarin ganin juna,

a takaqaice zuwan iffaat yayimusu dadi babban

yayan su mai suna Yaya Ali shine babba kuma

Allah ya azzurtashi matuqa tun bayan rabuwar

mamansu iffaat da babansu ta dawo birni gurin

yayanta dama chan su yayyen iffaat gurin yayan

mamansu suke suna karatu so basuyi zaman

qauye ba iffaat ce kawai gurin mamar kuma da

suka rabu da baban sai ya kwace ta da qarfi da

yaji... Yaya Ali Allah ya azzurtashi sosai bayan

business da yakeyi tareda qanin mamanshi yana

aikin Kaduna in short dai suna shanawa wannan

gidan ma da suke ciki shiya Gina ma mamashi...

Iffaat ta kalli gidanda suke ciki aranta tace

wannaan gidan kenan gadansune zatayi duk

abinda take so bawanda zai hanata rayuwa

sabuwa jin dadi sabo komai sabo saidai batasan

bazata iya chanza kuntacciyar xuciyartaba....

Lol.

[11:57PM, 5/5/2015] .: WACE CE ITA..?? 42

Na Hauwa M. Jabo

Rayuwa gidan mahaifiyarta Yana mata dadi

matuqa tana samun gata ta kowane fanni,

Sai yanxu ta gane cewa wannan garin garinsu

farhaaah ne, koda ko za'a kasheta bazata bata

gane gidan su farhaaan din amma dai ta gane

makarantarda aka sakata da tana gidansu

farhaaan nan guraren PZ ne. Yanxu kuma Hall

Mark international school aka sakata kuma duk

gurare dayane...

mama ta samo mata mai lesson Yana mata a

gida, islamiya ma tana zuwa anan unguwarsu ta

gyallesu,

saidai a tunanin iffaat xuwa gidansu gun

mahaifiyarta zai sa ta daina damu wa batasan

ba anan gixo yake saqaba ita zuciya kawai

burinta takai ga wannan abin da takeso idan ba

hakaba kuwa ba zaman lfya..

*****

Wata rana maman iffaat take tambayarta lfy

bata walwala? Tace ba komai mama. Mama tace

kodai bakyajin dadin zama damune?

Laaaa mama wallahi ba haka bane nafison nan

da ko ina har gidansu..... Sai kuma tayi shiru sai

mama tace har gidansu waye?? Ba kowa mama,

hmmmmm.

nidai da yawa mama nakanji banajin dadine

saina riqajin kamar inason wani abu Amma

bansan ko miyeba haka zan kasance chikin

damuwa.... iffaat tama mama bayanin abinda

takeji, tace wani abin mama sai idan na tuna

yaran gidan da nayi aiki,! Sai nayi tajin raina

yana wani iri, kawai mama shine ba wani abubw

kuma inaga kamar sabone ko mama, mama tayi

murmushi tace Eh inaga sabon ne kawai.

mamadai ta gano cewa iffaat wani take so

amma itama mamar bata fahimci ko wayeba

Kuma iffaat din har yanxu batada wayon da zata

san cewa ta fada tarkon soyayyar farhaaan ne,

mama da ta fahimci halin da yarta take ciki sai

ta dada janta jiki ko zata mantar da ita wannan

mugun ciwo da yake addabarta..

Sau da yawa idan iffaat ta shiga daki ta fara

tunane tunane sai taga kamar ba ita bace.. taci

kuka taci kuka har ta godewa Allah....

***

Wata rana iffaat bayan ta fito a class sai ga

wasu yan samari sun wuceta tana jikin class

suka fara mata hy yan mata ji mana,! iffaat

kamar bata jisuba, sukayi iskancinsu suka gaji

suka wuce bata ko daga kai ta kallesuba, har

sukaje suka dawo suka qara mata tayi banxa

dasu....

Bayan sun wuce tana zaune sai ta fara tunanin

iskanchin da aka mata ta gyale, anya nice iffaat

kuwa? Wacce Ko ba'akasa dani nakan siya,

nakan sayi fada da kudina bare a tsokaneni,

waima wayannan yaran zasu min iskanci na

gyalesu tayi tsaki kamar an tsira mata allura, ta

tashi ta fito tsakiyar makaranta don nemansu,

fitanta keda wuya tayi karo da malamai suna

kora a koma class juyawanda zatayi head boy

dinsu ya fara tsula mata bulala tayi class a guje

amma taji bulalar ba kadan ba taso ta bisu ta

musu nata rashin kunya aka koreta, ko minti 10

ba'ayiba ta manta da abin ta koma tunaninta da

baida natija ,.....

[12:11AM, 5/6/2015] .: WACE CE ITA..??43

Na Hauwa M.Jabo

*********

Wata rana Suna hira da mama take bata labarin

tanada ya,

yarinyar yayanta ne lokacinda babanki ya

kwaceki to lokacin aka bani ita, to ina take

mama? Tana Qatar karatu takeyi wannan

shekarar zata kammala data qare sai a mata

aure,! iffaat tayi dariya da shewa Ashe dai

mama mun kusa shan biki, kinsan kuwa inason

biki a rayuwata, lokacinda muna qauye kullum

sai naje biki ko ba'a gayyaceniba kuma ni

bandamu da su bani abinciba kawai mukanje

muyi tsokana, idan za'a kai amarya da dare mu

sami allura muyita tsikarawa matane ko Ku

muyiwa yayansu da suka Goya suyita kuka sai

mu boye, mama Dan tsabar dariya saida ta kai

kwance, tashajin ana cewa iffaat ta gagari Kowa

a qauye amma ba tasan abin yakai hakaba, nidai

jabo araina nace to iffaat kan tayi hatsabibancin

da yafi wannanma!! Yanxu kinga mama biki

namu sai yanda mukayi ko, mama cikin dariya

tace eh, da yake har baiko ma an mata ai.

Habawa? Ashe munada biki duk suka saka

dariya...

iffaat tanatason ta tambayi mama hoton yar tata

amma Sam ta manta har ta kusa dawowa!

***

Ranar da Yar mama zata dawo gidan mu yasha

gyara anyi girke girke kala kala, guraren qarfe

2pm ta sauka Kaduna daga chan aka daukota

aka kawo ta Zaria da yake an barni gida,

isowarsu keda wuya,

wazan gani a matsayin yar uwata?? Suhaila

matar da akayiwa farhaaah baiko da ita, wani

rass taji ni kaina jabo sai da naji bugun zuciyarta

kuma na tabbatarda kuma Masu karatu kunjiyo

kobakujiba????

Suhaila tana ganina tahau dariya tana

tambayata farahnax, cox ita achan tasañi, tace

iffo surprise dina kukayi haka? So happy wallahi

ina farahnax din? Itakam iffaat tsaye tayi tana

mamaki abinda take gani, wato Suhaila itace

yarinyarda aka baiwa mamanta kuma itace

matar farhaaah!

Sai yanxu ta gane kamar da akace sunyi da

Suhaila, Ashe jini dayane, sai yanxu ta gane

dalilin da yasa takejin Suhaila cikin ranta amma

kuma miyasa take tsanar ta?? Suhaila sai

washe baki take tana tambayarta farahnax,

mama tace keewai waya gaya miki tasan

farahnax? Ke dadi miji dadi dangin miji!! Laaa

mama wallahi gidansu fa nake ganinta farko,

itace wacce nace miki akwai wata cousin din

farhaan mai ban dariya kuma kunyi kama kin

tuna mama? Eh na tuna to itace, nifarko ma na

dauka aiki take a gidan sai ranan umman

farhaan tace ba Yar aiki bace yartace,

anan dai na fayyace musu komai mama da

Suhaila suka gane cewa gidan su farhaan goggo

ta kawoni aiki, mama taji dadin yanda umma ta

kula dani har tana cewa suruka ta gari......

Nida Suhaila mun dinke mun zama kamar abokai

dukda ta girmeni nesa ba kusaba cox lokacin ina

16 ita kuma tana 24 ne, duk iyayen farhaan sun

ganeni sunata jin dadi, mama kuwa hadda zuwa

godiya yanda aka kula da yarta har umma tana

cewa a qara bata ita...

****

Bansan miyasa nake tsanar Suhaila ba nakan

kwatanta boyewa araina amma duk ranarda naji

sunyi waya da farhaaah to kuwa duk yanda

zanyi sai nasan yanda zanyi muyi fada da

Suhaila da yake ita ba mai kulawa da qananan

abubuwa bace so bata kulawa dani Sam. Banxa

takeyi dani kamar ba da ita nake yiba, nayita

gabata har na gaji na sauko.

Mama ta kula kamar na tsaneta amma ita kanta

bata gano dilin hakan ba,

Ranar mama ta kirani take tambaya ta miyake

faruwa tsakanina da Yar uwata nafara kame

kame, ba komai, mamadai tayi ta min wayo har

na fara magana wallahi mama nikaina bansan

dalilin da yasa mafiyawan lokuta nake jin na

tsanetaba haka kawai take bani haushi kuma

wallahi mama banajin dadin abubuwan da nake

mata ta fashe da kuka, mama ta rarrasheta, taso

ta gano sirrin amma aranta tace bari saita qara

gwadata.

Tofa MUJE ZUWA MUJI IRIN GWJIN DA MAMA

ZATAMA IFFAAT...

DA KUMA WANE IRIN MATAKI ZATA DAUKA

AKAN HAKA, ZATA IYA ADALCI KO KUWA SON

KAI ZATAYI TSAKSNIN YARTA DA YAR

RIQONTA??

[11:13PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..??44

Na Hauwa M.Jabo

******

Ranar da farhaaah yazo Nigeria goben aranar

aka hada mai tarba ta musamman a gidan su

iffaat, duk da cewa bata iya komaiba kuma har

yanxu bata taba shiga kitchen da sunan girkiba

amma ta nemo hutunan girki a internet, an hada

kayan komai da komai ana jiran Yy farhaan, tayi

kwalliyar da itakaitaa bansan ta iyataba kuma

batasan dalilin da yasa tayitaba, Suhaila ta

tsaya tana kallonta kinganki kuwa wallahi kamar

wata amarya, please kimin irin kwalliyanki, ta

kuwa xauna gaban iffaat nidai jabo nace su

iffaat Masu haye hayen bishiya sune ake

kwalliya haka, ai yanxu kam taci uban Yar baqa

zainb khalifa da iya kwalliya iffaat ta dara tace

kina nufin kwalliyata tafi taki kyau? Sosai ma

kuwa nidai kimin tun basu qarasoba haka iffaat

ta tsinci kanta da gyashin yiwa yayar tata irin

kwalliyarta, ta nemi dalilin yin hakan ba dalili,

Suhaila har ta gaji da bibiyarta akan ta mata irin

kwalliyar ta iffaat ta nace akan bata iyaba itama

Sa'a tayi tama kanta.......

Guraren la'asar saigasu farhaan da farahnax sun

iso gidan ita Kuma tana dakin Yayanta tana

hada wasu kaya kamin baqin su Iso, dariyar

farahnax taji tana tambayar ina iffaat take, ta

hango farhaan, wani raaas taji zuciyata ta shiga

harbawa kuma batasan daliliba, farhaan guy ne

lafiyayye duk yanda namiji yake cikakke mai

lafiya to farhaah yana cikinsu dogo ne mai jiki

daidai shi yanada faffadan qirji haka yanada

sajee a fuskarshi wanda ya kwanta yayi luf a

fuskarshi, yana zuwa naga yy Suhaila taje ta

fada jikinsa ya rungumeta, iffat taji wani dum

dum dum...!!! wasu emergency hawayene suka

bulbulo daga fuskata, lokaci daya taji ta qara

tsanar Suhaila da farhaan, kee mi kikeyi anan ga

baqi chan tun dazu naji suna kwala miki kira,?

Ta waigo ba tare da tasan ko wayeba, idonta

sun Riga sun rufe, ta watsamai harara, miya

dameka da abin da nakeyi anan.!? Sokoko yayi

yana mamaki, iffaat kinsan wa yake magana

kuwa??

Tace a gadare nasani Yaya ameen ne yake

magana, kaiiii iffaat too lallai bakida kunya,

Ta kalleshi ido cike da hawaye tana kuka tace

Kaine bakada kunya, ni inada kunya Kaine kaine

Yaya, ta fada jikinsa tana dukan qirjinsa sai jin

yayi tayi deef tayi tana Neman faduwa qasa,

kamin kace kobo ta sumaaa.....

[11:20PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..?? 45

Na Hauwa M.Jabo

Ya riqeta ya dagota yana jijjigata yana kiran

sunan ta, amma iffatu ko motsi haka ya dauketa

chak dama ba wani aukine da itaba, yakaita

dakinsa yaci gaba da jijjigata yana fadin sunan

ta, farahnax yaji tana kiran iffaat iffaat kina

ina??

Ya xuba mata ruwa shiru,Yayi sauri ya tura qofa

yayiwa mama waya bata daukaba tana chan

suna gaisawa da suruki, ya dakko ruwa a fridge

ya qara zuba mata yarinya still ko motsi yaga

kamin yaje ya kira mama zata iya mutuwa, tuni

ya fara hawaye yana kiran sunanta yana jijjigata,

Muryar mama yaji, Aminu naga ka kirani lafiya?

Nidai kuje Ku gaisa fa yaron chan mai Neman

qanwarku Suhaila, mama kizo iffaat ba lafiya,

Subhanallahi.!! Miya sameta ta shigo da takalmi

a qafa taga yarta kwance kamar gawa ta fara

jijjigata, taqara watsa mata duka ruwann dake

cikin robar swan din, iffaat tayi wani gwauro

numfashi ta bude Ido kadan ta kalli yayanta ta

kalli mamanta ta fashe da kuka, mama ta

rungumeta tana rarrashinta, wai ya akayi haka

aminu miya sameta?? Wallahi mama kawai naga

ta tsaya jikin window tana kallon su farhaaah da

sukazo shine na tambayeta miya

faru,..................

Yayi bayanin komai umma ta kalleta taga ta rufe

ido lallai xatonta ya zama gaskiya, tayi jeeem

amma ba halin magana wannan tashin hankali

har ina.!?

Suna zaune jugun jugun dasu saiga Suhaila ta

shigo, iffaat wai ina kika shiga tun dazu sunata

nemanki Yy farhaan kuwa ya kawo miki....... Ai

bata qarasa zancen ma taga su mama an xuba

uban tagumi ta kallesu mama miya sami sister

na?? Hankalinta ya tashi, mama batace komai.

iffaat kuwa sai ma qara runtse ido tayi wasu

hawayen suka ci gaba da sauko mata, tsanar ta

takeji a ranta Yaya Ameen zai fara mata bayani

mama ta katseshi. Kije ki sallami baqinki ki dawo

mama wallahi ba zan iya komaiba sister na

acikin wannan halin mama miya faru da ita,?

bakomai bane kune kullum cikin saka takalmi

masu tsini garin rawar kai ta fadi kanta yadan

daki jikin qofa shine kawaifa,

Ta dafe qirji Allah sarki sister sannu kinji bara na

kirawosu anan suxo su dubaki ta miqe tana

sauri

Iffat da qarfin hali tace kada ki kirasu banason

ganinsu bana so, mama tayi sauri ta toshe

matabaki, Batasan lokacinda ta fada hakan ba

lallai iffaat soyayya tana wujijjigata, suhaila ta

waigo mi tace mama??

Cewa tayi kada ki kirasu,

Nima ina ganin ki barsu kada hankalinsu ya

tashi,...

[11:25PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..??46

Na Hauwa M. Jabo

To mama mixance dasu?? Yy amin yace kice na

aiketa har yanxu bata dawoba, ta tafi cike da

baqin cikin da jimamin faduwar Yar uwarta Allah

sarki Suhaila akwai sanyin hali.

Bayan ta tafi yaya yake tambayar mama miyasa

baki fada mata gaskiya ba?? To sai kawai nace

tana kallon su sai ta suma ai kaga dole aji

tabakinta kamin ayanke hukunci,ya jinjina kai

hakane, anan suka zauna har saida su farhaan

suka tafi, Suhaila taxo ta fada musu sun tafi, su

tashi su koma cikin gida. Iffaat tace ita batason

chikin gida dakin yayanta zata zauna, dama

iffaat da naci sukayi sukayi Amma inaaa ko bude

Ido batayiba bare ta tankasu suka gaji suka

barta, har sunkai bakin qofa, Suhaila ta dawo.

Suhaila tace Iffaat na kawo miki kayan da Yy

farhaan ya siyo miki??

Ta daka mata tsawa da bataso. saida su mama

suka jiyo kuma duk abinnan da akeyi idonta a

rufe suke taqi budesu, tana budewa hawaye ne

zasu fito..

********

Bayan faruwar haka da yan kwanaki iffaat yanda

take jin ta tsani Suhaila ba dalili yana matuqar

damunta, duk abinda takeyi idan Suhaila ta saka

hannu sai ta tsani wannan abin tabarshi kenan

har abada, idan kuwa ta saka bakinta sai ta

gwaleta gaban ko waye, ranar maman Suhaila

hajiya kulu taxo gidan yini dan yinin da tayi ta

fahimci yanda iffaat ke yiwa Suhaila sai ranta

baiyi dadiba har take tambayar Suhaila tana

kuwa jin dadi bayan xuwan iffaat?? tace lfy lau

idan kikaga tana haka to wani ya bata mata rai

a skull sai ta sauke akaina, maman Suhaila tayi

dariya tace kice iffatun dai har yanxu hukumace

kenan suka dara gabaki dayansu...

*****

Ranar iffaat tana zaune gindin bishiya a

makaranta tana shan malt da snack sai taji

wasu yan mata suna tadi akan soyayya ta kuwa

kashe kunne, dayar take bada labarin cewa

tanason yaron qanin baban ta amma batasan

yanda zata bullowa abinba tana bayanin duk

abinda takeji a ranta game dashi dayar ma tana

fadar nata keni Zumar abinda yafi bani haushi

baimasan inayi, Zibraheeem tace kar kuwa

kisake ya sani Dan raini ne zai shiga tsakaninku.

Iffat sai taji d same da abin da takeji suma shi

sukeji, ta juyo ta kallesu sun girmeta duka ta

musu sallama, please tambaya ce dani, naji kuna

wata magana, yanxu kuna nufin duk maijin

wayannan abubawan da kuka fada shine me,??

dayar tace its mean ya fada tarkon soyayya!! ta

kallesu, kuna nufin nima na fadane? Toni wa

nakeso?? Suka kalli juna suka kwashe da dariya,

mu muka San Wanda kikeso, dayar tace Wanda

kikejin haka

akanshi shi kikeso!!

Ta zare Ido kuna nufin YAYA FARHAAAH

NAKESO??

suka kalleta sukayi tsaki ke baquwace yarinya

dayar tayi dariya tace kinji suna mai dadi daji

gayen zai hadu, daji akwai zafi a gunsa har naji

inasonsa !! Iffaat ta juyo a fusace keeee ta

wanketa da mari.....

[11:28PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..??47

Na Hauwa M. Jabo

Yan matan gaba daya suka miqe tsaye, dayar ta

gefe ta kwasheta da mari itama dayar taci

kwalarta suka mata lilis,duk sun buge mata

fuska, suna tsaka da dukanta saiga baba sajeen

yana kora kamin yazo sun gudu bai tsaya duba

halinda iffaat take cikiba kawai yaganta kamar

tsugune yahau zuba mata bulala tun tana kuka

har tayi shiru. Ke wace irin mai taurin kaice?

Maza ki tashi ki wuce class bai tsaya kulataba

ya hango wasu yara biyu ya bisu a guje suka

tsere, iffaat dai an mata lilis baki sai jini yake

yaji duka gun yan mata gashi baba sajeen ya

qara mata wani, tana nan gurin taji ana cewa

still tanananfa, kixo mu dubata, nidai baxanjeba

ke kije , habadai sabida kefa na daketa kuma

kice bazakijeba, please kixo muje, sukazo gurin

iffaat sai kuka ganta tana xubar da jinin baki da

hanci duk hijabinta ya lalace, nidai jabo abin har

mamaki ya bani wai iffaat ce take daukar xilla

yau!! Rayuwa juyi juyi....!!!

Suka dagota suka tallabota hannu biyu dayar ta

ruga ta siyo pure water Leda daya sukaxo iffaat

bata iya koda magana, suka wanke mata jikinta

suka qaro ruwa suka wanke mata hijabinta da

duk gun da jini ya bata, dayar take gulma a

hankali tace kalli gashinta! Dayar tace ummm

nagani, suka kalli iffaat wacce ta bige mata

bakince ta fara bata haquri, sai dayar ma tac ci

gaba da bata haquri batace dasu komai ba,

hasali ita batajin zafin dukanda aka mata illa

xafin Cewar da akayi Yy farhaaan takeso.!

Sunata bata haquri ita kuwa tanata tunaninta.!

Wai yaza'ayi taso saurayin yayaryta?

Yaza'ayi taso Wanda nake kallo a matsayin

yayantaa?

Lokaci daya ta tuna da rashin kamun kansa

shegen Neman mata, ta tuna duk wani iskanci

nata yasanshi, shine yafi kowa sanin WACE CE

ITA, har abada baxai karbi soyayyar taba, idan

ma zai karba yazatayi da yayarta Suhaila, anya

ma gaskiya suka gaya mata da sukace sonshi

takeyi,???

[11:32PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..?? 48

Na Hauwa M. Jabo

Tayi ajiyar xuciya Ta juyo ta kallesu sunyi cirko

cirko dasu, da kunburarren bakinta take musu

magana, kiyi haquri Dan Allah wallahi bansan

lokacinda na daki qawarkiba, sukace ba komai

kema kiyi haquri, nan dai suka yafi juna suka

qulla qawance da ita da alqawarin zasu

taimakamata da duk abinda sukasan zasu iya.

Haka suka zauna Kowa shiru har aka tashi

makaranta..

***

iffaat na zuwa gida mama ta fara tambayar ta

lafiya kike kunbura haka kamar jabo tayi kuka??

Wallahi mama anyo korane, zasu shiga class tayi

karo da wata frnd dinta sai kuma ta fadi qasa

shine bakinta ya kunbura, Subhanallahi. Kinga

yanda kika kunbura kuwa? Allah ya tsare gaba

ta amsa da amin ta wuce dakinta.

Bayan ta shiga daki ta cire uniform, ta zauna ta

fara tunanin abinda yan matannan suka fada

tabbas kuwa idan har abinda suka fada shine

kaji kanason mutum to wallahi tanason Yaya

farhaaan, aiki jaa wanda zai zama mijin yayarta

takeso??

Dole ta dauki mataki wa zuciyarta.! Tayi

murmushi Kai amma so shegene shine ya hanata

sukuni shekara da shekaru! Amma so ya

wanketa! Waima miyasa bata ganeba? Tayi tsaki

ni ko zan mutu zan auri Yy farhaan ne gashi da

shegen son mata! Duk maganar da takeyi aranta

takeyinta amma Sam zuciyarta bata aminta da

ko kalma daya tataba, kawai tana fadane amma

tasan yanda takeji da gudu idan yace yana so

zata amince,...

Hmmmm dole zuciya taso Yy farhaan ta saba

dashi, yy farhaan duk inda namiji mai lfy zai

shiga yana shiga haka tayita karanto siffarsa da

maganar sa da tafiyarsa da murmushinsa tana

murmushi, lallai ta yarda tanasonsa but miye

mafita???

Dole ne ta ijiye sonsa taci gaba da danneshi har

Allah ya bata mijinta tayi aure??

Anya zata iya kuwa??

Zaki iya mana dayar zuciyarta ta bata amsa aiki

ja gabanta..

Suhaila ce ta shigo tana waya ta gane da

farhaan take wayar kuma taji yanayinda ta saba

ji amma ta basar.....

[11:37PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..?? 49

Na Hauwa M. Jabo

Ta juyo suka hada ido Subhanallahi sister miya

sameki? Tambayawa kawai tayi batayi tunanin

samun amsa ba, Dan tasan halin mutuniyarta,

cox jiyama da dare ma kamin su kwanta bacci

sun sayar da hali..

Ta miqe zaune Ki bari kawai Yy Suhaila..... ta

bata labarin abinda yanda ta baiwa mama labari,

Eyyah kinji yy farhaan yaba miki sannu Allah ya

kiyaye gaba, sai kuma taji sanyi aranta, nagode

bani mu gaisa, ta karba tana karba ya fara mata

tsiya anya faduwa kikayi ba tsokana kikayiba aka

miki duka?

Tasa dariya. Laaa wallahi aah faduwa nayi, koda

naga yanzu kin natsu kamar bakeba,amma kinfi

kyau da qiriniyafa, tayi dariya sai mu samo miki

miji mu aurar dake kowa ya huta, kar kuma mu

samo ki kashe Dan mutane da rigima, da yake

Suhaila tanajinta itama tayi dariya, Yy Suhaila

karbi wayar ki kinji tsiyar da yy farhaan yake min

ko !?

Ta bata waya chike da nishadi,

Ta shiga bayi ta kalli kanta a madubi taga yanda

ta kunbura kamar rukayyah qawarta ta qauye

Dan haka fuskanta take kamar fulawa ta kwana

ta tashi, tayi wanka ta fito, tanata Jan Suhaila

da hira itadai Suhaila abin mamaki yake bata,

cox tun dawowarta ba ranar da basa saida hali

har ta saba, idan basuyi da safeba tasan kamin

a kwanta sai anyi, dama ita bamai kulawa bace,

haka bata baiwa Abu muhimmanci...!

*********

Tun daga wannan ranar iffaat ta daina fada da

Suhaila idan taga tana wayarta sai ta tashi ta

fice gun mama ko ta danna eir ps dinta tana

sauraro waqoqinta. Ataqaice dai sun daina fada

da juna, bata kula da ita idan tana abinda tasan

zai bata mata rai,

Iffaat itada qawayenta. skull mate dinta zainb

Ibrahim da zainb Umar da ita iffaat Habeeb, da

yake sunan baban farhaan take amfani dashi tun

lokacinda ya sakata makaranta har yanxu.

Zan iya ce muku ZZ sun ninka su dijee iskanci

da rashin kunya kowa yasansu a makarantar

kuma anqi korarsu sai suka hadu da iffaat

Habawa sai abin ya qaru dama iffaat ba bayaba

soyayya ce ta dangwasheta amma yanxu kam ta

gano bakin zaren so bonewa takeyi bata baiwa

abin muhimmanci Sam duk da tana jin zafi cikin

ranta...

[11:43PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..?? 50

Na Hauwa M. Jabo

Suna zaune gindin bishiya sun fito break aka

fara kora ko ajikinsu tadinsu suke yi suna baiwa

iffaat shawara kada ta yarda ta nuna tanason

farhaan harma yanda suke gida daya da wacce

zai aura, daga sama suka ji bulala akansu

Malam tunde ne zibraheem ta tashi ta riqe

bulalarshi, haba sir miyasa kullum sai ka riqa

dukanmu Dan muna kunyar Kane kawai muka

sharewa but gaskiya ya isa haka.!

Ta fuske, ki sakarmin bulala Mara kunya, sai

nayi maganinku a skull dinnan, duk da English

suke zancen nan.

Da hausa zumar tace saidai muyi maganin juna

bayajin hausa so baiji mi sukace ba, yadai

qyalesu ya wuce gaba abinsa, iffaat tace

malamin nan Dan rainin wayo ne, suka kama

hanya ko wacce ta kama hanyar clss dinsu da

yake duk yara sun shiga clss sai su gagararru.

Koda iffaat taje clss malami ya shiga kuma

Malam jocob ne baya wasa ko kadan,economic

master, ta fuske yace from ware? Tace daga

gidanku da hausa ta fada duk clss suka saka

dariya, Habawa yaji haushi ya gane zagin sa

tayi ya fara zuba mata bulala taji zafi tuni tayi

cikin sa tana duka ta kamashi da kokowa clss

ya dau ihu ana buga table, saida sukaci uban

juna kawai ta saki jiki ta fadi wai ita mai aljannu

so aljanun sun tashi, dama su ZZ sun gaya mata

cewa tayi iskancinta idan ta qare ta fadi kawai

ita batasan tayiba,

Kaji iskanci...

Haka dai akasha oga jocob a banxa gashi ta

wawwaskamai mari ta karyamai glass..

Tofa iffaat hatsabibanci ya dawo.

Akaje gun principal tace ita sam batasan tayiba

sharri ake mata, haka a ka rufe case akasha oga

jecon a banxa.

Wata rana suna zaune suna tadinsu kowa ya tafi

class saisu kawai saiga principal ta biyo hanyar

duk yara suna clss amma su suna nan zaune

kamin ta qaraso iffatu tuni ta haye bishiya,

principal taga hawanta amma bata San

kowayeba, iffaat kuwa tayi tsanda a hankali ta

hau rufin classes din kamar mage taje qarshen

rufin ta diro qasa, koda taje class ta tarar

malimi ya shiga yana note ta lallaba ta shiga ba

tare da ya gantaba tayi sauri ta dauko note book

ta fara rubutu.

Tana fara rubutu saiga principal tare da ZZ

akaxo nemanta, malamin mu yace lallai koda ya

shigo ina clss din, students dinda suka ganni

sukace yanxu Na shigo malamin yaji haushi kuna

nufin kunfini ganine ko qarya nakeyi? ya za'ayi

mutum ya shigo clss banganshiba.....

[11:50PM, 5/7/2015] .: WACE CE ITA..??51

Na Hauwa M.Jabo

Duk sukayi tseet principal taja su ZZ aka Basu

punishment mai tsanani dama ansha kawo

qararsu gaskiya sunji jiki ba kadan ba ga duka

ga uban aikinda aka sakasu, duk sun kamawa

iffaat mutunci sunqi mata magana, aka tashi

suka kama hanyarsu itama tayi banxa dasu.

Gobe sukazo nan ma gaba sukeyi sun shirya

mata sharri da zataci duka amma bata saniba

tazo ta musu magana sukayi banza da ita har ta

juya sai Zumar tace ke banza ce wallahi, jiya

shine kika gudu kika barmu, mufa duk wani

hanyar dojewa mun koya miki amma ke baki

koya mana komaiba kalli Dan Allah jiya yanda

aka lallasamu, ta nuna mata hannunta dayasha

bulaloli.

iffaat tayi dariya son ranta sannan ta Basu

haquri suka fara tambayar ta ya akayi daga

saman bishiya ta wuce clss? Harda baba sajeen

aka saka yahau bishiya amma baki ba labarin ki

tayi dariya sosai lallai bakusan iffaatu Yar

mamaba nan ta Basu details yanda tayi sunata

mamaki lallai wannan yarinyar mayyace, kuma

hartashiga class malamin bai gantaba......

Sun shirya mata sharri ZZ kenan sun hada mata

gadar zare sukace sujee baya, sunje baya kuma

an hana xuwa wajen da yake iffat bata taba

zuwa gurin ba, kuma batasan an hana zuwa

gurinba suka turata sukace suna zuwa, har ta

shiga sai kawai ta hango bishiyar mangoro ya

nuna tayi murmushi haba Ashe dadi suka turota

tasha tuni ta haye bishiya ta fara tsinko mango

tana saman bishiya kawai sai taji maganar su

da wani malami wallahi tananan kullum nan

take zuwa mun gaya mata an hana zuwa tace

ba ruwanta. yanxu ma mungaya mata zamu

fada muku tace sai dai a kasheta, kaji mugayen

qawaye....

Iffaat tanajin haka tayi tsanda daga saman

bishiyar tahau garu ta dira a toilet, ta barsu a

gurin, taje da gudu ta kira principal tace tana

bayi taji maganar mata da maxa a bayan skull

principal taje da sajeen koda akaje aka gansu

duk sun cire hijabi suna Neman ta wai ko ta hau

bishiya coz ta gaya musu ta iya hawa bishiya ko

wace irikuwa.

jikinsu ya fara rawa ganin principal tana zuwa ta

fara yiwa Malaminda yake tare dasu fada mi

yaxo yi da yayan mutane anan bayan an hana

zuwa anan tasa aka tafi da su ZZ office.. iffaat

tayi wata dariya ta musu gwalo aranta tace

wallahi saidai Ku wahala duk case dn dana shiga

a duniya zan iya fitardakaina yanxu ya rage naku

ta kakkabe hunnu ta qara gaba.....

Muje zuwa.

[11:13AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 52

Na Hauwa M.Jabo

Anje dasu office ana tuhumarsu da aikata lalata,

Dan yan iska kawai suke zuwa gurin kuma duk

Wanda aka kama gurin qa'idace korarsa za'ayi

da sukaga lallai korarsu za'ayi suka fara kuka

suka fadi gaskiya principal abin ya bata dariya

tace a kira iffaat aka kirata akace ta fadi gaskiya

ko a hadasu a koresu ta fuske tace gaskiyar

kenan yanda ZZ suke kuka sai suka bata

tausayi, sai kuma ta tuna da ita aka kama

korarta za'ayi imani dai ya shigeta ta fadi

gaskiya...

abin ya ba kowa dariya wato ko junansu basu

bariba sharri suka mata tafisu zama yar duniya

ta rama, nan dai aka shirya su aka musu fada

akace suje class tun a hanya iffaat take musu

dariya tana maimaita abinda ya faru tun suna

daurewa har suka fara dariya lallai iffaat taci

jinjina duk abinda takeyi Allah yana

taimakonta......

Akwai lokacin da iffaat tayi zazabi aka bata

maganin mura da maganin bacci to maganin

yana Jakarta ne, sai kawai ranar tayi lettin shiga

clss to malamin akwai shegen gayu da jiji da kai

kawai ta karbi permission tace xataje bayi da

gyar ya barta ta fita taje ta siyo drink ta bude ta

saka maganin baccin har guda shida a ciki ta

girgiza ta kulle ta baiwa wata students tace ta

kaiwa malaminsu tace inji anti funke.

Aka kawo masa yana mamakin funke zata kawo

mai drink yace bari yayi sauri ya shanye kar azo

ace ba nashi bane, ya zuge banxa ko minti biyu

ba'ayi ya buge da bacci iffaat sukayi iskanci a

clss sir na bacci

sannan ta daukeshi hoto a wayarta ta bayan

kowa ya qare aka tayar dashi bacci ya fara na

yan giya tamai video, yanata sunbatu yana fadin

ya akayine baby??wallahi saida aka kwasheshi

ranar cox ya kasa ko bude idonsa..

Goben ranar aka saka bincike amma ba Wanda

ya gano anti iffaat...

Kai iffaat manyan duniya.

Kuma haka tayita tura video da hoton nasa gashi

malamin Dan gayu da jiji dakai tuni ta zubar mai

da clss a gurin yan matansa da sauran students,

yanxu sunansa ya koma ya akayine?? Cox

lokacin da aka tayar dashi bacci sai ya fara

fadar ya akayine baby yana layi....

Wasa wasa iffaat Iffaat an kai Ss2 su ZZ kuwa

ana final year sun yi hatsabibanci bana wasa ba

har andaina kulasa kuma iffaat ce leader

dinsu.......

[11:21AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 53

Na Hauwa M. Jabo

*******

An saka ranar auren Yy farhaan da Yy Suhaila

20/5 daidai da ranar brdy din Hauwa jabo.

Tunda aka saka ranar auren iffaat sukuni ya

qara kubce mata saidai ta fuske takeyi tayi

harka amma tana azabtuwa matuqa, ta fadawa

ZZ suka bata shawara taci gaba da haquri

kawai..

Lokaci sai matsowa yakeyi ita dai mama ta rasa

gane sirrin zuciyar iffaat farko ta gano cewa

tanason farhaan ne musamman lokacin da ta

suma, nan zatoñta ya zama gaskiya, sai kuma

yanxu komai ya tsaya mata yanda iffaat ta

chanxa gaba daya duk wani Abu da take da wa

suhaila batayinsa yanxu, hakan yana basu

mamaki sai kawai suce ta qara girmane....

An fara shirye shiryen biki su iffaat da farahnax

sune qirjin biki dama farahnax ta hada auren, shi

farhaan irin ya nuna yanason suhaila irin

soyayyar shan minti sai kawai farahnax taje ta

fadawa su umma, kuma Suhaila ce keson

farhaan sosai shi ba wani sonta yakeba, amma

ganin iyayensa sunshige gaba yasa ya sallama

ko banxa Suhaila kyakyawace kuma tana daga

cikin matan da yake so dalilin da yasa ya

amince da ita kenan. amma bai taba sontaba

daidai da rana daya..

hasalima mafi yawar da sukeyi ita take kiran shi

kuma ita Suhailar tasan ba wani sonta yakeyiba

haka take son kayanta. Allah sarki Suhaila tana

bala'en burgeni cox ba ruwanta abinda na

fahimta farhaan ya sace zuciyar Suhaila da iffaat

ne amma iffaat ta barwa Allah tasan ba yanda

za'ayi ya aureta bayan ma ya rainta gata

qanwar matarshi...

haka dai akayi komai cikin jin dadi auren ya

qayatar anyi komai cikin jin dadi da arxiki naira

taci ubanta...

An kai amarya dakin mijinta,

Hmmm Daren dai iffaat ba'ayi bacci ba gaskiya

na jinjinawa iffaat matuqa cox tayi jarrumta ba

kadan ba nidai jabo idan nice wallahi sai nayi

ciwo, Ashe Banida labari hadda iffaat anyi

zazzabin daurewa kawai takeyi, ta bani tausayi

matuqa kowa sai yace gajiya ce da kuma kewar

Yar uwarta har mama Dan yanxu mama ta gane

ba komai zatonta ba gaskiya bane,.....

[11:27AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..??54

Na Hauwa M. Jabo

Suhaila anachan ana barsar amarci da

angonta...

Iffaat kuwa ananan ana fama da axaba gwanin

ban tausayi....

ko wata Biyu ba'ayi farhaan ya fara chanza wa

ya gama da ita kenan, ya koma Neman

matanshi duk qoqarin Suhaila na kyautata mishi

ta ko wace hanya duk abinda tasan zaiji dadi

tana masashi iya qarfinta kuma qaryane yace

bata gamsar dashi cox a dare daya sai yayi

round biyu haka take haqura duk da tana jin jikii

burinta ta faranta masa, amma abanza takeyi su

farhaan kam ba hali.. dama mai hali baya barin

halinsa abin dai ba dadin ji sau tari takan

qyanqyasawa iffaat amma tace kada ta fadawa

mama.....

Ranar Suhaila ta kama farhaan yana waya da

wata akan zasu hadu wani guri, ranta ya baci ta

mai magana kuma tace sai ya fada mata ina

zaije sannan ta barshi ya fita...

Habawa kamar jiranta yake ya wani taso mata

kamar ya cinyeta hadda su gori wai albarkar

qanwarsa takeci ita tasa ya aureta, ba itace

choice dinsaba inda yake shiga banan yake

fitaba, maganganun farhaan sun qona Suhaila

matuqa ta shige daki tana kuka...!

Allah sarki Suhaila.!!

Kamar daga sama saiga iffaat yan mata dama

iffaat bata cika xuwa Gidan ba cox abinda take

gani ranta yana quna, idan dai kaga tazo Gidan

to aikota akayi, yanxuma wani tsimine aka kawo

mata daga sokoto shine akace ta kawo mata

aka aiko iffaat...

tin tsakar gida take kiran yy Suhaila har tashigo

palo bata nan, tashiga daki taganta tana kuka

hankalinta ya tashi tayi ta tambaya amma taqi

fada mata dagyar ta fada mata Ashe yana bakin

qofa yana jinta tana qare fada ya shigo a

fusace.. Kin gayawa uwata sai ta kasheni ko ta

hanani yin abunda naga dama wawuya kawai.!

Ashe bazaki iya rufawa mijinki asiriba..?? yayi

tsaki ya koma Palo tofa masu sayen fada da

kudin su bare an sami dalili,ta miqe tsaye ta

tsallake Suhaila ta fito Palo...

Taxo gaban sa ta riqe kunkumi amma wallahi

Yaya farhaan ka bani mamaki, ashe har yanxu

kana wannan mugun halin naka?? Koda ba abin

mamaki bane hali zanen dutse. Ta nunashi da

hannu abin kunya namiji kamilalle a fuska amma

xuciya ta shedan tirr da hali irin naka, koda ba

komai bane wayewace!!! Amma Allah wadaran

wayewa irin taka wacce akeyinta da Neman

mata ni wall...... Kamin ta qare farhaan ya miqe

ya kwashe ta da mari kuuut.....

[11:32AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 55

Na Hauwa M. Jabo

kaiiii..! Ya na sauke hannu itama ta wanke shi

da nata Marin, kamar daga sama saiga Suhaila

taga an mari mijinta tuni ta wanke iffaat da mari

tofa iffaat ansha mari ta daga kai ta kalli yayarta

taga yanda tayi wani iri haushi ya qara kamata,

dama ita iffaat duk bala'en da takewa farhann

da biyune ga kishin abin da ya aikata ga baqin

cikin rashin samunsa. Yayar ta fara mata masifa,

bata cewa yayar komaiba taci gaba da yimai

masifa da fitsara yayar tanata cewa ta bari tana

rufe mata baki Amma inaaa saida takai aya ta

zazzagemasa kwandon rashin mutunci Suhaila

abin ya qara kwabe mata baqin ciki kamar ta

hade rai ta mutu, ta qare tamai tsaki ta murguda

baki ta juyo gun yayar ke kuma ki zauna yana

qunsa miki baqin ciki kina shiga daki kina kuka

kamar wata doluwa.!

ta kama hanyar fita Suhaila ta bita tanason tace

kada ta fadawa mama farhaan ya daka mata

tsawa akan ta dawo, ta rasa yanda zatayi, taxo

gabansa ta tsuguna tana bashi haquri abin

mamaki yace ba komai ya wuce laifin sane

shima dama baiji dadin abinda ya fada mataba

nan dai suka shirya hmmm mata da miji sai

Allah hardai suka aikata aikin lada nan take,

farhaaan yasan bala'en iffaat yafi nashi nesa ba

kusaba cox shi yasan WACE CE ITA baisan

miyasa yake shakkartaba.!!

Ta isa gida a fusace amma kuma saita tsinci

kanta da kasa fadar abinda ya faru, ta rufa masa

asiri chaiiii soyayya bala'ece nan ma qarya ta

xubawa mama tace wasu samarine suka bata

haushi. mama tace nidai zanso naga mijinki

kullum cikin korar samari waike yarinya, tayi

murmushi ta wuce dakinta,. Tana shiga ta kulle

qofa ta fara kuka tayi nadamar dukan farhaan

koba komai ya girmeta kuma gashi mijin yayarta

haka kuma masoyinta ta tsinewa kanta yafi sau

dubu amma ita kanta batasan lokacinda ta

aikata hakan ba.!!

Farhaan kuwa duk ya damu yayi nadamar

abinda ya aikata qarshe yasa Suhaila ta kira

iffaat tana bata haquri itama ta bata haquri tana

ce mata ga yy farhaan zaiyi magana da ita ta

kashe wayar farhaan yace ta kyaleta amma ya

damu matuqa...

[11:38AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 56

Na Hauwa M. Jabo

Su ZZ an qare skull an bar su Iffaat yan mata

anata gwagwatawa Da students, dama ko ita

kadai tana abinda taga dama....

Cikin ikon Allah iffaat ana shirye shirye kammala

secndry skull any qara hankali amma fa har

yanxu tana jinyar soyayyar farhaan a zuciyarta,

ba Wanda yasani sai qawayenta ZZ....

******

Wata Ranar Suhaila taje sokoto bikin dangin

mamarta kusan sati biyu tayi bata gari, ana

gobe zata dawo tace wa iffaat taje ta gyara

mata gidanta tasan yayi qura ba kowa aciki

tunda tasan farhaan aikin banxa ne ba abinda

yake iya tabukawa kuma idan ta dawo ma ba

wani abin kirki zata iyaba gata da tsohon ciki

kwata 7 , dagyar iffaat ta aminta shima saida

aka hada da mama sannan ta aminta. mama

batasan sirrin ba iffaat tun lokacin da abin nan

ya faru bata qara zuwa Gidan Suhaila ba sai

wani zuwa da sukayi duba Suhaila itada mama,

sai kuma yau...

Waike Dan Allah idan bakiyimata wa zaki yiwa??

yarinyar tana qaunarki ta damu dake amma ke

kina Neman ki yanke zumunci mama dai haka

tayi fadanta dole tasa iffaat ta tafi Gidan..

Hmmmm Su farhaan ba'asan da zuwan iffaat

gidanba, kuma yasan sai gobe matar shi zata

dawo hankalinsa kwance shida karuwarsa...

iffaat tazo ta gyara ko ina na Gidan har ta

kammala Basu saniba suna chan ciki. haka

kawai taji tanason shiga dakin farhaan ta gyara

kuma batasan yana gidanba.

Takama hanyar dakinsa Ta buda qofar tajita

abude sai ta tsaya ta qara budewa Sanyin Ac da

qamshin turarensa ya daki hancinta ta lumshe

Ido ta dauke numfashi hadi da wani ajiyar zuciya

ta tura kai dakin tana bude ido sai taga mace

kwance tana sharar bacci daga ita sai wasu

tsinannun kayan bacci, numfashin tane ya tsaya

chak..!! tama rasa mi zata mata ta gane ta tsab

hafsa ce tsohuwar budurwar farhaan, ta tsaya

waige waige ta hango Yar yawo gefen fridge ta

Ciro ta zo zata fara zabga mata sai ta tuna duka

ana bacci bashida xafi sosai, ta bude fridge ta

samo ruwa ta juyesu a jug taje ta yaye bargon

da ta rufa ciki da qarfi, hafsa ta juya cikin

shagwaba tace dear kabarni zuwa anjima

mana.!! tace kinci ubanki keda dear. ta watsa

mata ruwan da qarfi a fuska, hafsa ta wani

zabura da qarfi tana miqewa zaune iffaat ta

kwashe banxa da mari saida ta koma kwance

tuni hafsa ta gigice, iffat kuwa batayi qasa a

guiwa ba tafara zuba mata bulala hafsa tana ihu,

ta mata lilis chan farhaan ya fito bayi da gudu

yayi turus da ganin madam iffaat.....

[11:41AM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 57

Na Hauwa M. Jabo

Bata tsaya ba taci gaba da chin uban hafsa

farhaan ya kasa aikata komai kunya ta isheshe

dagyar hafsa ta samu ta miqe tayi bayan

farhaan da gudu tana kuka, tabbas hafsa ta

gane iffaat Dan kuwa itace ta qona mata qafa

shekara wajen Shida da suka wuce, iffaat ji take

kamar ta hada da farhaan din ta musu lilis

amma bazata iya dukan farhaan ba, tsanar sa ta

rufe mata ido ta tausayawa yayarta da take

tareda fasiqi irin sa tagodewa Allah da bata

aureshiba, da saidai suyi kashin kai a gidan Dan

bazata dauki wannan iskancinba ta dakawa

hafsa tsawa tabar gidannan hafsa ta kasa fitowa

bayan farhaan ta qara mata tsawa wallahi idan

naxo sai na kakkaryaki, inbanda hafsa batada

gaskiya ai ko qanwar hafsa iffaat bazata iya

fada da itaba bare hafsa mai Shekara wajen 30,

zata kakkarya iffaat. amma tunda batada

gaskiya dole ta boye farhaan kuwa ya rungume

hannuwa yana kallon ikon Allah kunya ta isheshi

da nadamar abinda ya aikata, tayi cikin hafsa

da qarfi hafsa ta riqe farhaan da qarfi wani baqin

cikine ya qara tasomata yanda taga tana

rungume farhaan ta baya uhum su kishi manya

tayi cikinta da qarfi ta janyo gashin da tayi qara

da qarfi ta wurgata a kan fridge farhaan ya

dakawa iffaat tsawa akan miye haka ta juyo

tamai kallo keep quiet ina zuwa gunka kaima..!!!

tama hafsa gargadi kamin ta lissafa biyar tabar

gidannan hafsa dagyar ta miqe ta kwashi

kayanta a hannu taji jiki tana gudu tana tunanin

wai wannan WACE CE ITA?? House girl ce haka

kyakyawa kuma ta mata haka gaban farhaan.

Anya kuwa?? Bayan ta kori hafsa ta juyo ta kalli

farhaan ido cikin ido tana tunanin balbala masa

masifa ji take kamar zuciyarta ta fito Dan baqin

ciki aranta tace wai ita kenan inaga matarsa da

sukasan juna idan taga haka sai hade rai ta

mutu.! Ya dago ido ya mata wani kallo ta

mayataccun sexy eyes dinsa tuni ta manta

abinda takeson ta masa sai ya bata tausayi tayi

tsaki.....

Har zata fita dakin sai kuma ta daure ta dawo ta

gyara ko ina ta tattara sauran kayan hafsa data

bari ta miqa masa tace ga kanan tsohuwar

karuwarka nan idan ka bita ka kai mata.. ta juyo

kenan ya janyo mata gashi da qarfin bala'ee

saida tayi wata qara....

[12:12PM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 58

Na Hauwa M.Jabo

Ta sa hannu tana qoqarin kwacewa amma ta

kasa ya qara janyota da qarfi saigata saman

qirjinsa, ta daga kai tuni idonta sun cika da

kwalla Dan tsabar azabar da takeji, da qarfin

hali, tace, so bansan kacika wayayyeba sai ka

aikata abinda kake da niyyar aikata wa aikana.!!

yanxu ya gane manufarta tuni ya saketa yayi

tsaki ya fada bayi ya kulle kansa cike da baqin

ciki da nadama, a duniya ba wacce ya raina

kamar iffaat amma itace take gwadamai axaba,

iffaat kuwa tana samu ya saketa ta fita da sauri

ta wuce gida tana zuwa ta fada dakinta ta kulle

tana kukan takaicin rayuwa da mutum irin Yy

farhaan ta daga kai taga hoton Yaya Suhaila da

Yy farhaan sun rungume juna suna dariya tayi

tsaki,ta tashi ta cireshi ta saka a drawer ta

dawo taci gaba da tunaninta har barawo bacci

ya dauketa, bayan ta tashi taje gun mama..

Ah ah yaushe kika dawo?

Tayi murmushi wallahi tun dazu na dawo nasan

kina bacci lokacin shi yasa banma zo natayar

dakeba, okay suka yi tadi mama tana tanbayarta

ta gyara Gidan dakyau kuwa? Dan tasan son jiki

ya mata yawa

Laaa mama kin manta nayi aikatau suka saka

dariya gaba daya, Yaya Ameen ne yazo da Yaya

Ali suka zauna akayi tadin dasu suna cikin

magana Yy Suhaila ta kira...

Sister sorry na sakaki aiki da yawa,!laa kinji dai

Yy Suhaila wane aiki kuma idan ban mikiba

mawa xan yiwa, ta fara godiya, wallahi idan

kinamin godiya zan kashe wayata, to nabari yi

haquri, kin tarar da farhaan a gida?? Wallahi

Naso nace idan yananan ki masa Dan girki,

Tseeeet tayi kamar ruwa ya cita qirjinta yake

bugawa, lokaci daya ta tuna abinda ya faru

tausayi Yy Suhaila ya kama ta Amma bazata iya

fada mataba, hello kinajina kuwa sister? Tayi

xumbur ta dawo daga dogon tunanin da ta tafi..

Inaji Yy Suhaila, to ki bawa mama wayar na

miqawa mama ta tashi tsaye, Yaya Ali ya kamo

hannunta..

bayan sun qare yace wani abokinane yakeson ta

kinma sanshi Nurane mama tace nikam ko

sunansa banaso bare shi na tsani wannan yaron

akwai shegen rawar kai, iffaat tace wallahi nima

mama na tsani Nura kamar me nima dai jabo ba

abarni a bayaba gun tsanar sunan Nura mugu.

Duk aka saka dariya kowa ya tsani Nura Allah

sarki har ya bani tausayi......

**

Goben ranar tinda safe Suhaila tayi waya da iffat

ta gaya mata sun kamo hanya

Guraren qarfe 11 iffat na zaune da mama dasu

yaya da yake yau Saturday, wayar iffat tayi qara

laaaa yy Suhaila hatman sun iso, hello Yy

Suhaila kuna ina? Kun kawo hala?

Taji namiji yace ke sister din Suhailar ce ??

Tace Eh kai waye?

Sorry Dr ne daga Chika, yayar Ki sun sami

accident Allah ya mata cikawa driver kuwa

gashinan kwance ya kakkarye?

Iffaat wata irin qara ta saka ta fadi

sumammiyaaa....

[12:18PM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA..?? 59

Na Hauwa M. Jabo

Mama tayo kanta tana tambayar lafiya amma

ina iffaat ta riqa ta suma,

Yy Ali ne ya dauki wayan ya kira number Yy

Suhaila, Dr. Ya masa bayanin da ya yiwa iffaat

yace babbar motace ta shiga gabansu suka

yanka daji anan motar ta wuntsila rai yayi

halinsa Yaya Ali ma dashi da qarfin halinsa sai

da yayi kuka, ya yiwa mama bayani tuni gida ya

rude da koke koke Yy Ali yayiwa baban Suhaila

waya ya fada Masu abinda yake faruwa kamin

kace kwabo labarin rasuwar Suhaila ya baje

family namu kowa yaji mutuwar Suhaila cox

Suhaila mutunce mai mutunci ga haquri da

kawaici, bata shiga harkar da ba nataba kai

mutuwa tana dauke nagari. farhaan kam da ya

samu labari mutuwar tsaye yayi bai samu damar

maganaba saida yaga gawar Suhaila, sannan ya

fara kuka kamar qaramin yaro kamar wani

zararre, lallai ta tafi tana binsa basussuka cox

bayajin tayi wata biyu yana kyautata mata

kullum cikin muzguna mata yake, su farahnax

kam haka ta dawo kamar mahaukaciya, mutuwar

ta ratsa kowa a gidannan musamman iffaat da

farhaan da maman Suhaila.!!!

Iffat koda ta farfado har an kai Yy Suhaila

makwancinta wayyo Allah, mutuwa mai raba da

da mahaifi miji da mata Yaya fa qanwa aboki da

aboki. Mutuwa tayi yankan qauna a wannan

family...

cikinta ma anciroshi da ranshi amma da yake

wata7 ne kwana biyu yayi yabi uwar shi, cikin

da farhaan yayi burin ta zubar tun tana amarya

zan iya cewa ma bayason cikin.

Sauda yawa Suhaila tana kiran iffaat qanwarta

ta fada mata abinda farhaan yake mata amma

tace kada ta fadawa kowa, kuma bata taba

fadaba

Mutuwar Suhaila yasa iffaat ta qara tsanar

farhaan gani take kamar shiya kashemata Yar

uwa! amma fa still sonsa yana cikin zuciyarta,

hmmm soyayya manya..!

*****

Arba'en din Suhaila yayi daidai da fara jarabawar

su iffaat mutuwar Suhaila tadan natsar da ita

kadan dama iffaat ta iya matsuwaa idan Abu ya

faru da ita! sunyi neco da waec lfy sai jiran saka

mako, xubi xubi iffaat tana zuwa gidansu

farahnax ta gaida mamarshi da farahnax din da

kuma qawarta Yar baqa zainb khalifa,

Ranar tana zaune dakinta taji sallamar farhaan,

da yake Gidan idan aka shigo dakinsu yana daga

gefe ne sai dakin mama, tanaji ta gane tayi

banxa dashi.

Sunyi hira da mama, tanaji yana tambayar ina

iffaat tace tana daki,

Har ta manta da wani farhaan yazo gidan. Chan

taji sallamar sa a dakina, Dan amsa sallama

wajibine da nasan iffat ba zata amsa maiba, taci

gaba da aikinta, ya zauna ya fara sun batunsa,

yaga ba nasara, yace iffaat.......

[12:21PM, 5/9/2015] .: WACE CE ITA.?? 60

Na Hauwa M.Jabo

Iffaat miyasa kike min hakane? Koba komai ni

Dan uwankine tun kamin mu hadu da margayiya,

kuma naxo na auri yayarki, kina tunanin kodan

wannan ai bai dace ki riqa min wani gani ganiba,

ki tuna kin min laifinda ya dace na hukuntaki

amma na gyaleke na yafee miki..!

Anti masifa madam iffaat ta watsa mai kallon

banza hadi da wata uwar harara! Laifin me na

maka oga? Wato ma ni na maka laifi ko?? Ka

manta chin mutuncin da kake yiwa Yar uwata?

Kamanta wulaqancin da kake mata?? Ka manta

yaudarar da kake mata?? Sannan duk ka shuresu

kaxo kana cewa ni na maka laifi?? Ta daga kai

tayi karo da hotonta ita da Suhaila sun rungume

juna suna dariya. Hawaye ne suka wanke mata

fuska tayi missing din Yar uwarta abar sonta,

farhaan ya kamo hannun iffaat yana zaune iffaat

Dan Allah ki yafemin! Nasan ban kyautawa

Suhaila ba ko kadan, wallahi sai yanxu nake

ganin irin rashin kyautatawar Dana mata idan

kika yafemin tamkar itace ta yafemin ta kasa

kwace hannunta daya riqe batace komaiba.!

Tayi ajiyar zuciya ta karbe hannunta, ta zauna

har ya qare surutansa batace masa komaiba,

wallahi iffaat ina tsananin son Suhaila, ji tayi ya

daba mata wani gwaho a zuci har saida ya

gane. Nasan baxaki yardaba amma gaskiyane na

fada miki, ya gaji ya tashi Ya qara wuta..

*****

Iffaat yan mata result ya fito ana kiciniyar

shigarta jami'a ta sami damar shiga cikin nasara

an bata course dinda takeso kuma.

Dai dai lokacin auren farahnax ya matso sai

shirye shirye suke qawayen amarya, komai itace

gaba itada Yar baqa sai iyayi suke, anyi auren

farahnax lafiya ankai amarya Gidan mijinta da ke

abuja, iffaat dai kam kullum sai tayi sabon

saurayi amma ko kallo Basu ishetaba karatun ta

ta saka gaba.!

Ranar umma tayi rashin lfy sunje dubata itada

mama da maman suhaila, umma ke tambaya ta

yaushe zatay aure? Ko sai ta samo mini mai

saida ruwa irin na dijee, akasa dariya kunya ta

kamani na tashi na shige lanbu don demo

abincina na da na barsu su nan.....

KU BIYOMU DON JIN ABINDA IYAYEN

WAYANNAN YARAN ZASU TATTAUNA AKAI,

jiya banyi posting ba wallahi network yamin tsiya

nayi nayi fcbk dina ya bude yaqi buduwa kuyi

haquri.!!!

[10:49PM, 5/11/2015] .: WACE CE ITA..??61

Na Hauwa M.Jabo

Suna tsaka da labarin su saiga farhaan ya shigo

ya gaida surukansa yama ummanshi ya jiki ya

shige dakin abbansa,

Bayan ya wuce ne maman Suhaila take cewa

Allah sarki yaronnan har yanxu bai nemi

mataba? Umma tace kedai bari gashinan

Bansan mi yake jiraba, niko ga shawara, mizai

hana a hada farhaan da iffaat aure. Mama tayi

dariya kai hajiya kulu ina kika taba ganin rigima

da rigima sun hadu duk sukasa dariya umma

tace lallai kam Dan farhaan da iffaat basa zama

guri daya. Mama tace koda yake shi aure daban

ne wata qila sai kiga sun zauna lfy.

Gaskiyar magana dukansu sunyi na'am da

shawarar hajiya kulu maman Suhaila sun tsaya

akan zasu shawarci mazajensu suji,

Suna zaune suna tadi saiga iffaat da ta ciki

kyale da su mangoro da gwaiba umma tace um

um mai hali baya barin halinsa..! duk suka saka

dariya, taje ta wanko ta kawo musu suka

farasha, dama ita qa'idarta idan zatasha

mangoro saita mulmulashi yayi laushi yayi ruwa

sannan tasha. Ta kuwa miqe qafafu ta saka

basket dinda ta saka kayan a ciki ta fara shan

mangoronta tana zaune saiga farhaan ya shigo

ya kalleta, xaman da tayi ya bashi dariya ya

tuna mai da lokacin da take qarama sai yaji bari

ya tsokaneta komai ta fanjama fanjam.!!

Wai umma wannan Yar taki ba university take

xuwaba? Umma tace eh chan take kaga yata an

zama yan mata ko..!! Inafa yan mata har yanxu

bata wayeba! Kalli Dan Allah yanda take shan

mangoro kamar wata Yar ruga,! ruwan

mangoromangoro suna bin hannu, ya kwashe da

dariya hadda buga qafa ya gama quleta ya kalli

umma anya kuwa zata sami miji a haka??

Umma tace ka sakawa yata ido dayawafa miji

kam sai ta xaba Dan ma bakaga yanda ake

layiba dukansu suka dara nima dai jabo na dara

kuma Masu karatu sai Ku dara.!!

Iffaat tace umma ki barshi, ta dago ta kalleshi

ido cikin ido tace mijina sai ka Ganshi wayayye

na gaske ba irin wayewarkaba, ba Wanda yagane

habaicin da ta masa sai shi damu Masu karatu.

Yadan Sosa kai yayi murmushi qarfin hali mama

bari na tafi tunda kun hanani mangoro, umma

tace sai kace wacce da debo ta sammaka, yace

waa ai wannan tafi dijee rowa.! da zai fita ya

hada da gefen chinyarta ya take saida tayi qara

ta jefeshi da qallon mangoro......

[10:57PM, 5/11/2015] .: WACE CE ITA..?? 62

Na Hauwa M. Jabo

Mama tace Waike iffaatu bakida kunya ko, miye

na jifanshi da kwallon mangoro? umma tace

rabudamin da ya, wallahi shiya tsokaneta ina

kallonsa ya taketa, Dan ya taketa sai ta jefe shi,

karki sa mata baki Dan Allah ke iffaat tashi ki

shiga ciki.

Bayan ta wuce umma tace kin ganiko,? Haka

suke kamar tom & Jerry, hajiya kulu tace ai aure

daban yake alkhairin sa zamu nema kawai,...

***

Hajiya kulu na komawa gida ta sami mijinta

mahaifin Suhaila tamai xancen ai tuni ya amince

abbah ma da umma ta masa magana ya amince

100% mama ma haka tayi shawara da su Yaya

Ameen akan wannan auren kowa ya aminta

yanxu ya rage aji ta bakin gogayen...

Abba da umma suka kira farhaan aka fara masa

maganar Dan tsananin rudu da tsoro saida ya

manta yana gaban iyayensa, atafau farhaan yace

aah miye dalilinsa yace kawai matsayin farahnax

ya dauketa, shi bazai iya auren taba tun ana

lallashi har Abba ya yanke dole ya aureta ko

bayaso, kana tunanin zamu aura maka macen da

zakayi kuka da ita? Duk cikin mu ka fimu sanin

WACE CE ITA! cox ka zauna da ita tun tana Yar

mitsiyayarta,

Farhaan dai kawai yajisune amma Sam bai amin

taba,

Itama madam iffaat an mata maganar farko

dariya ta saka musu irin ga zancen nan Mara

kan gado.

Da taga dai da gaske akeyi kawai saita saka

musu kuka! Aka buga Sama da qasa tace bazata

auri mijin yayartaba...

Abba Suhaila ne yace sun Riga sun yanke

magana ba chanji ba mijin yayartaba ko waye

shi zata aura..

Nikam jabo abin mamaki ya bani yanda iffaat

tayi jinyar son farhaan tun batada wayo amma

yanxu ga dama ta samu tace batasosa! Uhum

kuma ga dukan alamu da gaske takeyi, ta daga

ba nasara taci gaba da kuka ta wuce dakinta,

Yaya Ameen ne yabi Yar qanwarsa yana lallashi,

Haba iffaat miye aibin farhaan? Kina gani wallahi

guy ne gashinatsatse ga kamala, wallahi yanzu

dagyar ki sami namijin na kirki kamarsa baya

shaye shaye baya Neman mata. ta dago kai da

sauri ta kalleshi amma sai ta kasa fadar cewa

yana Neman mata, kowa ya shedeshi ke kanki

shedace akan haka! Sabida kinyi rayuwa dashi,

iffaat dai batace komai ba har Yy Ameen ya qare

rarrashinta ya tashi ya fito!

Ta miqe wallahi da na auri farhaan gara na shiga

duniya....

[10:58PM, 5/11/2015] .: WACE CE ITA..?? 63

Na Hauwa M.Jabo

Tun daga ranar ta kamawa su mama mutunci ta

daina musu magana tadaina chin abinci ba

ruwanta dasu ita dole fushi, anyi sati biyu da

maganar sai ranar taji su yy da mama suna

maganar, ana maganar daurin aure kuuut saidai

wata ba itaba, ta miqe tsaye ta riqe kunkumi ta

fara shawara da zuciyarta yanxu ita iffaat har

sun isa su mata auren dole? Waima...! Idan ta

saka musu ido zasu aurar da itane, su Basu

damu da damuwartaba, abinda ya fado mata

kawai ta gudu, kai guduwa ba jarumta bace, duk

macen da za'ayiwa auren dole ta gudu ba

jaruma bace,so bataso ta gudu a ganinta ba

jaruma bace duk wani tunani sai taga bai dace

da itaba, nidai jabo zaune nayi ina kallonta ina

jiran muga abinda zata aikata, amma ga dukkan

alamu ba wani Abu da ya rage gwagwalwarta

bata aiki, sai fashewa tayi da kuka..

Yanda ta tsani halin Yy farhaan ko sonsa zai

kasheta bazata aureshiba, tanada mahaukacin

kishi

Tayita tuna yan matan farhaan din da yanda

yake musu ta runtse ido da qarfi ta daki madubi

tace Nooooooooooo, ta na kuka tana dukan

madubin duk ya yayyanke mata hannu, ashe su

mama sun jiyo mama ko a jikinta, Yy amin ne

yaxo gunta da sauri ya riqe hannunta duk ya

yayyanke, ya yiqeta ya kalleta yaga yanda ta

rame tana juyowa ta fada jikinsa tana kuka, tana

cewa Yaya ka taimakeni wallahi banason sa Yy

Ku aura min wani not Yy farhaan, yace to

shikenan kiyi shiru zamuyi magana da mama,

dagyar ya samu tayi shiru ya dauko first aid

yadan gyara mata hannun ta ta ta yayyanke, ya

jata da hira har tadan saki jiki, qarshe yace tazo

su fita yawoooooo...

[10:58PM, 5/11/2015] .: WACE CE ITA..?64

Na Hauwa M. Jabo

No ka tafi Yaya ni baxanjeba ya rarrasheta har

ta amince suka shirya suka fita. Sunje wani park

ne suna shan ice cream, hakan ya faranta mata

rai matuqa suna sha suna tadi a hankali yy amin

yake nuna mata illar abinda takeson tayi, suna

tsaka da magana tana yan kalle kalle charab ta

hango wani abu wacce ta hango ba shakka itace

ba qarya budurwar farhaan ce ramcy, tayi

murmushi su ramcy ananan da yake Yy baisan

taba tana kallon ta har ta shige ba'ayi minti

goma sai kuma ta hango farhaan, wani rasss taji

ko shakka babu tare suke da farhaan amma da

yake shi mai wayone a hankali yake takunsa, wai

farhaan wane irin jarababben mutum ne?

Tayi tsaki, yy amin yace miya faru kuma? Ta

kalleshi idonta sun kada sunyi jaa ba komai! Ya

ba komai, ta dago mai idonta da har sun zama

qanana tace ba komai yy, sukaci gaba da

tadinsu amma Sam bata tare da yy amin

tanachan tana tunanin farhaan, kusan 30mnt

Basu fitoba ta kasa haquri ta miqe tsaye, ina

zaki kuma? Y tace ina zuwa yaya ya kalleta,

yanxu zan dawo Yy, ta wuce da sauri ta shiga

Ashe cikin gurin hotel ne ta fara dubawa duk ta

zagaye gurin bata gansuba, sai taje gun

reception ta tambayi farhaan mutumin yace

mata yanada baquwa wani rass taji, tace ai na

na sani shi yace nazo na karbi saqo yayanane,

ya kalleta sosai sai ya gaya mata number

dakinsa wani dumm dummm dummmm takeji,

ana mata zagaye a zuciya ta isa gofar dakin tayi

jimm ta daure ta bubbuga saida ta buga uku

sannan aka bude, ramcy ce ta bude qofar iffaat ji

tayi kamar ta shaqeta ta mutu ramcy bata gane

iffaat ba Sam.! ta watsa mata harara, tace lfy

iffaat ta daure tace yy farhaan yace naxo na

karbi saqo na kaiwa umma, tanajin haka sai ta

saki fuska, okay bari na kirashi, ta kwala mai

kira yazo yana zuwa ya ganta.........

Tofa.

[11:19PM, 5/12/2015] .: WACE CE ITA..?? 65

Na Hauwa M. Jabo

hankalinsa ne ya tashi! Ya rude yama rasa

mizaice mata, itama haka wato wani tashin

hankalin sai mutum yama rasa mi zaiyi, ta

kalleshi tayi murmushin qarfin hali tace sannu Yy

farhaan.!! Kamin ya bata amsa hawaye ne suka

zubo mata batasan dalilin zuwansuba, gaskiya

hawayennan sun kwafsa mata taso tayi chin

mutunci cikin ruwan sanyi amma ina kuka ya

kwafsa mata, bazai yiwuba chin mutunci ana

kuka baiyiba, da sauri ta bar gurin tana juya

kenan sai ga yy amin yaxo nemanta, lafiya kike

kuka? Tace

Ta hadu da wata qawartace shine take bati

labarin mutuwar mijinta .........

Eyyah Allah yajiqanshi ina take? Tace sun wuce,

farhaan yana jinsu kuma yaji abinda tace, yayi

tunanin zata tona masa asiri amma ina bata

fadaba,

Suka kama hanya idon iffaat Sam bata gani

gabanta hawayene suke rally a fuskarta.! ta kasa

jurewa sai wani Abu takeji yana taso mata,ta

rasa gane kanta, Yy amin yana gefenta yanata

bata labari amma taqi bari su hada fuska kuma

taqi cemar komai, har suka isa suka zauna!!

Waike har yanxu kukan kikeyi?

Ta dago kai ta kalleshi, wallahi Yaya ta bani

tausayine tana matuqar son mijinta amma

mutuwa ta rabasu, sai na tuna da yy Suhaila...

yace Eyyah sai haquri Allah yajiqanta ya Dan

qara lallashinta har tayi shiru amma zuciyanta

cike da tunani.! Har suka dawo gida tunani

takeyi.

Shiko farhaan yana ganin sun bulle ya kori

ramcy tana tambayar lafiya ya daka mata tsawa

akan ta bace mai da gani, ta tattara yan kayanta

ta wuce, ya fada kogin tunani,!

Baisan miyasa wannan yarinya takeda bala'en

tasiri rayuwarsaba, duk abinda yake a boye yake

yinsa, amma kuma bawai yana damuwane da

kada a Ganshi ba amma yana jin haushi idan

iffaat ta Ganshi..! Gashi tun tana qarama

tasanshi da wannan hali,amma har yanxu

baidainaba, yasan yana fama da sonta kuma tun

tana qarama yakejin haka yaqi qasqanta hakan

ne, ya yakamata fa ya daina. Kai wannan

mitsitsiyar yarinyar tama isa ta hanashi abinda

yakeso!? Amma miyasa take yawan kamashi?

Yaja tsaki ya juya ya miqe tsaye yana zagaye

dakin. Chan ya daki iska yace auren ta kawai

zan aminta dashi shine zaiyi maganinta, shima

ya huta da azabar rashinta.

haka dai ya qare yan tunane tunanensa cike da

damuwa.

Iffaat kuwa ana isa gida ta fada daki ta kulle ta

fara sana'ar tata yanda take kishin farhaan

tasan wata rana kisan kai zatayi, gara kawai ta

nemawa kanta zama lafiya ta aureshi, ba wata

hanya da takeda da ta wuce ta amince masa

kamin baqin cikin sa ya kasheta ko banxa zata

rage azabar rashin ganinsa da take fama da ita,

haka har bacci ya dauketa, Yy amin ne ya tayar

da ita daga bacci, ya kawo mata pizza tayi

murmushi Yy amin ne kawai yake rarrashinta

idan tana fushi mama kam ko kallo bata

ishetaba itama haka....

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 67

Na Hauwa M.Jabo

20/5 idan ban mantaba yayi daidai da ranar

daurin auren yy Suhaila kuma shine ranar brdy

dina ni Hauwa Jabo wannan ranar itace rana

mafi girma da daraja a idon iffaat wannan ranar

ita ta chanxa ta daga jerin yan mata zuwa matar

aure a wannan ranar ne ta taka matsayi na

Chika da kamala,

Farhaaan kuwa jinsa yake gashinan dai ya rasa

abinda yake damunsa tsorone ko kuma murna

ko baqin ciki gashinan dai kamar ba angoba..

Ba wani shagali da akayi, Dan zance muku iffaat

har ranar dauren auren ta saida ta sulale taje

makaranta wayanda sukasan da zancen auren

suna ta mamaki irin ga serious student dinnan,

basusan dawar garinba, ai kuwa tana dawowa

tasha fada gun mama haka dai aka qare taro

akan gobe za'akai amarya gashi Kuma amarya

gobe ma tanada test gashi ance sai ta fadawa

ogan zata iya fita, sai kawai haqura tayi, ankai

amarya gurin su umma suka mata nasiha, nidai

tunda nake ban taba ganin amaryarda ana mata

nasiha tana kallon mutaneba sai iffaat ba Dan

sunkuyar dakai ba komai haka umma na mata

nasiha ido cikin ido tana kallon ta har abin ya

baiwa umma dariya amma ta fuske Abba ma

yayi har ya bata kudi yace ko zata buqaci wani

Abu. Daganan aka kwashi amarya aka kaita

Gidan mijinta PURHUUN...

Abokan ango sun rako ango yan matan amaryar

da suke nan su black one ZZ da najma da meena

slow sune suka sayi baki idon amarya tar

akansu Allah ne kawai ya dinke bakinta batayi

maganaba Dan kuwa taso tayi magana, an sayi

baki kowa ya kama gabansa amarya ta tashi ta

cire kayan jikinta dama sun dameta kuma gata

da jin zafi kamar me, ta saka wasu kayan tana

danna waya saiga farhaan ya shigo ta kalleshi

shima ya kalleta ta mishi kyau itama ya mata

kyau uhuuuuum ya zauna gefen madubi.

Iffaat ya kira sunanta koni nan Jabo saida na

jiyo bugawar zuciyarta, ta dago ta kalleshi,

Ya fara yan maganan ganun da ake yiwa amarya

sannan ya qara jadda mata cewa yanxu da da

ba dayaba akwai haqqinsa akanta itama haka

yana cikin mata nasiha sai yaga ta dauki waya

hello tana dariya, shiru yayi yana kallonta tana

rai nashi yana maganaba tana waya tsaki yaja

ya kwanta abinshi ta qare wayarta itama ta

kwanta nayita jira ko za'ayi wani Abu amma har

na gaji ba wani bayani na fito abina.....

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??66

Na Hauwa M.Jabo

Taci pizzar sosai suna dan labari sama sama

chan ya sako zancen auren ta da farhaan irin dai

yana son ta amince ya nuna mata illar fushin

iyaye akan yayansu, jiki a sanyaye tace mishi ta

amince, Dan murna baisan lokacinda ya tashi

yayi rawaba ya juya itama abin ya bata dariya

nima Jabo abin ya bani dariya, yana ta saka

mata albarka, yaje jikinsa na rawa ya gayawa

mama da Yy Ali sun ji dadi ko ba komai sun

yanke shawarar idan taqi aminta za'a bar

auren..

***************

Magana ta kowane ban qare ta kan kama iyayen

sai murna suke sunata shirye shirye, amma

amaren kam ko a jikinsu, ana saura kwana biyu

daurin aure saiga goggo da dijee da rukayya

sunzo, koda sukazo iffaat tana skull Dan ita

wannan shirye shirye bai hanata zuwa

makarantaba,

Koda ta dawo bakin qofar dakinta taga wasu

takalmi Masu kama da kito amma dai na

matane, ta shiga dakin saiga su dijee anyi arshe

arshe tsakayar daki da yayanta biyu rukayya ko

yarta daya da ciki ta kallesu ta kwashe da dariya

harda durqusawa qasa Dan dariya, tayi dariya

saida ciknta yayi ciwo suko sun tsaya kallon

ikon Allah ta dago ta qara kallonsu nan ma ta

kwashe da dariya dijee tace ke bamusun iskanci

Dan kin zama Yar birni zaki ijiyemu kina mana

dariya kamar Kinga tutu...!!

ta harareta ta zauna da kyau tana dariyar tace

wallahi mamaki nakeyi wai dijee da Yara har

biyu! Ta qara saka dariya dijee ma sai ta dara,

ta kalli yayan tace amma dai dijee kina dukansu

ko? Rukayya tayi charab ta chabke tace ai

yanzu duk bala'en dije akansune Dan har danbe

tanayi da uwayen yara akansu, dijee tace ke

rukayya banason sharri da zuwa ko gaisawa

ba'ayiba zaki fara mini sharri, nan dai qawayen

suka yini suna tadi suna dariya duk da qauyanci

su bai sa ta gyamacesuba tunda itama chan aka

fito sun cire mata kewa matuqa kuma bata bari

suka gane cewa auren nata sai a hankali bane....

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 70

Na Hauwa M.Jabo

Taje ta zauna sai ta kasa chin abinchin don an

hanata fita kuma sai a hanata xuwa skull...

Wasa wasa iffaat na Neman wata daya Gidan

farhaan baya kulata itama bata kulashi amma

rashin xamansa gida na damunta ko ina yake

zuwa Allah masani kuma bata gane takunsa,

Ranar tana zaune dabara ta fado mata yanda

zata gane ina yake tafiya, bayan ya dawo

gantalinsa na dare ya kwanta bacci, dama

batayi bacciba tana jiransa ya dawo ya ijiye

wayansa tana tabbatarda yayi bacci ta dauki

wayansa ta shige bayi ta kulle ta danna power

off screen din yayi duhu ta duba da kyau sahun

hannunsa ya yake zana pattern dinsa bataci

wuyaba tana zagaya yanda taga sahun

hannunsa yabi tayi sa'ar bude wayar pattern

dinsa ba wahala ma, tana budewa ta fara aiki,

farko saida ta budamai Google account sannan

taje play store tayi downloading din latitude

tamai register dama tana dashi ta dauko

wayanta tayi sending request ta karba shikenan

ta gama da wannan duk inda yake matuqar data

dinsa a kunne take zata Ganshi baya buqatar

GPS latitude din, ta shiga SMS bata sami

komaiba taje contact ba wani number da bata

yarda dashiba harda searching na sunayen yan

matansa data sani amma babu ta duba logs nan

ma babu da qanqaro WhatsApp a kulle yake

kuma da pin number kawai zai bude bata

wahalda kanta ba taje gallery ba wasu hotuna

daga nashi sai iyayensa sai kuma na margayiya

Suhaila, gasunan sunfi 100 wani qololon baqin

ciki da kishi ya taso mata ganin hotunan da

Wanda suke tare da Wanda rake ita kadai amma

ba nata ko daya kamar ta goge amma kawai

saita fasa har zata fita sai taga wani folder ta

shiga akwai wani aciki ko wanne an rubuta

empty haka tayita dannawa saida ta wuce folder

14 sannan takai gunda aka rubuta Mrs

PURHUUN, ta shiga ciki hotunan tane aciki daga

kan wayanda ya mata lokacinda ta fara koyon

gayu gun Yar baqa Dana zuwa qauyen da yayi

wasu ma ya saka su a cikin frame mai heart

wasu kuma itada Suhaila ne amma an gutsure

Suhaila ko farahnax wasu ma batasan ya

dauketa suba irin tana zaune dinnan tana shirme

ko kuma tana surutunta tun kamin ta qare

wayewa gasunan dai kala kala, mamaki da jin

dadi suka mamaye mata zuciya ganin ya damu

da ita hatta hotunanta a wayar, sai wani video

da ta gani rawar da suka tabayine itada

farahnax a daki sukayi video ko ina ya samu

ohoooo tana tsaka da kallo taji yana qwanqwasa

bayi tsoro da tashin hankaline suka

baibayeta.....

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 69

Na Hauwa M. Jabo

Tace Idan da kana dukana ada yanxu akwai

banbanci wata qila ada ina gyalewa ko kuma ina

ramawa to ka sani yanxu akwai banbanci, ni

matar aurece inada yanci kuma nasan yancina

so ka kiyaye hannunka daga Taba matar aure.!

Ta sake mai hannu da qarfi Ta wuce abinta ya

bita da kallon Mamaki hadida zargin abinda ya

kawota yi anan ya akayi tasan yana nan ya daki

iska baima jira karuwarshiba ya fito da qarfi

koda ya fito bata ba labarinta ya shiga mota

gudu yake kamar ya ya hira sama koda ya isa

gida bata isoba yayi kusan 30mnt sannan ta iso

da ledojin abinci a hannu.! Tana zuwa ya daka

mata tsawa ina taje? Ta kalleshi dukda taji tsoro

amma bonewa tayi, ta danqaramar uwar harara,

kamar ma bada ita yakeba, tana Neman guri ta

zauna ya fincikota ke badake nake maganaba, ta

kalleshi ido cikin ido tace mai inda yaje chan

taje? Mi kikaje yi achan nanma ta bashi amsa

abinda kajeyi achan shi najeyi.? Idonsa suka

kada sukayi jaaa sun firfito waje iffaat kinsan

abinda kike fada ya qara fincikota ya mannata a

garu kinada auren nawa zakije gurinnan ? Ko kin

manta ke matar aurece. Taji tsoro iya tsoro

amma ta daure ta bashi amsa ta kalleshi idonta

cikin nasa tace, au auren akan mace kadai yake

kenan kaima ai kanada auren nawa kaje gurin

nan ko kaman ta kanada aurenane akanka? Idan

kuma akwai banbanci tsakanin mu let me know.

Yanda idan ka'aikata badaidaiba za'a maka

hukunci haka nima za'amini so miye

banbanci?? Wani baqin cikin kishi ya turnuqeshi.

Muryansa na rawa yace iffaat tell me the Truth

mi kikajeyi a gurin nan ? Ya bata tausayi yanda

ya sassauto, nace abinda kajeyi shi najeyi.

Sakinta yayi ya fuskanceta dakyau iffaat mi

kakajeyi a gurinnan Har kika ganni? Tace abinci

naje siya,

Ya manna mata arniyar harara, daga yau na

soke baki ba fita sayen abinci idan dai ba

makaranta zakijeba baki ba fita, abincin kuma ki

shiga ki girka da kanki!!

Tsaki tayi ta wuce shi,

Farhaan ya tsargu matuqa yauda ta kamashi da

wata ai bai isa ya shigo gidannan ba..

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 68

Na Hauwa M. Jabo

Gari ya waye ma amaren farhaan yana jiran

amai breakfast amma shiru har 12 yunwa ta

isheshi ya duba ko ina ba alamar girki sai

hayaniyar mutane, Yakama hanya ya fita abinsha

bai dawoba sai guraren daya na dare bata

damuba cox yan ganin amarya da qawayenta

sunanan sunyi girki sun debe mata kewa, bayan

sun tafi sannan ta fara tunanin ina yaje!? Daya

na dare ya dawo daya shigo tamai kallon

tuhuma tana Palo bai kula da itaba ya wuce

dakinta,

Koda ta shiga ya shiga wanka ta zauna bakin

gado har ya fito ta kalleshi yana goge kai alamar

wankan xxxxxx yayi. Ta fuskanceshi da kyau,

tace ina kaje yau? Gurin abokaina ya bata amsa

yana chire doguwar rigar dake jikinsa dagashi

sai towel bata taba ganinsa hakaba sai yau tsoro

yakamata ta tashi ta koma palo, ranar dai batayi

bacciba zuciyarta cike da tuhume tuhume, sai

guraren asuba bacci yayi awon gaba da ita bata

farkaba sai guraren 12 Subhanallahi yau tayi

lettin lecture dole taje ta nemo abinci ta tashi ta

fita direvan bayanan an ma fita da motar da ake

kaita skull da ita tayi tsaki tafito ta taka sosai

sannan ta sami mai adaidaita sahu ya dauketa

koda taje Al nasiha restaurant abincinda takeso

ya qare aka mata kwatancen wani guri inda zata

sami abincin ta qara tsayawa chan saiga mai

adaidata sahu ta tsayar dashi suka tafi sun isa

gurin tace ya jirata ta fito tana zaune tana jiran

a hada mata abincin taji ance farhaan, wani rass

taji mace ce ta kira Sunansa ta juyo ta kalleta

ga dukkan alamu tasan ta amma ta manta ina

tasanta Dan kamar ta qara fari yanxu, ta kashe

kunne taji tace Tana xuwa yanxu. Iffaat tace ina

xataje oho? Tana fita tabi bayanta Tana kallo ta

tsallaka titi sai taga ta shiga wata villa a gun,

tayi tsaki, ta dawo abinta ta karbi abinchinta ta

shiga adaidata sunxo daidai villa taga motar da

ake kaita makaranta....

Jiki na rawa ta tsayarda mai adaidaitan tace

Tana xuwa qirjinta kamar ya fito Dan tsananin

tashin hankali wata zuciya tana kije wata na

fadin kada kije, haka ta shiga gurin taje gun

Masu coffee ta nuna musu hoton farhaan

mutumin ya gaya mata dakin da yake zama

kullum, taje dakin da qarfin guiwa za'ayi kashin

kai wallahi!

Ta bubbuga farhaan ya taso ya bude mata,

tsaye yayi yana mamakin mi tazo yi anan gurin

ya kalleta mi kikeyi anan ta watsa mai harara

abinda kakeyi shi nakeyi ta shiga dakin ta duba

ko ina ba mace, tazo ta kalleshi karuwar taka

bata Iso bane??

Keeee waike bakida hankaline?? Mutum bai isa

ya fito shaqatawa ba sai ace yaje gun karuwai

wall.......

Sheeee ta katseshi da Dora hannu a lebenta...

da kunnena naji kana waya da karuwarka kana

taxo ka iso tazo kuyi iskancin da kuka sabako??

Ya daga hannu zai wanka Mata mari tuni ta riqe

hannunsa,...

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??71

Na Hauwa M. Jabo

Ta sadaqar kawai har zata danna power Off ta

kulle wayar sai ta tsaya tayi clear din duk abinda

ta bude tabar wayanda ta gani ta danna power

off ta bude bayin, Tana jiran ya fara masifa akan

me zata Taba mai waya amma taga ya shiga

bayin baima kalleta ba tana ganin haka tayi sauri

ta ijiye masa kayan sa tana ijiye wa ko hannu

bata daukeba alarm ya fara bugawa na sallar

asuba.

Allah yasota da ya buga Tana bayi ai da asirinta

ya gama tonuwa, tayi murmushi yana fitowa

itama ta shiga tayi alwula tayi sallah......

**********

Aiki ya sami iffatu duk yinin ranar Tana biye

dashi a latitude duk inda yaje Tana biye dashi

haka tayita saka mai ido har kwana uku ta gano

gurin da yake xuwa kullum ta gano gunda yake

yawon dare, hatta gurinda yake parking din

motarsa ta gane so zata fara aiwatarda aikinta

akansa.

Farkon abinda ta farayi ta Riga ta gano gunda

yake parking kuma tasan lokacinda yake xuwa

gurin, saida ta tabbatarda yana office ta kira

driver tace yakai motarta gurin ya ijiye tamai

kwatance ya kuwa je ya ijiye farhaan an qare

aiki akazo gantali tashin hankali abinda ya fada

kenan lokacinda ya hango motar ta, ko miya

kawo wannan yarinyar anan gurin?? Ya fara

tunanin ko tazo nemansane ya tafi akan tazo

nemansa ne kawai, bai tsaya bata lokacinsanaa

jikinsa na rawa yabar gurin bayan ta duba taga

yaje sai kuma taga ya bar gurin ya nufi hanyar

nasiha restaurant Tana ganin haka Tama driver

dinsu magana akan yaje da sauri ya dauko

motar bayan ya ijiye motar a gida dama tayi

kwalliya kamar wata amarya, yana dawowa ya

ganta kuma, ya kalleta kwalliyan ta ya sakashi

zargi,! To Ina taje miye na kwalliya ma! Cox bata

taba masa irin wannnan kwalliyar ba, Yanason

Ya mata magana amma yana tsoro, yasan

zatace shima mi yajeyi a chan? Ko kuma tace

ina ya ganta? Tinda bai gantaba gara ya bari

har y kamata da kanshi, haka ya zauna yana

tafarfasa har yayi bacci Dan baqin ciki ranar ko

fitar dare baiyiba..

Goben ranar sai baije gurin ba daga office ya

dawo gida kuma idan ya dawo saiya ganta gida

zaune ba inda tajee har kwana uku ranar na

hudu yaje gurin tana ganin haka ta tura driver

yaje yayi parking din motarta daga kan hanya

hanya ta yanda dole dole yaga motar tazo tayi

kwalliya abinta ta kame bayan ya fito hotel din

yaga motarta, mamaki ya kamashi, tana kallon

duk wani moving dinsa a latitude yana yawo

hakan ya tabbatar mata da nemanta yakeyi a

gurin tayi murmushi ya fito wajen gurin yayin

parking yana jiran ta fito kusan awa daya yana

jiran ta tafito amma bata ba labari, ya gaji. ya

riqa ya tabbatar da cewa nan gurin tazo yaja

mota Kamar wani mahaukaci.....

[7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 72

Na Hauwa M. Jabo

Tana ganin yabar gurin dama driver yana gurin

tamai waya tace yayi sauri ya dawo da mota

gida yayi gudu sosai farhaan kam traffic ya tsare

shi a hanya ga uban go slow ya biyo ta PZ shi

kuwa driver ta by pass yabi kamin farhaan ya

kawo tudun wada tuni an dawo da motar gida

yana shigowa gida yaga motar, yana huci Kamar

kasa tana zaune a Palo ta saka fura gaba

tanasha yana xuwa yasa qafa yayi ball da furar

gaba daya ya finciko gashin kanta ya wurgata

saman kujera, yazo Dai dai da ita zai kasheta da

mari ta wani riqe hannunsa da qarfi, tayi tsaye

saman kujerar wallahi idan ka mareni ba mijina

bane ko waye kai sai na rama...

A fusace yace ke Dan ubanki ubanwa kike yiwa

kwalliya kina kina fita?

Ta watsa mai harara tace ubanda ya

chanchanchi na yiwa kwalliya shi nake yiwa.! Ya

daki iska ya juya yana huci iffaat ni kike yiwa

rashin kunya?? mi kike zuwayi a Zaria hotel? Mi

kikiye achan?? tsaki ta masa ta diro daga

kujerar ta kama hanyar dakinta ya biyo ta

kinsan Allah wallahi idan bakiyi magana zan iya

kashe ki iffaat wallahi xan sallantar da

ruwuyarki..!!

tashin hankali lallai farhaan yafi iffaat kishi

hadda zancen kisa ta bala'en jin tsoro ta juyo ta

kalleshi taga yanda yayi wani iri dashi, tayi sauri

tabi gefensa ta fita bata tsaya ko inaba sai

Gidan su farhaan tana zuwa ta fada jikin umma

tana kuka... Akayita tambaya amma ba amsa

umma ta kira farhaan tace maxa yaxo tana

Neman sa ya kuwa zo, umma ta fara tambayar

sa mi ya mata haka duk ta firgice shiru yayi ya

kasa magana umma ta dakamai tsawa ya mata

bayanin komai tsaki tayi, rudadden banxa wai kai

mi yake damunka ne? Ko kunya bakajiba Dan

Allah kace ka ga mota amma baka gantaba

kuma ka dawo ka tarar da ita gida, haba wane

irin shirme ne wannan umma wallahi har

kwalliya fa takeyi.! Umma tace to mace a Gidan

mijinta batayi kwalliya idan batayi kwalliya ba mi

kake son tayi kaji shiriritar banxa, kai waya gaya

maka haka ake kishi da hauka, ka bari sai ka

tabbatar sannan ka yanke hukuncin waima kai

uban me kakeyi a Zaria hotel? Da har kaje kayita

ganinta? Ya Sosa kai iffaat data narke jikin

umma ta dago ido ta saci kallonsa ya duqar

dakai, yace umma baqi nake saukewa a gurin.

Tayi tsaki wallahi ka shiga taitayinka. kada ka

qara daga mata hankali da haukarka kaji na

gaya maka sannan duk abinda kakeyi ka bari sai

ka tabbatar sannan ka yanke hukunci farhaan

kam ya rasa bakin magana umma ba fahimtar sa

zatayiba tonon asiri ne ma zai yiwa kansa idan

yace zaiyi ma umma bayani har ta gamsu,!!

akace ta tashi ta bishi ta sa kuka ita bazatajeba

dole umma tace ya tafi gobe ya dawo ya tafi da

ita,

Na gaya muku iffaat fa taji tsoro matuqa taji zai

kaita lakhira...

Dole ta chanxa wata hanya...

Muje zuwa muji hanyar da zata komawa.

[9:32PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??73

Na Hauwa M. Jabo

Farhaan kuwa zaune ya kwana yana ta tunane

tunane, kamar ya hade rai ya mutu Dan baqin

ciki...

Ya janyo wayarsa ta bude hotunan ta yana kallo

tabbas yasan yana son iffaat babban abinda

yake damunsa idan ya tuna WACE CE ITA.. Yar

aikinsace fa wannan gani da yake mata har

kullum shi yakesa baya darajata, amma yasan

yanasonta babban dalilin da yasa ya qara

aminta da auren Suhaila Dan sunyi kama da

iffaat ne, hakadai yayita mulmula saman gado

kamar an xuba lemu a paranti sai zagayawa

yakeyi yana juyi wata zuciya tace idan ma Yar

aikinkace ai matarkace yanxu yakamata ka bata

haqqinta na matarka, ko ka sami sauqi, chaiiiiii.

qarshe ya tafi akan iffaat bazata taba aikata

hakanba amma xaiyi magana da driver dinta yaji

gaskiyar magana,.

Hmmmm nidai jabo Bantaba tunanin farhaan

yana son iffaat hakaba ba sai yau Ashe shima ya

kamu bamuda story,

Haka gadon ya masa fadi yasaba da kwanciya

tare da ita koda ba abinda sukeyi amma yana jin

qamshin jikinta, yanajin dadi amma yau babu...

Tunda qarfe 8 yaje daukota umma tace sai ya

dawo office sannan yazo ya dauketa..

Yinin Ranar dai bai gane komaiba gashinan sai a

hankali, har ya taso ya dawo office yazo umma

tamusu fada musamman shi, sannan suka tafi,

iffaat dai taji tsoro fa yanda ya mata ya firgitata

ba kadanba, amma bata nuna masaba

So ta yanke shawarar bazata qara kai motar ta

gurinba...!! Iffat Kura ga tsoro ga ban tsoro.!!

******

Farhaan ma haka bai qara xuwa Zaria hotel ba.

Bayan yayi bincike ya gano shirinta dariya kawai

yayi, lallai wannan yarinya akwai rigima..

Yanxu ta saka masa ido sosai a latitude tana

yawan ganin yana zuwa wani guri so abinda ta

farayi shine ta sami mai adaidata sahu ta

biyashi tace kawai ya bishi na kwana biyu yaga

mi yakeyi a gurin ai kuwa an kawo mata labari

wata yarinya yake dauka gurin tasa aka duba

mata gidansu yarinyar da komai nata, ta riqa ta

shirya abinda zata mata ta kiyaye lokacinda

yake sauketa ya wuce. ta sami almajirai su biyar

tace aiki zasu mata farhaan na sauketa ta riqa

ta tare hanyar tasa yaran suka tareta har ta fara

xaginsu iffaat taxo ta wanketa da mari tace

wayannan almajiran sun fiki daraja Yar iska

yarinyar.! mamaki ya cikata hakadai iffaat tace

ta shiga wani kongon gida zasuyi aiki, ta turje

sai tasa almajiran nan suka durata cikin kongon

gidan taso tayi taurin kai sai taga batada mafita

illa miqa wuya, bayan sun shiga iffaat ta zauna

saman wani bulo tabata almakashi tace ta yanke

gashin kanka ta fara gaddama iffaat ta qara

waske banxa da mari saida bakinta ya fashe da

jini ba shiri yarinyar ta karba ta aske iya yanda

zata aiya iffaat tace bai mataba haka tasa reza

ta mata tall kobo almajiran sai dariya suke nima

jabo dai na dara cox mace ba gashi batayiba!!

bayan ta mata gwandal tace saura Abu biyu

kuma, matar ta fara kuka tana tataimaketa iffat

tace ta rufawa kanta asiri ta bari suyi aikinsu

idan ba hakaba zata qara mata wani

punishment,mata kuwa sai kuka take tana roqon

iffaat tayi haquri amma iffaat ko kallonta

batayiba tasa almajiranta suka danne mata ita

ta mata bille guda biyu a fuska sannan ta fito

da bulalarta ta zaneta saida ita kanta ta gaji da

dukan nata sannan ta barta tace idan an

tambayeki wa ya miki haka kice iffaat ce ko kice

Mrs PURHUUN..... ta fita tabarta nan tana

kuka.....

[9:38PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 74

Na Hauwa M.Jabo

Yarinyar taji jiki matuqa sai kuka takeyi, babban

baqin cikinta billen data mata cox gashi zai fito

nan gaba amma bille bazai baceba har abada ta

fara tunanin WACE CE ITA?? Mrs PURHUUN

kuma?? waima da wane dalili ta mata haka??

Ta gaji ta rarrafa taje gidansu tana kuka..!

Ran iffat yayi sanyi farhaan na dawowa ta

kalleshi ta kwashe da dariya ya juyo ya kalleta

yace lafiya? Ta wani daga ido alamar dawa

kake? Yace hmmm yasan tabbas akwai abinda

takema dariya, sai daibai bazai kulataba.

Iffaat haka ta riqa bin farhaan a latitude saida

tama yan matanshi shida aski hadda su ramcy

ko ina hafsa take ohoo taso ta aske hafsa ta

mata bille....

*******

Ranar sun fito lecture ta hadu da wata tsohuwar

qawarta Aisha armiya'u mada. Sun Dan yi skull

tare da ita tanason iffat sosai bayan sun gaisa

take bata labarin tayi aure tanata tayata murna

hardai tace zataje gidanta bayan lecture sunje

gida akan hanya ta siya mata abinci Dan iffaat

har yau bata iya girkiba hasalima bata taba

girkiba saidai dafa tea, hatta kunna gas har yau

bata iyaba....

Bayan sun qare chin abinci suna tadi saiga

farhaan ya shigo, armiya'u ta gaidashi ya amsa

iffat kam ko motsi tadai kalleshi kawai, bayan ya

wuce ta kalleta tace iffaat wannan ne mijinki?

Tace eh kinsan shine? Tace Eh nasanshi, iffaat

aranta tace wallahi zan miki bille kuwa. Ina kika

sanshi? No tunda dadewa sunyi soyayyah da

wata cousin dina but Allah bai qaddari

aurensuba, iffaat tace eyyah aure nufin Allah ne.!

Eh hakane har an bar zancen amma iffaat sarkin

kishi abin yana cinta.

Chan tace ya sunan cousin din taki? Tace hafsa,

amma sun rabu yanda tace min wai yasa house

girl dinsa ta mata wulaqanci abin dai ba dadin ji

wallahi...

Nidai nace ko baka son mace ai ba haka ya dace

kayi Dan ka rabu da itaba....

Ka gaya mata bazaka auretaba sai a zauna

lafiya iffaat tayi murmushi wato abinda ta mata

ya rabasu da farhaan lallai aikinta yayi kyau..

A munafunce tace Allah sarki kinsan mazan

yanxu sai a hankali , tanason ta sami

information a gurinta,

Kuma ai farhaan ya damu da ita har ya bani

labarinta, armiya'u najin an fadi haka sai ta saki

jiki dama tana tsoron tayi siririn baha ya

zamana batasan da zancen ba.....

[9:45PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 75

Na Hauwa M.jabo

Armiya'u tace Wallahi kuwa hafsa taso farhaan

kamar rayuwarta ta bashi kanta sabida tana

gannin kamar zai aureta, kai ai hafsa tayi jinyar

rabuwa da farhaan, iffaat ta gyara zama tace ai

yace min tanada jarumta sosai, armiya'u tace

uhum Ashe dai kinsan komai kena,? nama daina

jin tsoron fada, iffaat tace eh duk ya fadamin

yace har matarsa ta farko tananan yana tare da

ita yace har gida yake kawota.! armiya'u ta

gyara zama za'ayi gulma ai iffaat in gaya miki

yanda hafsa ta bani labari mijinki akwai tsananin

buqata kuma yanason jarumta matuqa gurin

harka, idan kika kiyaye haka wallahi zaki

sameshi a hannu shiyasa ma hafsa ta daga tuta

duk cikin yan matanshi yafi ji da ita, idan kika

kiyaye sai yanda kikayi dashi.!

Iffaat dai duk da qunan da zuciyanta keyi bai

hanata saurareba, wai har wata tasan asirin

mijinta Allah wadaran halin farhaan, Kinga mijin

ki Dan gayu ne, so wallahi sai kin kasa kin tsare

yanda yan mata sukayi yawa idan ma Allah ya

tsareki bai miki kishiyaba to zai nemi mata a

waje amma idan kika gyara kanki kin gama

komai Dan maganin matannan kinasha kwalliya

duk ki riqayi kissa da kisinsina ki zama first

class gaki da gashi kiyi yanda kikasan mijinki zai

ji dadi, Dan girkinnan duk ki xama kece kan

gaba, wallahi nasan yan matan da suke son

mijinki ba adadi kuma duk sun fiki girma da

wayo, ko wacce tasan yanda zata sace zuciyar

namiji so ki zama very careful iffaat kam ta

sassauto da kishi tana sauraren jawabin qawarta

Aysha armiya'u mada lallai ita tasan inda duniya

ta Nufa kuma itace qawa ta gari....

Armiya'u tace ki duba yanxu ina kallo mijinki ya

shigo baki gaisheshiba kuma ko ruwa baki

kaimasaba bare abinci, iffaat tayi murmushi

batace komai ba

Armiya'u dai ta baiwa iffaat darasi kuma ya

shigeta matsalar batasan yanda zata fara bane,

bayan sunyi sallama ta tafi saiga farhaan ya fito

a daki dama jiran tafiyarta yake yaxo yayi tsaye

yana kallonta wannan yarinya akwai kwarjini sau

da yawa idan ta masa Abu ya tunkareta sai ya

kasa..yaga idan ma masifa zai mata aikin banxa

zaiyi don ba jin masifar takeyiba so gara ya

mata magana cikin ruwan sanyi....

Ya kira sunan ta tana kwance ta dago ta

kalleshi, ki tashi zaune batace komaiba ta miqe

zaune yace ki ijiye waya, zamuyi magana kafada

inajinka kawai.

Ya kira sunanta, Iffaat tace na'am ki ijiye waya,

sai ya bata tausayi ta ijiye waya ta fuskanceshi

dakyau yace iffaat abinda kikayi kina ganin kin

kyauta? Ta xaro ido mi nayi kuma? Kin fini sani,

aah Malam kada amin sharri ina zaune lafiya mi

nayi?? mi kika yiwa yaran mutane? Ta bone

kuwa wayanni yara kuma ?? Yace abokan aikina!

Uhum yy kenan abokan aikinka kuma? Ya za'ayi

nasan abokan aikinka? Iffaat wannan serious

issue ne, miyasa kika aikata hakan?? Nifa yaya

ban gane mi kake fadaba kamin dalla dalla

kawai, yaga zagaye zagaye ba nashi bane yace

yaran da kika yiwa aski da bille Kuma kika

dakesu....!!

[9:59PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??76

Na Hauwa M. Jabo

Au kace min karuwanka koda yake suma abokan

aikine tunda dasu ake iskancin no no no na

manta wayewace, ko ba wayewa bace?! ranshi

ya baci, sai ya share yaci gaba da magana

kinsan kuwa kan haka wata har qara ta shigar

kotu dagayar na rufe case dinnan,? iffaat tayi

dariya hadda kwalla, wallahi da ka bari an tafi

dani kawai kaga sai kaji dadin kawo su har cikin

gida kamar yanda ka saba,! shiru yayi aransa

yace wannan duk abinda aka fada tanada amsa,

shikam gara kawai ya nemi shiri gunta koya

sami sassauci dama laifin sane dabai nuna mata

shi wayeba da yanxu rawar ta chanxa amma

soon zata shigo hannu.. chan yace iffaat kinsan

kuwa ina tsananin sonki? Kinsan tun yaushe

nake fama da sonki cikin rayuwata? Please iffaat

kidaina wahala min da zuciya... Wani sanyi taji a

ranta inaga tinda tazo duniya bata taba jin

kalma mai dadi kamar wannan ba, amma bata

nunaba Sam, iffaat ki tausayawa rayuwa wallahi

wasu abubuwan duk rashin ki yake sa ina

aikatasu...¡!

Ta kalleshi ta watsa mai harara Malam Dan

kawai yan matanka sun gudu shine zaka lallabo

gurina ka min wayo ko? To kayi letti

bazakasamu hakanba,

No iffaat ni ba sai na sami komai a wajenkiba

just kawai ki amince dani maisonkine, mudaina

rigima nagaji. wallahi ina axabtuwa da rashinki,

guntun tsaki taja, ta koma ta kwanta ta dauki

wayanta ta danna recoding duk abinda yake fada

tana dauka har ya qare batace dashi komaiba,

ya qare yazo kusa da ita tayi sauri ta kashe ya

dafa kafadarta ta watsomai ido miye haka wai?

Ta bani dariya miji ya taba mata tana miye

haka!?

Yace ba komai yakai hannunsa akan gashinta ya

shafa yace kizo na gyara miki gashin ki!

Kallonsa kawai tayi yanda ya chanza ya bata

tsoro ta yinqura zata tashi ya danneta ta koma

kwance ta kalleshi wai mi kakesone Malam? Ya

kawo bakinsa daidai da kunnenta ya mata rada

saida tsikar jikinta ta tashi yace ke nakeso

iffaat, tace Banganeba! ina nufi matata nakeso!

Tofa yau akeyinta gata kwance duk ya dabai

bayeta, yana zauna qasa hmmm kawai tace bata

ce komaiba tana jinsa yana Dan mata wai waye

a qirji alamar yanason ya aika hannunsa ciki,

Yya farhaan ina zuwa bari nayi fitsari. Ya gane

guduwa takeson tayi sai yace muje na rakaki,!

Burinta dai ta tashi zaune ya daga mata ta tashi

zaune muje mana. Ta harareshi nama fasa

xuwa. Murmushi yayi yace idan kina tsiwa kinfi

kyau.! aransa yace sai kin shigo hannunna

yarinya ya miqe ya shiga daki,

Iffaat kam dadine yake Neman ya hallakata

dama Ashe yanasonta? Da tasani ta tambayeshi

tun yaushe yakesonta tayi murmushi ta shafa

gashinta, ta tuna shine mutum na farko daya

fara gyara mata gashinta! Ta qara murmusawa

ta tashi tayi sallah...

Goben ranar farhaan ya ya fitowa office wata

budurwarsa ta kirashi tace su hadu wani guri

kamar bazai jeba sai kawai ya wuce gurin iffaat

kuma tana sukul bayan ta fito lecture sai ta

duba latitude dinta taga farhan yananan kusa da

skull dinsu, har ta qara shiga lecture ta fito bai

motsa daga gunba tayi refreshing still yana gun

tayi zooming sosai taga gurin a qafa ta tattaka

koda taje ta qara refreshing taga itama tana

gurin nisansu Kadan ne, koda ta daga kai sai ga

motarsa da wata mota,! Tayi tsaye ta rasa

yanda zatayi, ta duba ba kowa a gurin, sai mai

gadi, tanuna ma mai gadin gurin hotonsa tace

yaga wannan yace eh yana ciki.! tayi shiru ya

zata shiga gurin aka nuna mata dakin tana

kallon dakin amma ta kasa qarasawa sai ta fito

Dan tasan baqin ciki kawai zata gani idan ma

taje din tana hanyar dawowa sai taga police

station tayi murmushi wallahi yau farhaan sai ka

kwana a Gidan yayan sanda direct gurin su

taje........

Muje zuwaa

[10:07PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 77

Na Hauwa M. Jabo

Ta je gurin yansanda ta sami babban su tace

tanason yan sanda hudu ya tambayeta dalili

batasan abinda xataceba tace wanine yake bata

mata qanwa kuma ta rabasu sunqi rabuwa shine

takeson akama- matasu duka biyu taga kamar

baxasu bataba tana dubawa sai taga gun cirar

kudi anyi Sa'a ATM yana cikin jaka ta chiro kudi

tazo ta miqewa Dan sandan jiki na rawa ya

karba ya bata kwalawa hudu tace kuma kada

abada belinsu karma a bari suyi magana taje

tanuna musu gun tayi sauri ta dawo skull,

policawa kuwa sun cika aikinsu suka kama

farhaan da budurwarsa dama iffaat tace kada a

sakeshi kuma kada a sauraresu dukansu sai taxo

gobe zata karbesu kuma kada a bari yayi

magana da kowa!! farhaan kam Dan baqin ciki

har kuka yakeyi mi yake faruwa dashine tunda

yake ba'ataba kamasahiba sai yau an

wulaqantashi ba kadanba.. tsanar bariki ta shige

mai zuciya yayi nadama, yayi yayi abari yayi

magana amma ina sunqi kulashi tunanin sa daya

iffaat yanda zata kwana ita kadai..! Uhum,

itakam hankalinta kwance tanajin dadi koba

komai tamai rashin kunya da safe ta chaba ado

na gani na fada ta saka kayanda ita kanta tasan

tayi da saka glss dinta ta wuce skull bayan ta

fito lecture taje gurin yansanda, tace yazo beline,

aka fito da farhaan da matar tace a maida matar

sai an qare case din farhaan aka maida matar

wata jaka da ita sai jalkuna, yana ganinta ya

rude ya ma rasa abinda zai fada kamar gaske

tace ma yansanda Dan Allah a bata belin sa

mijintane bazai sakeba ayi haquri.!! ya kalleta

cike da mamaki iffaat waya gaya miki inanan?

haka kawai ya samu damar ce mata..! tace naji

a jikina kaje abinda ka saba an kamaka.! Ta

kalleshi but so happy wallahi Allah ya qara

maganin irinku kenan masu bata yayan mutane..

Sosa kai yayi, police din yace kai kanada

wannan baby mixakayi da waccan ashawon

kalleta haddadiya da ita kunya ta rufe shi da

haushin dansanda ina ruwanshi da matarsa.. ta

cika takardu aka saki farhaan sun fito ita dashi

ta kalleshi ta nunashi da hannu, kalleka Dan

Allah namiji har namiji amma ba halin kirki.! Tir

da hali irin naka, idonta suka ciko da kwalla

amma da yake ta saka glass sai baxai ganiba

nayi nadamar kasan cewa tare dakai a matsayin

matarka. Kullum cikin tunanin kana ina mi

kakeyi!!? kallonta yake tamai kyau iffaat baby ce

shima yasani kullum qara cika takeyi tana wani

fresh murmushi yayi ya janyota jikinsa ya

rungume yana bata haquri, tayi tayi ta kwace

kanta amma ta kasa sai ta barwa Allah.......

Dagyar Tasamu ya saketa hawaye ta gani a

idonsa tausayi ya bata, ta bude mai mota ya

shiga itama ta shiga taja suka tafi,mamaki yake

ya akayi ta iya mota? Waya koya mata? waima

waya gaya mata yana gurin baiso ta saniba

Sam har suka Isa gida bata kalleshi ba tana

tauna chewing gum a hankali suna Isa gida

kuma sai yaga motarsa......

[10:14PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 78

Na Hauwa M. Jabo

Ya kalleta chike da mamaki yaga batama kula da

mamakinsaba sai shima ya basar.! sun shiga

gida ta kawo mai abinci abinda bai taba samuba

tunda ya aureta yasan ba ita ta girkaba amma

duk da haka yaji dadi ya zauna yaci yana chi

tace, nasan police station ba abincin kirki shi

yasa na kawo maka wannam, lokaci daya har ya

hargitse, tayi dariyarta ta mugunta ya dago ya

kalleta tace kaima ka dandana kwana Gidan yan

sanda ko? Ta qara yin dariya tace dadi ko??

Baice mata komaiba ina tambaya.! ya kalleta

wai ya akayi kikasan ina chan ? Tayi murmushin

mugunta tace sabida ni na saka a kamaka..!

Ya zare ido Kamar ya? Tace Kamar haka.!

Please kimin bayani ya akayi kikasan ina gurin?

Wallahi Nina tura a kamamin kai, kuma yanxu na

fara duk lokacinda na ganka da wata mace

wallahi saina kulleka. Mamaki yakeyi dukda cewa

yasan iffaat fiye da hakama zata iyayi amma ta

bashi mamaki, miyasa duk motsinsa akan

idonta,? Ya akayi kikasan gunda nake zuwa?

Tace sabida ina iffaat, baice komaiba aransa

yace Ko ta saka a riqa bibiyarshine? Kallonta

kawai yayi Dan gaskiya tamai yawa,!! yana

zaune wayanshi tayi qara ya daga abbanshine

ya gaisheshi anan abba yake gayamai zai

aikeshi Thailand, kuma ya tafi da matarsa,

bayan ya qare waya ya mata bayani ido bude

tace baxataba karatunta zai sami matsala kuma

tafiya har wata biyu ko uku, yaso ya tafi da ita

wataqila ma achan su shirya amma taqi.

Farhaan yama Abba bayanin abinda ta masa

bayani Abba yace ba komai...

Tunda tun cikin Daren yabar gida yaje Kaduna

yana shirye shiryen tafiya, mai sami kansaba har

ya tafi,

Farhaan dai an tafi Thailand yabar iffaat ita

kadai a gida an kawo mata wacce zata tayata

zama kamin mijinta ya dawo...

Tunda matar maman nargees tazo ta kula iffaat

abincin take siyo musu, tanason tayi magana

amma dai tana tsorooo ace tayi shishigi.....

[10:19PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 79

NA Hauwa M.Jabo

Kusan sati daya da tafiyar farhaan amma still

siyo abinci take ta kula iffaat akwai saurin sabo

kuma batada matsala amma kuma batason

shishigi, ranar suna zaune sai matar tace yau

nayi mafarkin Dan wanke, iffaat tace Allah ko! Ki

bari anjima idan na fita sai na siyo miki, matar

tace aah gara dai mu girka kayan mu ko mi kika

gani, iffaat tace gaskiya ban iyaba, sai na koya

miki ko bakyaso tace tanaso, anan iffaat tabata

labarin cewa tunda take bata taba girkiba, matar

nata mamaki ace mace bata iya girkiba, haka dai

matar ta dage ta koyama iffaat girki kunna gas

yanda akeyin komai tace akwai books na girki ta

siya, tace mata, wallahi girki shine mace duk

kyanki da yanga idan baki iya girkiba baki cikaba

bakida daraja a gurin miji, matar dai ta kula

iffaat gayun banxane bata iya komaiba, a labari

iffaat take fadamata cewa ai idan taga mijinta

yana magana da wata ubanta takeci ta mata

aski da bille matar tayi dariya sosai wai bille,

tace to aike iffatu ba haka akeyiba baki

kyautatawa miinkiba ya za'ayi yaqi Neman

mata, kina gani maxan yanxu ko kin kyauta tasu

ya kuke qarewa bare baka kyautata musu,

wallahi kiyi hankali ki San ciwon kanki ki fara

dafe mijinki sosai sannan idan kin Ganshi da

wata sai kisan abinda zaki mata, amma haka

kawai baxaki hanashi abinda yakesoba ke baki

biya mai buqatansaba ki hanashi ya nema!! Ai in

gaya miki kina zaune saidai kiga kishiya, ta dafe

qirji kishiya!!? Sosai kuwa kishiya, Allah ya

rabani da kishiya, Yan zu maman Nargees ya

zanyi,? Ya zakiyi kuwa illa ki koyi girki ki iya

kwalliya koda naga kwalliya ke ajin farkoce ki iya

shagawaba idan yana gida ki manne masa duk

motsinsa akan idonki, iffaat ta kwashe da

dariya.! Miye abin dariya? Tace ba komai, haka

dai tayita gaya ma iffat abubuwan ta bata

sirrikun mallakar miji wani abin iffaat tayita

dariya tana mamaki, bayan ta tashi taje ta

kwanta a nan ta fara tunanin maganganun da

ake fada mata gaskiyane dole ta fara saba masa

da kanta sannan taje chin uban na waje....

[10:30PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??80

Na Hauwa M. Jabo

To amma ai ba laifinta bane? Shine bai

nemetaba! Wata zuciyar tace yaga fuska bare ya

nemeki? Aike ya dace ki kwatanta kiga yanda

zai dawo hannunki, wata zuciyar tace kawai ya

rainakine yana jiran kikai kanki ya qare dake,!

Tayi tsaki. Miye mafita idan bata mantaba Aysha

armiya'u mada ma haka tace mata farahnax ma

da taxo haka tace mata a skull ma idan suna

tadi zancen kenan daya kyautatawa miji, ga lada

ga la'ada. Tayi murmushi ta janyo wayarta ta

dauko hoton farhaan tana kallo tana zooming

batasan lokacinda tayi kissing din bakinsaba tayi

jimm gatada miji har miji amma manemin mata!

Lallai ta bala'e bazata wani gyarashiba ya

kamata ta dandana masa Zumar ta sannan ta

kasa ta tsare idan ta kama ta raka anan ne idan

yaqi dainawa taci gaba da chin ubansu..

100% ta aminta da haka so tana jiran dawowar

farhaan ne taga yanda zata fara, kunya takeji

anya zata iya? Taya zata fara!? da shedana da

wasa zata cusa kanta, har komai ya daidaita, ta

lashe lebenta tayi murmushi ta rungume pillow

Allah ya shirya min kai Yy farhaan.. Haka dai

madam iffaat tayita tunani har bacci ya dauke

ta,...

*************

suna waya akai akai amma dai ba wani chanxi

data nuna mai, shikam hadda cemata yake yayi

missing dinta takanso tace bawani Dan tasan

yana tare da yan matansa amma kuma sai ta

share...

kwanci tashi har farhaan yayi wata daya a qasar

iffaat kuwa lokacin ta gama iya girki nikaina jabo

idan tayi girki badan kada aga kwadayinaba

wallahi dasai naci, amma ba hali, girkinta haka

yake qamshi kamar me maman nargess hatta

yanda ake tafiya gaban oga saida ta koya mata

da yanda ake shagwaba a narke jikin miji duk ta

koya mata cox practice sukeyi maman Nargees

ce iffaat iffaat ce farhaan sai tace ta fita waje

tana shigowa maman Nargees taje ta rungume

ta tana mata wani Abu iffaat Dan dariya har

hawaye takeyi, anya zata iya yin haka kuwa??

Maman Nargees kuwa sai qarfafata takeyi, har

dai taji zata iya, ga iffaat gwana gashi dama ba

auki zatayi dadin kakkarya jiki....

Daidai wannan lokacin farahnax ta haihu ta

sullubo yarta kyakyawa kamarsu daya da

farhaan idan kaga Yar kace ta farhaan ce Dan

kamar har ta baci da iffaat ta tura mai hoton

baby ya gani yace da babyn Suhaila ta rayu da

itama yasan kamar shi zata dauko iffaat dai

batace dashi komaiba, yace amma insha Allah

ina dawowa zan samo wata zaki tayani nemowa,

tayi kamar bata gane mi yake nufiba, tace eh

mana duk inda ake siyowa kaima ka siyo yayi

murmushi ya basar Da maganar....

[10:33PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 81

Na Hauwa M. Jabo

Anyi suna lafiya ansha shagali taga yanda ake

soyayyah gurin farahnax ranarda mijinta yaxo

tana wani mai shagaba tana narkewa abin dariya

yake bata, kuma gaban kowa zata mai haka

saidai a bata guri badai ita ta basu guriba

abinsu yana burgeta, farahnax takance niko

sister iffo zanso naga ranarda zaki daina halin

ki, takanyi murmushi baatace mata komai. duk

abinda sukeyi tana recoding a kanta kuma shima

yana shiga cikin list dinta zata ma farhaan dinta

fiye da wannan idan ya dawo...

Duk kudinda abba yake xuba mata da wayanda

farhaan yabar mata taje ta siyo arnar nyte dasu

ta siyo English wr masu zafi ita kanta tasan dole

ya girgixa idan ya gansu gashi yana sonta dole

kuwa yayi sha'awarta..

Nidai sai kallo nake wai iffaat ce take tanadin

kayan da za'a sakawa miji, batada matsala gurin

kwalliya ta iya kayanta tana biye da group chat

duk abinda akace yana saka ni'ima saitaci tasha,

duk wannan tanadin na PURHUUN dinta ne,

Ranar tana zaune a Palo ta qare gyara gunba

yatsunta sunyi kyau abinta, tayi zaune tsakayar

daki saman center carpet tana kallo taji

tsayuwar mota ta dauka maman Nargees ce Dan

taje siyyah kasuwa kuma kayan sunada yawa da

zata siyo, ko motsi batayiba taci gaba da

kallonta daga bayan ta taji mutum ya Dora

wuyansa akan kafadarta ta wani zabura da qarfi

amma qamshinsa ya bayyana mata wayeshi!

farhaan ne batasan lokacin da maqalqaleshiba

tana dariya yayi surprised dinta ba kadanba

mutumin da akace zaiyi wata biyu koma fiye

amma yau kwana 48 ya dawo, farhaan kam

murna yakeyi yauga iffaat dinsa a jikinsa kuma

da ra'ayin kanta, ta sakeshi ta riqe kunkumi tana

dariya tace, wai Kaine naka gani ko kuwa

mafarki nakeji, yace sosai nine farhaan na dawo

na gaji da rashinki kusa dani koda kuwa kasheni

zakiyi gara ina ganinki tayi dariya na Isa na

kashe yayan farahnax, yayi dariya dhima ya

janyota jikinsa uhum su farhaan an sami yanda

akeso....

[11:34PM, 5/14/2015] .: WACE CE ITA..??82

Na Hauwa M Jabo.

Ya jata kujera Suka zauna tace Bantaba tunanin

zaka dawo yanxuba shine ko waya kaqi gaya

min ai da sai ko girkine a maka, mamakine ya

cikashi shikam gara da yayi tafiyar nan tayi

missing dinsa, hadda su girki,! ana wani mai

murmushi shida idan yaga dariyar ta to tabbas

tamai mugunta ne take dariya....!! .

mai gadi ya fara shigowa da kaya niqi niqi yana

ijiye wa gefen qofa, ya rungumota sosai jikinsa,

Abu daya ta manta bata tambaya ba idan miji ya

dawo sai yasha ruwa sannan zaiyi wanka yaci

abin ci ko kuma sai yayi wanka sannan yaci

abinci, ta rasa yanda zatayi kamar taje kitchen

ta ma maman Nargees waya ta tambayeta sai

tace bari kawai ta masa yanda ta iya, ruwa ta

kawo masa da drink ta zuba masa yace

hannunsa ya gaji saidai ta bashi a baki, dariya

tayi ni ban Iya baiwa ko yara abinciba bare

manya, yace ai nima yarone a gurin ki ko

bakyaso,? murmushi tayi aranta tace shima yaxo

da nasa kwandon iskanci, tace inaso mana,!

Yace to ki baiwa babyn ki ruwa ta kuwa taso ta

tsuguna gabansa ta bashi ya kwankwade yace a

qaro ta qara mai ya kwankwade yace a qaro

tace aah ya Isa,yayi murmushi idan dai ke zaki

bani xan tasha har sai na shanye duka,murmushi

kawai tayi batace komaiba, tace muje kayi

wanka, yace iyeeeee duk ni kadai gaskiya dole

duk sati na riqa yin tafiya tunda idan na dawo

gata ake min, ta waigo ta Dan qaramai harara

ta murguda baki, saida ya tuna da ita a yanda

take da tamai gata gwanar murguda baki,tuni

yayi tsitt kamar ruwa ya cishi, suka shiga bayin

zata fito yace kixo muyi wankan tare mana tace

ni nayi daxu kai kayi yace to kixo ki wankemin

bayana hannuna baya kaiwa, kallon sa kawai

tayi ta wuce abinta duk shekarunda kayi kana

wanka wa yake wanke maka bayanka!

Shikam murna da dadi ya ma rasa abinda zaiyi

dan murna, iffaat ta rasa mi zatayi girki zata

masa ko kwalliya zata tsaya tayi, sai kawai ta

Yanke shawarar girki, ta shiga ta duba duk wani

abinci idan tace tayi shi zata bata lokaci sai

kawai tayi sauri ta hadamai danbunb cos cos

da busashen kifi yaji ganye, duk Wanda

Yaji qamshin girkin to zaisan cewa abincin ma

zaiyi dadi dambun cos cos dan taga yafi sauri

dama farhaan idan ya shiga wanka sai mutum

ya manta da cewa ya shiga, taxo gaban madubi

ta Dan goga powder ta gyara fuskar batayi

kwalliya ba kada ya rainata da xuwa yaga ta

fara shafe shafe, taje ta Dora mai abincin akan

table ta dauko mai wasu kaya da taga idan yana

gida yake sakawa.....

Muje zuwa muji shin kulawar iffaat zata sa

farhaan ya chanxa ko kuwa halinsa dai!!

Idan bai chanxaba wane mataki anti iffaat zata

daika,?

Ya soyayyah zata guda tsakaninsu!? KU BIYO

YAR MUTAN JABO KUSHA LABARI....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..??83

Na Hauwa M. Jabo

Yana fitowa wanka ya saka tufafin data ijiye

masa ya feshe jikinsa da turare yadauki waya

ya kira abba ya gaya masa ya iso anjima zaizo

ya kawo mai report din komai, Abba yace ya bari

sai gobe idan ya qara hutuwa,ya kira mama da

umma da hajiya kulu duk ya gaishesu ya gaya

musu ya iso, iffaat ce ta shigo tace Au har ka

fito? Ya kanne ido yana Neman janyota jikinsa

yace nayi missing dinkine Dan shiga bayin da

nayi shi yasa nayi saurin fitowa, bata bari ya

kamataba ta zille, tayi murmushi, tace sai tsara

zance, nidai muje kaci abin ci tana gaba yana

Binta baya sun Isa Palo ta zasu fara chin abinci

farhaan yasa rigima shi dole sai ta bashi a baki

idan ba hakaba bazaiciba, aranta tace anya xan

juri Wannan shiriritar kuwa? Mutum da girmansa

yana Wannan Abu, yaji shirun yayi yawa yace

bari naje na kwanta, ta kalleshi da dara daran

idonta abincin fa? Ba kinqi bani abakiba, yanda

yayi ya bala'en burgeta kuma sai taji wani

sonsa ya ninku a zuciyanta Allah ya shirya min

kai mijina!, tace to bari na baka ya kuwa gyara

zama tafara bashi duk taje saka mai loma sai

rabi ya shiga rabi ya xube hakadai taga chi da

chokali shirititane ta ijiye tafara bashi da hannu

nan ma da gangan ya riqa chijeta wai ya dauka

kifine, suna tsaka da wannan drama saiga

maman Nargees ta dawo, ta wangale baki taji

dadi ba kadanba, ga dawowar farhaan ga kuma

abinda tagani wai iffaat tana baiwa farhaan

abinci a baki, hmmm.

Ta gaidashi, iffaat nason ta daina bashi shi kuwa

sai haaaaa yake mata baki yake irin na yara,

haka dai ta bashi sama sama.

sun gaisa yake mata godiyar xaman da tayi da

iffaat tace ba komai yiwa Kaine. Ta wuce kitchen

ta jera kayan data siyo ta wanke kayan da iffaat

tayi aiki dasu tsab sannan ta fito koda ta fito

sun tashi gurin duk yayi abinci tayi murmushi

tace sai kace an baiwa jinjiri abinci, ta share

tsab, ta gyare.!

Iffaat bayan sun qare chin abinci farhaan yasa

wata rigimar wai wallahi bayan sa kamar ya

bude Dan gajiya, taxo ta masa tausa, tace

bakyau ana qare chin abinci a kwanta Dolensa

yayita zagayawa a daki har yaji ya gaji kuma ya

hanata tafiya bayan ya qare ya kwanta bacci....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA.. ??84

Na Hauwa M.Jabo

Bayan ya kwantane Ya nace saita mai tausa

gata bata iya tausaba haka dai tayi ta dannawa

tun yana wash wash har dai baccin gaskiya ya

kwashe shi, tana tabbatar da yayi bacci ta janyo

bargo ta lullubeshi, ta zauna akan madubi tana

kallonsa, tana tunani,

Dama ana cewa namiji daidai yake da jinjiri idan

kana mai abinda yakeso to ka gama dashi,

saidai ita kam nata mijin mayen mutane Allah

dai ya shirya matashi hakadai tayi ta tunani...

chan ta tuna da maman Nargees tayi sauri taje

Palo koda taje ta hada kayanta bayan ta gyara

palon, iffaat ta kalleta Dan Allah kiyi haquri

wallahi na manta kin dawo! Ya naga kin hada

kaya ina xuwa??

Zani gida mana aikina ya qare gashi tun ba'aje

ko inaba har an fara mantawa dani, iffaat tayi

dariya tace wallahi ba komai mukeyibafa ! nace

wani Abu kukeyi?

Naji dadi sosai wallahi nan dai maman Nargees

ta qara bata wasu shawarwari sannan tace duk

da haka ta riqa ja masa aji ba komai bane jiki na

rawa zata masaba, tayi dariya taso ta bari

farhaan ya tashi ya sauketa amma tace ya gaji

kuma ta hanata itama ta kaita wai idan ya tashi

bata ba zaiji dadiba, uhummm maman Nargees

dai ta gyara aure sosai ta tafi...

Bayan maman Nargees ta tafi iffaat kayan da

aka shigo daso ta musu muhalli bata budeba

Dan tasan bata aikesaba!!

Ta gaji Dan aikinda tayi ta zauna tanata tunanin

yanda xuwan farhaan ya chanza ta tayi

murmushi tasan dai har yanxu bazata iya bari

suyi wani abubua Dan tsabar kishi irin nata, bari

tayi wanka har zata shiga bayi sai tace bare taje

S.P ta dauko Yar figaggiyar rigar wankanta ta

saka taje ta fara wanka,.

Ashe farhaan ya tashi yana kallonta ta window

yana murmushi yanda take wasa da ruwa kamar

kifi, Yaji bari yaxo shima ayi dashi tana cikin

ruwan kawai jin tayi mutum ya fado ciki da yake

tafi shi iyawa shi farkon ruwan yake tsayawa ita

ko har gurin xurfin take tafiya..

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 85

Na Hauwa M. Jabo.

Tana ganin yazo kusa da ita kunya ta kamata

Dan kayan sai a hankali komai na jikinta suna

nunawa gasu irin masu hade da wandone, yayi

qoqarin kamata amma yana xuwa kusa da ita ta

gudu ya kuwa biyota sai ji yayi kamar ana jansa

tuni ya nemi nutsewa a ruwan tana mai dariya

sai taga da gaske yakeyi yanda yake dukan

ruwa, ba shiri tama manta da wani kayan jikinta

da boyon da takeyi kada ya ganta tayi sauri ta

rungume shi ta janyoshi bakin ruwa farhaan duk

ruwan dayasha bai hanashi jin laushin fatar

jikinta ba jikinsu ya hadu sun kawo bakin ruwa

amma farhaan da iskanci yayi lamo a jikinta yaji

fresh fata ba irin ta gardawan yan matansa ba,

ta kalleshi ta jijjigashi ya bude ido a hankali tace

mai sannu ko? Ya harareta ya murguda baki

yanda yake murguda baki ya bata dariya ta

kuwa dara, yace dariya ma kike min ko bayan

kin wahaladda ni, tace to ai Kaine kasan baka

iyaba ka biyoni, ya qara narkewa a jikinta to

yanxu ka fita waje kamin nazo yace ba inda zaije

saima ta koya masa yanda takeyi, tayi tayi

amma ya nace ba inda zaije sai ta koyamai

yanda ya maqalqaleta ne ba yafi damunta tace

to sakeni sai muje! Yace wayo zaki min ki gudu

tace zan koya maka amma ba yanxuba yace

shiko idan har bazata koya mai yanxu baisaidai

su kwana chikin ruwa, Tace to, ya maqalqaleta

har suka kai gurin sannan ya saketa, ta fara

nuna mai farhaan kam kallonta yakeyi ba kallon

abinda take koya masaba....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 86

Na Hauwa M. Jabo.

Data gane kallonta yake tace a bari sai gobe

yace ai bai gwada ya ganiba ko ya iyaba, ta

riqoshi tana nuna mai ya bata wahala ba

kadanba amma fa shima yasha ruwa....

Hmmm , soyayyah cikin ruwa dadi wallahi, tana

Neman fita ya kamo gashinta saida tayi qara

tana waigowa ta zabgamai cizo shima saida yayi

qara tace ka tsani gashinnan nawa kodan ina

aske na yan matankane kakejin haushin nawa.!?

ya tun karo ta da qarfi tuni tayi wani super a

ruwa ta gudu yasan idan ma ya bita wasu

ruwan zaisha sai ya gyaleta, ko banxa tayi

tsokana bare ta sami abin fada, yana kallon ta

ta fita ruwan ya qurawa halittarta ido iffaat

akwai chinya, ga uban hips dinnan ta take

juyashi kamar me yayi murmushi ya lashe lebe

aransa yace Allah yayita bani sa'arki, har ta

wuce ta juyo taga yana kallonta tasan dama zai

kalla yanda ta saka wannan kayan haka tamai

bye tayi sauri ta wuce ya Dade a ruwa yana

tunani sannan ya fito ya shiga gida koda yaje ta

shiga kitchen daura abinchin dare, yaje ya saka

tufafi ya biyo ta kitchen ya rungumeta ta baya,

yayi kissing din wuyanta. Tace Dan Allah kaje ka

kalli ball dinka gashichan an fara. Yace au

korana ma kikeyi ko??

Ta baxan tafiba, tace yi haquri mana, yace kibar

girkin anjima sai mu fita muci tace itakam ba

inda zata chin abinci. Haka yayita damunta

kuma ya qi sakinta, saida yaga ta daure fuska ya

kama kanshi, ya dan samu tana sake mai idan

ta daure mai ai ya shiga uku yace tayi sauri ta

qare yana jiran ta,

Ayanda iffaat takeda saurin aiki yana burgeni

cikin lokaci kadan zatayi aiki ta qare dama tasan

farhaan akwai chin amala kamar Dan yarbawa

cox lokacin da tana mai aiki kusan kullum sai

anmai amala, ita kuma lokacin komai aka bata

chi take dukda bata gane abincin amma haka

take chinyiewa, to itama amala ta hada mai da

miyan agusi yaji kayan ciki yana qamshin

attarugu da carry ta hada mai fruit salad ta

kawo ta ijiye...

Uhummm su farhaan fa za'a fara dandana dadin

aure...

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..??87

Na Hauwa M. Jabo.

Bayan ta qare girki ta ta fito yanata mata sannu

murmushi kawai tayi, ta shiga bayi ta watsa

ruwa tayo alwula sannan ta fito shima yayi

alwula ya tafi masallaci ta zauna saida ta qare

kwalliyarta tsab sannan tayi sallah, nima ta

burgeni Allah ya qaro min yawan gashi nasamu

na kuri irin iffaat... Ta fito tsab da ita taje Palo

farhaan ya dawo kenan ya ware hannu irin taje

dinnan ta murguda masa baki abin ya bashi

dariya ita iffaat komai sai ta murguda baki...

Akaxo chin abinci nanma yace baxai iyaciba

itama tace bazata iya Chiba tofa sai Yaya wai

sai dai ya bata ta bashi haka sukayi kuwa

wannan karon bata batamai tufafi sosai ba, Dan

tana kallon yanda yake bata sai itama tana yin

hakanan suna chi yana bata labarin Thailand har

suka kammala suka tashi suka Dan zaga palon

Dan abincin ya fada musu, bayan sun qare

iffaat ta zauna farhaan yaje ya bude kayan da ya

siyo abinda yafi bata dariya hadda kayan baby

kuma bana babyn farahnax bane wai na babyn

da zasu haifane nan da wata Tara a yanda yace

murmushi kawai tayi ta tattara kayan ta saka a

wardrobe ta dawo ta zauna, yayi miqa kixo muje

ki kwanta mana, ta yatsina fuska kaje kawai

zanzo, habadai kizo muje kin gaji, tayi fari da ido

kaje mana idan naji bacci zanxo, ya dawo ya

zauna ni bazan kwanta idan bakiba...

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 88

Na Hauwa M. Jabo.

Okay.! zauna muyi kallo ya zauna suna kallo har

guraren 1 na dare iffaat idonta gyam akan TV ko

motsi yanayi yana satar kallonta amma batada

niyyar tashi, ya fara gyangyadi, ya karbi remote

ya kashe dole sai sunje sun kwanta, iffaat kuwa

ta fuske tace yaje xatazo yaga dai batada niyyar

tashi sai ya wuce yace yana jirinta tace mai OK,

iffaat dai anan ta gyangyade sai bacci da asuba

farhaan ne yaxo ya tayar da ita bacci yana Dan

shashafata har ta bude ido tamai murmushi ta

tashi taje tayi alwula tayi sallah ta dawo Palo

zata kwanta farhaan yasha gabanta yace idan

dai dannine ki kwantar da hankalin ba abinda

xan miki murmushi kawai tayi ta rabashi ta

wuce, taje taci gaba da baccin ta qarfe 9 ta

tashi ta hada mai breakfast ta shirya a D table

ta dawo tayi kwanciyarta sai goma ta tashi da

yake ba lecture ta Dan dima abincin a taje

taganshi yana sharar bacci wanka ta shiga ta

fito ta dandasa kwalliya ta saka wasu arnan

kaya cikin kayan da tasiyo ita kanta tasan tayi

ta fesa turare taxo kusa dashi ta shafa

kumatunsa a hankali ya bude ido ya kalleta

tamai murmushi ya janyo ta jikinsa sosai yayi

kissing dinta a kumatu, tadan goce ka tashi

muje kayi wanka, yayi miqa hadi da salatin

annabi ya miqe yaje wanka bayan ya fito tazo

tayashi goge jiki da shafa mai, daxai chanxa

kaya sai ta miqe xata fita ya janyo ta ina

xakije,? ta Sosa kai xan dauko abune a Palo yayi

murmushi aranshi yace mata da mijinta amma

tana guduwa. Ya saketa bata dawo ba saida ta

tabbatar da ya saka kayan sannan ta shigo.....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 89

Na Hauwa M.Jabo

Ta kalleshi ta riqe kunkumi iyeee kaganka

kuwa.!? Kayi kyau kamar sabon ango, ya kalleta

ya kanne ido yace ai angonne ko kinmanta har

yau baisha maiba,! Ta gane mi yake nufi sai ta

basar da zancen muje kayi breakfast kaje ka

gaida su Abba da umma, yace to my princess,

sun zauna ta kawo breakfast nan ma yasa

rigima har yanxu bai warwareba sai ta bashi a

baki, haka ta riq biye mai tana bashi yana chi

idan ya cijeta tace sai ta rama haka zata samu

wani guri shima ta chije shi har suka kammala,

ta rakashi har mota ta dawo ta tattara kayan

gudu gudu cox tanada lecture 12 gashi 11:30 ya

wuce ta qare ta wuce skull.

*********

Zaman iffaat da farhaan dai xan iya cewa lafiya

lau duk wani kula dashi tanayi ba abinda za'

nuna mata tun daga kwalliya har girki da tattalin

miji saidai har yau taqi bada hadin kai farhaan

yayi yayi amma taqi..

Ranar dai ya tirketa tana baccin rana a daki

yaxo ya dabai bayeta ya fara yan shafe shafensa

chan ta farka ta bude ido ta kalleshi tace miye

haka?? Yace mata sunnace haka, tace sunna

kuma? Yace eh bakisan annabi yace duk Wanda

ya aikata Wannan sunnatawaba daidai yake da

Wanda yayi jihadi ya kashe arna dububa. Ta

kalleshi ta kyalkyale da dariya har saida tayi

kwalla, sannan tace Yy farhaan watana hudu

gidannan watanka uku muna kwana daki daya

gado daya bargo daya bakasan da a kashe arna

ba sai yanxu farhaan kam ya fara nisa ba wani

jinta yakeba tuni tasa qarfi ta tureshi gefe ta

miqe zaune ta kalleshi rai a bace wallahi kada

ka qara kuskura kace zaka kusanceni! Ya kalleta

ido sun wani Kada haba iffaat mi yasa kike min

hakane? So kike na koma abin farko da nakeyi?

Wannan kuma ya rage naka ko yanxu waya sani

ko ana lallabawa dubunka ce bata cikaba na

kamaku, ko kuma anji tsoron cell shiyasa ake

kama kai amma dai badan iffaat ba kuma ba

Dan tsoron Allah ba.!.

Ta wuce Palo ya zauna saman gado yayi tsaki

wannan yarinya mayaudariyace wallahi, ta

koramin yan mata kuma ta hanani kanta kuma

gata kamar aljana duk abinda nakeyi tana gani,

yayi tsaki yadan kwanta akan gadon qafafunsa

suna qasa ya dafe kai miye abinyi??

Da gaskiyar ta Dan tsoron cell naqi Neman

matana amma yakamata na bari Dan Allah

badan kowaba. Yayi ajiyar numfashi...

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 90

Na Hauwa M.Jabo

Ya biyo ta Palo tana sauraren waqarda kusan

kullum saita saurareta koda waqar hausa bata

burgeshi amma har ya haddace wannan wai

kuma baiti dayane yakejin tana maimaitawa

kullum shine na badi ba rai soyayyah jigon

rayuwa ana cewa " itadai soyayyah maiyi bai

samun sauqi, a jini take yawo wasu gunsu tana

hanin aiki, na shiga cikinta ta xafar tamkar doki,

na shaida sone mahadi gun rayuwa"ya kalleta

yayi murmushi iffaat sarkin rigima normal

xatamai duk abinda yakeso amma da xaran ya

buqaceta sai taqi, ya zauna kusa ida ya daura

kanshi akan chinyoyinta yana wasa da jelar

gashinta, yace yakamata amin tafsirin wannan

baitin waqar kullum shine a bakinki tun kina

qarama nakejin kina yinsa, tace kace dai tun ina

Yar aikinka nakeyinsa, tayi murmushi, nidai jabo

da zasu ce na musu tafseer din wannan baitocin

waqar da zanyi page 100 dashi amma basu bani

damaba, iffaat ya kira sunanta ta kalleshi mi

yasa kike guduna? Tace gudu kuma? Yace eh

mana, tayi murmushi tace Sabida lokacin auren

mu ba'ayi su dinner, su party su lunching ba

wani Abu da akayi kaga kuwa kamar ba'ayi

aurenbane ya miqe zaune yanxu kinason ayine?

Tace eh ayi, shine matsalarki?? Eh to yanxu dai

shine na farko, yayi murmushi wallahi duk

abinda kikeso xa'amiki ya miqe zaune ya shiga

dakinsa ya kira abokinsa wannan da iffaat tayi

wa fitsari farhaan yace monkey din gidansune,

yamai bayanin komai kuma yana son ayi komai

cikin satinnan..

Bayan kwana biyu farhaan ya kawo mata IV

yace ta rabawa qawayenta taji dadi sosai ta

shiga rabo, duk Wanda ya tambayeta ba tayi

aureba sai tace na jin dadin aurene wannan.

tayi qayyar mutane farhaan ma haka su umma

dai kam saidai su saka musu ido Dan sunga abin

nasu wasane farahnax taxo su ZZ duk an hallaro

Yar baqa ma haka hatta su dijee da rukayya

ba'abarsu a bayaba.....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 91

Na Hauwa M. Jabo

Abin sai Wanda ya gani, farhaan har tausayi

yake bani wai wannan kudin da ya kashe duk

Dan cika umurnin Mrs purhuuun ne, anyi komai

cikin jin dadi da kwanciyar hankali su mama kam

sai fada sukeyi wannan bidi'a haka aure na

Neman shekara amma sai yanxu ake wani

qaqale qaqale iffaat kam taji dadin komai d

farhaan ya mata hatta kayan aure saida ya mata

sabbi akwatuna kamar dai sabuwar amarya koda

ai sabuwarce tunda har yanxu, wane yare da

sukecewa ((dast na khurde )) budurwar kenan

wacce batasan mazaba,

An sallami kowa cikin aminci inda amarya da

ango suka dawo gidansu farhaan kam hadda

shan maganin qara qarfi irin yau za'a suburbudi

iffaat...

mutuniyar kuwa ko a jikinta Dan tasan batada

tsarki, su farhaan anxo ana lalabe lalabe iffaat

ta dakatar dashi ta hanyar gayamai batada

tsarki kuma ta gaji ya barta tayi bacci, ga injin

dinsa ya riga yadau zafi, farhaan Dan takaici ya

rasa abinda zaiyi sai daukar key yayi ya fita yaje

kozai samu gunda xaiyi aiki yanda yayi tsingau

dinnan, iffaat ta gane ina ya nufa amma Sam

bata kulashiba.

farhaan bayan ya tafine yaje kuma yakasa

Neman matan banxar, haka ya samu daki ya

kwanta yanata juyi har bacci ya daukeshi bai

farkaba sai guraren 3 Subhanallahi, ya tashi da

sauri ya dawo gida koda yaxo ya tarar da iffaat

zaune tana kallo abin ya bashi mamaki kallon

iffaat cikin dare....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..??92

Na Hauwa M. Jabo

Yana shigowa ko kallonsa batayiba, duk kunya

ta kamashi, gashi ma abinda yajeyi ya kasa

aikatashi ya Dan Sosa kai yace bakiyi bacci ba!?

Tace nayi faarkawa nayi yanxu, yaga kamar

batayi fushiba sai ya matso kusa da ita zai

zauna tayi xunbur ta tashi kada ka kuskura ka

matso kusa dani tamai kallon raini kamar taga

wani kashi,

Ta kalleshi ai shi mai hali baya barin halinsa

tunda ka saba da Neman mata wallahi ba abinda

zaisa ka daina, ya xa'ayi na iya bacci bayan na

auri miji manemin mata, ido cikin ido ta kalleshi

tace farhaan nayi Dana sanin aurenka, nayi

baqin cikin kasan cewa tare dakai, babban abin

godiya ga Allah shine ba'abinda ya shiga

tsakaninmu, bare ayi xancen hada zuri'a na

tabbatar da yarana sai sunyi baqin ciki da

samin uba mazinaci irinka.!! Amma yanxu kaga

Hankali kwance zan nemi wani miji nayi aurena

kuma wallahi saina fadawa umma halin da kake

ciki..

Farhaan zuciya tayi xafi waishi take gayawa zata

nemi miji tayi aure, yaso ya mammaketa amma

sai ta wuce shi nan ya zauna yana Allah

wadaran halinsa yayi tsaki yafi sau dubu ya kasa

shiga dakin har bacci ya saceshi, iffaat kam ko

dar bata ga bacciba gari ya waye kamar kada

tamai breakfast Amma ta daure ta hada mai

taxo tasa qafa ta shureshi ya tashi, ta kalleshi a

wulaqance tace to aje ayi wanka a tsarkake jiki

ayi sallah, a karya aje gun Neman wasu matan,

aranshi yace wai dan wulaqanci da qafa xata

tayar dashi yaji bala'en haushi Dan kuwa da

atayar dashi da qafa gara a gyaleshi, kuma ga

magan ganun banxa tana gayamai ya kalleta

waike waya gaya miki Neman mata naje?! Cikin

isa da tsabar rasjin kunya Tace sabida ba

namijin kirkin da xai bar gidansa 12 na dare ya

dawo 3 sannan yace ba gun banxa yake

zuwaba, bare kaida akasan halinka na Neman

mata....

Farhaan dai ya kasa magana yayi wanka ko

karyawa yakasa yi ya Dan saba tana bashi a

baki yau kam yasan koxai mutu bazata bashi

abakiba,

Haka ya dawo office guraren yamma ta qare

girki tayi kwalliyarta kamar ba itaba.

..

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..??93

Na Hauwa M. Jabo

Tamai sannu da zuwa, ya amsa bayan ta juya

ya kalleta mace kamar hawainiya sai chanxa wa

takeyi, yaje yayi wanka.

ta kawo mai abinci Dana safe Dana rana na

yamma ma Dan ba yanxu yakeciba da sai ta

hado mai dashi kuma duk sai ya cinyeshi, ta ijiye

tace yaci wai ya qoshi, tamai kallon banxa kasan

Allah wallahi sai kacishi, ya kalleta yanda ta

hade fuska hakadai yayita durawa yana qarewa

yaje yayita amai ko sannu bata cemaiba yana

fitowa tace Allah yasa dai matan basu maka

cikiba!! dagachin abinci sai amai ta bashi dariya

sosai wai ciki, ya nemi guri ya zauna, bai

tankataba haka dai iffaat take da farhaan kullum

cikin yi masa habaici take, da rana taci uban

kwalliya da dare ta saka arnan kayan bacci ta

kuma fuske abinta, ranar da ya qara nemanta

tace sai yaje asibiti an duba shi idan bashida

rashin lafiya, farhaan kam ya shiga uku kullum

cikin baqin cikin yarinyar nan yake, lallai yanxune

yake sanin haqiqanin WACE CE ITA... dama

hausawa sunce Dan hakin daka raina shi yake

tsole maka ido, ai kuwa ga iffaat tana wanashi

Son ranta, farko yace bazaije asibiti ba daga

baya da yaga jan ran nata yayi yawa sai tsingau

yakeyi haka ya daure yaje aka dubashi, lafiya

lau yake ya kawo mata result tana kwance da

kayanta na daukar allhaki ta tashi zaune ta

duba taga lafiyanshi lau tace saura Abu daya

kuma yace bayason yaji ko miye wallahi sai ta

bashi haqqinsa, iffaat taga da gaske yakeyi

idonsa sunyi jaa sai xuba masifa yakeyi

hankalinta ya tashi tasan ba hanyar guduwa

amma ta fuske ta nuna kamar bataji tsoroba

farhaan kam matseta yayi ya cire mata kaya

duka cizo duk yasha amma ina saida yayi

nasarar kawar da budurcinta Allah sarki iffaat ta

bani tausayi.....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..??94

kuka take tamkar ranta zai fita,

Yaxo yana lallashinta yana bata haquri ya samu

ya mata wanka da gashin jiki yayi toweling dinta

ya kawota daki gaskiya taji jiki ba kadan ba

bakinnan nata haka ya mutu murus kamar ba

itaba, ba'ajima ba sai xaxxabi, farhaan shi

kanshi yasan bai mata dakyauba yama manta

sabon shigace an saba da masu wakeken abu

shiga daya kamar an kada guga a rijiya, wannan

kam a tame take fam shima da gyar ya samu

shiga, ko Suhaila ma kusan haka take but na

iffaat yayi yawa,

Ya kira Dr. su yamai bayani ya kawo mai yan

magunguna ya tayar da ita ya bata taqisha yayi

yayi amma taqisha sai rawar dari take ga

xafinda takeji a gurin, itakam ji take kamar ma

ya yageta, farhaan dai anyi jinyar iffaat bata mai

magana Sam, ko kallonsa ma batayi idan yaxo

rufe idonta takeyi yaxo yayita surutansa ya gaji

ba amsa...

Kwananta uku a kwance ko lecture bata xuwa,

ranar na hudu ta tafi skull, bayan sun fito lecture

ta hadu da armiya'u suna tadi armiya'u dai

kullum maganarta daya a kyautatawa miji a sha

Abu Dan qara ni'ima, iffaat ta kalleta, ke kullum

xance daya abinda ko dadi babu! Armiya'u ta

kalleta tayi murmushi yarinya baki maida

hankalinki bane abinda kawai zance miki wallahi

so sweat, iffaat kam bazata iya fadar cewa sai

yanxu ta shigo system ba sai ta basar da

maganar...

Ta dawo gida taga farhaan zaune batako

kalleshiba ta wuce daki tayi wanka ta fito taje

tayi girki, ta kawo mai yace dauke abinki

baxanciba kamar bataji mi yake fada ba ta kama

hanya ta wuce abinta janyota yayi da qarfi nace

ki dauke baxanciba, kallon mamaki tamai taga

yanda ya daure fuska aranta tace ai tunda ka

biya buqatarka shikenan banida daraja. har

zatayi magana kuma sai ta fasa da duqa zata

dauki abincin farhaan ya janyota wato daukewa

zakiyi ko? Bazaki tambayeni dalilin yin hakaba,?

Haba iffaat miyasa kike min hakane? kuka ya

kubce masa iffaat miyasa kike min hakane

eeeh ? Kullum kina azabtarda zuciyarda ta

damfaru da qaunarki, Dan kawai Kinga na damu

dake matseta yayi sosai jikinsa itama dai

hawayen suke xuba a idonta, ta fara magana

tana kuka basai na kawo mukuba kawai akan

Neman matanshine shi kuma yace tuni ya daina

koda bata aminta 100% ba amma taji ta

gamsu....

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA..?? 95A

Na Hauwa M. Jabo

Hmmmm.

Wai har sun shirya an yafi juna sunci abincin

tare...

Wata sabuwar soyayyah ce a Gidan ma'auratan

gwanin bansha'awa suna kula da junansu yanda

yakamata.

Yanxune iffaat take fahimtar abinda armiya'u ta

taba gayamata na cewa farhaan bamuqacine na

gaske lallai hakane kullum dai yajishi ciki

uhummm.

Abin ba'a cewa komai.

Iffaat ta cika alqawari takai goggo makka kuma

ta dauko qawayenta na qauye dije da rukayya an

baiwa mazajensu lebaranci a companyn su

farhaan suna shanawa suma ga dukkan alamu

suma su waye su xama yan gayu, amma bana

tunanin dijee zata waye Dan har yanxu tana nan

sai a hankali..

Bayan shekara 7

Koda naxo naga iffaat da yara uku mamaki ya

kamani naso naga iffaat da ciki amma ina

banganiba sai yayanta na gani..

Mace daya namiji biyu

Macen taci sunan Suhaila sai maxan dayan

sunan mahaifin iffaat mahmoud dayan sunan

mahaifin farhaan habeeb.

Farhaan ya zama kamilallen mutum kamar

bashiba, iffaat kam har yanxu saidai idan

ba'asamu damaba..

Dan Ko yau da naje muku gidan, saman bishiya

na ganta tana tsinkowa tana wurgowa qasa

yaranta suna cabewa sunata jin dadi, farhaan ya

shigo ya duba bata yasan ina taje ya girgixa

kai, yaje ya kirata tana ganinsa ta diro saman

bishiya saida naji tsoro na dauka ta karye sai na

tuna fiye da wannan ma tayi..

taje ta rungume shi tanamai oyoyo yace bawai

na hanaki hawa saman bishiya ba, ta kanne ido

tace waya iya raba monkey da hawa bishiya

dariya yayi ya tuna lokacinda tayi mai fitsari

saman bishiya yace monkey ne,

Suhaila ce ta shigo itada habeeb cox shi

Mahmoud jinjirene, Suhaila da wayo tace Abba

mu anti amarya mukeso.! gidansu hameed na

uncle Ali an musu anti amarya kullum sai yace

mana mu bamuda anti amarua, muma munason

anti.... iffaat tace kiji yarinya da gulma xanci

gidanku yanxu, ba anti amyaba anti ango bace

min da gani, sakarya kawai...!!

Suhaila ta wuce tana gunguni,

Farhaan kam dariya yakeyi sosai, iffaat ta

kalleshi miye haka.?? Daga jin anyi xancen

amarya sai wani washe baki kakeyi...

[8:07PM, 5/17/2015] .: WACE CE ITA.. ??95B

Na Hauwa M.jabo

To amaryaf taxo ina daidai da ita, yadan

muskuta dama akwai wata yarinya Dana gani ta

kwanta min arai inaga xan kawoma su Yy

Suhaila ita tunda tanason anti amarya, Yy

Suhaila suke kiran Yar tasu da ita.

iffaat hararanshi tayi tace wallahi baka isaba,

yayi dariya yace kefa kika ce taxo kina daidai da

ita,! Ta fuske tace eh ta murguda baki, farhaan

yayi dariya ya tashi ya shige, har yakai qofar

bayi bari nayi wanka xan kawo miki ita ki

ganta..

Iffaat kam taji ba daidaiba, harya fara wanka ta

kasa haqura ya fito ta bishi bayi Yy farhaan

waida gaske kakeyi? Yayi dariya sosai sannan

yace eh mana ya wanke ko ina xai dauraye jiki

ta kashe fanfo ta fara bala'e wallahi baxai

yiwuba, ai wannan sharrine, yace aah kinji

yarinya ke kinxama chuss dole na dauko sabuwa

a Leda na bare ta kenifa sai nayi mace hudu Dan

ki sani, kii kunna min ruwana mana, ta fara

kuka, wallahi sai ta gayawa umma yace umma

ai xataso a kawo mata sabuwar suruka ta haifo

mata jikoki, ba kece kin daina mini wankaba ai

dole na nemo mai mini wanka Dan ni Dan lelene,

cikin kuka tace xan riqa maka wanka wallahi,

yace to ki fara yanxu, ta kuwa kunna ruwa tamai

wanka Tass suka fito ta shirya shi sai yan

hawaye takeyi, abin yabana bashi dariya ba

kadan ba, tana zaune saiga Yy Suhaila ta shigo

iffaat tace ke get out masu tsokane tsokane

kawai, yarinya tayi tsaye bata gane dawan

gariba, farhaan yace Yy Suhaila kuje wasa kinji

yarinyar anti amarya tace yeeeeeeeee ta tafi da

gudu, farhaan yaga yanda iffaat ta hade fuska ta

miqe da qarfi zata fara yankomai bala'e ya

janyo ta ta fado jikinsa haba Yar gidan umma ni

na Isa na qara aure yanda nake da mace kamar

ki ai kin wuce 1 of 4 ke ta dabance kullum sweat

kike qarawa, ya fara kissing dinta, tace bayan

kace min chuss yace wallahi wasa nake miki

kinfi komai daraja a gurina kece sanadin

shiryuwata kuma kin haifomin Yaya masu kyau

masu kama dake, ta qara shigewa jikin sa tana

mai nata salon nidai sai na fito na basu guri

suci soyayyah kar na makance,....

TAMMAT BI HAMDILLAH....

Qarshe wannan littafin kenan

Ina godiya ga dinbin masoya da suke bibiyar ta a

wannan Dan qaramin littafi na WACE CE ITA.. ina

godiya ga masu bani shawara da Masu mini

gyara hadda masu zagi ban barku a bayaba ina

godiya matuqa Allah ya saka da alkhairi,

Nasan hausar tawa sai a hankali kuna qoqari

gurin karantawa...

Naso littafin yafi haka, akwai abubuwan da naso

na saka wayanda zasu qara nishadantar daku

amma kuma inaa exam ta matso kusa... Ayi

haquri da wannan sai mun hadu wani book mai

suna...........

nagode sosai

Don shawara ko gyara ga number ta +98936 594

4638

Banda tambayar wane guri nake please...

HAUWA MUHAMMAD JABO take muku fatan

alkhairi.

0 Response to "WACECE ITA Hausa Novel"

Post a Comment