-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Idan zuciya ta gyaru Hausa Novel

Idan zuciya ta gyaru Hausa Novel

 Idan zuciya ta gyaru Hausa Novel



1-01

Posted by ANaM Dorayi on 07:28 AM, 27-Jan-16

Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU

______________Na

______Fauziyya D Sulaima

19/81992.

"Chalo! Chalo! Chalo!" Zazzakar muryar

hatsabibiyar yarinyar ta fadi, ko ba'ayi bayani

ba kasan abinda kalmar chalo take nufi, wato

tsokanar fada ne da 'yan wani layi ke yiwa wani

layin, ko 'yan wata unguwa zuwa wata unguwar.

Jama'ar dake gefen hanya masu saida rake zuwa

goba, da yalo da doya suka fara hada kayansu,

daya daga cikin su ke fadin, "Kowa ya hada

kayansa don shegiyar yarinyar nan tun da ta

ambaci wannan kalmar ta chalo, to kuwa wanda

yayi sakaci zai yi a..." maganarsa ta tsaya tsak

dai-dai lokacin da ya hango zugarsu sun nufo su

da gudu, sun biyo wasu, ya suri farantinsa

wanda aci bal-bal ke tsakiya na kifi, suma 'yan

uwansa suka rufa masa baya kowa na neman

inda zai adana kayansa. "Chalo! Chalo! Chalo!!!"

Muryar zugar yaran dake biye da Abu suka

cigaba da fadi suna biye da 'yan uwansu

wadanda suka biyo, sukuwa yaran da aka biyo

sai kuma kara gudu suke yi, domin kada a

badesu da barkonon tsohuwar da su Abu ke

wulwulawa. Toka ce ake hadata da citta da

barkono a dake sai a kulle ta a leda a sanya

dutse a tsakiya a sanya zare a dinga wulwula ta,

idan aka cillata daga nesa sai ta fashe kamar an

cillah tiyagas (barkonon tsohuwa), duk mutumin

da ke harabar gurin sai yayi tari ko ya shide,

idan kuwa akaci karo da mai cutar (ASMA) kuwa

sai ta tashi. "A cilla- A cilla." Muryar Abu ta

kuma futowa tana baiwa abokan ta umurni

kenan, dan ganin yaran da suka biyo sunyi

musu nisa, ai kuwa babu bata lokaci suka hau

cillah kullinan tokar dake hannun nasu ji kake

tush! tush! tush! Tana fashewa a tsakiyar yaran

dake neman tsira daga farmakin su Abu,

wadanda Allah ya taimaka sun tsere wadanda

kuma keda rabon shan wuya tokar ta fashe a

tsakiyar su don haka suka fara tari da atishawa,

hatta mutanen dake makota dasu suma sun hau

atishawa, balle maza dake zaune a kofar gidaje

ana hira duk suma sun hau atishawa. Su kuwa

su Abu dariya suka sanya gami da ihu suna

fadin "Eye! Eye! Eye! Munci gari ba namu ba,

munci gari ba namu ba- munci gari ba namu

ba, munzo gidansu mun cisu" Wani mai kanti

dake kokarin zuba kananzir dai-dai lokacin da

abun ya fashe, ya shide kalanzir din ya zube a

kasa ya hasala don haka ya shiga shagonshi da

sauri yana atishawa ya dauko dorina yayi kansu

yana fadin "Shegun yara masu kama da iblisai

ba a sati guda baku bada mana wannan jarabar

ba, wallahi yau duk wanda na kama sai na fasa

masa jikinsa da dorinar nan" Yayi kansu da

gudu, Abu ta fara hangoshi don haka ta kuma

fasa ihu tana fadin "Kowa yayi ta kansa! Nima

nayi ta kaina, kowa ya guje dai, nima na guje

dai, kowa yayi ta kansa." Ko batayi bayani ba

sun san abunda take nufi, wato wani ya taho zai

doke su don haka kowa ya gudu, wai ai kuwa sai

suka kama gudu mai kantin nan ya bisu da

wasu samari biyu, da suma ke cin abinci aka

bude su su da abincin da kura, basuyi nasarar

kama ko daya ba domin yaran sun fisu gudu

tamkar barewu don daman sun san za'a biyo

su. Don sun saba duk randa aka yi biki ko suna

a gidan wasu aka kai musu cingam din fati

akube-kube sai anyi fada, don haka iyaye da

yawa ke hana 'ya'yansu zuwa akube-kube (fati),

yauma haka dince ta faru domin 'yan layinsu

Abu (Hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati)

tofa shine wani dan bayan layin nasu ya

warcewa 'yar layin..

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

yauma haka dince ta faru domin 'yar layinsu

Abu (hatsabibiya ce) ta gayyaci akube-kube (fati)

tofa shine wani dan bayan layin nasu ya

warcewa 'yar layin su kwanonta na akube-kube

lokacin da suke tsaka da rera wakar akube-kube

sai walo, munje mun dawo sai walo, sannunku

da zuwa sai walo, ga kwanan fati sai walo. Tofa

shine Abu tace a futo da kwanon suka kiya

shine fa fada ya harke ana ta karawa sannan

aka bada oda a dauko bom, shine fa aka biyo

'yan bayan layi. A bakin wata makarantar boko

suka dinga zubewa suna haki don sun san sun

tserewa wadanda suka biyo su. Sai tillikar dariya

sukeyi suna mai da yanda akayi. Abu ta fito da

kifi a hannunta soyayye tace, banzaye nifa mai

kifin nan da yake gudu sai dana suri kifi daya

wanda ya fado, nan fa kowa yayi karaf yace

raba dai-dai (wato wata sarace ake kullawa idan

kuka kulla raba dai-dai to da kaga mutum yana

cin abu idan ka riga shi fadin raba dai-dai to sai

ya raba biyu ya baka idan shima yaga kana ci

yace maka haka to sai ka bashi kaima, idan

kuma mai cin abin ne ya riga fadin bazai bada

ba). Abu ta sha kunu tace "Dallacan wa zan

baiwa wa zan hana" Ta bare ta cire kayar ta

lunkuma a bakinta tana muzurai, kowa ya tsaya

yana kallonta don dai ita masifaffiyace tsoronta

ake ji, wani yaro ne a cikinsu yayi karfin hali

yace "Gaskiya mu kwance ke Abun nan." Ya

mika mata hannu "Idan kece kika ga mutum

yana ci kika ce raba dai-dai idan bai baki ba

warta kike yi, amma idan kece sai kiki badawa."

Ta cire dankwalinta taci dammara dashi tace

"Anyi din, duk wanda ya isa ya kwata wallahi"

Habu yace "Banza ai ba tsoronki ake ji ba, daga

yau mun kwance nima." "La-la-la, ni kake zagi

wallahi ba zan yadda ba." Ta danki kasa a

hannu biyu ta matsa gabansa tace "Gata tsiya

gata arziki." Ya tankwabe ta tsiyar ai kuwa sai ta

rarumeshi, nan fa dambe ya kaure sauran yaran

suka rude da ihu eyeh-eyeh-eyeh, sannu suna

musu wata waka, "Ku chasu arna ku chasu, ku

chasu ba mai raba ku, wanda ya raba su shi

yayi barna, kai ku chasu arna ku chasu, ku

chasu ba mai rabaku." Su kuma tamkar ana

kara zugasu sai dambe suke yi, da yake Abu

'yar dama-dama ce mai kiba gata da karfi da

karfin zuciya ta daga Habu ta naka shi da kasa,

aka kuma rudewa da ihu da kyar aka janye ta

daga kanshi tana fadin "Wallahi da kun barni

yau da sai na chas-chas karashi." Shi kuwa ihun

da ake masa ya sanya ya fashe da kuka yayi

hanyar gida, suma saura suka bishi ana masa

ihu, ita kuma Abu sai kuma masifa takeyi tana

tafa hannuwa tana fadin "wallahi mutum yaje

ya fada a gidansu wanshi yazo ya tabani gobe

nima na zane shi." Sauran 'yan fadan ta suna ta

zugata tana dariya, a haka suka isa kowa ya nufi

gidansu, Abu tace "Bari naje na dauko gyada ta

na kasa wallahi kuma naji yaro ya zageni ya

sani." Ta shiga gidansu har lokacin da

damararta, Babarta dake zaune wacce asalin

sunanta Salamatu ne suke ce mata Sala tace

"Yauwa 'yar albarka yanzu nake tunaninki tun

da kuka tafi akube-kube baku dawo ba." Ta

fashe da dariya tace yau na gaya miki Sala

wallahi na chas kara yaron nan Habu, daman ya

raina ni har kuka na saka shi wallahi ya tafi

gidansu yana ta kuka. Sala ta fashe da dariya

tace "Yata giwar mata, wanda ya tabaki ya tabo

ramin zuma, bana son sanya ki cigaba da chasa

duk wanda ya kawo miki wargi ni na saka ki."

Tayi dariya tana gyara kashin gyadar tata tace

"Ta nawa ce Sala?" Tayi dariya tace "Haba

maitsada (Sunan da take kiranta dashi kenan) ai

ke ba sai an kirga miki ba, ke ai me kan arziki

ce yanzu zaki dawo nasan kudina ba zasu bata

ba sai dai ma su karu, dauki kawai kije da dai

Karimatu ce mai kan kwantai (kanwar Abu ce)"

Abu tayi dariya gami da daukar farantin wanda

aci bal-bal ke tsakiyarsa tayi waje da kujerar

zamanta.

Can hanyar 'yar kasuwa ta nufa inda masu lemo

da agwaluma da rake ke saidawa, tun da ta fito

aka karbi kujerar wata kawarta Laraba, suka tafi

suna tafe suna hirarsu akan fadan da suka yi da

Habu, da kuma chalon su. Sanda ta isa bakin

'yar kasuwa ta ajiye farantin ta, samari suka

fara zagayeta kowa ya dauki gwangwani guda

yana ci ana hira, rabin hirar duk batsa ce,

amma da yake Abu ta saba jin irin wannan hirar

sam bata damu ba, sai dai ta sheke da dariya

tace shege wane, can wani Rosi yace "Ke ai

wallahi Abu har yanzu baki waye ba, ki duba ko

kwana bakiyi a waje kullum kina gida." Ta mike

tsaye tace "Kan Uban can, har zaka ce ban waye

ba, don Allah dubeka Rosi din nan kaifa wallahi

tsami ne, don dai yayana jarababbe ne wallahi

da nima kwana zan dinga yi kamar Laraba ko

yaya kikace kawas?" Ta bawa Laraba hannu suka

tafa

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

. Mudi Niga yace "A'a ba wani Laraba taso muje

muyi zancen mu bayan makaranta kada 'yan sa

ido su ganmu." Abu ta tabe baki tace "Wallahi

nima don jarababben yayana ya saka min ido

ne, yanzu da an ganni za'a gaya masa yaci

ubana, wallahi da nima acan zan dinga zancen,

amma zan yi maganinsa." Su Laraba dai suka

mike suka tafi ita kuma suka cigaba da hira da

su Rosi. Karfe goma da rabi sannan ta dauko

kayan tallarta tana ta mita a fili "Banza su Rosi

din nan shiyasa bana sakar musu fuska, da

Kwage ne ko Damisa ai da tuni sunyi mini juye

mtss!" Taja tsaki, yanzu da kwantai zan koma

gida? bari dai na biya gurin dan Oga dan nasan

shi dole ne kila ya siye yanzu. Ta nufi chemist

din nasa da fitilar kwai a bisa tebur, yana zaune

a bisa kujera mai kama da tsohon soja, babu ko

sallama ta bankade dan yalolon farin yadin dake

kofar da sunan labule ta shiga tana fadin dan

oga kana nan baka tashi ba? Ya mike cike da

murna yace Wow! Habu yanzu kana rena wallahi

ina son ka da gani (cikin gurbatacciyar muryarsa

yake mata magana) ita kuwa ta ajiye gyadar

bisa wannan tsohon tebur din ta hure aci bal-

bal din tace "Daman zan biyo yanzu ga gyadar

zaka siya duka ko?" Ya matsa jikinta yana cewa

"Habu Habu, wallahi kana da cho, ina ta sonka

da yawa, amman zaka kwana anan ko?" Ta zaro

ido waje tace "Kaifa baka da hankali wani

lokacin, idan na kwana a gurin ka nace me a

gida....." Ya jawo ta jikinsa yana mata abinda ya

saba duk da ba gamsuwa yake yi ba, domin dai

lalubeta yakeyi, don taki amince masa dari bisa

dari sai dai yayi abinda ya samu (Allah ya

shirya, jama'a ku duba diya mace ta futa har

zuwa wannan lokacin uwarta bata neme ta ba,

tur da irin wannan Uwa). .

鈥u ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Can tace "Malam na gaji zan tafi kada

jarababban can ya biyo sahuna don ma nasan

Sala zata kareni sallameni na tafi." Ya mike yana

gyara riga yace "Habu-Habu, wallahi yarinyar

nan baka da cho kina yawo da akalina, amman

zan rama ne." Tayi dariya tana fadin "Dan oga

kenan." Ya miko mata Nairori har na Naira

ashirin tace "La-la nagode." Ta sunkuci farantin

gyadar ta fuce da sauri tana fadin "Duka gyadar

ma ta naira ashirin ce amman ya bani Naira

ashirin" Shi kuwa sai kiran sunanta yake yana

dariya har ta kulewa ganinsa.(Wallahi sai mun

zamo masu taka tsantsan da irin kabilun nan da

suke mu;amala da yaranmu)鈥�.Sanda ta isa gida

an turo kofar da tirmi ba'a kulle ba, don haka ta

tura a hankali ta shiga da kullin namanta na

naira daya da ta siyo don kudin dake hannunta

naira ashirin da shida ne ga kuma sauran

gyada. Ta shiga dakin Sala ta taddata abisa leda

tana ta sharara bacci kamar matacciya (Ku duba

irin wannan Rashin tunani, ki tura diyarki talla

tayi dare amma ko damuwa bakiyi ba, bacci ma

kikeyi hankalinki kwance!!) A hankali ta dinga

taba ta tana fadin "Sala! Sala! Sala! Na dawo."

Sala ta mike tana magagin har ta wartsake tace

"Diyar arziki kin saida ko?" Abu tayi hamma

babu ko rufe baki balle salati, sai wani nishi da

tayi hmmmammman har bakin ya rufe da

kanshi, sannan tace na dawo ga kudin nan da

sauran gyadar dai, Sala ta sha kunu tace "Haba

Abu, kince fa a kunga-kunga har ta kare...." Tayi

shiru da zancen da taga ruwan Nairori a

gabanta, ta debo su da sauri tana kirgawa sai

ga naira ashirin har da Uku. Ta washe baki tana

fadin "Diyar albarka lallai kice samuwa kika yi

daga sama, wannan fa shine riba biyu ga kudi

ga sauran gyada, na baiwa Shehu da safe ya

karasata idan kin tafi makaranta, kin siyo

naman? Domin mai nema idan baya ci wata

rana shi za'a tafi nemowa." Abu ta nuna mata

ledar naman ba tare da tace komai ba ta mike,

Sala tace "Gwara dai aje a huta don ai kin gaji

na sani, sai da safe mai tsada." Tace to Allah ya

kaimu. Ta fuce a tsakar gida taci karo da Sadiku

yayanta ya shigo yana huci, ke don Ubanki ina

kika biya naje bakin 'yar kasuwa ban ganki ba

kuma ban dade da barin gidan nan ba? Ta

murguda baki gami da harararsa tace "To ina

ruwanka dani eyeh malam...." "Ke don ubanki

rashin kunya zakiyi mini? To yau idan baki gaya

mini inda kikaje ba wallahi sai na faffasa miki

jikinki." Yayi kanta ai kuwa suka kwasa da gudu

tayi dakin Sala wacce sukayi karo a bakin kofa.

Cikin hargowa da bala'i Sala tace "Malam meye

haka zaka biyo mini diya da gudu salon taje ta

karye ka cuceni? Wallahi yaron nan ka futa daga

idona na rufe kaji ko? Kai waye ne da zaka

matsa mata eye? Ko kai ne uwarta daka haifar

mani ko kuma kai ne Ubanta eye?" Cikin

hargowa take bala'in, ita kuma Abu tana gefe ta

rike kugu tana murguda baki da gatsina fuska.

Ransa ya kuma baci yace "Haba Sala, yaushe

zaki rufe idonki kina ji kuma kina gani Zainabu

ta dinga kaiwa dare a waje kuma idan ance

za'ayi mata fada kice baki yarda ba, yanzu ki

duba agogo karfe sha biyu har da rabi na dare

ace sai yanzu yarinya mace zata dawo gida." "To

Ubana ai sai kazo ka rufeni da duka, nace kazo

ka rufeni da duka!" Ta fadi da hargowa, kana ta

cigaba da cewa "Ina ruwana da wani lokaci ko

karfe dubu na dare zata dawo bai shafeka ba, ai

ba kai ne ka haifar mini ita ba, kuma da kake

cewar neman kudi hauka ne inace kaima nan

kake shigowa kana rara gefe a sammaka abinci,

kato dakai ba don tana nemowa ba zakaci ne?

shi solobiyon Uban naku idan muka daka ta

tashi zamu rayune? tun yaushe ya bar gidan

nan tun asuba ya tsallakemu ya gudu har yanzu

bai shigo ba sai mun kuma wani bacci, to zamu

zauna ne mu mutu idan bamu nema ba?

Wallahi ka fita daga idona ka samawa yarinyar

nan lafiya idan ba haka ba ranka zai baci." Ta

kuma cigaba da masifa.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

A gidan nan dame zata ji, da tsanar ta da 'yan

unguwa sukayi ko ko da jarabarka, yanzu daga

safiya suwa yanzu kasan nawa ta samu tun safe

kake,zan bata maka rai wallahi." Ya kwantar da

murya duk da ransa a bace yake yace "Sala ki

fahimce ni, ba wai ina yiwa Zainab fada don

bana sonta ba, sai dai a matsayina na

dan'uwanta ba zanso ace ta lalace ba, ki dubi

yanda kowa ya budi baki a unguwar nan

maganarta zaiyi, idan tsokanace itace gaba, Sala

yaushe... Kai rufe mini baki sai kwarara zance

kake babu kwama babu fulsu tof, ratatata

kamar zubar ruwan sama. To tayi din uban wani

ya hana, wato kafi so a dinga koro mini ita da

duka ko? To ban haifi sallamammiya ba, kai

tunda sallamamme ne sai kaje kayi tayi, ta dubi

Abu mai tsada shige daki kici namanki kiyi

kwanciyarki kamar tsumma a randa, naga

shegen da zai kuma takura miki." Abu ta kuma

murguda baki gami da yin gatsine ta shiga cikin

dakin su ita da kannenta duka uku duk matane

ta haye bisa katifarta ta bude namanta tana ci

gami da kunna rediyonta da wani saurayinta ya

bata, wakar lagireto ta fara futowa a hankali.

Itama Sala daki ta shige tabar Sadiku a can

tsaye kamar ya hadiyi zuciya ya mutu yake ji

don takaici, me ake da irin wannan rayuwa ace

kiri-kiri an san gaskiya ake takewa saboda son

duniya? Yaja tsaki yana fadin "Allah ya ganar

daku gaskiya." Ya nufi dakin sa dake soro yayi

fakare cike da tunani, jin kidan dake tasowa a

rediyon Abu yake yi har cikin ransa, don dai

yana shakkar bala'in Sala ne da wallahi sai ya

maka rediyon da kasa uban kowa ma ya huta,

yana nan kwance ya jiyo ta kashe da alamu

bacci zatayi kenan. Ba'afi minti talatin da hakan

ba yaji alamun shigowa, ko ba'a fada masa ba

ya san Babansu ne, ya dubi agogo karfe daya

da minti goma sha tara, yaja tsaki cike da

takaici, yana jinsa ya rufe kofar gidan ya leko ta

tsakanin labule yana kallonsa takalminsa a

hannunsa suke sai sanda yake sadaf-sadaf! Da

haka ya nufi daki, daga inda yake yana jiyo

munsharin Sala da alama bacci yayi awon gaba

da ita, ya saki labulen ya koma ya kwanta yana

tunanin wannan mummunar rayuwa da suke yi

da iyayensu, a haka har bacci barawo yazo ya

sace shi.

Da sassafe ta tashi ta shiga bandaki tayo alwala

tayi sallah, sannan aka jawo kayan kwalliya aka

maka mai, hoda da jan baki wato dai tayi tsaka

tsami kenan. Jagirar nan da aka ja har ta kusa

taba kunne ga jambaki an saka shi an kawo baki

an zagaye saman leben dashi, anyi wani digo a

tsakiyar goshin akayi wani bisa hanci, ga gefen

haba,sannan aka bude adaka aka dauko wata

atamfa 'yar kaduna Nichem, aka sanya aka yafa

gyale a kafada bayan ta daura dan kwali disko,

ta kalli madubi tayi kyau matuka, tayi murmushi

ta futo tsakar gida. Sala dake can kicin tana

suyar funkaso da miya tace "A'a kin shiryo, to

maza a dauka mai kan albarka kada lokacin

makaranta ya kure gashi nan na zuba miki

naki," tace To, kana ta nufi gurin da aka ajiye

mata nata din cikin watan fanteka, da miya a

cikin bokitin fenti, ta dora a kanta su kuma

kannenta suna ta mikawa na kofar gida dake

zaune suna siya. To maza mai kan albarka kada

a dawo da ko guda daya kinji ko? Bata ce komai

ba ta fice da digirgire don gwana ce gurin

daukar kaya a kanta. A hanya suka hadu da

Laraba, itama tana dauke da waina bandashe

mai kuli da mai da albasa) suka tafa kana suka

rankaya bakin tashar 'yan kifi, suna tafe suna

shan hirarsu suna dariya. Karfe takwas da minti

arba'in ta dawo, Sala ta tareta tana cewa

"Yauwa diyar arziki maza sauke ki shirya kada ki

makara, na zuba miki kici ne?" Tace "A'a naci

acan bakin tasha." ta mikawa Sala kudin ta

shige cikin dakin ta sanyo kayan makarantar ta

bulu din uniform da farin hijab, amman bata

sanya hijab din ba sai cin damara dashi tayi ta

rumgume littafai a hannu ta fice. Sala tace "Ga

kudin mota." Tace, "Ina da kudi ki barshi kawai."

"To a dawo lafiya a dawo dai da wuri." Tace to.

Ta fuce da sauri, tana fita ta sami hayis ta haye

aka sauketa a kofar makarantar 'yan mata ta

G.G.S.S Dala. Sanda ta isa ana taron 'yan latti

ko ma nace an gama, don wadanda aka tare din

an tura su cikin makaranta tsintar bola, sai

Discipline master da prefect ne a bakin kofa.

Babu ko shayi ta nufi kofar tana taunar cingam

din ta kas-kas, malam Kabiru discipling master

ya dubeta da takaici sanda take shirin shigewa

ko kallonsa ma bata yi ba yace "Ke zo nan."

Babu ko shayi ta nufeshi tana taunar cingam. Ya

dubeta a kufule yace "Ni sa'an Ubanki ne da

zaki tsaya mini?" Ta murguda baki tana kunkuni

taki durkusawa, ya zanbada mata bulala yace

"Kade doron sha-sha-sha."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta murguda baki gami da cigaba da yin

kunkuninta ta durkusa "Me kike cewa?" "Uwarka

nace" Ta fada a hankali, da motsin bakin ta yaso

ya fahimci abinda tace yace "me kika ce?," Tace

"Ni fa bance komai ba malam." Yayi ajiyar

zuciya kana yace "Mai yasa ke kullum sai kinyi

latti ne eye? Idan baki son makarantar ki daina

zuwa mana sai kace an miki dole, shegiya tun

baki tafasa ba zaki kone, kina aji daya tal amma

kin gallabi kowa, to wallahi idan bakiyi hankali

ba sai an kore ki daga makarantar nan,tunda ta

uwarkace ba?" Ta fadi a hankali, yaso ya juyo

amman bai fahimci abunda tace din ba, don

haka yace "me kike cewa?" Ta dubeshi da

shagwaba "Haba malam ni fa ban ce komai ba."

Yace shikenan tashi kibi 'yan uwanki kuyi tsintar

shara. Ta ce "To shege." Ta fada a hankali,Ta

mike ta nufi inda ta hango dalibai sunbi, sai a

sannan ya hango hijabinta daure a kugunta "Ke!

ke!! ke!!! Zo nan." Ya kuma kwala mata kira

amman tayi banza "Ke! Zainab ba kiranki nake

yi ba?" Ta juya tace "Au ai naji kana cewa ke ne

bansan dani kake ba, gani malam." "Ki cire

hijabin nan ki saka a jikinki." Ta yamutsa fuska

tace "Gaskiya malam zafi nake ji, bazan iya

yafawa ba" Da haushi yace "Idan baki yafa ba

ko zan zaneki a gurin nan." Lallai Malam Kabirun

nan bai san Abu bane, ta murguda baki gami da

dafe kugu da hannu daya tace "Allah ko kasheni

zakayi ba zan yafa ba don zafi nake ji, haka

kawai ba za'a sanya kurajen gumi su futo mini

ba, dan babu mai sai mini magani." Ya hasala

sosai ya nufeta da fushi ya daga bulalar dake

hannunsa zai maka mata, amman ta rike ta

gam tace "Allah malam ba zan yafa ba." Can

wata firifet ta hasala tace "Malam ka barmu da

shegiyar yarinyar nan taurin kai ne da ita bata

da mutunci, kusan kullum haka muke da ita taki

ta daina yin latti," Bata gama mai maganar ba,

ya fisge bulalar daga hannun Abu ya tsula mata,

Ai kuwa sai ta fasa wata uwar kara kana tayi

kansa ta cakumu wuyar babbar rigarsa ta shige

ciki, ya rasa yanda zai yi da ita sai hargowa yake

yi yana fadin "futo don ubanki, kina ina ne?"

Tana ihu ya rasa yanda zaiyi da ita dole ya cire

babbar rigar data makale a jiki ya kalleta da

takaici yace "To tashi kije ki wanke bandakin can

na seniors." Ta wurgar da malum-malun din "ni

gaskiya ba zan wanke kashin wasu garada ba,

haka kawai?" Ya rasa yanda zaiyi da ita, yau

Allah ya hadashi da shegiyar yarinya mara tsoro,

duk yanda ake jin tsoronsa a makarantar banda

ita,ya mike ya nufi Ofis din principal yana fadin

"Yau zaki ci Ubanki wallahi," babu ko shakka ta

bishi wata firifet tace, Zaki ci ubanki yau, za'ayi

maganinki. Ta dalla mata harara tace "banza kiji

da wadannan hakoran naki masu kama da kaca,

"Ke ni kike gayawa haka?" Tayi kanta da bulala,

ita ko ta tsaya kyam tana jiran ta karaso ta huce

a kanta, wata ce ta rike ta tace ke me yayi miki,

Malam Kabiru ya kwala mata kira da yayi nisa,

ta debi littafanta dake hannu ta bishi kamar ba

zata taka kasa ba. Ya shiga Ofis din principal

dake zaune a wata katuwar kujera taci

kwalliyarta ta sha glass dinta, daga ganinta kaga

tsohuwar 'yar boko. "Yaya dai Malam Kabiru

lafiya ne na ganka rai a bace?" Ya sami kujera

ya zauna yana huci yace "Hajiya yau wata

fitinanniyar yarinya ce ta bata mini rai bari ki

ganta." Abu ta shigo Ofis din babu ko sallama ta

dubi principal din tace "Sannu Ma." Bata amsa

ba illa kara gyara glass dinta da tayi tana duban

Abu dake tsaye kerere tace "Kika tsaya mana a

kanmu kamar wasu sa'anninki." A hankali Abu

tace "Da fa?" Sannan ta tsugunna. Malam Kabiru

yace "Kinji ko da kunnenki?, tun dazu wannan

kun-kunin take mini bana jin abunda take cewa,

sai dai ina zaton zagina take yi." Hajiya Kubra

tace "Malam Kabiru sanar dani me ya faru

kwantar da hankalinka." Babu bata lokaci ya

zayyane mata komai tun daga farko har karshe.

Hajiya Kubra ta dubi Abu da harshen nasara

tace mata "Haka ne abinda yace?" Da yake Abu

jaka ce bata iya turanci ba, domin ba zuwa

makarantar takeyi ba sai taga dama, idan tazo

kuma din bata yin komai sai hatsabibanci, don

haka bata iya komai ba, hakan ce ya sanya ta

yiwa shugabar makarantar shiru tana guna-guni.

Shugabar makarantar ta hasala ta doka mata

tsawa gami da kara maimaita mata abinda ta

tambayeta da fari.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Abu tace "Maa nifa bana jin abinda kike fada

gwara kiyi mini da yarena, don ni bana jin

abinda kike fada." Tana wani fisge-fisge take

wannan maganar. Ran Hajiya Kubra ya kuma

baci, don haka ta dinga zagin Abu da turanci,

tana fada mata "Banza jaka, baki san komai ba

sai shegen iskanci da rashin mutunci, a haka

za'a gama karatu ba'a san komai ba sai a kare a

auren dan dako ko dan acaba."Kalma daya Abu

ta fahimta a duk cikin maganar Hajiya Kubra

wacce tace mata "donkey" wato jaka, hakan ne

ya sanya ta fahimci irin cin mutuncin da ake

mata dan haka ta kama guna-guninta tana

fadin "gaki nan babbar jaka, ki dubeki fa tamkar

kayan wanki." "Me kike cewa?" Shugabar ta

tambaya da dacin rai jin Abu na magana kasa-

kasa. Ta murguda baki tace, "Ni fa bance komai

ba." Hajiya Kubra ta dubi Malam Kabiru tace,

"Malan zane mani ita kafin na bata horon da

zan bata tukunna." Duk da gabansa ya fadi dan

yana gudun makalewar da Abu take masa,

amman sai ya daure yayi ta maza ya nufeta da

zabgegiyar dorina. Ai kuwa yanda tayi masa

dazu haka tayi masa yanzu, ta cukwikwiye shi

tana ta zabga ihu, amman babu ko alamar

digon hawaye a idonta, da kyar ya samu yayi

mata guda Uku yana mai da numfashi.Hajiya

Kubra tace "To maza dauki tsintsiya ki share

harabar malamai duka yanzun nan." Ta mike

tana guna-gunin nata tace "Oho dai! Ko yanzu

na wahalar daku,"Me kike cewa?" Ta tambayi

Abun wacce tuni tayi fucewarta, ta kuma duban

Malam Kabiru tana fadin "Lallai yarinyar nan

bata da mutunci, shegiya irinsu ne idan suka

hadu da maza jahilai irinsu suke lakada musu

duka." Shi dai baice komai ba, yayi godiya ya

fuce domin dai Abu ta wuce iyakacin tunaninsa.

Abu tayi zaton abun na wasa ne, sai gashi

wankin hula yana neman ya kaita dare, dan

bata kammala ba har aka fita tara (break),

sannan ta nufi Ofis din shugabar makarantar

(principal) tace "Maa na gama." Ta dubeta a

wulakance tace "Ki yafa hijab dinki, sannan kada

ki kuma yadda a kawo mini kararki Ofis dina,

idan ba haka ba sai na koreki ko kuma kizo da

Baban ki." Abu ta cire hijab din nata ta sanya

wanda daman dan mitsitsine tace "To!" Sannan

ta fice daga Ofis din. Hajiya Kubra tayi kwafa

gami da yin tsaki tana fadin "Dakikiyar banza,

bata san komai ba sai iskanci." Ita kuwa Abu

tana yin nisa daga Ofis din ta cire hijab din

daga kanta ta kuma yin damara dashi sannan ta

nufi ajinsu. Kawayenta ne suka tarota ana ta

ihu suka rungumeta suna mata kirarinta, domin

wadanda abun ya faru a gabansu sun basu

labari, da haka suka karasa aji suna shewa har

aka koma break. Sai dai da zamanta da rashinsa

kusan duk daya ne a ajin, domin dai bata

tambayi abinda akayi ba da bata nan ba,

sannan yanzu ma da malami ya shigo bata tsaya

ta saurareshi ba hirarsu kawai sukeyi da wata

kawarta, kusan sau uku malamin yana

gargadinta akan tayi shiriu amman batayi

shurun ba, har ya gaji dai ya tambayeta kamar

haka "Abu, tell me how many are types of

letter?" Yana nufin ta gaya masa kashe-kashen

wasika. Tayi tsuru-tsuru don bata fahimci

tambayar bama balle tasan amsar da zata

bashi, sai wani murguda baki kawai takeyi tana

guna-guninta. ganin bata da niyyar bada amsar

ne ya sanya ya kuma gargadin ta akan tayi shiru

ta saurareshi, dan darasin turanci yana da

amfani ga dalibai don ta haka ne zasu koyi

yanda zasuyi magana dashi, amman har ya fita

daga ajin nan Abu bata daina surutunta ba sai

dai ta rage murya ba kamar da farko ba.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Da aka tashi ma sai da sukayi fada da

kwandasta domin dai idan da sabo ta saba,

domin dai maimakon ta bashi naira biyar sai ta

bashi naira uku ba kuma don bata dasu ba, a'a

dan dai neman jidali kawai irin nata.

Kwandastan ya dubeta ransa a bace yace "Ke!

Malama cika mana kudin mu saura naira biyu."

Tayi tafi gami da doka cinya tana fadin ba zata

cika ko kwandala ba don haka kudin motar

yake. Nan fa rikici ya rincabe amman Abu ta

kekashe akan ba zata cika ko kwabo ba. Daga

karshe yace wallahi idan bata cika masa ba zai

warci dankwalinta, maimakon ta saduda ina sai

ma ta cigaba da tsiwarta tana tafa hannu,

kawayenta na ta zugata. Abin ya hasala direban

yace masa ya cire dankwalinta tunda bata da

mutunci, dan haka ya cire dan kwalin nata. Sai

dai abu da kwandastan bai sani ba shine tuni

Abu ta gama dana masa tarko, don haka da ta

sauka kafin ya hau motar tace masa "Malam ka

bani dan kwalina." Yace "Na karfi ne, idan kina

son dankwalinki ki cika mini naira

biyu.......Warce gudar Naira ashirin da fellewarta

da gudu ne ya katse masa zancensa, ya saki

baki galala yana kallonta tamkar zata tashi sama

dan gudu, don Allah ya yi mata baiwar gudu.

Direban ya hau masifa sanda ya ankara da

abinda ya faru yana fadin "Banza sakarai, kana

me wannan 'yar mitsitsiyar yarinyar ta warce

kudi a hannunka? ai sai ka shigo mu tafi." 'Yan

cikin motar banda dariya babu abinda suke yi,

shi kuwa cike da jin haushi yake fadin "Haba

Oga baka ga shammata ta tayi ba? An bani

murtala ina shirin bada canji ta fisga ba?"

"Kawai kazo mu tafi, shegiyar ta bamu a can"

Direban ya katse masa magana. Ya dubi inda

Abu tabi ko alamunta baya gani dan akwaita da

gudu tamkar filfilwa, hayaniyar fasinjoji ce ta

sanya shi shiga motar yana fadin "Ai na gane

wallahi duk ranar da Allah ya kuma hadamu sai

taci ubanta." Ya shiga mota har lokacin wasu

fasinjoji suna dariya abinda ya kara kular dashi.

Ita kam Abu tunda ta falla da gudu bata tsaya a

ko'ina ba sai a tsakar gidan su, ta zube a kasa

tana mai da numfashi. Sala dake kwashe wake

da shinkafa ta dago tana dubanta a rude tace

"Yaya dai Maitsada, lafiya kike wannan hakin

kamar wacce tayi tseren gudu?" Sai data

numfasa sannan ta kwashe da dariya harda rike

ciki, duk da Sala bata san ko dariyar me take yi

ba sai ta hau tayata tana fadin "Hatsabibiya,

yanzu haka tsiyar taki kika shuka tunda naga

kina wannan dariyar." Tayi kokarin tsagaita

dariyar sannan ta fara magana "Bari ke dai Sala,

yau wani shege na hadu dashi zai nuna mini

zara bai san na fishi ba....." Ta kwashe duk

abinda ya faru ta sanarwa da Sala din, gami da

karasa zancen da cewar "Shegen kinga ashirin

din dana warto, gobe ma ya kuma."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Sala ta kuma fashewa da dariya tana fadin

"Lallai kinyi maganin dan iska shege, banda

iskanci akan naira biyu sai ya warce miki

dankwali? Da ba'a cin arziki ai da bai sami

kwandastan ba tunda nasan ba motarsa bace,

amman maganinsa kenan kinga ai gobe ya

kuma. Maza tashi ki shiga wanka kada lokaci ya

kure Abulata mai kan alheri, ba irinsu O'o ba

mai kan kwantai Wato tana nufin Karima kanwar

Abun, domin dai ita bata da hali irin na Abun

dan tana jin irin nasihar da Yayansu yake mata,

dan haka ma basa shiri da Sala sam. Ta mike

har lokacin tana haki da dariya ta shiga

bandakin, kwandan wankanta daban ne, dan ita

sabulunta dankwali ne kamar yanda take cewa

giv da dai sauransu, ba irin nasu Karimaba dan

yanka. Bayan ta fito daga wanka aka kuma

zauna zaman kwalliya, Jagira kam da aka jata

har saida ta tabo kunne, ga kuma dige-dige da

aka yi a fuskar ko ina, leben nan kuwa yasha

baki sama da kasa, sannan aka cokala daurin

dan kwali ture kaga tsiya aka fito. Sala nayi

mata kirari ta nada gammo ta dora a kai, akayi

digir-gire da fanteka wacce ke dauke da wake

da shinkafa da robobi a gefe da mai da yaji duk

a kai, sai hannunta data dauki wani bokiti

wanda dashi take wanke kwanukan da sukayi

datti, aka fice babu addu'a sai da kirarinta data

bita dashi, sai da ta fice daga soron sannan Sala

ta bita da sauri ta leka duk rabin jikinta a waje

ta kwala mata kira ta juyo tana guna-guni. Sala

tace "Yi hakuri Abule na dawo dake, na manta

ban tina miki maganar makarantar allo ba kada

jarababben yayanki yaga ba kije ba ya hadani

da malam, wanda yake jin kamar ya jefani a

wuta dan dai nafi karfinsa ne kawai. Don ba dan

jarabar su ba daga bokon har allon daina zuwa

zaki yi tunda dai kin sami na sallah." Ita dai Abu

batace komai ba ta juya ta tafi tana kun-kuni

tana fadin "Kawai daman akan wannan maganar

kika dawo dani, wallahi da na san a kanta ne da

ba zan dawo ba." Sala din kuwa tace "Mai kan

arziki a kukkunga kada a dawo da ko kwalli

daya, na san ki, ai ba kya kwantai." To kawai

tace sannan ta wuce. Kai tsaye tasha ta wuce

tashar kofar Wambai, tana isa kwastomominta

suka yi mata caaa, domin akwaita da araha ga

sakin fuska da tsafta, idan kana so takai maka

har shagonka zata kai maka

Tun karfe hudu saura minti goma abincin nata

ya kare amman sai ta tsaya hira da samari da

wasan jakai da kawayenta 'yan talla. Can ta

hango Rodimasta, wani da take bi kudi tuntini,

ai sai ta cire gyalanta tace dammara dashi tana

fadin "Yau Allah ya kama tsinannan can, wallahi

idan bai bani kudina ba sai nayi masa rashin

mutunci wallahi, dan yau sai anyi bala'i a cikin

tashar nan wallahi." Laraba kawarta ta riketa

tana fadin "Haba Abu yawa ne, ki kyale shi

kawai kin san halinsa dan akuya ne..." Ta fincike

tana fadin "Dalla malama sakeni ai ya san

wadanda yake yiwa akuyancin nasa, ni idan ya

kawo raini ai sai inci (ta kunduma zagi)." Ta isa

gabansa yana shan tabar wiwi sai wani lumshe

ido yake yana rere wakoki kala-kala na gambara

zuwa wakokin 'yan dambe da na barayi, kai

gasu nan dai barkatai. Abu ta rike kugu tana

wani karkada kafa tace "Kai barawo bani kudina,

rannan na zuba maka abinci ka gudu baka bani

kudina ba, to yau Allah ya kama ka, ko ka bani

kudina ko nayi maka rashin mutunci wallahi. Ya

dubeta yana murmushin mugunta yace "Banza

ke wallahi karamar arniya ce, har kin isa kiyi

mini wata barazana, to na cinye na karfi ne ki

kwata." Ta tafa hannu tana fadin "Kan Ubancan,

lallai yau ka tabo ma kanka, yau zan nuna maka

kai karamin dan iska ne, dan ko sama da kasa

zata hade sai ka bani kudina." Ta kama kwalar

rigarsa ta cukwikwiye tana cigaba da bala'i. Shi

kuwa sai dariya yake yana fadin "Yarinya kece

mai aikin yi, in dai nine wallahi mu kwana a

haka." Ya cigaba da zukar wiwinsa yana lumshe

idanu. Jama'a sukayo gurin suna bada hakuri,

Abu tace wallahi ba zata cikashi ba sai ya bata

kudinta idan kuwa ba haka ba zata dauko masa

folis ita kam Laraba da yake matsoraciya ce sai

hakuri take baiwa Abun. Maimakon ta hakura

sai ta doka mata tsawa tana fadin "Dalla can

malama gafara daga nan, Uwarsa ta kauye ce

take bani jari ko ubansa na karkar....." "Ke Abu

don kazanki ni kike zagi?" Rodimasta ya katseta

a hasale dan ya fara kufula da rashin mutuncin

da take masa. Babu tsoro balle fargaba tace "An

zageka din, kai wanene da ba za'a zageka ba

eye?" Ya kuma hasala da zafin rai yake fadin "Ke

wallahi idan baki sakeni ba zan tattakaki a gurin

nan na farfasa miki jiki." Tayi shewa "Ahayye!

wallahi Bismillah dan halak ka fasa, don ka sani

duk mari daya a folissitashan naira dari yake,

don wata kila sai an hada da gonar kauye

sannan za'a biya kudin marin....." "Ke Abu dan

Allah kiyi hakuri ki sake shi, wannan ai ba

mutuncin ki bane kina mace kina fada da

maza."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta kalli mai maganar tana fadin "Kaga Baba mai

taba ina ginin mutuncinka dan kana biyana

kudina ba irin wannan dan bashin ba, dan haka

kawai ka bar gurin nan sai ya biyani kudina zan

sakeshi." "Kinga ya isa sakeshi nawa ne kudin

naki na biya, tunda shima ya rantse ba zai biya

ba dan idan rigimar tayi zafi har mu zaku jawo

wa tunda dai haka 'yan sandan can ke so a fara

fada suzo kame." Ta murguda baki tana fadin

"Ai wallahi nima ba zan sakeshi ba sai dai idan

ka biyani, naira biyar ne dan haka sai ka biya."

Ya dauko naira biyar a aljihun gaba rigarsa yace

"Gata shike nan rigimar ta kare ko?" Ta saki

rigar Rodimasta tana fadin "Banza matsolo

matsiyaci, yau Allah ya rufa maka asiri da yau

kaga karshen rashin mutunci." "Ke! Ya isheki

tunda dai an biyaki kudinki 'yar matsiyata, dan

wallahi kika zageni sai na tattakaki." Ya fadi

yana nunata da yatsansa. Ta tsaya ta rike kugu

tana wani girgiza tana fadin "Wanda bai fasa ba

baya kaunar uwale da ubale..." Laraba ta

janyeta tana fisfisgewa da kyar aka samu ta

kama hada kayanta tana cigaba da bala'i ta bar

tashar. Tana isa gida ta dire fantekat kayan ta

mikawa Sala kudin wacce ke washe baki, ta fada

daki ta kwanta. Sala taji shiru ta leka dakin ta

ganta a kwance ta bude baki da mamaki tace

"Au Abula kwantawa kika yi? Ke da zaki je

makarantar allo? kada jarababban yayanki yazo

ya ishemu da mita." Ta mike gami da daukar

allo ta fice tana kun-kuni. Miskili kafi mahaukaci

ban haushi, Sala ta fada tana dariya. ta dora da

cewar "Abula diyar Salamatu wani lokaci idan

kina shan kunu ko miskilancin naki ya motsa sai

na ganki kamar wata diyar wani sarki, sai da

lallashi Abula ta." Bata dai ce komai ba ta

ficewarta.

Makarantar dake kusa da gidansu, dan

tsakaninsu gida uku ne, koda taje dinma hira ta

kamayi da kawayenta sai da malam din ya doka

musu tsawa sannan suka rude da hayaniya wai

su nan dole karatu sukeyi. Da ya kirawo ta ta

biya allonta kuwa inda-inda ta kama yi, nan fa

ya hauta da fada, tayi kum da baki kamar ba

Abula diyar Sala ba, dan idan akwai wanda take

tsoro da shayi a duniya bai wuce malam da

yayanta ba, dan malam din bai mata ta dadiba

tun tana 'yar mitsitsiyarta kuwa, gashi babu

yanda zasuyi dashi dan shine kamar matsayin

kakanta na gurin Uba, ya kuma maimaita mata

ta karanta kuwa tsaf. Domin dai duk iskancin da

takeyi tana sane don da ace tana maida hankali

akan karatu da mai kokarice ita dan

kwakwalwarta akwaita da saurin rike abu, sai

dai shiririta da wasa da ta sanya a ranta, dan

yanzu data koma gida zata fita yawo da wasa

dan da kyar gobe zata iya biya yanda ya biya

mata, rudewar da akayi da karatun tashi ne ya

kwace ta. Ana cewa fatiha kowa ya mike yara

suna ta waka suna fadin "Tashiiii." Su Abu da

zugar kawayenta kuwa tsayawa akayi ana maida

yanda aka yi, dan wai wata Lantana tayi

gulmarta, wai yau zasu dirji bakin Lantana da

rubabben kwai. Ai kuwa suka saka ihu aka

sanya Lantana tsakiya tana kuka, sai waccan

tace nima kince mini kaza kince mini kaza, sai ta

tabe baki tana fadin, "Laaa! Ni din?" Sai kuma ta

sanya kuka, Laraba ce ta kuma tunzura fadan

da tace "Eh, nima rannan kince mini wai Abu

tana zuwa gurin Dan Oga mai kyamis, Kutumar

uban can, lallai yarinya a gulmar taki har da ni?

dan ubanki?" Abu ta shiga masifa tamkar zata ci

babu, taci dammara da gyalanta tana cigaba da

girgiza gami da ambaton sunan iyayanta tana

kunduma musu zagi gami da dungure mata kai

da lakuce mata hanci, yara sai ihu suke yiwa

Lantana wacce banda kuka babu abinda take yi.

Malamin sune ya farga da abinda ke faruwa

yayi kansu da dorina, ya samu daya ya caula

mata ta gantsare gami da fasa ihu, abinda ya

ankarar dasu kowa ya bazama da gudu dan

gujewa bulalar malam, wannan ne ya ceci

Lantana daga fasa mata baki da akayi niyya da

rubabben kwai. Ana idar da sallah Abu ta fito

daga gida tana rera wakar kiran wasa don tunda

ta taso itace ke kiran 'yan wasa don ita ce boss

din, don haka ko yara ne ba'a gani ba gidansu

ake zuwa nemansu Sala tayi ta bala'i. Ta fara

rera wakar wasa kamar haka: "'Yan wasa ku

futo wasa, idan baku zo ba ubanku yazo, bani

na fada ba bature ne, baturen ma na kasar

borno. 'Yan wasa ku fito wasa." Ai kuwa sai sai

ga yara suna fitowa daga gidajensu da gudunsu

maza da mata.Yayanta Sadiku dake shagonsa

yana jinta, ji yake tamkar yaje ya shaketa, sai

dai yana gudun jarabar Sala ne, don shi a

zatonshi tun da ya samar mata makarantar

gaba da firamare zata daina wannan wasan

haukan, amman sai yaga babu abinda ta daina,

dan haka yayi niyyar hanata da tsiya amman

Sala tayi tsalle ta dire tace Wallahi bai isa ba ya

kyale mata yarinya ta wataya.

"Aljana a kwaba ba tsari, aljana a kwaba ba

tsari....." Wannan wakar ce ta katse masa

tunanin da yakeyi, ya mike ya leko da sauri don

yasan wa suke tsokana. Ai kuwa yana hango su

sunyi zuga suna biye da wata karuwa da taci

kwalliya da wani matsats-tsan siket kanta babu

dankwali balle mayafi, tana tafe da kyar da

sauri tamkar siket din zai yage, kanta tamkar

tozon rakumi ga takalmi sakadale tumeme da

kafarta, amman sunki saurara mata sai binta

suke suna mata wakar da ihu gami da bula

mata kasa. Can wasu dattawa wadanda ke

zaune suma suna zabga uban musu, dan sunan

majalisar tasu ma majalisar 'yan musu, suka yo

kansu sanda suka ankara da duka.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Nan fa suka runtuma da gudu suna dariya, sai

da sukayi nisa sannan suka zube a kofar wani

gida sunata dariya. Can Abu tace "Laaa! Ku tsaya

kuji wallahi yau mu kai sumame gidan shegun

can Karuwai mun dade wallahi bamu je ba ko?"

Yaran suka amsa da "Eh! Wallahi mu badawa

shegu tiyagas din toka." Abu tace "To kowa ya

tsaya bari naje gida na samo toka da citta a

gurin Sala." Ai kuwa cikin kankanin lokaci suka

hada citta da barkono dakakku da kuma toka

cikin ledoji suka kulle da dutse a tsakiya suka

nufi gidan karuwai ta bayan layi don kada a

gansu. Sun yi sa'a kuwa da yawan karuwan

suna daki suna hira da lalatattun maza 'yan

uwansu, wasu kuma ma suna caca da masu

aikata babbar alfasha. Suka shiga cikin gidan da

sanda kamar wasu barayi, har tsakar gidan suka

isa, cikin daga murya Abu ta bada umurni, "A

fasa! A fasa!!.Ai kuwa ji kake tush-tush-tush,

nan da nan karuwai suka kama ihu da atishawa,

na daki suka yo waje da gudunsu wasu daga su

sai siket, wasu kuma sai zani, harda masu dan

kamfai. Su Abu suka fasa ihu suna dariya gami

da ficewa da gudu daga gidan dan kada a

kamasu, sai da suka isa wani kofar gidan can

nesa da gidan karuwan suka zube suna dariya,

suna hango yanda suke ta atishawa.

Hantsi ya dubi ludayi sanda Abu ta dawo daga

tallar waina. gashi anyi sa'a ranar babu

makarantar boko, dan haka ta zauna a tsakar

gida tana baiwa Sala labarin yanda sukayi da

karuwan jiya suna ta kwasar dariya, Sala kam

harda durkusawa tana rike ciki. Can suka jiyo

sallama, tun kafin sukai ga amsawa aka shigo,

mutane guda biyu da kayan 'yan sanda a jikinsu

riga da siket, sun daure kugunsu da bel. Sala ta

mike cike da mamaki tana tambayarsu "Yaya dai

bayin Allah lafiya ko? Don ganinki babu alheri."

Daya daga cikinsu ta fara magana "Hajiya munzo

mu tafi da 'yarki mara mutuncin can Abu,

domin dai ta addabi uban kowa a unguwar nan,

idan yaso idan munje folis sitashon kya ji abinda

ta yi." Abu ta mike da sauri tana tillika dariya

dan tasan kwanan zancen tana fadin "To muje

din mana, Sala kiyi zamanki yanzu zan dawo."

Sala tace "A'a ba zan iya bari ki tafi ke daya ba

muje." Ta dauko gyale akan igiya suka fice tana

fadawa Karimatu ta lura da abincin da ta dora

kafin ta dawo. 'Yan sandan suka fara kuluwa da

dariyar da Abu take musu, dan haka suka ce

wallahi idan bata daina ba zasu yi mata shegen

duka, ta gumtse baki tana yi a ciki don bawai

tsoronsu takeji ba, a haka suka isa har folis

sitashon din. Ganin karuwai sun jeru ne har da

'yan daudu ya sanya ta kuma tabbatar da

zargin da takeyi, kamar ta fashe da dariya

amman dan tana gudun sharrin 'yan sanda ya

sanya ta gumtse bakinta. Ta isa gindin kanta

inda wani dan sanda yake zaune da gashi buya-

buya a bakinsa wai shi nan sajan ne. Yana wani

muzurai ya dubi Abu yace "Ke mai ya sanya kika

je gidan wadancan masu zaman kansu kuka

barbada musu toka hade da yaji?" Abu tayi

shiru taki cewa komai, ya kuma maimaita mata

maganar amman taki tankawa. Wani kurtun dan

sanda dake tsaye ya daga kulki ya maka mata a

gadon baya, ta gantsare gami da fasa ihu tana

sosa gurin tana fadi "Wayyo Allah na na shiga

uku, wallahi idan ka karya mini kashin gadon

baya na bazan yadda ba." Ya kuma dagawa zai

maka mata amman mai mukamin sajan din ya

hanashi domin idan da sabo sun saba da halin

Abu, sannan ya maida dubansa gurin Abu ya

daka mata tsawa ya kuma maimaita tambayar

da yayi mata da gargadin idan ta kuma yin

shirun zasu saba mata. Ta murguda baki gami

da kallon sa kyar da idonta babu alaman shakka

ko tsoro tace "Wallahi ko zaku kasheni ba zan yi

magana ba sai dai muje gaban (D.P.O)." Sala

tace "Abu kiyi magana kada su tsamama miki

jikinki." Ta kuma hasala tace "Sala kiyi shiru,

haka kawai sai su kama dukana bayan basu

kama ni da laifin komai ba? Ai nasan 'yancina

dan haka ba zanyi magana ba sai dai muje

gaba." Ran 'yan sandan ya kuma baci suka yi

mata caa tamkar zasu cinyeta amman ko gezau

batayi ba, ana cikin haka sai ga (D.P.O) din ya

shigo,

Da mamaki ya dubi Abu yace "A'a, Abu lafiya na

ganki a nan?" Ai kamar jira take ya shigo sai ta

fasa kuka kamar wacce aka yiwa dan banzan

duka, amman fa idon nan nata babu alamar

hawaye ko digo sai dai burarin kawai da takeyi

tana rike bayanta . (D.P.O) din yace su shigo

daga cikin Ofishinsa su duka, Dan daudun dake

tare da Karuwan ya rike haba yana fadin "Oh!

Ni Hajiya Ladi yau na gamu da shegiyar yarinya

mai sharri, wallahi ko kwallaba nan ta ganki ta

kyale, ai wallahi ko mutuwa zakiyi ba kuka ba

sai kinci ubanki." Ya karasa maganar yana tafa

hannu da cinya. "Kai! keep quit kayi mana

shiru." Wani kofur ya doka masa tsawa. Yayi fari

da ido gami da fadin "Lalala! Ka manta wallah

Hajiya Ladi nake ba kai ba." Da haka suka shiga

ofishin D.P.O din. Mai tuhumar Abu Sajen

Barewa ya karantawa D.P.O tuhumar da ake

yiwa Abu, da kuma abinda ya faru. Ya dubi Abu

yace "Kina jin zargin da ake miki? haka ne ko ba

haka na ne?" Ta lankwashe murya cikin ladabi

tamkar mutuniyar arziki tace, "Yallabai karya

suke mini, ni jiya da daddare ma ina gurin

tallan gyada ta, har kazo wucewa kace na kai

maka gwangwani goma a majalisarku ko?" Ya

dubi karuwan yace "To ku kunji abinda wacce

ake tuhuma tace, ko kuna da wata hujjar da

zata nuna mana itace din ta bada muku toka?"

Hajiya Ladi ya tafa hannu yana fadin "La'ilaha

illallahu, Allah na yarda yarinyar nan shegiya ce

kwalba." "La-la-la ka zage ni?" Abu ta fadi ta

dora da cewar "Yallabai kana ji yana zagina a

gabanka hakama acan waje yayi ta zagina."

D.P.O ya doka masa tsawa yana fadin "Kada ka

kuma zaginta." Ya rike haba yana fadin "O! Ni

Hajiya Ladi na shiga uku, tuba nake Yallabai ayi

hakuri na daina zagin, amman kwaran-kwatsa

dubu jiya ina suyar doya na shiga bandaki dan

na rage marata, na jiyo hayaniyar su Abu, kafin

na farga har na fara tari da atishawa a cikin

bandaki da kokarin shidewa har zani na yana

faduwa, da kyar 'yar fisuwa ta kamoni ina

kokarin bankawa cikin masai. Ko ba haka ba

'yar fisuwa?" Ya kalli wata karuwa da taci uban

bilicin, kan nan tamkar tozon rakumi daga ita sai

gajeren wanda iyakacin gwiwa da riga tishet.

Tana tsaye rike da kugu tace "Haka ne yallabai,

tabbas yarinyar nan ce ta gayyato mana yara

suka watsa mana toka mai yaji, dan da muryar

ta ma muka gane ita ce" "Karya kike yi bani

bace, daga jin murya sai kice ni ce? Idan kuma

kin yarda ki rantse da Allah ko a kawo Qur'ani

ki dafa." Abu ta katse ta. D.P.O ya ce "Kunga

tunda dai abun nan baku da shaida zargi ne

kawai kuke yi, dan haka ki basu hakuri ke Abu,

idan yaso a gaba sai kuyi kokarin kama koma su

waye ke muku haka."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ya dubi Sala ya cigaba da magana "Ke kuma kije

ki baiwa sajan din da ya karbi laifin kudin shan

ruwa, na kashe case din kowa ya fita." Sam ba

haka karuwan nan suka so ba, amman tunda

dai basu da cikakkiyar shaida dole suka hakura

suka fice, ita kuma Sala ta baiwa Sajan Barewa

Naira hamsin tace ya sha ruwa. A harabar caji

ofis din suka kuma cin karo da karuwan da

Hajiya Ladi suna mai da yanda aka yi.Abu ta

dubi Hajiya Ladi tana dariyar keta har da gwalo,

Hajiya Ladi ya dalla mata harara yana nuna ta

da yatsa alamun kashedi, ta kuma sanya dariya

gami da sanya hannu a wuyanta ta ja shi alamar

yanka, sannan ta nuna Hajiya Ladi. Hajiya Ladi

ya saka Salati "La'ilaha illallahu, ni zaki yanka?

Lallai yarinyar nan baki da mutunci, to gwara na

koma na fada su zama shaida tun bamu bar

gurin ba." Yana magana da karfi yana tafa

hannu da buga cinya, gaba daya hankalin

jama'ar dake gurin yayi kansu. Abu ta

marairaice tana fadin "Dan Allah jama'a wa yaji

sanda na yiwa mutumin nan magana balle har

nace zan yanka shi? to muje din mana a kwatar

mini hakkina tunda abin naka sharri ne, tunda

dai kowa yana ji anan bance da kai komai ba."

Sannan tabi bayan Hajiya Ladi da sauri dan su

koma ciki tare. Hajiya Ladi ya tsaya da sauri

sororo yana kallon Abu, domin dai lallai ya hadu

da wacce tafi shi sharri da iya iskanci. Da zolaya

Abu tace "Yaya ka tsaya mu tafi mana." Ya

dallawa Abu harara yana fadin "Kwalba uwar

sharri, kada ki kuma kirana da kai sunana Hajiya

Ladi, idan kuma jurinki iskanci zamu kuma

gauraya sai na nuna miki ke din baki isa komai

ba wallahi." Ya tafa hannu gami da bugawa a

cinya yana wani murguda baki da karkafa ido,

ya dora da cewar "Kun ga kuzo mu bar harabar

police station tun shegiyar yarinyar nan bata

haddasa mana ciwon zuciya ba, kunga tafiya ta."

Ya gyara daurin zanin dake bisa wandonsa gami

da dane hannu yana tafiya yana wani yanga,

suka rufa masa baya suna mai da yanda aka yi.

Abu ta kyal-kyale da dariya gami da nufar gida.

Sala tana biye da ita itama tana dariya da yi

mata kirari, "Abula tawa, kowa ya ja dake yaji

kunya. Mahassada kun sha kashi. Yarinya mai

tsada kalar manyan maza."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

KANO 11 GA WATAN 6, 1993.

Rayuwa mai sauyawa, sai dai ga Abu sauyi da

aka samu kalilan ne, domin dai cigaban nata bai

wuce na daina daukar abinci akanta,sai dai a

dorawa dan dako tana biye dashi ba, sai kuma

chalo da ta daina zuwa da dibar 'ya'yan jama'a

a tafi tsokanar fada duk ta daina. Sannan

kyawun ta da kirar da Allah yayi mata mai

daukar hankali sun fara bayyana. Sai kuma Abu

mafi girma da za'a idar bai wuce daina tallar

safe ba, saboda shugabar makarantarsu ta

budewa Abu wuta saboda jarabawa da aka yi ta

shiga aji biyu na sakandire amman sai ya

zamana Abu ce ta dauki na karshe a ajinsu,

sannan ko a jikinta (wai an mintsini kakkausa).

Abun ya konawa Hajiya Kubra rai, don haka ta

sanya aka tara mata duk wadanda suka zo na

karshe na kowanne aji, ta sanya su a gaba tayi

musu kaca-kaca, sannan tace lallai sai kowacce

tazo da mahaifinta domin tana son jin dalilin da

ya sanya basu mai da hankali akan karatun ba

har suka zo na karshe, dukkansu yaran jikinsu

sai kyarma yake yi kowacce a tsorace take

amman banda Abu dake ta murguda baki tana

magana kasa-kasa, sarai Hajiya Kubra ta ganta

amman sai ta rabu da ita da zummar idan

mahaifinta yazo za tayi mata hukunci a

gabanshi, haka nan suka tashi kowacce ta nufi

gidansu tun lokacin tashi baiyi ba. Abu tana

shiga gida babu ko Sallama bagazan-bagazan-

bagazan ta yadda jaka da hijabin tana fadin,

"Wallahi Sala ba zan kuma zuwa makarantar nan

ba, don na gaji da masifar shegiyar principal

dinmu, sai kace wata uwata haka kawai ta tsane

ni." Sala ta dubeta da kulawa tana tambayarta

"Mai tsada yaya akayi ne? Mai ya faru naga ko

lokacin tashi daga makarantar bai yi ba." Ta

tabe baki kana tace "Wai kawai dan munzo na

karshe shine ta sanyamu a gaba tanata

zaginmu, baki ga sauran ba jikinsu har rawa

yake yi, ni kuwa duk abinda tace sai na bata

amsa amman dai a hankali, kuma tama yi sa'a

dan 'yan arzikin a kaina da saina rama," "Kinyi

mini dai-dai, sai kuma aka yi yaya?" Sala ta

katse ta. "Wai kuma duk cin mutuncin da tayi

mana bai isheta ba wai lallai sai mun zo da

Babanmu, ni kuwa wallahi bata isa ba ai dai ba

karatun shiga Aljanna bane."

Sala ta amshe "Wannan tsabar rainin hankali

ne, haka kawai dan kunzo na karshe sai ace

wani sai kunzo da Babanku? To ai ba laifinku

bane sune basu iya koyarwa ba, ai zuwa

makarantar ba dole bane kiyi zamanki kin huta

da tashin safe ma." Wannan ne ya sanya Abu ta

share gindi tayi zamanta a gida har kusan sati

biyu bata je makaranta ba, sai rannan da Sadiku

ya shigo da hantsi wajen karfe goma, shima ya

dawo makaranta sai kuwa suka yi kicibis, yayi

kanta da masifa yana fadin mai ya hanata zuwa

makaranta. Ta zura dakin Sala da gudu dan duk

iskancin Abu tana tsoron Sadiku dan bai mata ta

dadi, dan babu wuya ya lakada ta. Sala ce ta

fito tana hargagi gami da sanar dashi yanda aka

yi. Ya kuma kulewa yace maza ta shirya ya

maida ta idan kuwa ba haka ba sai dai idan ta

daina fita ne wallahi sai ya karya mata kafar

talla. Sarai Sala ta san halinsa dan haka ta

lallaba Abu dake ta kunci ta fita suka nufi

makarantar. Sanda suka isa ofishin (principal)

shugabar makarantar ya dinga bata hakuri yace

Babansu ne baya gari shi ya sanya ba'a kawo ta

ba, shi kuma bai sani ba yana makaranta sai

yau da ya dawo ya taddata a gida. Da farko

Hajiya Kubra tace ba zata saurareshi ba sai dai

idan ya nuna mata katin shaidar cewar shi

dalibi ne I.D card, tayi mamaki sosai da taga

abinda yake karantawa (Law) amman kanwarsa

muguwar dakikiya. Ta bashi guri ya zauna

sannan ta sanar dashi irin mugayen dabi'un Abu

da kuma dakikancin ta. Yayi kwafa cike da

takaici yace "Babanmu yace a baki hakuri

sannan yace kafin na bar Ofis din na kiyi mata

bulala guda hamsin, kuma yace daga yau

kowane irin laifi tayi a daina korata gida tunda

ba fada takeyi ba dan bata son karatun, a dinga

bata horo mai tsanani kowanne iri ne." "Karya

kake yi wallahi, yaushe har kaga Baban mu daya

fada maka haka?" Ta katse masa magana da

rashin kunya da hargowa. Mamaki da takaici ya

kama Hajiya Kubra, wato bata bar na gida ba

balle na waje ma. Shi kuwa Sadiku saboda

tsabar takaici kasa magana ma yayi, sai dai yaga

wata bulala a kan teburin Hajiya Kubra dan haka

ya dauko ya hau zabga mata, tun tana ihu da

makaleshi har ta gaza bakin nan nata sai da ya

mutu, gashi babu Sala mai kwatarta ita kuwa

Hajiya Kubra dama a cike take da ita dan haka

ko uffan bata ce ba, daman duniya idan akwai

abinda take tsoro bai wuce dukan Sadiku da na

Malam ba, domin basa mata na wasa, gashi

sune kadai zasu daketa a duniya su daki banza

dan babu abinda Sala zata iyayi, sai dai tayi

hargaginta ta gama dan ba zata iya rama mata

ba, su kuma bata isa ta dauko musu 'yan sanda

ba kamar yanda ta saba.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Yawan dukan da yayi mata ne ya sanya ran

Hajiya Kubra yayi haske, ta tabbatar lallai akwai

mai kwabar Abu jine kawai da bata yi. Bayan ya

jibgeta ya gaji ya dubi Hajiya Kubra yace "Hajiya

ki bata fartanya tayi noma da kuma wankin

bandaki." Abu dake kwance tana kuka ta kuma

kurma ihi tana fadin "Wayyo Sala na shiga uku

kizo da kanki,A zuciye ya kuma kai mata duka a

bakinta wanda ya sanya ta yin shirun dole dan

sai da bakinta ya fashe, amman bata daina

harararsa da murguda baki ba. Haka ya tafi ya

barta saida tayi noman nan da wankin bandakin

dalibai wanda yayi kaca-kaca da kashi babu

kyan gani, dan saida ta daure hancinta da

dankwalinta sannan ta iya wankewa, shi dai

Sadiku yayi tafiyarsa, amman yasan yau bala'i

sai yasha ya more gurin Sala. Ai kuwa haka din

akayi domin dai data dawo gida taga idonta da

bakinta sun kumbura ta zabura da sauri tana

tambayar abinda ya faru. Abu ta zube a tsakar

gida ta dora hannu a kai tana zunduma ihu

kamar wacce akayi wa mutuwa ko kuma a

sannan ake dukan nata tana fadin "Wayyo Sala

na shiga uku, wallahi bazan taba yafewa Sadiku

ba ko kabarinsa zai dinga balbala da wuta..."

"Wai me ya faru? na san za'a rina daman, me

yayi miki?" Sala ta tambaya a rude. Ta kwashe

duk yanda akayi ta sanarwa da Sala tana ajiyar

zuciya dan babu alamar hawaye ko kwalli a

idonta. Habawa ran Sala idan yayi dubu ya baci,

ta dinga sirfa masifa tana fadin "Ai makarantar

ba dole bace da har za'a kama ki da wannan

dukan a fasa miki baki da hanci, tunda kin iya

daurin dankwali ai magana ta kare, ladan ya isa

haka. Shi kuwa dan Baba zaizo ya sameni

wallahi sai nayi mummunan saba masa, sai ya

yabawa aya zakinta."

Haka nan ta wuni tana mita kamar zata ci babu.

Shi kuwa Sadiku yana sane yaki dawowa gidan

da wuri sai da ya bari dare yayi ya lallaba kicin

dan ya dauki abincinsa, ai kuwa tayo waje

daman lambo tayi tace dawa Allah ya hadamu,

donma dai ya wuce duka ne da ranar sai yasha

duka a gurin Sala, shi kam ko kala baice ba da

yaga ba'a ajiye masa abincin ba ya juya ya fice.

Ta bishi har zaure tana fadin "Babu zuciyar

nema sai ta ci, ita dai wacce ka tsana din ce ke

nemo abinda kake ci kuma wallahi ko ruwa ba

zaka sha a gidan nan ba, idan kayi zuciya ka

siya, wanda na san ko sisi baka da shi baya ga

tarin takardu da bakar zuciya." Shi dai dakinsa

ya shige ya kwanta ranar haka ya kwana da

yunwa, ita kuwa saida ta kusa kwana tana mita.

Wannan shine sanadiyyar daya sanya dole aka

daina tallar safe, domin dai Sadiku yace duk

sanda tayi laifi a daina turata gida tayi noma da

wankin bandaki, abinda ta tsana a rayuwarta,

ya kuma rantse idan ta daina zuwa makarantar

sai ya ballata yaga da kan da kafar da zata yi

tallan, dole kanwar naki aka hakura da tallan

safe dan ta dinga zuwa da wuri. Da farko Sala

tace bata yadda ba amman ganin da rana ma

ana samun ciniki mai yawa kuma ita Abu tana

tsoron bala'in Sadiku ya sanya dole suka

hakura, sai dai su Karima suyi tallan safen kafin

su tafi makarantar, amman ita da yake ba irin

halinsu daya da Abu ba takanyi hanzari ta saida

ta tafi makaranta, domin ita halinsu kusan irin

na Sadiku ne shiya sanya basa shiri da Sala

sosai kullum tana mata fada da cewar mai kan

kwantai.

Misalin karfe biyu na rana ta fito daga gidansu

dan dakonta yana dauke da fantekar abinci da

kwanuka da miya a kansa, ita kuma tana rike da

farin bokitin roba mai haske an yanka salak da

tumatir da albasa, daya hannun kuma kaji ne

soyayyu cikin irin farin bokitin, anyi wanka an ci

kwalliya, zanin nan an daurashi kwauri a waje

anja jagira lebe yasha jambaki da baki, sai dai

anyi kilin an daina dige-dige da kwalli, hatta

takalmi dan madina dake kafarta yasha wanki

sai sheki yake yi, ana tafe dagwas-dagwas

kamar mai jin tausayin kasa, domin tun can

daman Abu akwai tsafta da kwalliya balle yanzu

da aka fara zama 'yan mata, gwalli da feleke ya

karu, duk cikin kawayenta tafi kowa iya tsara

kwalliya, daman gata ba baya ba gurin kyau.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

zandakata a nan,insha Allahu Zuwa yamma

zamu dora,domindai aikin Littafin yayi bisa,Wata

tangarda ce ta hanani farayimuku a

ana,nagode..




Zaharaddeen Shomar

Whatsapp  08168575100




Idan Zuciya Tagyaru 1-02

Posted by ANaM Dorayi on 05:26 AM, 28-Jan-16

Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU

_________________ Na

________Fauziyya D Sulaiman____

Mustafa dake zaune kofar gidansu bisa farar

kujera karkashin bishiyar Umbrella, yana

karatun jarida kamshin Abu ya bugi hancinsa ya

daga kansa da sauri yana dubanta, kusan sati

guda kenan yake ganinta tana wucewa irin

wannan lokacin, kwarai yarinyar ta kwanta masa

a ransa, da kuma dai alamun ba za'a sha

wahalar samun kanta ba, kullum yana son yi

mata magana amman ya rasa ta yanda zai fara,

yau dai dabara ta fado masa dan haka ya fara

kwala mata kira. "Ke! Ke mai abinci! Kawo." Ta

tsaya turus gami da waigowa tana dubansa,

domin bata saba saida abincinta cikin unguwa

ba sai ta dangana ga tashar kofar wambai,

amman sai taga yayi mata kwarjini ba zata iya

kin saida masa ba, domin dai abincinta sai

wanda taga dama take saidawa, don haka ta

hau kwalawa almajirin dake dauke da abincin

kira "Kai Mudi! Kawo abincin za'a siya. Babu

musu yayo ribas ya juyo, ya isa gaban Mustafa

wanda ke zaune akan farar kujera mai tambarin

kamfanin coca-cola ya tsaya kerere. Ta galla

masa harara tana fadin "Kai fa tamkar jaki kake

komai sai ance kayi zaka yi ko? To sauke kayan."

Sannan ta dubi Mustafa tace "Malam na nawa

za'a zuba maka?." Yayi wani mayaudarin

murmushi yana mata wani duba na yaudara da

kwarewa a harkar iya soyayyar 'yan zamani yace

"Haba 'yan mata babu ko gaisuwa?" Tabbas yayi

masifar yi mata kwarjini, hasalima tunda suka

hada ido taji wani abu ya bugi zuciyarta wanda

ya sanya ba zata iya yi masa musu ba ko rashin

kunya, shi kansa ya gano hakan a kwayar idonta

ya kuma san haka nan Allah yayi masa kwarjini

da farin jini ga kowa, domin dai da wani ne

cewa zatayi, ban iya ba ko kuma tace baka kai

matsayin da za'a gaidaka ba din ne, amman shi

sai ta tsinci kanta da ce masa "To ina wuni?"

Yayi dariya yace "Ko ke fa, lafiya kalau, yaya

sunanki ne, dan kallon farko naga kin mini dari

bisa dari."

Ta kosa da zancan nasa ta daure dai tace "Ka ga

sauri nake kada rana tayi mini, na nawa za'a

baka? Dan kada kaja nayi kwantai." Ya kuma

murmushinsa dake kashe mata jiki yace "Haba

dai, ai kyawawa basa kwantai, ko domin kyanki

ai a sayi abincinki." "Ka ga nifa zan wuce kana

bata mini lokaci, wallahi dan kaine kawai na

tsaya." Ta fada tana yamutsa fuska. Ya kanne

mata ido daya yace "Haba dai ke kya soma

tafiya ban san sunanki ba? domin dai zaman

nan naki ne, dan tun randa na fara ganinki

Allah ya dasa mini tsiron sonki a raina wanda

kullum yake kuma girma, dan haka nake zama

kawai naga wucewarki naji dadi. Ta dubeshi cikin

ido, yanayin kallon da yake mata ya kashe mata

jiki ta gaza masa komai, amman sai ta dubi

Mudi da ya baza kunnuwa kamar na zomo yana

sauraran abinda suke fada tace "Mudi dauki mu

tafi yana bata mana lokaci." Mudi ya yunkura zai

dauka amman sai Mustafa ya dakatar dashi

yana fadin "Kai ajiye, maza nemo 'yan uwanka

almajirai ka raba musu, kyaky-kyawa kamarki ai

kin wuce tallan shinkafa, ke fa gimbiya ce."

Yana maganar yana dubanta da wani kallo daya

bambanta da wanda samarinta kucaku ke mata.

Mamaki ya cikata amman sai ta gaza cewa

komai tayi shiru kawai tana dubansa. "Kaje

mana ka kira 'yan uwanka ka raba musu ka

baza kunnuwa ka saki baki sai kuda ke fadawa."

Yace da Mudi wanda ya saki kunne da hangame

baki yana dubansu. Mudi dai gani yake kamar

da wasa yakeyi, amman da yaji ya doka masa

tsawa ya kuma nanata masa ya sanya ya fara

kwalawa 'yan uwansa kira. "Alalan Alalan

almajiri, Alalan Alalan kazoo kaci, Alalan Alalan

Alalan kai ba tumatiri." Ai kuwa nan da nan

gurin ya cika da almajirai, yace "To maza abi

layi." Ya kalli Mustafa dake kallon su. Mustafa

yace "Ka rarraba musu mana." Ai kuwa nan da

nan ya fara zubawa almajirai kafin kace kwabo

sai fanteka da bokitin salad. Abu na tsaye rike

da kugu cike da mamaki tana kallonsa, lallai

wannan mutumin dan rikice ne, ko tambayarta

kudin abincin baiyi ba yasa aka raba, zata yi

maganinsa kuwa yau, don wallahi sai ta tsuga

masa kudi masu yawa. Ya dubi Mudi yace "To

maza a hada kayan a koma gida uwar dakin

naka zata taho yanzu." Sai da yaga Mudi yayi

nisa sannan ya dubeta na dan wani lokaci tana

tsaye rike da kugu da alamun mamaki da

shakka a fuskarta. "Adon gari tunanin me kike

yi? Har yanzu baki fadi mini sunanki ba." Ta

yamutsa fuska tace "Sunana Abu......" "A'a

babban suna Zainabu Abu mai tagwayen suna

kenan, gaskiya Zainab baki dace da kalar tallah

ba, dubeki fine baby ace kina daukar tallah? to

gaskiya ni dai daga yau na soke tallar nan." Ta

dubeshi a tsiwace tace "Ka ji mu da mutum sai

kace wani Ubana? ko kai ne zaka dinga biyana

kudin da nake samu eye?" Yace "Eh mana zan

dinga biya ko nawa ne, don gaskiya bana son

rana tana taba mini kyaky-kyawar fuskarki,

kyanki hutu Zainabu."

Ta tabe baki don zancen bai gamsar da ita ba,

don tasan bai san yawan kudin bane shiyasa

yake wani cika baki amman yanzu zata yi

maganin firiritarsa. Don haka tace "Ka ga ka cika

ni da surutu bayan baka biyani kudin abincina

ba." Yayi dariya yace "Haba Zainab, baki yarda

dani ba naga alama, ko don kin ganni da dan

wando jeans da shet? kin san mu 'yan boko

bamu san kaya masu nauyi, amman nawa ne

kudin? Kila idan na baki hankalinki yafi

kwanciya." Ta murguda baki wanda ya zame

mata kamar al'ada sannan tace "Dari uku da

ashirin da biyar ne, sai nama na naira talatin da

biyu...." "A'a Zainab, duka zaki hade mini?" Tayi

dan duru-duru don tasan zulake tayi duka

kayan nata basu wuce na dari biyu da tamanin

ba, don haka ta kasa hadewa ta fadi don bata

iya lissafi ba (bata da Maths tab akin yara), da

ya fahimci halin da ta shiga sai ya zura hannu a

aljihunsa ya debo 'yan murtala (Naira Ishirin)

har na dari hudu yace, "Ga dari hudu ma ni na

kara miki." Mamaki ya cikata matuka, hannunta

har rawa yake yi gurin karba don tana ganin

kamar zai maida yace ya fasa ne. Sai da taji

dumin kudin a hannunta sannan hankalinta ya

kwanta ta dube shi da mamaki tace "To nagode!

Zan tafi gida." Yace "A'a ai dole na yiwa gimbiya

rakiya ko don naga gidansu." A wannan karon

bata yi masa musu ba don yayi mata ba zata,

don haka suka nufi hanyar gidansu, a kofar gida

yayi mata sallama yace sai gobe tace Allah ya

kaimu. Ta shiga gida da gudunta Sala na zaune

tayi tsuru cike da shakkun labarin da Mudi ya

bata, gaskiya tafi zargin bari kawai suka yi yace

wani wai juye wani saurayi dan gaye yayi mata.

Abu na shigowa ta mike da zakuwa tace, "Ke

maza sanar dani menene ya faru?" Abu tayi

dariya gami da nuna mata kudin da saurayin ya

bata, ta fizge daga hannun Abu da azama ta

hau kirgawa, Abu kuwa sai dariya takeyi. Sala ta

kammala lissafawa ne ta dubi Abu cike da farin

ciki tace "Diyar arziki yau kuma wane mai arziki

kika hadu dashi? Kai wannan diya da kan arziki

kike, shi ya sanya aka tsangwameki a unguwar

nan, ki dubi yadda su Sarai da Sakina kawayenki

suke kwantai kullum sai sun dawo da ragowar

abinci, sai dai a cinye ko kuma akai dakalin 'yan

kwantai da daddare abincin naira biyu a karyar

dashi naira daya koma sis daya. Abu tace "Bari

ke dai Sala, ni tunda nake ma ban taba haduwa

da mutum mai ban mamaki irin wannan ba."

Sala tace, "Yaya ne sunansa?" Ta tabe baki tace

"Oho!!! Ni ko tambaya ma banyi ba." "Kiji

sokuwa, arziki yana kiranki kina masa kutufo, to

gobe ki tambayi sunansa kuma ki saki jikinki

dashi, kin san su irin wadannan basu son ki

dinga dari-dari da su, idan abin ma gaba

daya....." Abu tayi dariya gami da shigewa

dakinta. 鈥� Allah ya shirya.

Washegari ma haka ce ta faru, Mustafa yayi

mata juye ya rako ta gida, sai dai wannan karan

ya tsaya sun dan taba hira duk da ya lura

sokuwa ce sam bata waye ba, da kuma alama

girman jiki ne kawai da ita babu shekaru, sai dai

ko menene shi dai yaji ya gani yana kuma so a

haka.

Yau da gobe sabo da shakuwa ya shiga

tsakaninsu har ya zama an daina fita da abincin

ko ina sai dai a bawa almajirai a gida. Abu an

daina fitowa kamar yadda Mustafa yace bai son

kyaky-kyawar fuskarta ta baci da zafin rana don

haka tana gida kullum. Wani abu kuma da

Mustafa ya koya mata shine cin dadi, yanzu

abincin kala-kala take ci ba irin wanda take ci

ada can ba, ga kaya da yake kawo mata na

kwalliya da na sanyawa, sai ga Abu ta kuma

futowa fes da ita kuma yanzu da motar Babansa

ma yake zuwa zance gurinta ko ta Mamanshi

don haka cikin motar suke zancensu. Ta futo

daga wanka tana tsakar gida bisa tabarma da

kayan kwalliya a gabanta ana ta kwalliya da

hasken wutar nefa, dan Mustafa na gab da

zuwa, Sala ta zauna daga bayan ta tana kallonta

cike da murmushi tace, "Kai diyar nan wallahi

akwai ki da kwalliyar daukar ido, dubeki kamar

wata sarauniya. Ai ba don bamu gama cin kudin

ba da kin auri yaron nan don ya dace dake, ga

kyau ga kudi, sai dai na lura kamar dai iyayensa

ne masu kudin ba shi kansa ba ko?" Abu ta

tabe baki tace, "Oho! Ni ban sani ba, ke idan

banda abinki ma Sala yaushe na isa aure? Ni

yanzu ma sai nayi digiri, don Mustafa yace mace

idan tayi ilimi wai tafi kyau da tsada. Ni fa yanzu

Sala dan-na-sanin talla ma nake yi, ki dube ni ki

gani yanzu kamar wata diyar wani basarake."

Sala tayi shewa gami da rangada guda tace, "Kai

Allah nagode maka, ai abinda nake ta nusar

dake kenan tun da can, ki sami samarin da zasu

dinga kashe miki kudi mu huta da tallan, yanzu

ba gashi munyi kyau ba? Ga kudi suna shigowa,

wannan shegen yayan naki yana saka mana

ido." Ta ja tsaki, "Mtsw! Wallahi idan ya sake sai

nayi masa baki, wai har ni zai kalli idona yace

mini sai Allah ya tambaye ni duk abinda muke

aikatawa, wai don kina zance a mota, wai 'yan

unguwa sai zarginki sukeyi gashi kin daina talla

ma a ina kike samun kudi yanzu? Nace a gidan

ubansa. Sai fa da nayi masa wuta-wuta sannan

na samu ya fice daga gidan nan, kuma nayi

masa barazanar duk randa ya kuma shiga

shirginki sai na tsine masa, idan muka biye ta

tashi zamu rayu ne? Da yanzu mun mutu,

Mtsw!" Ta kuma jan tsaki. Abu ta hasala ta

murguda baki gami da tsiro shi gaba tace, "Ki

fita harkarsa kawai Sala, na lura talauci ne ke

damunsa, kuma wallahi yayi sa'a shi yayana ne

da wallahi 'yan sanda zan dauko masa." Sala

tace, "Ai bake ba ni kaina ba don gudun abin

kunya ba da saka ido irin na tsinannun mutanen

unguwar nan, da wallahi sai na hadashi da 'yan

sandan sun lallasa mini shi." Sallamar da wani

yaro yayi ce ta katse musu hirar tasu tamkar

wasu kawaye, su kuwa sauran kannan nata duk

sun bazama tallar gyada a can kofar gida. "Kai!!

Meye ka ishemu da sallama?" Sala ta katse shi

cike da haushin katse musu hirarsu da yayi ba

tare da ta kai aya ba don ko amsa sallamar ma

bata yi ba. "A'a daman wani ne a mota ke

sallama da Abu..."

"Au! Yi hakuri na hauka da fada, kace tana zuwa

dan albarka, ka ji?" (HMMM) Yaron ya fice yana

fadin to. Ta dubi Abu da ta mike ta nufi daki

don sanya kaya tana dariya tace, "Yau dai naga

kwalliyar nan ta daban ce, kiyi sauri kada ki

bata masa lokaci." Ita dai bata ce komai ba ta

shirya ta fito sai kamshi take yi, kai tsaye ta fice

ta nufi gurin da Mustafa yake, yana hango ta ya

bude mata gaban motarsa wato kusa dashi sai

wani malalacin murmushi yake mata na

tsananin yaudara irin na gogaggun samari, ita

kuwa sokuwar sai wani kara zobara baki takeyi

tana wani yauki har ta shiga ciki ta zauna tana

wani fari kamar 'yar tsana. Ya shaki kamshinta

gami da lumshe ido, cikin mayaudariyar

muryarsa yace, "Kai Zainabu, kin yi kyau kamar

wata sarauniya." Tayi dariya cike da jin dadi

tace, "Haka ma Sala tace wai nayi kyau sosai."

Yayi murmushin jin wautarta, Ya riga ya gama

karantar halin Abu da Sala, don haka ya san ba

zai sha wahala gurin samun hadin kan Abu ba,

don haka ya mika hannuwansa ya kamo hannun

Abu yana wasa dashi yace, "Kai yatsunki akwai

ban sha'awa, dube su zara-zara. Dadi ya kuma

cika ta na yabon da yake mata tace, "Haka kowa

ke cewa, wai yatsuna da na hannu da na kafa

suna da kyau kamar ba nawa ba." Yayi dariya

yace, "Gaskiya haka ne, amman kyanki ai yaci

suma suyi kyau." Cikin dabara ya jata jikinsa

yana fadin, "Ya dace dai yau na shaki kamshin

nan naki da kullum ke ruda ni." Ga mamakinsa

sai yaga Abu ta saki jikinta har ma tana kokarin

taya shi, abin ya bashi mamaki don yayi zaton

sai yasha wuya zai sami kanta, sai gashi ya

same ta a ruwan sanyi, amman sai ya danne ya

dinga aiwatar da mugun nufinsa da zuciyarsa ke

ingiza shi. (Allah ya kiyashe mu da aikin assha.

amin).

Da ya tabbatar ba zai sami wata matsala da Abu

ba, sai ya lankwashe murya yace, "Abu ko zaki

rakani wata 'yar unguwa?, daga can kin ga sai

mu wuce nayo miki siyayya ko?" Tace "Babu

damuwa muje kawai." Ya dubeta ta dan hasken

dake cikin motar na farin wata da ya shigo yace,

"Kina ganin babu matsala idan Sala ta aiko bata

ganki ba? dan kada tayi fada." Ta tabe baki tace,

"Kada ka damu ba zata ce komai ba tunda dai

ta san siyayya zaka yi mini, kuma ta san ai

muna tare." Yaji dadin abinda tace dan haka ya

tada motar gami da karo sautin wakar dake fita

a cikin rediyonsa, muryar Bob Marley ce a

wakarsa ta One Love, duk da Abu bata jin

turanci wakar tana mata dadi musamman da

yake koda yaushe za kaji kaset din Bob Marley

Mustafa ke sanyawa, har ma ta iya bin wakar

tana girgiza kai duk da ba daidai take fadin

wasu kalmomi ba. Suna tafe a hanya suna hira

har suka isa wani hotel, kasancewar kaurin

sunan da hotel din yayi baka ganin jama'ar kirki

a cikinsa domin kada sunansu ya baci, wannan

ya kara baiwa 'yan iska damar cin karensu babu

babbaka, gurin shiru babu alamun jama'a, sai

ka shiga daga ciki zaka ga kamar tsakiyar rana

ce dan haske da tashin kida. Ya dubi Abu yana

murmushi yace, "Zainabu ya dace mu dan tsaya

a nan musha lemo mu huta, kafin na wuce yi

miki siyayyar domin har dan kunne da sarka na

gwal zan sai miki, kema ki shiga sahun manyan

mata ko?" Yana mayaudarin kallonsa yake

maganar. Tayi dariya cike da jin dadi tace "Babu

damuwa." Ya sami guri ya faka motar tasa, ya

bude ya fito sannan ya bude mata ta fito suka

jera, Abu jin kanta take yi da girma saboda ta

fito daga mota, a ganinta ta gama cinyewa.

Sanda suka isa cikin reception din hotel din sai

ta kama zare idanu cike da kauyanci, domin

tunda take bata taba ganin guri mai kyawun

wannan ba, ta saki baki galala tana kallo ga

hasken wuta ga fankoki suna juyawa ga A.C da

Tibi, ga 'yan mata nan kala-kala kowacce da

shiga ta rashin mutunci, sai taji ta raina kanta,

lallai ta yadda da Mustafa da yace zai nuna

mata rayuwar 'yanci da wayewa, gashi kuwa ta

fara gani. Sai ta kama muzurai kamar ta koma

gida ta sanyo atamfarta Wagambari da tafi

kowacce kyau da tsada, amman sai taga ai ko ta

sako ba zata yi kyawun wadannan ba, ta

shagala da kallonsu tana fadin dama itace

wannan, can kuma idan taga wata sai taji tafi

waccan tace, kai waccan zan zama, shi kuwa

yana can yana biyan kudin dakin da zai kama

musu. Ya kammala ya amshi makulli ya nufe ta,

sai yaga sam hankalinta baya tare da ita har

hannu take sanyawa tana taba duk abinda ya

burgeta, ya kama hannunta suka nufi dakin da

ya kama musu. Sanda suka shiga dakin kuwa sai

labari ya sha bamban, sai taga ai can wajen ma

ba'a sanya komai na more rayuwa kamar nan

ba, ta fada kan tumemiyar kujerar dake falo da

karfi tana fadin, "Kai bari muga za ta loma

kuwa?" Ta saka wata dariya ganin ko motsi

sosan baiyi ba, can idon ta ya hango mata wani

gilas dake dauke da ruwa da kifaye da wasu

'yan kananan bishiyoyi, ta mike da sauri ta isa

gurin, ta saki baki tana kallo da shafawa, can ta

kuma fashewa da dariya tana fadin "Wallahi

kifin da ransu kuma yawo suke kamar a teku."

Shi kam Mustafa yayi tsaye yana dubanta,

hannuwansa cikin aljihu yana dariya saboda

ganin irin kauyancin da take yi, lallai ya kuma

tabbatarwa Abu sokuwa ce mara wayo, sai dai

rashin kunyar, domin da ace tana da wayo ba

zata yi wannan kauyancin ba, ko kuma dan bata

da wasu shekaru da yawa ne? Can ya hango ta

tana kiciniyar bude wata kofa sai turawa take

iyakacin karfinta.

Ya karasa yana dariya yace "Dakin bacci ne, bari

kiga yanda ake budewa." Ya kama marikin kofar

ya murda a hankali sai gashi ta bude. Ta kuma

bude baki cike da mamakin ganin wani irin

katon gado kuma dan karami ba irin na Sala mai

rumfa ba, ta nufi gadon da gudu tayi tsalle ta

fada tana kyalkyala dariya har da rike ciki tana

kuma birgima. Can kamar wacce aka kuma

tsikara sai ta kuma mikewa da sauri saboda

hango wata kofa da tayi ta san lallai wani abin

kallon zata kuma gani, wannan karon bata sha

wahala ba ta bude domin taga yanda ya bude

waccan, ta rufe bakinta cike da tsananin

mamaki taca cewa "Na shiga Uku ni Abula,

menene wannan kuma?" A cikin kunnenta taji

yana mata rada, "Wannan bandaki ne gurin

wanka irin na 'yan gayu, idan kina son irinsa zan

gina mana." Ta juya tana dubansa da mamaki

dan bata yarda da abinda yace ba, yaya ma

za'a yi aga bandaki a cikin daki kuma ga wasu

irin abubuwa a ciki kamar daki ma? Ya daga

mata kai alamar haka ne da gaske, ta nufi gurin

kwamin wanka ta shiga sai ya sakar mata

shawa, ta firgita ta fito da gudu tana ihu,ta

kankame shi domin ta firgita, ya fashe da

dariya. Lallai Unguwarsu da manyan gidaje

amman bata taba shiga ciki taga yanda suke ba,

domin ita kam bata iya jure wulakanci ko kaka

yake, su kuwa 'ya'yan masu kudin unguwarsu

wulakanci ne dasu, sam basu kula su ko fita

zasu yi ma sai dai a mota, shi kansa Mustafa

sanda ya fara cewa yana sonta tayi mamaki

sosai, sai daya dinga yi mata kalamai masu dadi

da yaudara sannan ta yarda, har yana cewa

shifa so babu ruwansa da mai kudi da talaka

duk yana shigarsa, da haka ya samu kanta dan

wani lokacin har mamakin kanta take yi data

afka son wanda ta tsana a da can. Tasha yiwa

motocin jama'a faci domin ta tsani gudun da

sukeyi a layin suna kade kaji da akuyoyi wani

lokaci harda mutane, idan anyi magana sai su

biya dan suna da kudi, sai da takai duk kofar

gidan da aka ganta sai an koreta domin idan ta

kullawa mutum duk sanda taga mota a kofar

gidansa koda ta baki ce sai ta koma gida ta

dauka kibiya ta kitso ta sossoka a tayoyin, dan

masu gadin da sun ganta zasu bita da bulala. Ya

janye ta yana dariya saboda yanda ya ga ta

tsorata yace "Bari naje na samo mana abinci da

dan ruwan lemo." Bata ce masa komai ba illa

tafiya da tayi gurin wani abin tana tabawa. Ya

dawo dauke da wani katon faranti mai dauke da

abinci da manyan kwalabe na giya (wa iyazu

biLlahi) ya ajiye bisa tebur din dake falon kana

ya shiga ya kirawo ta, da kyar ya samu ta baro

bandakin tana cewa ya tsaya tana kallo, yace In

dai kina son kallon kullum zan dinga kawo ki."

Dadi ya cikata, da wannan dabarar ya samu ta

futo. Abinci ya mika mata mai dauke da naman

kaza zuku-zuku, ta amshe kuwa da azama ta

fara ci, shima yaja nasa farantin yana ci yana

kallon ta yana dariya ,Can ya dauko kwalbar

Shandy dinsa ya bulbula a kofi ya kafa kai ya

kyankyama ya dire kofin. Ta dubeshi da mamaki

a tsorace tace, "Kai Musty (haka take ce masa)

Giya ce fa? ba zata bugar da kai ba? Naga dan

tasha idan ya sha yayi ta maye har kwata yake

fadawa." Yayi murmushi gami da lumshe

idanuwansa kana ya bude a hankali, "Ai shi

karamar giya yake sha wato burkutu shi ya

sanya yake maye, amman wannan original ce

wato mai kyau din ce, bata sanya maye bari na

zuba miki ki sha kiji." Ta manne kafada da sauri

tana fadin "Kai bana sha tsoro nake ji ni dai."

Yace, "Haba dai tawan don Allah kisha wallahi

ba zaki bugu ba sai dai kiji karfi." Da kyar ya

samu ta sha kofi guda, can kuma sai ta wawuro

kwalbar ta kafa kai ta dinga kyankyama, ta dire

kwalbar bisa tebur din. Ya fashe da dariya gami

da tafa mata yana fadin Wonderful, wato

mamaki ta burge shi, ya zira hannu cikin

aljihunsa ya zaro tabar shedan wato wiwi) ya

kunna ta ya zuka kana ya mika mata, wannan

karon batayi gardama ba ta amshe da azama ta

zuka domin bata cikin hayyacinta, sai dai zuka

daya ta kware ta kama tari, ya tashi da sauri ya

nufe ta yana rike ta har tarin ya lafa.

Amman don ta saba maimakon ta hakura sai ta

kara zuka don abin ita sha'awa ma ya bata, don

ta dade tana sha'awar yanda ake shan taba

musamman idan taga wanda ya kware mai

fesar da hayaki ta baki ta hanci. Dadi ya kama

Musty sai ya kuma zaro wata cikin aljihunsa ya

kunna ta ya hau zuka. Ta fashe da dariya karan

tabar na tsakiyar yatsunta guda biyu shima ya

taya ta suka dinga dariyarsu da zukar tabar

shedan din har suka gama, sannan ne kuma

Abu ta soma tangadi tana zage-zage da yarfe

hannuwa. "Wallahi karya ne! Babu wani sauran

shege da zai raina mana hankali wallahi! Ha-ha-

ha." Ta fashe da dariya. Ya isa inda take da

azama yana fadin "Kwantar da hankalinki

yarinya." Ta fada jikinsa shabar tamkar kayan

wanki, ai kuwa ya sami yanda yake so don haka

ya shiga aiwatar da mugun nufin da zuciyarsa

ke kintsa masa, da fari bai samu matsala ba sai

da abu yayi nisa data fara jin zafi sannan ta

nemi kwace kanta, amman da yake a buge take

hakan bai samu ba har sai da ya cimma burinsa

a kanta (Wa'iyazu billahi). Duk irin iskancin Abu

da gantalinta namiji bai taba aike mata kai tsaye

ba don tana tsoro da gudun kar aji mata ciwo,

ko su Dan Oga da dan tasha da suke siyan

abincinta, basu taba samun hadin kanta haka

kai tsaye ba sai Musty, yau ya samu daga sama

don haka shine mutum na farko da ya fara

sanin Abu diya mace, abunda ba zata taba

mantawa ba a kundin tarihin rayuwarta. A nan

bacci ya dauke su don duk cikin su babu wanda

ke cikin hayyacinsa. Basu ankara ba sai da gari

ya waye tangararau, sannan suka farka a firgice

Abu ta saki kuka da ta tuno abinda ya faru a

daren jiya, shi kuwa Musty kwantar da kansa

yayi ya dinga bata hakuri harda guntun

hawayensa, karshe dai yayi mata alkawarin kaya

da zai sai mata kala-kala har ya samu ya shawo

kanta don ya lura muguwar kwadayayyiya ce, ya

samu ya lallaba ta ya hada mata ruwan dumi

cikin bahon da tayi kauyanci daran jiya ta shige

ciki. Shigar ta bandaki da kuma tuno irin

alkawarin kayan da yace zai siyo mata ne ya

faranta ranta har ma ta daina ganin aibun

abinda suka yi din, don haka da kwarin

gwiwarta ta fito shima ya shiga don ya shirya.

Sanda ta kammala shiryawa ne gabanta kuma

ya soma dafuwa tana tunanin me zata ce da

Sala yanzu don ta Babanta sam bata jinsa,

domin sam ba zai lura bata gidan ba, domin bai

shigowa gidan sai dare ya raba, haka nan daga

gurin Sallar Asuba yake wucewa majalisarsu,

idan ka ganshi a gida da rana to lallai Alhazan

da suke wa a dawo lafiya sun kawo musu zakka

zai zo yaci abincin rana a kudinsa, yakan ce sai

ya ci guminsa wai, sai kuma jarababban yayanta

da take tsoro kada ya gane bata kwana a gida

ba. Ya fito shima ya gama shiryawa, ya dubeta

sanda suke karya kumallo sai ya ga ranta har

lokacin a bace yake, gabansa ya shiga faduwa

domin shi yanzu ma yaji ya fara sonta, don

haka ya kwantar da murya ya kamo hannunta

yana fadi, "Wayyo masoyiya ta, mene ne? Har

yanzu fushin ne? Ko baki huce bane?" Yanda

yake maganar ya kashe mata jiki, ta dinga jin

soyayyarsa da kaunarsa suna ratsa jikinta, ga

wani shaukinsa, ta kwantar da kai tace, "Wallahi

na huce, ina dai tunanin yanda zan sanar da

Sala ne, don ka san ban taba kwana a waje ba."

Ras! Ras! Shima gaban sa ya fadi don sai yanzu

ya tuna ya fito da motar Mominsa gashi ya

kwana, me zai ce mata yanzu? Lallai yasan zai

sha fada a gida, amman sai ya dake domin dai

yanzu matsalar Abu ce a gabansa.

Ya kuma kwantar da murya yana wasa da

hannunta yace, "Kada ki damu za muje nayi

miki siyayya ta ban mamaki wacce zata faranta

ran Sala din, na san ba zata yi fada ba muddin

taga kayan, ga kuma kudi da zan baki, kada ki

damu kinji ko?" Tayi ajiyar zuciya gami da cewa,

"Shi kenan." Wani katon kantin sayar da kaya

suka je. Bayan sun shiga yace ta zabi duk

abinda take so. Lallai kam yaga hauka domin

dai haka ta dinga jidar kaya kala-kala tana

sanyawa cikin dan keken da suke turawa har sai

da taga babu gurin da zata sa ta hakura, dan

wani abun ma sam bata san amfaninsa ba take

dauka, in dai taga kwalin yayi mata kyau to an

gama, domin har abin aski na maza sai da ta

dauka, shi dai binta kawai yake yi da kallo cike

da mamaki, amman bai ce komai ba domin dai

lallaba ta yake yi kada yayi magana yayi laifi. Da

suka isa gurin biyan kudin aka lissafa aka gaya

musu, kudin tsababa ne amman shi ko a jikinshi

domin dai yasan ta cancanci ya sai mata abinda

yafi haka ma. Ita kuwa 'yar jidalin wani kallo

tayi wa mai karbar kudin tana fadin, "Kai malam

dan wannan kayan ne zaka tsugawa wannan

kudin wanda yafi na buhun shinkafa 'yar

gwamnati? Kawai kayi mana ragi idan ba haka

ba mu fasa saya wallahi." Ta karasa maganar

tana tafa hannu da doka cinya. Kunya ta kama

Mustafa dan dai ta nuna cikakkiyar 'yar kauye

ce ita wacce bata taba zuwa irin wannan wajen

ba. Ya dubi mai karbar kudin sanda yake ajiye

masa kudin yace, "Ka yi hakuri daga kauye aka

kawo ta." Cikin harshen turanci yayi maganar

dan haka sam bata ji abinda yace ba. Mai

karbar kudin yace "Babu damuwa." Tana kallo

ya biya kudin don ma kada tayi magana ya

kama hannunta suka fice yana fadin ma'aikatan

su biyo shi da kayan, kamar jira ake su fita sai

wadanda ke gurin suka kama dariya. Tana daga

can ta hango suna mata dariya dan haka ta

kutuntuma wani zagi tana fadin, "Lallai ma

wadancan mutanen 'yan rainin wayo ne, ni

sukewa dariya? Wallahi bari naje nayi

maganinsu." Ta nufi gurin nasu da sauri. Ya riko

hannunta yana fadin, "Haba Zainabu na kada ki

mai da kanki 'yar kauye mana, ki zama

wayayyiya." Tayi kwafa tana dubansa tana huci

tace, "Wallahi sunyi sa'a da yau sun gane

kurensu, ni kawai ka fasa siyan kayan ma ka

bani kudin kawai na rike abuna." Yayi murmushi

yace, "Don Allah kiyi hakuri in dai kudi ne zan

baki." Da haka ya lallaba ta suka saka kayan a

mota suka wuce gida. Bayan sun shiga motar ta

turo baki gaba tana fadin, "Gaskiya wadannan

mugaye ne, dan wannan kayan zasu ce kudinsu

kenan, wallahi zai sayi buhun shinkafa har da

na wake ma, kai zai iya kai mutun Makka da

Madina ma." Dariya ta kwace masa har yana

dukan sitiyari yace, "Kai Zainabu akwai ki da

wauta wallahi, koma dai nawa ne yawan kudin

ai kinfi karfinsu a gurina, fatana dai kawai ki

dinga bani hadin kai, zaki zama tauraruwar

mata gagara-gasa a cikin unguwarku, zaki zama

abin kwatance." Ranta yayi fari kal! Amma bata

ce komai ba har suka isa kofar gidansu ya

tsaida motar. Ta dubeshi bata ce komai ba

amman ya lura da fargaba take yi dan haka

yace, "Kin ga kada ki damu tsaya kiga dabarar

da zamu yi." Ya bude motar ya fito ya kirawo

wani yaro yace maza ya shiga da kayan cikin

gida zai bashi lada, nan da nan yaron ya fara

jidar kayan yana shiga dasu cikin gida, su kuwa

suka cigaba da hirarsu, har saida yaron ya gama

shiga da kayan ya sallame shi. Ya dube ta da

salon da yake kashe mata jiki yace, "Yaya dai

Zainabu ina fatan babu matsala." Bai jira ya ji

abinda zata ce ba ya zura hannu cikin aljihunsa

ya zaro wata sabuwar ambulan mai dauke da

sabbin murtala (N20) ya mika wa Abu yana

fadin, "Ga wannan kyautar faranta mini rai ce,

sai da daddare idan na dawo." Ta fizgi kudin da

sauri kamar wani ne zai kwace, ta bude murfin

motar babu ko sallama ta fada gidansu da

sauri. Ya girgiza kai cike da dariya sannan ya

tuka motarsa ya nufi gidansu amman gabansa

na faduwa dan bai ma san irin karyar da zai

shirya ba.

Abu ta fada gidan babu ko sallama kamar wacce

aka hankada, a tsakar gida ta tadda su Sala da

kannanta suna kallon kayan da aka shigo dasu,

fuskar Sala cike da annuri. Tana shigowa Sala ta

mike da azama ta rungume ta tana fadin "'Yar

albarka, jiya sam banyi bacci ba na dinga darura

da sake-sake ko 'yan yankan kai ne suka yi

gaba da ku, sai yanzu da naga ana shigowa da

kayan nan hankalina ya kwanta nace na san

dare ne yayi muku a inda kuka je kuka ki

dawowa saboda 'yan sa ido, ai gwara da kika

kwana a can din ma dan baki ga yadda

jarababban yayanki ya dinga sintiri ba, sai da

nace masa kina daki kina bacci sannan ya

hakura ya kwanta, shi ya sanya na dinga

fargaba kada ki dawo ki buga kofar yaji ya hau

surutu da wa'azin nashi tamkar dan sarkin

Limamin Makka." (Kuji fa irin wannan Uwa,

wacce ya dace a ce hankalinta ya tashi saboda

kwanan da diyarta tayi a waje amman ko a

jikinta saboda tsabar kwadayi da son duniya,

Allah dai ya shirya). Abu kam da taji abinda Sala

ta fadi sai taji hankalinta ya kwanta, don haka

ta share karya da ta shirya da zata fada, cewar

wai mota ce ta lalace musu a hanya da suka

dawo daga siyo wadannan kayan, sai da gari ya

waye sannan suka sami masu gyara. Sai kawai

ta dauko kudin da ya bata na ambulan tana

fadin "Sala har da kudi fa ya bani." Sala ta

amshe da sauri ta kama kiciniyar farke ambulan

din ta hau kirgawa, Naira dubu biyu cif! Nan fa

suka kama tsalle da murna Sala tana fadin, "Kai

wannan yaro dan arziki ne, dan haka Abu ki rike

shi da kyau, Ubangiji ya sanya ya gama da

duniya lafiya." Haka nan suka dinga murna,

ranar nan dai ko abincin sayarwa Sala bata dora

ba. ga Abu kuwa wannan daurin gindi da ta

samu daga gurin Sala shine ya kaita ga

fandarewar da duk wanda yake da hannu gurin

lalacewar tata sai yayi da-na-sani wata rana,

rana mara alkhairi a kansu gaba daya, da-na-

sani mara amfani. (ALLAH YA KIYASHE MU DA

SHARRIN SON ZUCIYA, WANDA BAHAUSHE YACE

鈥淏ACIN ZUCIYA鈥� Ameen)

KANO: 22|12|1993

Rayuwar Abu gaba daya ta sauya daga fari zuwa

baki, idonta ya kuma budewa da harkar banza,

domin wannan dan lokacin ta iya shan tabar

shaidan ta hanci ta baki, sannan kowane dare

kai wata rana ma har da rana Mustafa sai ya zo

ya dauketa sun tafi hotel sun sheke ayarsu.

Amman fa a wannan dan tsakanin sun sami

kudi mai dama a jikinsa, wanda duk iyakacin

shekarun da Abu tayi tana talla basu samu ba,

karatunta na boko kam sai dai muce sam barka,

domin Mustafa mai son ilmi ne dan shi ma dan

boko ne, dan ya kan sanar da ita irin yanda

mutum kan zama idan yayi karatu, yana zama

wani a duniya. Karatun allo kuwa tuni ta watsar,

Malam yayi hargagin a banza dan ba sai ya

ganta ba ma sannan zai doka ba. Sai dai kullum

tayi wanka taci kwalliya tana taku daidai a

unguwa, su Larai duk ta raina su yanzu idan

tayi kwalliya takan zagaya su tana musu yanga

idan sun dawo daga tallah. Baba Abubakar ma

sanda ya isa da fuffukarsa da Malam ya sanar

dashi halin da Abu ke ciki, ya shiga gidan da

fuffukarsa yana yiwa Sala korafi. "Yanzu Sala ba

zaki dinga tsawatarwa da yarinyar nan ba tana

neman ta jawo mana magana a unguwar nan,

kina kallonta....." "Kai Malam rufe min baki!"

Sala ta katse shi, ta dora da cewar "Kai har wani

namijin arziki ne da zaka zo kana mini wata

maganar banza, to tsaya kaji na gaya maka,

wallahi babu shegen da zai takura wa Abula a

garin nan, tun da dai ba Uban wani ya haifar

mini ita ba, kuma Uban wa muka je muka ce ya

taimaka mana da abinda zamu ci? Ko uban

waye ke ciyar damu? don haka babu wanda ya

isa yace mata 'yar iska na kyale shi. Shi kansa

Malam din da yake wannan fuffukar 'ya'yan

nasa ba karatun boko suke suna sheke ayarsu a

can ba? Har makarantar kwana sukayi fa, don ni

Allah ya bani yarinya mai kashin arziki za'a saka

mu a gaba? To wallahi ba'a isa ba, kuma daga

yau idan ka kuma zuwar mini da irin wannan

maganar sai ranka yayi mummunan baci, soko

sobarodo da baka yin maganin sisi, sai yau zaka

hau ni da fada." Duk da tsananin hakuri irin na

Baba Abbakar sai da ransa ya baci da tijarar

Sala yau, ya dubeta a hasale sanda ta diga aya

yana fadin "Au dan na gaya miki gaskiya shine

kike mini wannan tijarar? Wato dan kinga bani

da shi ko? Don da ina da shi baki isa kiyi mini

irin wannan rainin hankalin ba, dan haka ki

shiga taitayinki, idan ba haka ba ranki zai yi

mummunan baci wallahi Salamatu." "Ahayye

ayyururuuuiii!" Ta rangada guda da tafa hannu

sannan tace, "Lallai yau mazantakar za'a nuna

mini kenan ko? To tsaya kaji Abbakar, wallahi

baka isa ba, ka yi kadan, idan kuma kayi wasa a

cikin daren nan sai mu baiwa hammata iska." Ta

kama cin damara da wani zani dake yashe a

gefenta tana wani girgije-girgije da buga kafa.

(Tambaya: wai shin akan samu masu irin halin

Sala a wannan Zamanin kuwa????)

Ya fi kowa sanin halin Sala, don a shekarun

baya gidansu kamar silima yake gurin kallon

dambensu, sai dai shi da jarabar ta ishe shi ya

sallama mata, don haka yanzu ma ba zai iya

biye mata ba, don haka yabi lafiyar gadonsa na

karfe yana fadin, "Kanki ake ji, wai mahaukaci

ya fada rijiya, da girmana da 'ya'yana aga muna

raba hali a titi, ki yi da wani ba dai dani ba." Ya

runtse idonsa duk da ba bacci yake ba. Ta ja

dogon tsaki gami da fadin, "Oho dai! Kai dai

kawai kace ka ji tsoro, wallahi da ka tsaya da ka

gane kurenka yau, munafuki kawai wanda ake

gulmar 'ya'yansa da shi maimakon ya hana sai

maya kara tunzira abin." Ta haye gadonta na

katako tana cigaba da mita, "Ba ku da aiki sai

zaman gindin bishiya kuna gulma, sam ba a iya

juya kwandala ta koma Naira, ba don Allah ya

bani mata masu daukar min tallah ba ai da

nasha haushi, ka dubi wannan yaron da ya

kwaso matacciyar zuciya irin taka, idan don taku

ne sai dai yunwa ta kashe mu." Haka nan take

ta bala'in ita kadai, shi dai bai kula ta ba har

bacci yayi awon gaba dashi don dare ya tsala,

domin bai shigowa gidan da wuri sai dare yayi

sosai. Duk yaran nasu suna jiyo abinda suke yi

amman basa fahimtar maganar da suke yi sai

dai hayaniya kawai da suke ji, Sadiku yafi kowa

tashin hankali don tun yana yaro yake takaicin

abinda iyayan nasa keyi don ma abokinsa Zaid

na bashi baki. Sai dai addu'a al'amarin nasu,

lallai ba a sakewa tuwo suna, haka nan ba'a

sauya iyaye, shi kam da tuni ya sauya da ace

suyo su ake yi, domin kowanne da tabonsa. Sala

masifaffiya mai shegen son kudi da abun duniya

da son 'ya'ya, yayin da Baba Abbakar ya

kasance mai matacciyar zuciya da gulma da

munafurci, don sana'arsa kenan kullum yana

gindin dirimi shi da abokanan sana'ar ta shi

(magulmata) suna ta sana'ar tasu, bai saida

komai balle ya sanya ran zai samu ya kaiwa

iyalansa, 'yar sana'ar tasa ta saida shayi ya

watsar tuni zuciya ta mutu, sai dai gulma a

gindin dirimi. Don haka a cikinsu akan rasa na

zaba, shi dai yana godewa Allah da ya sanya bai

dauko halin ko daya ba a cikinsu, amman dai

yana takaicin irin rayuwar da 'yan uwansa da

iyayensa ke yi, don haka ranar da bakin ciki da

takaici ya kwana, amman yayi alkawarin zai yi

maganin abun da kansa, koda kuwa Sala zata

tsine masa ne Allah dai yaga niyyarsa.

*******************

Karfe takwas na dare Mustafa ya tsaida motarsa

a kofar gidansu Abu, ya tura yaro ya kira masa

ita, kusan tare suka futo da yaron taci uwar

kwalliya da atamfa mai barewa, tayi daurin

Hindu Rufa'i, ana wani tauna cingam wai ita

dole ga 'yar gayu, leben nan ya sha jambaki a

sama baki da kasa, an ja jagira mai cin birki a

gefen kunne. Ta hasken wutar lantarki ya hango

ta kamar ya yi dariya, don kwalliyar tata kamar

'yar kauye tayi mata, sai ya dake don kada ya

tsokanowa kansa don yasa halin tsiwar Abu. Ta

isa ta bude gaban motar aka zauna irin a

karkacen nan ana wani fari da ido wai ita a dole

ga 'yar gayu. Ya kamo hannunta yana dariya

kasa-kasa yace, "Kai gimbiya, kin ga yanda kika

yi wani kyau kuwa? Irin wannan kwalliya ai

sai....." Finciko ta da aka yi ne ya sanya shi yin

shiru cike da mamaki da razana. Sadiku ne ya

finciko ta ya watsar a tsakiyar titi, sannan ya

kalli Mustafa dake kallon sa sororo cike da

mamaki yace, "Kai dan iska mara mutunci

wallahi daga yau na kuma ganinka a kofar gidan

nan sai nayi maka rashin mutunci, don haka ka

ja tsummar rayuwarka ka bar kofar gidan nan

tun ba sanya yara sun maka atile ba." Ya juya

kan Abu wacce ta mike tana goge jikinta wai ita

nan ya bata mata kwalliya, sai murguda baki

take yi tana kun-kuni wanda ya san zaginsa

kawai take yi, ai kuwa yayi kanta ya zabga mata

mari sannan ya sanya kafa ya haure ta. Ta zube

a kasa gami da rike cikinta ta fasa ihu gami da

fadin, "Wayyo Sala na shiga uku!" Ya kuma kai

mata duka amman ta yunkura ta mike ta kwasa

da gudu ya rufa mata baya da bel din

wandonsa da ya zare. A soro suka ci karo da

Sala wacce ta futo a gigice saboda jiyo ihun 'yar

lelenta da tayi. Ai kuwa Abu na ganin Sala din ta

zube a soron tana fadin, "Wayyo Sala na shiga

uku zai kashe ni cikina Sala, zan mutu na shiga

uku (Kuji Makirci). Sala tace "Na shiga uku, wane

shegen ne ya taba mini ke Abula?...." Shigowar

Sadiku yana huci ne ya sanya ta gano abinda ya

faru. Sala ta zaro ido waje cike da bacin rai tana

fadin, "Lallai ka cika mara mutunci, yarinyar

tana zancen ta kawai za ka kama dukanta, to

me tayi maka, mugu?" "Haba Sala wane irin

zance? Iskanci dai kawai. Waye a unguwar nan

bai san abinda yarinyar nan takeyi ba? Haka

kawai ta sanya ana zaginmu da raina mana

hankali, wallahi na kuma ganinta da shegen

mutumin nan sai na karya ta." Sala ta kuma yi

masa kallon banza tana fadin, "Sannu Abbakar

Ubanta da yayi cikinta, to tsaya kaji na gaya

maka, kayi kadan kai uban da ya haife ka ma

yayi kadan balle kai karan kada miya, haka

kawai ka takurawa yarinya ka hana ta rawar

gaban hantsi? Kai ne ka haifar mini ita ko kaine

ka halicceta, eye? Bala'in naka ya wuce na baki

har ka fara kai hannu kana dukan ta? Za ka zo

kana gaya min ana gulmarku a unguwa, ina

ruwana da wasu 'yan unguwa 'yan saka ido

sana'ar banza ana ruwa suna kirgawa, su bari

su koma sata yafi. To bari inyi maka mai gaba

daya ta mahaukata tunda naga abun naka yana

neman ya wuce gona da iri,Wallahi daga yau

idan ka kuma taba mini yarinyar nan ko ka

kuma shiga rayuwarta da sunan fada ban yafe

maka nonona da ka sha ba!" Sadiku ya dafe kai

cike da tashin hankali yana fadin, "Innalillahi wa

inna ilaihi raji'un, Sala mai yasa haka? Yanzu

dan ina gaya muku gaskiya dan gudun kada ku

fada cikin halaka ya sanya zaki tsine

mini....."gaskiya ko kuma munafurci da sanya

ido? Kai waye ya shiga rayuwarka? Kullum kana

yawo da kodadden wando jins da rigar gwanjo

kamar tsohon matsiyacin bature." Ya girgiza kai

cike da takaici yace, "Shike nan Sala Insha Allahu

kome Abu zata yi a unguwar nan da gidan nan

na daina yi mata magana, taje in dai duniya ce

ta ishe ta riga da wando, za ta koya mata

hankali." "Ka ga malam kada kayi mata baki,

koda yake ai ba kai ka haife taba balle bakin ka

ya bita ba, wadanda ma suka fika sunyi sun

gama babu abunda ya same ta sai ma cigaba

balle kai, don kurwar Abu kur! Maye yaci kansa."

Sadiku bai kuma cewa komai ba ya juya ya fice

daga gidan, don sai yaji gaba daya gidan ma ya

ishe shi. Sala ta kama Abu dake zaune dirshan

tana kallonsu don taji yanda Sala ke afke masa

ta wanke mata zuciya, Sala din tana fadin "Tashi

muje gida ki kwanta kinji? Koda yake Alhaji

Mustafan yana can yana jiranki. Goge idonki kije

ku cigaba da zancenku, ki gaya masa ya kwantar

da hankalinsa kamar tsumma a randa, nayi

masa maganin dan saka idon can, ba ku da

sauran mai matsa muku yanzu, muje na raka ki

ko yana kofar gida a labe bai tafi ba." Ta daga

ta tana goge mata idon ta wanda babu ko

alamun kwalla ko guda daya, daman kukan nata

na sharri ne bawai na zafin duka ba. Suka nufi

kofar gidan tare, sai dai babu motar Mustafa

babu alamarta sai dai filin wajen kawai, dan

yana ganin sun yi cikin gida ya ja motarsa yayi

gaba don kada Sadiku yazo yayi masa tijara a

cikin jama'a har asirinsa ya tonu, don haka ya ja

motarsa ya gudu. Ai kuwa suna ganin baya nan

ran Sala ya kuma baci suka koma cikin gida tana

ta masifa da bala'i, wanda har makota suna

jiyota, ita kanta Abun ma taji takaicin tafiyar

Mustafa dan ta saka ran ya bata wasu kudi yau

na ankon bikin Larai, dan haka dai sun dauki

laifi gaba daya sun dora akan Sadiku wanda ya

bar musu unguwar ma gaba daya. A daran nan

Sala batayi baccin kirki ba sai bala'i da masifa

kawai take yi har Baba Abbakar ya dawo tana

yi, shi dai yayi mata banza bai kulata ba dan dai

yasan 'yan bala'in ne suka motsa, idan kuma

suka motsa babu wanda take saurarawa dan

haka shi dai ya lallaba ya haye gadonsa na

karfe yayi lamo kamar mai yin bacci amman a

zuciyarsa Allah wadarai yake yi da halin Sala,

har ya tuno wata mata data wuce ta gabansi

dazu suna majalisa wani yayi subutar baki a

cikinsu yace "Ka ga wannan matar idan ta fara

bala'i sai ta kwana tana yi." Ashe matar nan ta

jiyo shi don haka ta dawo ta tsaya a kansu gami

da rike kugu tana kallonsu shekeke tace, "Mai

kuka ce, eye?" Wanda ya fadi maganar ya yi

murmushi irin na matsorata yace, "A'a Hajiya ai

yabonki muka yi nace duk unguwar nan babu

irinki a mutunci, ba irin babata ba 'yar bala'i,

idan ta kama masifa sai ta kwana tana yi." Jin

abunda yace ne ya sanya tace, "Allah ya so ka

wallahi, da yau na lakada maka duka a unguwar

nan na ga mai kwatarka, da sai kaga karshen

masifa ta." Sai da tayi nisa sannan suka fashe

da dariya suna zolayarsa sai yace, "Ku ai gwara

da na yi haka, dan wallahi yanda na ga tana

wata girgiza bata ki mu casu a tsakiyar titin nan

ba, ni kuwa ina zan iya da ita kana ganin mace

kamar bishiyar kuka? Ai irin wadannan sai da

lallashi." Lallai kam haka ne sai yanzu ya gano

gaskiyar Malam Sabo, masifaffu ba'a iya musu

sai dai a bisu da lallashi ko kuma ayi musu

banza kawai. Shi dai har bacci ya dauke shi bai

san sanda Sala ta gama masifarta ba.

Da safe ma da bala'in Sala ta karya dan Sadiku

ko koko da kosan da ake bashi ranar ba'a bashi

ba sam, shima bai nema ba ya tafi makarantar

sa da yake yana karatun Low ne a B.U.K,

karatun da yake matukar shan wahala a kansa

dan babu wanda ke taimaka masa a iyayansa

sai Malam ne ma yake taimaka masa wani lokaci

da kuma rufin asirin Allah, dan ya iya zane idan

ya samu ya kan yi, ko kuma idan bashi da lakca

ya tsaya shagon wani abokinsa ya taya shi aski a

bashi wani abu, da kuma tallafi na karatu da

suke samu (Scholarship), haka nan yayi

ficewarsa da yunwarsa gashi banda kudin mota

bashi da ko kwandala. Ita kuwa Abu 'yar mulkin

ko shirin makaranta bata yi ba, don kwanciyar

ta ma tayi tace kanta ciwo yake yi, yinin ranar a

daddafe tayi shi dan takaici, ita kuwa Sala sai

kawo mata kayan dadi takeyi kala-kala wai dan

ta kwantar mata da hankali. Yamma na

karatowa aka yi wanka aka ci uwar kwalliya ta

jiran Mustafa aka kame akan kujera, duk yaron

da ya shigo gidan sai taji kamar ita zai ce ana

kira, gashi ita yanzu ta daina kula samari dan a

ganinta ita kalar manya ce kamar yanda

Mustafa ke gaya mata. Sai dai me? Har kusan

karfe goma na dare babu Mustafa babu alamar

sa, har gajiya tayi da lekawa amman babu shi

babu alamunsa. Daga karshe dai ta sanyawa

Sala kuka tana fadin "Sala ina ga fa Mustafa

fushi yayi da wulakancin da Sadiku ya yi masa

jiya, dan baki ji maganganun da ya dinga gaya

masa ba, shi ya sanya ya yi fushi ya ki zuwa."

Sala tace, "Bari ke dai Abula ai wannan yaron ya

goga mana bala'i, yanzu idan yaron nan ya

daina zuwa ina zamu sanya kanmu? Ki duba ki

ga irin kudin da yake bamu a sama ba tare da

mun sha wahala ba, yanzu idan ya daina zuwa

sai dai mu koma abincinmu kenan." "Abinci

Sala? Cabdijam!! Wallahi Sala na fi karfin tallar

abinci yanzu, dube ni fa ki gani? Ni samari ma

tsami na daina harka da su balle wani tallah,

idan mutum bashi da kudi ko kallo ma bai ishe

ni ba." Sala tayi dariya tana fadin, "Ho Abulata,

kinyi gaskiya wallahi kin fi karfin talla yanzu,

tunda Allah ya baki abun neman kudi ai shike

nan. Ki sha kuruminki na ma sani zai dawo,

watakila wani abin ne ya tsre shi, dan na san ba

kowa ne zai sami kamarki ya yasar ba... Ke

kamar na ji karar mota ma." Sukayi shiru, can

Sala tace, "Allah karar mota ce." Suka bazama

suka yi kofar gida har suna karo da juna, sai dai

me? Kurar mota kawai suka gani ta wuce tuni,

haka nan suka dawo suna zaman tsammanin

warabbuka, Malam ya ki noma yana jiran

sadaka. Sai dai har suka fara gyangyadi babu

Mustafa babu alamarsa, haka nan suka hakura

kowacce ta kama makwancinta cike da takaici.

Abu kamar wasa karamar magana ta zama

babba inji Garba Sufa, dan yau kwanaki shida

kenan amman babu Mustafa babu alamarsa,

uwa da 'ya sun shiga tashin hankali, tun suna

tunanin zai zo har sun hakura sun fidda ransu

da zuwan nasa, shi kuwa Sadiku da har yau bai

daina shan bala'in Sala ba murna yake yi don

ko babu komai ya kori Mustafa, lallai barazanar

da ya yi masa tayi tasiri a kansa. Daran daya

cika kwana bakwai suka yanke shawarar zuwa

gidansu dan su bashi hakuri, domin dai kudi

sun fara musu karanci don ma su Karimatu

suna daukar abinci da funkaso, don ita macece

mai jarababban neman kudi dan tun tana

budurwa bata iya zama babu sana'a ba.

Washegari da yamma Abu taci kwalliyar ta duk

da kanta da yake mata ciwo, ana taku dai-dai

kamar ba zata taka kasa ba, aka nufi gidan su

Mustafa wanda yake can gangaren layinsu.

Sanda ta isa ta tsaya tana kallon gurin da yake

zama bisa farar kujera karkashin bishiyar

Umbrella, lokuta da dama da jarida a hannunsa,

sai dai yanzu babu ko alamarsa ko kujerar tasa

ma babu a gurin. Katuwar koface wacce ke

garkame, bata mantawa da can suna zuwa

tsokanar kare, idan ya biyosu su zunduma da

gudu ko kuma suyi ta jifansa, wata rana sun

taba fasa masa kai mai gadin ya bi su da gudu

ya kama daya a cikinsu ya zane, shine fa suka

kulla masa, ai kuwa rannan maigidan ya futo da

motar zai tafi sai kuma yayi mantuwa ya koma

cikin gidan, su kuwa daman suna fakonsa dan

haka suka dauko wani abu mai tsini suka soka a

tayar gaba ta sace, ai kuwa sanda mai gidan ya

futo ya gani ya dinga yiwa maigadin fada daga

karshe dai sai wata ya hau ya bar wannan a

nan, bayan maigidan ya tafi suka dinga yiwa

maigadin ihu da tsokanarsa, ai kuwa ya bisu da

gudu sai dai kasa kama kowa yayi dan 'yar

zilliya suka dinga yi masa, haka nan ya gaji ya

koma yana nishi, don haka yanzu take fargaba

kada ya gane ta. Ta daure dai ta kwankwasa

kofar, ya bude ta 'yar karamar taga ya leko dan

yaga wanda ke magana, yana ganin ita ce ya

zaro ido waje yace, "Me kike nema a anan,

eye?" Yana maganar fuskar nan tasa a murtike.

Ta rike kugu da murguda baki a hankali tace,

"Banza dan gadi, kai ba don ta kama ba ka isa a

wani tsaya ana magana da kai, dalla ka bude da

wani bakinka duk gansa-kuka." Ya kuma hasala

dan dai bai ji abinda tace ba amman da alama

zaginsa take yi, dan haka ya bude ya futo da

wata zungureriyar bulalarsa yana muzurai. Ko a

jikinta bata ji ko dar ba don ba dabi'ar ta bace

tsoro, ta kuma ayyana a ranta wannan tsohon

ya tabata zai gane kurensa dan wallahi sai ta yi

masa sharri, ta kuma gyara tsayuwa. Ya hasala

matuka dan haka da zafin rai ya fara magana,

"Ke yarinya bana son rashin mutunci, don a

haife kin san na haife ki ko? Don haka ki bar

gurin nan tun ban zane ki ba." Ta yi masa kallon

baka isa ba sannan tace, "Ka ga Malam ni ba

wani abu ya kawo ni ba Mustafa nazo nema,

idan yana ciki kace masa Abu tana magana da

shi, ka daina mini surutu kana feshe ni da

yawu." Mamaki ya bayyana a kan fuskarsa, mai

ya hada Mustafa nutsatstsen yaro da wannan

hatsabibiyar yarinyar? Amman bai san alakarsu

ba, dan haka ya dan saki fuska ya ce, "Mustafa

fa kika ce?"

Ta motsa fuska tace, "Ko kana mamaki ne?" A

ransa yace, "Kai wannan yarinyar 'yar bala'i ce,

gwara ya lallaba ta su rabu lafiya. Don haka ya

kuma gyara tsayuwa ya fara kora mata bayani,

"Ai Alhaji Mustafa ya koma don daman hutu

yazo da kuma ciwon Babansa da ya tashi na

hanta, dan a can kasar waje yake karatunsa,

yau kwanansa shida da komawa, kuma ba shi

da ranar dawowa dan tun da ya tafi shekara

uku sai wannan karon ya dawo." Ta dafe kirji

cike da tashin hankali ta ce, "Yanzu ya tafi wata

kasar babu daman na ganshi dan Allah?" "Af! Ai

kuma sai kiyi, mutumin da aka ce miki bai kasar

gaba daya ma, kinga komawa ta ma." Ya koma

ya garkame kofar tasa. Kafarta ta yi mata nauyi

ta kasa dagawa, yanzu yaya zata yi da

rayuwarta? Don Mustafa ya koyar da ita darussa

masu wuyar mantawa, yanzu waye zai dinga

bata shandy tana sha? Waye zai dinga bata

tabar shaidan tana sha? Waye zai dinga kai ta

hotel taci kayan dadi ta hau gado mai laushi?,

waye zai dinga bata kudi mai yawa irin na

Mustafa? amsar ita ce babu, babu wanda zai

maye mata gurbin Mustafa ko ta ina. Da kyar

take iya gane hanyar da take sanya kafarta duk

hankalinta a tashe yake, don ma Allah ya

taimake ta ba wata tafiya bace mai nisa, da

kyar ta samu ta lallaba ta isa gidan dan zazzabi

da ciwon kai sun hadu sunyi mata taron dangi.

Bisa wata tabarma da ta tadda a tsakar gidan ta

zube, wacce Sala ta shimfida ta shiga kicin dora

sanwar dare, ta zauna idonta na zubar da

hawaye, azaba biyu take ji a jikinta gata rabuwa

da Mustafa ga kuma ta ciwon da ke addabarta,

ta zame ta kwanta ta kama juyi da malailaikuwa

a tsakar gidan tana kuka mai ciwo da taba rai.

Sala ta futo daga kicin dan ta dan huta, sai dai

mai zata gani? Abu ce 'yar lelenta tana birgima

a tsakar gida tana kuka dafe da kanta. Ta isa

gurin da sauri tana tambayar ta, "Abula diyar

kirki yaya aka yi? Bai hakura ba ne Mustafan?

Idan bai hakura ba ni sai naje da kaina na bashi

hakuri. Kwantar da hankalinki, banda abun dan

yau ma ai saurin fushi ba nasa bane ba, idan

yayi mana haka ai yayi mana tsiya, bari naje da

kaina na bashi hakuri ina ne gidan nasu?" Ta

mike tana neman gyalen da za ta yafa. Abu da

taga da gaske take yi ta ruko hannunta, ta juya

tana kallon ta amman ta gaza cewa komai, cikin

kuka Abun tace, "Kada ma kije Sala, ko kinje ba

zaki same shi ba don baya nan wai daman a

kasar waje yake karatu hutu ya zo, yanzu ya

koma yau kwanansa shida da komawa. Wayyo

Sala cikina zan mutu." Ta karasa maganar da

kuka tana rike ciki. Sala ta rude sosai ta ruko

hannun diyar tata tana mata sannu gami da

lallashinta tana fadin, "Kiyi hakuri Abula na san

zai dawo ya nemeki komai dadewa, domin ke

din mace ce da duk namijin da ya ganki sai ya

rude balle shi Mustafa da yake sonki, share

hawayenki ki daina kuka kinji Abula ta? Na san

zai dawo komai dadewa." "Ni fa cikina ne yake

mini ciwo. Wayyo Sala ciki....." Sai ga amai kyah!

kyah! kyah! Tana kwararawa. Sala ta kuma

rudewa ta mike da azama tana neman fo don

taimakawa diyar tata, tun tana yin amai na

abinci da ruwa har ta koma na majina take yi,

da kyar suka samu aman ya fada. Sala ta

taimaka mata ta raka ta bandaki dan ta wanke

jikinta, ita kuma ta dawo dan ta gyara gurin

zuciyar ta na cike da tsananin tausayin diyar

tata, dan ta gano ta fada kangin soyayyar

Mustafa.

Haka nan ta karasa yammacin a kwance ga juwa

da tashin zuciya dake damunta, daga karshe dai

Sala tace bari ta je gurin dan Oga ta karbo mata

magani ko aman ya tsaya. Tana isa dan oga ya

kama wage baki yana fadin, "A'a mana ne?

Sannu ka da zuwa. Ina Habu ne dan bana ganin

shi yanzu?." Sala tace, "Abu tana nan, yanzu ma

ita na zo na karbawa magani bata da lafiya." Ya

kuma wage baki yana fadin, "Habu babu lafiya?

Bari a bata magani mama, ka bari kudinka ma."

Ya kama hada magunguna bayan ya kammala

yayi mata bayanin yanda za'a sha kowanne, ta

amsa da azama ta nufi gida. Sanda ta sha

maganin kamar gaske dan aman ya tsaya har ta

sami bacci, sai dai wajen karfe goma sha daya

aman ya kuma dawowa dan shi ma ya tashe ta

daga bacci, sai da ta amayar da duk maganin

da ta sha samman ta sami sa'ida, sannan ta

sami wani bacci ya dauke ta. Da safe kuwa sai ta

tashi jikin babu laifi dan aman ya tsaya, sai dai

jikin nata babu kwari daga kwanciya sai

kwanciya, har ta samu ta tsakuri abinci kadan ta

ci, Sala sai ta kama murna jiki yayi kyau. Sai dai

yamma tana yi amai ya dawo sabo, har dare

yayi ana abu daya, sai da aka kuma samo wani

maganin. Sala kam bala'i ta hau yi tana fadin,

"A'a na gamo lagon abin ma, wato marasa

mutuncin nan ne ke neman kama mini diya

(mayu), lallai kam zan yi maganinsu, don ga

alama nan ciwo baya tashi sai almuru yayi,

wallahi duk shegiyar matar da na san mayyace a

unguwar nan sai naci ubanta, za su san wannan

karon sun ciwo mai zafi, dan ba zan yadda da

rainin hankali ba, dan sun ga diyata ta taso bul-

bul da ita gwanin sha'awa ga farin jini shine

zasu lashe mini ita? To wallahi kurwarta kur! Kai

bari ku gani ma ba'a bori da sanyin jiki, ai mune

maganin mayu." Ta debo garwashi ta gumbuda

garin tazargade da wani maganin mayu, nan fa

gida ya tirnike da hayaki sai tari suke yi. Sannan

ta kuma jika tazargadan a cikin ruwa ta mikawa

Abun tana fadin, "Amshi nan shanye, mayu za

su ci kan ubansu yanzu a gidan nan." Cikin ikon

Allah har ta gama shanyewa ba tayi amai ba

don da duk abinda ya shiga cikinta sai ta

amayar da shi, amman wannan ya zauna. Sala

tayi dariya tana fadin, "Ahaf ai na sani, mu za'a

gayawa zancen banza? mu maita ma bamu so yi

bane, abinda ake saidawa a kasuwa." Haka nan

ta dinga mita da balokoko a tsakar gidan kamar

wadan da take zargin suna nan a tsakar gidan.

Cikin kwana biyu sai jikin yayi kyau, domin in

dai ta sha ruwa da tazargade a ciki bata yin

aman, hankalin Sala ya fara kwanciya da ita

kanta Abun, sai abu daya da ya dawo musu da

hannun agogo baya bai wuce dawowar aman

ba. Tana tsaka da bacci aman ya taso mata, tayi

kokari ta fita amman ina ya riga ya yunkuro dan

haka ta zauna a nan ta dinga kelayawa.

Kanwarta Karimatu ce ta mike ta yi dakin Sala

da gudu tana gaya mata, ai kuwa a rude Sala

din ta taho, ta rike Abun kam-kam tana mata

sannu har dai suka samu aman ya lafa ta dan

sami bacci. Sala ta koma daki ta kwanta, sai dai

ba'a yi awa guda ba Karimatu ta kuma komawa

da gudu taba buga kofar dakin Sala gami da

fadin aman ya dawo.

Sala ta tashi a rude, sai ta kalli Baba Abbakar

dake ta shararar bacci ta kuma hasala, ta

daddage iyakacin karfinta ta maka masa duka,

ya tashi a gigice yana ta soshe-soshe, ta galla

masa harara tana fadin, "Ka saki baki kana ta

sharara bacci bayan ka san Abula bata da lafiya,

ko sisi baka taba bayarwa kace a sai mata

magani ba sannan sannu ma ta gagara? To ka

zo muje ka ga jikin nata kada ta mutu." Ta shiga

gaba yana binta a baya zugui-zugui kamar

makaho da dan jagora, ai kuwa yanda suka ga

Abu hankalinsu ya tashi dan ta galabaita sosai.

Sala ta rude matuka ta saki kuka tana fadin,

"Wayyo Abula! Dan Allah kada ki mutu ki barni,

na shiga uku ni Salamatu." Baba Abbakar ne ya

dinga lallabata da kwantar mata da hankali,

zuwa gurin asuba kuma sai Abu ta fara suma,

dan haka gari yana dan kara haske aka samo

mota suka kwashe ta sai asibitin murtala

(Murtala general hospital). Sun yi sa'a suna

zuwa aka karbe ta, nan da nan aka rubuta musu

abinda zasu siyo, Baba Abbakar babu ko sisi a

jikinsa don haka ya zame ya gudu, Sala ce ta

kwance jakarta ta dauko kudin ta bada, nan da

nan aka daura mata karin ruwa, sai da babbar

leda ta shiga jikinta sannan ta fara dawowa

hayyacinta. Cikin ikon Allah kafin azahar ta

dawo hayyacinta, da taimakon Allah da

taimakon karin ruwan da aka yi mata. Sai

washegari da likita ya dawo yaga jikin ya dan

fara kyau ya rubuta mata gwaje-gwaje bayan

'yan tambayoyi da yayi mata, gwaji kala uku aka

rubuta mata, akwai na taifot da na maleriya sai

kuma wanda yake tantama a kansa dan ance

masa budurwa ce, amman dai ya zama dole a yi

din don ya tabbatar da binciken sa gwajin masu

ciki. Sala ce ta taimaka mata suka nufi dakin

gwaje-gwajen aka auna komai aka basu

sakamako cikin ambulan, suka ce ta kaiwa

likitan da ya turo su, suka koma dakin da aka

kwantar dasu suna jiran zuwan likitan. Sai da ya

gama ganin marasa lafiya sannan ya dawo dakin

nasu, ya fara bin gadaje yana dubawa har ya zo

kan na Abu. Ya gyara gilashin din idonsa gami

da kara tambayarta jikin nata, Sala ce ta amsa

sannan ta bashi sakamakon dake cikin ambulan.

Ya amsa ya farke yana dubawa, ya kuma gyara

gilashin din dake idonsa yana kallon Abu,

sannan yace da Sala, "Baba kika ce budurwa ce

ko?" "Fil ma kuwa a ledar ta. Don ko kudin toshi

ba'a kawo ba balle a sanya rana balle kuma ta

kai ga biki ba." Sala ta bashi amsa da sauri. Ya

girgiza ka ya ce, "Haka ne." Yace, "Baba ku

same ni a ofis dina yanzu zan baku sallama dan

ta warware." Bai jira jin amsar su ba ya wuce

gado na gaba. Sun dade tsugunne a kofar ofis

din nasa da kayansu a zube suna jiransa, har ya

zo ya bude ya shiga suka rufa masa baya, ya

nuna musu gurin zama sannan ya dauki wata

takarda ya fara rubuce-rubuce a cikinta




Zaharaddeen Shomar

Whatsapp 08168575100




Idan zuciya ta gyaru 1-03

Posted by ANaM Dorayi on 07:50 PM, 28-Jan-16

Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU

_________________ Na

________Fauziyya D Sulaiman_____

Bayan ya gama ya daga kansa yana kara kallon

Abu wacce tayi wuki-wuki, ya ma rasa ta inda

zai fara, can dai ya daure yace, "Baba wannan

diyarki ce?" Batayi mamakin tambayar ba don

jama'a da dama kanyi mamaki idan aka ga

'ya'yanta wanda sam basa kama da ita, dan

kamar mahaifinsu suke yowa wanda idan ka

gansu tamkar Larabawa suke, ita kuma gata nan

bakikkirin, don haka baki a hangame tace, "Ka

ga bamuyi kama ba ko? Ai mutane da dama na

mamakin ace 'ya'yana ne don idan suna yara

suna kuka a gidan biki har cewa ake na

maidawa uwarsu sai anga na ciro mama ina

basu tukunna ake yarda nawa ne, ai diyata ce ta

biyu. Ha ha ha" Ta saki dariya daga karshe.

Ya girgiza kai cike da takaici ya ce, "A yanda na

gani a jikin kati yanzu shekararta goma sha

hudu ko?" Ta kuma yin dariya tana fadin, "Haka

ne likita ka ganta gaba-gaba haka nan take da

girman jiki babu shekaru, ka ganta kamar 'yar

shekara ashirin ko? Girman jikin ne kawai

musamman yanzu da take cin kayan dadi sai

tayi wani fari da kiba kamar diyar wani

basarake, bul-bul da ita gwanin sha'awa."

Likitan yayi murmushi don ya gano inda Abu ta

samu matsala, wato rashin uwa tagari ne, dan

haka babu wani boye-boye ya ce, "Hajiya ke da

yarinyarki ta sauya kin tambayeta dalilin da ya

sanya ta sauya?." "Haba dai likita wace irin

tambaya ai jin dadi shi ke sanya mutum ya

sauya, ka ga dai yarinyar nan kullum da sai ta

dauki talla safe da dare, yanzu kuwa ta samu

mai ba ta kudin sai dai taci ta kwanta sai dai

makaranta." Ya girgiza kai cike da takaici ya ce,

"Haka ne, to tsaya na gaya miki diyarki tana

dauke da juna biyu, ma'ana ciki, dan haka

wannan sauyawar da tayi ba wai ta jin dadi

bace illah ta ciki....." Sala ta mike da tashin

hankali ta dafe kirji cikin karaji tana fadin, "Me?

Likita cika fa kace? Lallai baka san aikin ka ba,

dubi Abulan duka nawa take da zata yi ciki? Kai

dai ka kara dubawa ka gani ko katin wata ka

dauko." Ita ma Abu dake zaune tana jin caftar

da Likita da Sala ta dafe kirkji da sauri tana

fadin, "Na shiga uku ciki ne dani." Sai ta saki

kuka. Sala ma ta sanya kuka tana fadin, "An ya

likita ba karya ka fadi ba? Ko kuma aljanu ne

suka hura mata ciki ka ga kamar ciki ne da ita,

dan yaushe ma ta fara al'ada duka, ka dai sake

dubawa." Shi dai rubutunsa kawai yake yi akan

wata takarda, sai da ya gama sannan ya daga

kansa ya mika mata kayin yana fadin, "Ko ki

yarda ko kada ki yarda 'yarki tana da ciki, dan

haka idan baki yarda ba sai kije wani asibitin a

duba miki ita, na gama daku sai ku tafi, a gaba

a dinga kula da tarbiyyar yara." Ta kuma

fashewa da kuka tana fadin, "Don Allah likita ka

taimake mu, yanzu yaya zamu yi da wannan

abin kunyar? Na shiga uku ni Salame....." "Kinga

Hajiya ku fita can kuyi kukanku don na tashi zan

kulle ofis dina." Ya mike yana hada kayansa. Ta

tsagaita kukan tana fadin, "Likita yanzu babu

wani taimako da zaka yi mana?" "Kinga Baba

babu wani abu da zanyi bayan addu'a Allah ya

rabata da shi lafiya, kuje waje zan kulle ofis dina

nace." Yana magana yana kallon agogonsa. Haka

nan suka fice daga Ofis din Abu tana kuka Sala

kuma duk ta gigice, suka yi zaune turus a gaban

kayansu kowacce tana kuka, har yazo ya wuce

su bayan ya kulle Ofis din nasa. Can dai Sala ta

daure ta ce, "Wai ni Abula garin yaya kika yarda

har yayi miki ciki ne ma? Ai da kince yayi wasu

'yan dabarun da bazaki samu ciki ba" (Fauza

tace, kuji fa jama'a bata bakin ciki da lalata

mata diyar da aka yi sai ra samun cikin, shima

don tana jin kunyar idon jama'a ne, kai tir da

irin wadannan iyayen). Abu ta cuno baki gaba

tana wani kumbure-kumbure tace, "To nima na

san zan sami cikin ne Sala? gashi yanzu ya gudu

ya barni da ciki. Kuma na san 'yan gidansu ba

zasu yadda shi yayi ba, na shiga uku yaya zanyi

da gorin 'yan unguwarmu? Ga shi dama sun

tsane ni, yanzu idan suka ji ina da ciki zasu

dinga tsokana ta."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Sala ta fyace hanci wanda ke kwaranyo da

majina ga hawaye sun hadu sun cakude sannan

tace, "Au!! Gaya musu zamu yi? ai kama

bakinmu za muyi muyi shiru, ko Abbakar ba

za'a gayawa ba, dan kada dadin hira ya kwashe

shi a majalisarsu ya kwaza, kin san shi da

shegen surutu, kija bakinki ki yi shiru har mu

zubar da shi....." "Zubarwa Sala?" Abu ta fadi a

kidime. "Eh mana zubarwa zam yi, dan da

kunyar duniya gwara ta lahira, kuma ma ai ma

tuba kafin mu mutu. Goge hawayenki ni na san

ta inda zan bullowa al'amarin, ki sha kuruminki,

bari na samo mana mota mu tafi gida." Ta fita

ta samo musu mota suka loda kayanzu suka

nufi gida da sunan Abu ta warke. Tana isa gida

ta sanya aka samo mata madaci ta hada da

darbejiya da omo da kanwa ungurnu ta dafa su

suka dahu sannan ta kawo wa Abu daki. Tana

kwance lamo ta ce, "Abula na tashi ki kafa kai

maza ki shanye wannan." Ta mika mata kwanon

dake dauke da hadin. Babu musu Abu ta karba

ta kafa kai ta kama kyankyama tana rintse ido

saboda rashin dadinsa da daci kamar zai yanka

mata harshe, ko kofi guda bata sha ba amai ya

ciyo ta, ta yadda kwanon ta kama amai, gaba

daya hadin ya zube, wanda ta sha kuma ta

dinga dawo dashi tamkar zata amayar da

'ya'yan hanjinta. Sala tana tsaye ta yi tagumi,

sai dai tana ganin aman ya lafa ta kuma dauko

wani kwanon cike da maganin tace, "Maza Abula

na daure ki shanye wannan....." Ta girgiza kai

cike da fargaba tana fadin, "A'a Sala gaskiya

babu dadi, hanjina kamar zasu tsinke ji nake

kamar zan mutu." Sala ta waro ido waje tana

fadin, "To dama waye yace miki dadi ne da shi,

eye? Daman ai za ki sha ne dan ki rabu da

wannan jarabar dake tare dake, da don dadi ne

yaushe zan baki? Da dadi nake so kiji sai na sayo

miki kaza da madara, amshi ni ki sha tun raina

bai baci ba ko asirinmu ya tonu ba." Abu ta

amsa idonta na fidda hawaye ta amsa ta kafa

kai tana sha, ai wannan karon ko rabin kofi bata

sha ba aman ya kuma dawo wa, ta dinga

yunkuri kamar za ta amayar da 'ya'yan

hanjinta, hankalin Sala ya kuma tashi, haka nan

suka hakura dan babu yanda zasu yi suka yi

zugui-zugui da su cike da tashin hankali. Sadiku

ya shigo gidan da Sallama, Sala tace da Abu,

"Maza kwanta ki rufe idonki zan ce bacci kike yi,

Waye......? Tsaya ina zuwa." Bakinta yana

kyarma take fadin, ta fita da sauri tana kokarin

gyara daurin zani dake shirin faduwa. Ya dubeta

da mamaki dan ganin yanda ta fito a firgice,

idanuwan nata duk sun yo waje. Ya kalle ta da

damuwa a ransa ya ce, "Lafiya Sala ko ba ki jin

dadi ne?" Da sauri Sala tace, "Lafiya ta kalau me

ka gani? Jiya ne dai 'yar uwarka ta tashi da

ciwon kai har muka kai ta asibiti kana

makaranta, amman yanzu jikin da sauki dan har

an sallamo mu." Yace, "Allah ya sawake." Ya

dauki bokiti ya zuba ruwa ya shiga bandaki, ta

yi tsaye tana muzurai wai dan kada ya shiga

dakin, har ya gama ya futo daga bandaki. Sanda

ya futo har tsoro ya ji dan ganin yanda ya bar

ta haka ya tadda ta tana tsaye, ya dube ta da

mamaki ya ce, "Sala yaya dai, lafiya?" Ta gatsina

fuska ta ce, "Lafiya kalau, ina shan iska ne

kawai."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ya dubeta sosai ya ji gabansa ya fadi dan ganin

yanayin ta, amman sai ya dake kawai ya wuce,

har ya isa soro sai wani tunani ya darsu a ransa,

sai ya juyo har lokacin tana tsaye tana dubansa.

Ya kalle ta da kyau yace, "Sala kunje asibiti kika

ce? Me suka ce yana damunta?" Munje mana da

Baba Abbakar muka je ma jiyan ta sami sauki

yanzu haka bacci take yi. Bai yadda da abun da

tace ba, dan haka ya ce, "Ki bani katin na duba

ko da wani abu da suka ce." Kululululuuu!

Cikinta ya duri ruwa, amman sai tayi saurin

yanko karya tace, "Laaa! Ka ga sai yanzu ma na

tuna da katin, ai mun baro shi a can asibitin

wallahi, ai tama warke idan ka ganta kamar bata

yi ciwon ba ma." Kamar ya kuma yin magana,

amman sai ya ga rashin dacewar yi din dan

haka kawai ya juya ya fita ya nufi dakinsa, sai

dai ransa cike yake da zargi kala-kala amman

yana ta addu'ar Allah ya sanya abin da yake

zargin ya zama ba gaskiya ba ne. Sai da Sala

taga ya shige dakinsa sannan tayi ajiyar zuciya

gami da shiga dakinta da sauri tana fadin, "Oh!

ni Salame yaro sai shegiyar tambayar tsiya

kamar dan jarida? Koda yake an ce ai karatun

Lauya yake yi sun iya sharri, ai da na gaya masa

abinda ya faru na shiga uku da surutunsa

kamar wani ubana." Kusan daran nan a zaune

suka kwana suna sake-saken abinda zai fish-she

su, daga karshe dai sun yanke shawarar

komawa asibitin watakila su sami wanda zai

zubar musu da cikin tunda an ce ana zubarwa.

Amman sun yanke shawarar ba zasu je asibitin

Murtala ba za suje Kuroda ne dan kada Likitan

jiya ya tona musu asiri. Sanda suka isa asibitin

suka bi layi har ya kawo kansu suka shiga,

bayan sun zauna likita ya dubesu yana

tambayar abinda ya faru. Sala ce ta fara

kwantar da murya tana fadin, "Wallahi likita

tsautsayi ne ya faru da yarinyar nan, yarinya ce

'yar albar....." Ya dubi katin yana magana,

"Hajiya kece Zainabun ne?" "A'a ba ni bace gata

nan." Ta nuna Abu. Ya maida dubansa ga Abu

ya ce, "Zainabu me ke damunku?" Idonta ya

kawo kwalla ta dubi Sala tana matse idanu, Sala

ta daga mata kai alamar ta yi magana, ta

kwantar da murya ba kamar da ba da take

magana a tsiwace tace, "Daman kaina ne yake

ciwo da ciki na da kuma amai....." Ya dubeta da

kyau sannan ya maida kansa ga katin yana

rubuce-rubuce, ya daga kansa bayan ya gama

ya ce, "Hajiya zaki kai ta ayi mata gwajin fitsari

da jini." Ya dubi wata ma'aikaciyar jinya (nurse)

yace, "Sister nuna musu dakin gwajin jini."

Ma'aikaciyar jinyar ta mike tana fadin, "Hajiya

taso muje mana."

Abu ta kalli Sala wacce ko motsawa bata yi ba,

Sala kam wani busashshen yawu ta hadiya da

kyar sannan tace, "To likita ai daman a babban

asibiti anyi mata gwajin, an gano tana da ciki

ne.... Daman zuwa muka yi ka taimaka mana

kamar yanda Allah ya taimake ka ka zubar...."

"Me?" Likitan ya tambaya da mamaki, ya dora

da cewar, "Hajiya an gaya miki muna zubar da

ciki ne mu?" Bai bari ta bada amsa ba ya cigaba

da maganarsa, "To ki sani mu bamu zubar da

ciki a nan, idan kika kuma kasadar zuwa wani

asibitin na gwamnati da sunan a zubar miki da

ciki za'a iya kama ki a daure, wato kina jin

kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko? Wato

kinfi jin kunyar duniya ba kya tsoron Allah ko?

Me yasa kika yi sakaci da tarbiyyar 'yarki har

tayi ciki? A ce kamar wannan karamar yarinyar

da bata gama sanin kanta ba balle ma ta san

mecece rayuwa ta yi ciki....." "Ai dai kaddara ce

ba ta wuce kanka ba kai ma." Abu ta katse shi

tana murguda baki da wani kyafta idanuwa. Sala

ta kai mata duka tana fadin, "Kin ci Ubanki

nace, ana neman ya raba ki da wannan kajagar

kina masa rashin kunya?" "Kin ga Hajiya ku tashi

ku fita na gama da ku, don ina da marasa lafiya

dake jirana." Likitan ya katse mata maganar.

Sala ta gurfana bisa gwiwowinta za ta fara roko,

amma ya katse mata hanzari ya daga mata

hannu yana fadin, "Hajiya I said get out of my

Office, (Na ce ki fita daga Ofis dina)." Jikin Sala

ya yi sanya ta mike duk da bata ji abinda yace

ba ta gane korarsu yake yi, Abun ce ma ta dan

gane wani abu tunda ta san (get out) dan haka

suka fice babu shiri. A bakin titi suka yi tsaye

cike da tashin hankali, dan duk iyakacin

dabararsu ta kare. Abu ta fashe da kuka tana

fadin, "Yanzu Sala shi kenan gorin da nake yiwa

Ladi mai danwake ta haifi shege nima haka za'a

dinga mini? Kin gani har hana ta fitowa muke

muna bula mata kasa idan ta fito, gaskiya

Mustafa ya cuce ni, Gashi ya gudu ya barni da

abin kunya." Sala ta matse ido cike da takaici

tace, "Bari ke dai diyar nan, na rasa inda zan

tsoma kaina da wannan abun kunyar, wallahi

yaron nan ya shammace mu, da ina ganin sa

yaron arziki ashe dan tsiya ne." Tayi kwafa gami

da fyace majina da hawayen dake zubo mata da

gefen gyalenta.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Abu ta dube ta tace, "Sala yanzu gida zamu

koma?" Sala tace, "Eh, to! Ko dai zamu je gurin

bokan can na kan tudu mu gani ko za'a sami

maganin zubar da ci....." "Sannu Hajiya." Wata

murya ta katse mata magana daga bayanta,

gaba dayansu suka juya da sauri dan ganin mai

musu magana. Ma'aikaciyar jinyar nan ce da

suka gani a dakin likita, wadda ya ce ta raka su

dakin gwajin jini. Ma'aikaciyar jinyar ta fara

magana, "Ina ta addu'ar Allah ya sanya daman

baku tafi ba, na dan tsaye bata lokaci ne dan

kada likitan ya gane ku na biyo. Ai shi na gaya

muku dan ka'ida ne ba ya zubar da ciki, yana

wani fama da gemu kamar gaske. Don ma bai

kama yi muku wa'azi ba, shi ya sanya sam

bama shiri da shi, amman daman ka'ida ce duk

asibitocin gwamnati ba'a zubar da ciki idan na

da matsala ba, sai dai zan taimake ku yanzu dan

kun bani tausayi, bai dace yarinya karama

kamar wannan rayuwarta ta lalace tun yanzu

ba." Fuskarsu ta fadada da fara'a Sala ta ce,

"Kai amman likita mun gode miki kuwa, Allah ya

sanya ki gama da duniya lafiya." Ma'aikaciyar

jinyar tace, "Amin." Sannan ta fara yi musu

kwatancen wani asibiti mai zaman kansa inda

za'a cire musu cikin. Sala ta dinga godiya kamar

ta kwanta don durkuso tana godiya.

Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Babu komai idan baku

gane ba dai ku fada mini, sai dai yanzu rana ta

yi gobe da sassafe za kuyi sammako kuje." Sala

tace, "Mun gane ma." Haka nan sukayi Sallama

suka tafi suna ta godiya. Daren ranar dai cikin

farin ciki suka kwana, sai zumudi suke yi gari ya

waye su tafi, dan abun da ya so tauye musu

farin cikin su ma da farko bai wuce rashin kudi

ba, sai dai da yake ance mai kadara ba

matsiyace bane, sai suka daga wasu kayansu na

sawa har da wani saitin dankunnen gwal wanda

Mustafa ya saiwa Abu suka kai kasuwar Rimi da

kasuwar 'yan tsaye suka saida, Cas suka amso

kudinsu, dan haka suka daina fargaba suka

kwana da farin ciki wanda rabon su dashi tun

ranar da suka ji Abu tana da cikin. Sai dai idan

za suyi magana kasa-kasa sukeyi dan sun lura

da Sadiku ya sanya musu ido, ko ma su kulle

kofar.

Da sassafe suka yi sammakon shiryawa suka

nufi kwatancen asibibin da Ma'aikaciyar jinyar

nan ta musu, basu wani sha wahala ba suka

gano a nan cikin Sabon gari yake. Sanda suka isa

suka cika da mamaki dan ganin wannan

Ma'aikaciyar ta jiya, ta tare su tana dariya tace,

"Kun gan ni anan ko? ai ina aiki anan ma sanda

bani da aiki a can. Dan haka ne ma ya sanya

nayi muku kwatancan nan din, kuzo muje gurin

likitan." Wani katon Inyamuri ne kansa da sanko

ya sha kot, idanuwansa jajir suke da alamun

shan taba a lebensa, ta cikin gilashinsa ya dinga

leken Abu yana wani lasar lebe. Cikin harshen

turanci Ma'aikaciyar jinyar ta yi masa bayani

duk abinda ke damun Abu. Ya yi dariya cikin

gurbatacciyar hausarsa ya ce, "O.k na gane,

Yarinya ka zauna mana." Yana magana yana

dubanta kamar maye. Duk rashin tsoro irin na

Abu sai da ta tsorata da ganin mutumin, dan

haka ta tsaya ta kasa zama. Sala ta dubeta da

kulawa tace, "Abula zauna mana, shine zai raba

ki da wannan kajagar da ke tare da ke." Ta

zauna tana cigaba da kallon sa har lokacin

hankalinta bai kwanta dashi ba. "Hajiya ciki wata

nawa take?" Ya tambayi Sala. Tace, "Ban sani ba

likita, sai dai ka duba ka gani." Ya Umurci Abu

da ta kwanta a wani gado da aka zagaye da

labule sannan ya shiga yayi mata awo. Sai da ya

kammala sannan ya fito ya dubi Sala ya ce,

"Hajiya yarinyarka tana da shiki na wata uku ne,

amman kada ka damu idan da akwai kudi za'a

cire shi yanzu." "Nawa ne kudin? Mun zo da

shi." Sala ta fada da saurinta. "Ka je can waje ka

biya za su gaya maka kudin." Sannan ya dubi

Abu yana fadin, "Ka sauko za muje da ke dakin

aikin yanzu." Sala ta je ta biya duk kudin da aka

caje ta suka bata takardar shaidar ta biya, duk

yawan kudin bata ji kyashin biya ba. Bayan ta

karba ta kai masa ya amsa ya karanta ya

umurci Abu da ta shiga wani daki ita kuma Sala

ta jira a can wajen shakatawa. Sai da ya sanya

ta tube kayanta sannan yace dole sai ya fara

kusantarta sannan zai mata aikin. Hankalin Abu

ya tashi matuka ta mike ta daura zaninta tana

masa wani duba na tsana da tsiwa ta ce,

"Sannu tsohon dan iska Bunsuru, bayan an biya

ka kudinka, to na fasa ai ba kai kadai bane mai

aikin ba, ka biya mu kudinmu mu tafi wani

gurin." Hankalin likitan ya tashi don ya kwadaita

da Abu dan ya jima bai yiwa yarinya karama

mai kyau da kyan sura irin tata aiki ba, dan

haka ya kwantar da kai da gurbatacciyar

hausarsa ya dinga lallashinta, amman fir Abu

taki yadda. Da dai ya ga ba zai shawo kanta ta

haka ba sai ya ce, shikenan ya fasa ta hau

gadon yayi mata aikin, bata yi musu ba ta

kwanta, tana ji ya zurkuda mata wata allura

wacce ko minti uku bata yi ba taji duk jikinta ya

mutu ko hannu ba zata iya dagawa ba, bakinta

ma ya kasa buduwa balle tayi magana, za mu

iya cewa tayi karamar suma ne,

Amman tana jin duk abinda yake faruwa sai dai

ba zata iya yin ko motsi ba dan allurar bacci

yayi mata da yake tana da karfin jini ya sanya

ba tayi baccin ba. Tana ji tana gani katon

Iyamirin likitan nan ya biya bukatarsa amman

bata da halin hanawa, sai da ya kammala dan

kansa sannan ya dauko kayan aiki ya fara yi

mata. Sanda ya tura karafunan da zai dagargaza

abinda ke cikin nata ji tayi kamar ana zare mata

rai dan azaba, amman ko motsi ba zata iya yi

ba, sai dai hawaye dake zubowa ta gefen

idonta. Shi kuwa katon kedarin ko a jikinsa, ya

sanya karfan ya burge abun da ke cikin kamar

yanda ake markada kayan miya, bayan ya gama

watso abinda ke cikin ya kuma sanya wani ruwa

mai magani ya fara wanke cikin, sai da ya

wanke shi tas sannan ya maida mata kafafunta

yanda suke. Azaba dai ta sha ta, hawaye sai da

ya jika gefen da take kwance, ajiyar zuciya kawai

take yi amman ba zata taba mantawa da

wannan azabar a rayuwarta ba har abada. Yayi

mata wasu allurai na rage radadi sannan ya tura

ta can dakin hutu, cikin dan kankanin lokaci duk

kamanninta sun sauya saboda tsabar azaba.

Sala ta isa kanta da sauri tana mata sannu

sanda aka sanar da ita an gama, sai a lokacin ta

sami bakin magana ta fashe da kuka mai ciwo.

Wannan Ma'aikaciyar jinyar ce ta shigo dakin

hannunta rike da magani ta yiwa Abu sannu

sannan ta ce, "Likita ya gama da ita babu komai

a cikinta dan haka nan da awa uku idan ta huta

zaku iya tafiyarku, sai dai Hajiya daga yau sai ku

daina sakaci ciki yana shigar 'ya'yanku, don ke

Zainabu yanzu kin ji azabar da kika sha, dan

haka gwara ku dinga rigakafi kafin ciki ya shiga."

Sala ta dube ta da mamaki tana fadin, "Dakta

yanzu akwai wani abu dake hana daukar ciki

dama?" Ma'aikaciyar jinyar ta ce, "Eh akwai

mana, allura ce da magani har da kulle mahaifa

ana yi, in mace tayi daya daga cikinsu ba zata

sami ciki ba." Sala ta amshe cike da mamaki a

fuskarta, "Oh! Ni Salamatu ki ji wata fasaha,

rashin sani yafi dare duhu, da mun sani da

yaushe za mu sha wannan wahalar? Kin ji fa

Abula." (Sala ba ta ji tsoron Allah ko yin nadama

da abin da ya sami Abu ba, ba ta hankalta da

isharar da Allah ya nuna musu ba har take

neman hanyar da diyar ta ba za ta kuma yin ciki

ba, hakan ke nuna daman tashin hankalin da

suka shiga na samun ciki ne ba na gyaruwar

zuciya ba. Menene amfanin irin wadannan

iyaye? Kai, tir! Da su, domin su ne tushen

gurbacewar al'umma a ganina).

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ma'aikaciyar jinyar ta yi ta musu bayani, Sala

tana ta girgiza kai cike da mamaki, ita kam Abu

ita kadai ta san abunda take ji, sai dai tana jin

dadin bayanin likitar, ta kuma yi alkawarin ba

zata kuma samun ciki ba, yanzu ma rashin sani

ne. "To, yanzu likita a ina ake samun maganin

tsarin iyalin?" Sala ta tambaya. Sister din tace,

"Ai ana samu a duk asibitocin da kika je, sai dai

su asibitin gwamnati suna da ka'ida, basu

bayarwa sai matan aure, ko kuma idan kinje da

mijinki, har wasu masu zaman kan nasu ma

akwai wadanda ba sa zubar da ciki saboda

rakiyar asara, amman kin ga mu nan babu

ruwanmu za ki iya zuwa ki siya ko a chemist

dina." Sala ta ce, "Kai likita mun gode da

wannan kirkin naki." Ta yi murmushu ta ce,

"Suna na Sister Asibi, ko da wata rana kunzo

neman wani taimako,ta yi musu kwatancen

gidanta ta tafi ta barsu cike da murna, dan

itama tana da nata kason, don ka'idar asibitin

nasu idan mara lafiya ya zo ta sanadiyyar ka

kana da kaso mai tsoka musamman ma zubar

da ciki. Karfe biyar suka koma gida, shatar mota

ma suka dauka, da kyar Abu take iya taka

kafarta, san da suka isa jama'a na ta kallonsu,

masu zargi na yi masu addu'a kuma na yi, da

haka suka shige gida. Da suka isa daki suka baje

Sala ta dauko naman da suka yo tsaraba da shi

suna ci suna mayar da yanda aka yi suna ta

dariya ta abunda suka dinga yi jiya har da

kukansu. Ita kuma Abu sai baiwa Sala labarin

irin azabar da tasha take yi. Sala ta ce, "Ai an

gama, da kin samu kwarin jikinki zamu koma su

yi miki allurar da suka ce din, tunda dai duniyar

ta sauya gwara mu fizgi rabonmu muma, dan

na san idan kika murje kika goge, Alhazan birni

ne zasu yo miki caaa, tun da dai kina da kyau

da sura mai daukar hankali." Suka kwashe da

dariya har da shewa. Sadiku da duk maganar da

suke yi a cikin kunnansa ya daga labulan ransa

a bace hankalinsa a tsananin tashe, nan fa suka

yi tsamo-tsamo kamar wadanda aka watsawa

ruwa, cikinsu aka rasa ko mai tari balle su yi

magana, dan daga ganin fuskarsa sun san ya ji

duk abin da suka ce. Shaf! sun manta basu rufe

kofa ba, ko su yi a hankali ba. Da kyar ya iya

bude bakinsa cike da takaici ya ce, "Sala yanzu

tsakaninki da Mahaliccinki Ubangijin da ya

halicce ki kun kyauta abinda kuka yi? ko tsoron

Abu ta rasa ranta a gurin zubar da cikin nan

baki yi ba, daman tun ranar da na ga kin gigice

na yi zargin wani abu na shirin faruwa koma ya

faru, na yi iyakacin iyawata a kan tarbiyyar

yarinyar nan har kina jin haushina. Sannan

wannan abu da ya faru bai zame muku ishara

ba sai ma kara kangarewa da Abu ta yi? Shin

Sala kun san sanda zaku mutu? Ba kwa tsoron

Allah? Ba kwa tunanin Ubangiji ya dauki

rayuwarku kuna cikin wannan mummunan

sabon? Da nayi niyyar fita daga harkarku sai dai

ya zama dole na tunatar da ku gaskiya koda

kuwa zaku tsireni ne nauyi ne a kaina, tunda shi

Babanmu ya gaza. Sannan ke Abu azabar da

kika sha ba zata zame miki ishara ba? dan bata

kai kashi daya cikin dubu ta azabar lahira ba,

dan haka ki hankalta ki san..." "Kai! Ya isa haka

malam." Sala ta katse shi. Ta dora da cewar,

"Ka wani saka mu a gaba kana mana surutu

mara ma'ana sai kace wasu 'ya'yanka, idan

aljannar ta ubanka ce ka hana mu shiga, sannan

idan kace za'a yiwa Abu azaba dan tayi ciki shi

kuma mai saka ido sana'ar da babu uwa babu

riba yaya za'a yi dashi? Ka saka mana ido

kamar wani Ubanmu, wallahi ba dan a tsakar

dakin nan na haife ka ba da asibiti ne sai nace

musanya miki kai aka yi, dan baka kaunarmu ka

tsane mu, to ta Allah ba taka ba dan saka ido."

Yayi wani murmushi mai cike da takaici yace,

"Sala ina kaunarku a matsayin wadanda bani da

kamarsu a duniya, wannan ya sanya ni nake

gaya muku gaskiya, dan wanda baya kaunarka

bai gaya maka gaskiya.......Malam ka ishe mu

haka, ba'a san gaskiyar taka soko shashasha,

har ni zaka ce zaka gayawa gaskiya? Tun kafin a

haife ka na san gaskiya. Bace min da gani tun

ban daga maka nono kabi duniya ba." Ya saki

labulen jikinsa sanyi kalau zuciyarsa tana suya.

Abu tace, "Sala kiyi masa kashedi kada yaje yayi

ta fadi a duniya yace nayi cikin shege mun

zubar." "Hakane fa." Sala ta fadi da sauri ta

daga labulan tana fadin, "To, saura naji wannan

maganar a bakin wani, ranka zaiyi mummunan

baci Sa'idini, sarkin sa-ido." Shi dai baice komai

ba don ko juyawa ma baiyi ba ya cigaba da

tafiyarsa ransa yana cigaba da suya. Sala kuwa

cigaba tayi da balbalin bala'inta tana fadin,

"Haka kawai an saka wa yarinya ido dan anga

Allah ya bata kirar da zataji dadin rayuwarta,

dan haka babu ruwan uban kowa koda sadaka

take bada kanta balle ma da makudan kudi

ne." (Ubangiji ya shirya mu har wadanda suka

bata, mu gane gaskiya kuma ya bamu ikon

binta, Amin).Ku ziyarci blog dinmu domin

karanta Littatafai masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

KANO: 15/5/2003

Kyakykyawar budurwa fara tas, sai dai bata cika

tsawo ba dan haka koda yaushe zaka ganta da

dogon takalmi,ba ta da gashi mai tsaho amman

akwai yawan gyara shi, tana da dogon hanci

wanda ya fito da ainihin kyawunta, bakinta

kuwa irin dan karamin nan ne kamar na yara,

sai idanuwanta wadanda ke ruda 'yan maza duk

sanda ta kalle su da shi saboda girmansu da

kuma kyansu, har wata digon zaiba ce a ciki, ga

ta da dan karan yanga da iya kwalliya,

wadannan abubuwan suka hadu suka maida ta

irin matan da zamani ke yayi. Tana sanye da

riga da siket na atamfa wanda ya matse ta

tsam-tsam daga kugunta, 'yar kibarta ta yi cas-

cas cikin kayan, fatar jikinta na da laushi tamkar

'yar jaririya, tana sanye da katon takalmi mai

kama da tsani don tsaho, fuskar nan tasha ado

irin na wayayyu, sai ta shafa jambaki kalar

kayan jikinta, bata sanya kwalli ba, sai dai ta

zizara jagira cikin idon nata, gashin girarta ya

kwanta luf-luf gwanin sha'awa, daga yanayin

shigarta da tafiyarta kadai ya isa ya yaudaro

'yan maza dan duk inda Zainabu ta bi sai an

kalle ta. Kayanta kalar katuwar jakarta ce, ga

wani kamshi da ke tashi a jikinta kamar kana

kantin sai da turare, tana da matukar fizgar

hankalin duk wanda ya dora idonsa a kanta,

sannan hatsabibiya ce ta fannin mu'amala,

domin ta kware ainun a iyar tafiyar da namiji

don haka duk mutumin da ya kusance ta ko sau

guda ne sai ya kidima a kanta. Ta fito daga

dakin nata bakinta sanye da wata alawa mai

tsananin kamshi tana tsotsa, Sala dake shan

kayan marmari wanda Zainabun ta kawo musu

tsaraba jiya da ta dawo daga Abuja, zaune ta

bararraje a tsakar gida tana kallon Zainabu, duk

da ranta a bace yake sai da ta yi murmushi dan

ganin yanda Zainabu taci uwar kwalliya, tana

dubanta da fara'a tana fadin, "A'a 'yar albarka

kin fito? Sannu da fitowa." Zainabu ta yamutsa

fuska gami da amsawa. Salan tace, "Jiya na so

muyi maganar yarinyar nan sai naga kin dawo a

gajiye, ga shi kun yo dare....." "Wani Abu ne

kuma ya faruwa?" Zainabu ta katse Sala din

(don yanzu ta tashi daga Abu ta koma

Zainabunta). "A'a a kan dai maganar nan ce ta

kwanaki ta matsiyacin yaron nan da ta nacewa,

shi kuma wannan yaron dan saka ido yana ziga

ta kamar shine uwarta, to yanzu wai iyayansu za

su aiko, ni kam sam ba na son tayi auren nan,

me take da shi? Ita ko sha'awarki bata yi, koda

yake ko ba tayi auran ba ma bata da wani

amfani tunda ta ki yarda ta ciwo arziki, dan

haka sai kiga shegiyar tayi sati biyu bata da ko

kwandala, sai dai idan an yi musu albashi ya

sanmata, wanda duka albashin nasa bai wuce

kudin takalmi da jakarki ba."Zainabu ta yamutsa

fuska tana fadin, "Sala ki barta ta yi auran nan

taji, in dai Maza ne ai zata gane kurenta, banza

ana neman a samo mata mai maiko tun da ta

nace sai tayi auren tana ki tana wani rawar kai,

ki rabu da ita kawai, dan rannan baki ga wani

abokin Alhaji T.J ba yanda ya mato a kanta, har

na nuna masa ya rabu da ita kanwata ce, sai ya

rantse mini da cewar shi da aure yake sonta,

amman babu yanda banyi ba yarinyar nan ba

taki ko kula shi, haka ya hakura ya kyale ta don

ya yi-ya yi ya gaji, shi da mata ke sonsa kamar

me? Shine fa kwanaki ya bani kujerar Makka

guda ukun nan da na kai ku ke da Baba."

"La'ilaha Illallahu, kai amman yarinyar nan bata

da rabo, arziki yana kiranta tsiya tana janye ta,

ina ga fa matsa mata zamuyi ta aure shi kawai

ko ta tsiya ko ta dadi." "A'a Sala ina ruwanmu?

Ita ce fa zata zauna da mijinta, sannan yanzu

idan muka hada su haushinmu zata dinga ji,

gwara mu kyale ta ta yi hankali, ni bari na wuce

kada na yi latti, kin san nace miki muna da bikin

cikar Asma shekara ashirin da biyar, zan je mu

fara shiri saboda shi na dawo jiya." "To-to, Allah

ya kiyaye, zaki dauki shatar mota ne?" Zainabu

tace, "A'a Alhaji Danlami sabon kudi yana waje

yana jirana." "To Allah ya tsare, ya bada sa'a."

Tace, "Amin." Gami da ficewa. Yana cikin mota

zaune ya sha manyan kaya kamar wani

mutumin arziki, tunda ta fito ya zuba mata ido

tamkar maye, ita kuma tana tafiya tana rangaji

tamkar ganyen bishiyar da iska ke kadawa,

tafiyar dake dauke hankalin 'yan maza. Tana

isowa ya bude mata kofa yana murmushi gami

da fadin, "Barka da warhaka Hajiya, irin wannan

shanyar haka har na bushe?" Tayi wata

mayaudariyar dariya ta jan hankali, tace, "Lallai

kam, to waye ya gayyace ka? Ina ga kaine fa ka

sakani fitar nan, da ka gaji ba sai ka tafi abinka

ba na huta." Ya kanne ido yana mata wani kallo

yace, "Ni na isa? ai kina da tsayawa mutum a rai

Zainabu, kusan duk aikin da nake fa idan kika

fado mini bani samun sauran sukuni muddin

ban iso gareki na ji duminki ba, ko matana na

kasa zama da su kamar ke, anya Zainabu kina

tausaya mini kuwa? Dan Allah ki daure ki aure

ni mana ko na sami nutsuwa." Tayi masa wani

malalacin kallo ba tare da tace komai ba ta

kauda kai gefe, ya kuma rudewa ya matsa kusa

da ita jikinsa har rawa yake yi. Ta kuma

matsawa gefe tana harararsa gami da fadin,

"Haba Malam, ko dai dan bunsuru ne ka

saurara mu bar kofar gidan ubana da kuma

tsakiyar ranar nan, duk iskancina ban taba yi a

kofar gidan ubana dan ina mutunta gidan." Ya

ja baya yana shafa haba yace, "Kai Zainabu kina

juya ni wallahi kamar waina, amman babu

komai zan matsa lamba har ki zama mallakina."

Ya tada motar yana ta sumbatunsa, ita kuma

murmushi kawai take yi, ta gama kashe shi da

kissarta da kallonta gami da tsananin kamshinta.

Sai da ya kaita wani babban gidansa na

shakatawa suka gama watsewarsu sannan ya

cika mata jaka da kudi dan ya san Zainabu mai

tsada ce, sannan suka dauki hanyar gidan

Asma, har lokacin yana ta sumbatu a kanta da

yaba kyanta da iya mu'amalarta. Sanda suka isa

gidan Asma ya kwantar da murya kamar wani

abun tausayi ya ce, "Yaya dai Hajiya, karfe nawa

zan dawo na dauke ki?"

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta galla masa harara tana fadin, "Kai fa tsiyata

da kai kenan ba ka iya cin kwan makauniya ba,

to ai ni din ba matarka bace da zaka hana ni

sakewa." Ta kammala maganar tana murguda

baki. Ya lankwasar da kai yana fadin, "Tuba

nake Hajiya, kece din sai a hankali, amman na

hakura sai gobe zan bullo." Ta daga kafadarta

gami da fadin, "Kai dai ka sani, sautun

mahaukaciya." Ta fice daga motar. Har tayi nisa

yana kallonta kamar ya kuma binta yake ji.

Zainabu macece hatsabibiya mai tsayawa

mutum a ransa, ta san yadda take iya tafiyar da

shi kamar wacce ta karanci abun, ya rasa

abinda ya sanya matansa ba sa masa irin yanda

Zainabu ke masa, da zai sami mai masa kamar

Zainabu cikin matansa ai da babu abinda zai

sanya shi yawo ana wulakanta shi, dan yana ga

idan ya sami Zainabu ta aure shi yana jin ko

kofar gida sai anyi da gaske zai fita, da kyar ya

samu ya iya jan motarsa ya bar kofar gidan. Ta

shiga gidan da ihu babu ko sallama, Asma dake

zaune daga ita sai gajeren wando da 'yar rigar

mama tana busa tabar wiwi tana wani lumshe

ido, ta mike tana ihu suka rungume juna. Asma

ta ce, "Shegiyar, wallahi na yi zaton ba zaki zo

ba, da kin kwafsa mini." Suka zauna suna mai

da numfashi, sannan tace, "Haba Hajiyata ai kin

san dole na zo, yaushe zan yarda chasun nan ya

wuce ni?" Asma ta fashe da dariya tana fadin,

"Dan akuyan naki ne na san shi da jaraba ko

bunsuru ya rufa masa asiri, na san da kyar zai

barki ki dawo, ko da yake Zainabun akwai iya

iskanci, har tsoro nake ji idan na ga saurayina

yana kallonki, don har ta kafa sigina kike yiwa

namiji,suka fashe da dariya gami da tafawa.

Zainabu tace, "Wai ni yaya shirye-shiryen fatin

ne? Ina fata kin tanadar mana komai?" Asma ta

tabe baki tace, "Kin san akwai maza 'ya'yan

wahala wadanda iyayensu da matansu suka

sallama mana, sun gama komai. Senator Tanko

ya kama mana hotel dama komai da za'a ci a

gurin, sai dai shegen wai ba zai zo ba dan kada

'yan adawa su sami abin da zasu soke shi a

kafafan watsa labarai. Oho, ni ko a jikina dan

daman bana son ganin wannan mummunar

fuskar tasa wacce zata hana samari 'yan bana

bakwai isowa jikina mu sha minti, dan kin san

sun kwana biyu sai a hankali, dan wallahi duk

sanda na kalli fuskarsa sai ta tuno mini da wani

tsohon goggon biri." Suka kuma fashewa da

dariya gami da tafawa. Zainabu ta zira hannu

cikin jakarta da dauko kwalbar Shandy ta kama

tsotsa, ta jingina da kujera tana lumshe idanuwa

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Asma ta kalle ta gami da fadin, "Ke 'yar duniya

babu ko dandano? Kin kafa kai kina tsotsar

abun ki?" Zainabu ta dube ta da ido daya dayan

kuma ta kanne shi, "Malama kada ki matsa mini

ki bar ni na yi dif! Ina ce tadda ke na yi kina

busa tabar mulki kin mini tayi ne?" Ta kuma

matsawa gabanta tana kwantar da kai tace,

"Haba tawan ki yiwa Allah ki ba ni na kurba ko

sau daya ne, na kwana biyu ban tsotsa shandy

ba" "Amshi 'yar jaraba ba zaki bar ni na sha ta

ishe ni ba." Ta mika mata kwalbar giyar, sannan

ta dauko nadaddiyar tabar shaidan a jakarta ta

bata wuta, hayaki ya fara gauraye dakin, Asma

ta sakar musu kidan Bob Marley nan fa suka

tashi suna cashewa suna wani gantsare-

gantsare, daman Zainabu gwana ce gurin rawa.

Misalin karfe goma na dare motoci suka fara

sauke mata a kofar hotel din da zasu yi fatin,

sun ci uwar kwalliya sai dai babu wacce zaka

kalla kace diyar Hausawa ce balle Musulmai, don

duk irin shigar turawa suka yi, daga masu

gajerun wanduna sai masu damammnun kaya

da 'yan kananan wanduna. Dakin taron kuwa

kida ne kawai ke tashi kamar zai tsaga daki,

kowacce da saurayinta take shigowa. Shigowar

Zainabu da Asma ne ya sanya kallo ya koma

kansu, dan komai iri daya suka sanya, wani

gajeren siket suka sanya wanda ya tsaya

iyakacin gwiwarsu ya matse su sosai yana ta

kyalli, sai wata 'yar yalolowar riga mai rawa ta

zauna das a jikinsu, takalmansu har gwiwarsu,

sai gyaran gashi da suka yi, duk da Zainabu

bata fiye sanya gashi ba yau ta sanya, fuskar

nan ta dauki kwalliya sai wani kamshi ke tashi

daga jikinsu. Mai jawabi sai kwarara musu kirari

yake, "'Yan mata adon gari, 'yan matan da

duniya ke yayi, Asma ta Zainabu manyan Bebis

da duniya ke yayi, kun girmi kwailayen Kano,

kuna ruda mazan kano." Aka fashe da ihu.

Zainabu sarkin rawa sai ta hau taka rawa dan

daman yanda ka san mazari haka take, gaba

daya sai ta dauke hankalin mazan dake gurin

dan Zainabu daban ce, irin matan nan ne masu

kamar fitila duk inda suka je sai sun haske shi,

nan fa maza suka yi caa a kanta, ana ta mata

liki amman miskilar ko a jikinta dan babu wanda

ta baiwa fuska.Zainabu daban ce ko a duniyar

barikin tasu, dan idan namiji bai yi mata ba duk

kudinsa bai isa ko kallo a gurinta ba, tana jan

zaranta yanda take so, dan ta san Allah yayi

mata kirar daukar hankalin maza, an sha dambe

da yanke-yanke a kanta, ko waye kai idan zaka

kwana dubu kana mata magana ba za ta tanka

maka ba, musamman idan tayi dif da Shandy

dinta. Sai karfe hudu na dare aka tashi daga

fatin nasu, an rakashe an cashe an sha kayan

maye kala-kala, Zainabu kam tangadi take yi

dan ta cake da yawa, ganin haka ya sanya Asma

ta sanya ta a motarta suka nufi gidanta don ta

san 'yan gidansu basu san tana shan giya da

wiwi ba sai dai tana fita yawon gantalinta. Sai da

gari ya waye sannan ta dawo hayyacinta, bayan

ta farka ta shiga ta yi wanka ta yi ramuwar

Sallar dake kanta sannan ta yi shirin tafiya gida.

Tana sanye da doguwar riga ta atamfa super da

aka ciwa mutunci, dinkin ya kama ta tsam daga

kirjinta yayin da yayi baza daga kasa, hannun

rigar tamkar shimi yake, ta yafa karamin gyale,

sai tsireren takalminta mai kama da tsani, ta

sanya zobba na gwal kirar dubai, da wani dogon

dan kunne a kunnenta, kamshin dake daga

jikinta tamkar kamfanin turare dan Zainabu

ma'abociyar son kamshi ce. A adaidaita Sahu ta

sauka dan bata nemi dan rakiya ba, duk yawan

mazan da ta dauki hankalinsu daran jiya dake

neman shiga, ta shiga gidan nasu da sallama

muryarta tamkar sarewa. Sala da ke zaune ta

mike tana hangame baki gami da fadin, "A'a

diyar albarka har kun dawo? Har an gama fatin

kenan." (Kuji wannan Uwa fa, diya budurwa ta

kwana ta hantse a titi amman wai mahaifiyarta

tace har ta dawo? Hmmm, su Sala ko sai yaushe

za鈥檃 dawo kan hanya).

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta zauna jabar bisa tabarmar da Sala din ke kai

tana fadin, "Mun dawo Sala, wallahi fatin yayi

kyau.Yaya na ji gidan shiru ne ko duk ba sa

nan?" Sala ta tabe baki gami da fadin, "Yaran

dai basa nan amman Karimatu na nan, dan jiya

nayi wa yaron nan tas mai hure mata kunne,

nace kada ya kuma zuwar mini gida shine take

ta kumbure-kumbure, motarsa fa daya ce tal

Abula, mai na sama ya ci balle ya baiwa na

kasa, mtsw!" Ta yi tsaki cike da takaici. Zainabu

ta yi kwafa kana tace, "Ke ma Sala da son bata

ranki kike a banza, ina ce tun jiya mun gama

maganar, tunda ta dage sai shi ai sai ki rabu da

ita ta aure shi, kowa rai yayi ma dadi baya ga

mai shi ne." Sala tace, "Ai shike nan, kina ji ke

Karimatu sai ki gaya masa ya turo iyayen nasa

ko ma huta da naci kamar maye." Sala dai

kamar tsoron Zainabu take ko dan tana kawo

mata kudi? Duk hukuncin da ta yanke a gidan

babu wanda ya isa ya ja da shi koda yayanta

kuwa. Karimatu dake daki tana karatun Kur'ani

dan ta sami sassauci a zuciyarta saboda kwana

tayi tana kuka saboda yanda Sala ta bada ita ga

saurayin, wanda ko da ya aure ta ba zai kuma

ganin darajar Mahaifiyarta ba, tayi hamdala ga

Allah gami da yin Sujjada tana kara gode masa,

don Allah ya sani tana son Abbas kamar ranta,

shima yana masifar son ta, soyayya suke mai

tsafta, sai dai tun da ta kawo shi gidan da

sunan wanda zata aura Sala take aibata shi,

daman yaya lafiyar kura balle ta yi hauka? Don

daman basa shiri sam da Sala, dan tun tana

yarinya taso ta yi hali irin na Abu amman ita

Allah ya tsare ta shine fa Sala ta tsangwame ta

kamar ba diyarta ba, ko da harkar karatunta

Sadiku ne ke tallafa mata da komai,Don zamu

iya cewa kusan su kadai ne shiryayyu a gida,

dan kannanta dake bin ta maza duk sun fara

shaye-shaye, Sadiku ya yi dasu har ya gaji don

yana tufka Sala na warwarewa ne, su kuma 'yan

kannansu mata kanana guda biyu suma tallan

suke yi, kusan hanyar da Zainabu tayi rayuwa

suke kai, sai dai karamarsu ce ta dauko halin

Karimatu da alama sai kuma autansu. Bayan

Karimatu ta gama godiya ga Allah ta dauko

wayarta da sauri duk da tana jin nauyin Abbas

din amman haka ta yi kiransa, bugu daya ya

dauka don tun jiya yake neman wayarta har ya

gaji ya hakura, ita kuma ta rufe ne saboda

nauyinsa da take ji don ma kada ya kira ta bata

san mai zata ce masa ba kuma.

Gaba dayansu suka yi shiru kowanne yana jin

nauyin dan uwansa ita kam har da kunya ma.

Shine ya daure ya ce, "Yaya dai Karimatu, tun

jiya nake neman wayarki a kulle, har hankalina

ya tashi na yi zaton ko kin daina daga waya ta

ma." Tayi wata doguwar ajiyar zuciya kana tace,

"Abbas kunyarka nake ji ban san da idon da zan

kalle ka ba, don na sani Sala jiya tayi maka cin

mutuncin da ina jin ba'a taba yi maka ba, sai

dai ba kai tayi wa ba illa ni, don Allah ka yi....."

Kuka ya kwace mata ya hana ta karasa maganar

tata. Ya kwantar da murya yana fadin, "Kin ga

Karimatu ki kwantar da hankalinki, na riga na

san halin Sala tuntuni na kuma ji na gani don

babu gudu babu ja da baya a son ki, na san tayi

haka ne dan na yi fushi na rabu da ke, ni kuwa

sai na ji ma yanzu na fara son ki, dan haka ki

kwantar da hankalinki mu yi batu a kan abinda

zai fishshe mu." Ta dan ji sanyi a ranta dan

haka ta sami kwarin gwiwar gaya masa abunda

ake ciki, na yanda Sala ta amince ya turo da

iyayensa, abin ya bashi mamaki sai ya ga kamar

mafarki yake yi don shekara nawa suna fama da

Sala, amman ace lokaci daya ta amince? Sai

Karimatu ta nuna masa kawai karfin addu'ar da

suke yi ne ya sanya hakan ta faru, ya amince

da lallai hakan ne dan haka ya dinga hamdala

ga Allah, daga karshe suka yi sallama cike da

farin ciki. Abbas kam jin sa yake kamar yafi

kowa farin cikin zai mallaki Karimatu, duk da

sanda ya fara nuna wa abokansa yana son

Karimatu sun kwabe shi dan suna cewar waye

bai san iskancin da yayarta Zainabu ke yi a

unguwar ba 鈥榢aruwar gida鈥� haka suke kiranta a

bayan idonta, yace shi kam ya ji ya gani dan ko

Allah bai kama wani da laifin wani, Tunda kowa

ya san halin Zainabu da na Karima ba daya ne

ba, don babu wanda zai ce gida daya suka taso

ma, sai dai kamar su da tayi daya baya ga

Zainabu gajera ce amman ba can ba, sannan

tana da dan jiki yayin da Karimatun ta kasance

doguwa siririya, Allah ya kuma sanya iyayensa

masu ilmi ne kuma wayayyu dan haka suka

goya masa baya gami da yi masa addu'a ta gari,

wacce ita ce ke dawainiya da shi a duk inda ya

sanya gabansa.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

*************

Ba da wani dadewa aka sanya rana ba wata uku

ne kacal, sai dai tun da aka sanya ranar Sala ke

mitar bata da shi, dan bata ga abinda Karimatu

ta yi da zata mata kayan daki ba, dan ko sanda

suka yi talla banda kwantai babu abun da take

yi, balle yanzu da bata da ko na sayen kwalli.

Shi kuwa Baba Abbakar ba'a ta tasa, don kudin

da aka kawo na zance ma so ya yi ya cinye sai

da Sadiku ya yi masa jan ido, shine ya ji haushi

shima yake fadin, "Ya ga mai yin gadon." Shi dai

Sadiku kallon su kawai yake yi yana ta kokarin

ya rufawa 'yar uwarsa asiri. Biki ya rage saura

kwana uku Sadiku ya shigo da kayansa na

katako irin wanda ake yayi, da kujerunsa masa

kyau da tsada. Maimakon Sala ta yi murna da

sanya albarka sai ta hau tabe baki tana fadin,

"Eh! Da yake Karimatu ce kayi mata kaya masu

tsada, da Abula ce da ka tsana da ko tsinke ba

zaka yi mata ba." Sadiku yayi murmushi ya ce,

"Sala kenan, da Zainabu da Karimatu duk 'yan

uwana ne, ita ma ta daina iskancin ta fito da

miji kin ga idan ban mata wanda ya fi wannan

ba." Zainabu da ke zaune tana yankan kumba

tana zaune bisa darduma ta doka tsalle tana

tafa hannu ta ce, "Wallahi karya ne, na fi karfin

na tsaya ka yi mini kayan daki, dan yanda kake

aiki nima ina yi, da kake ce mini 'yar iska ai na

gode Allah tunda ba na neman mata, ka duba

ka ga yanda yanzu mata ke neman....." "Dalla

can, rufe mana baki marar kunya, ki yi abinda

duk kika ga dama ai rayuwarki ce, na san komai

dadewa zaki gane kurenki, Karima dai Allah ya

rufa mata asiri, ba ta yi irin halinki ba, dan haka

kuka tsane ta gidan nan....." "Ahaf! Ahaf!, Wato

dai ni kake gayawa magana ko?" Sala ta amshe

da saurinta, "To ka ga fita daga gidan nan tun

ban bata maka rai ba, duka yaushe ka fara

samun kudin? Kafin ka fara rike dubu daya

Abula ta rike dubu goma, kuma duka albashin

naka nawa ne? Abin da ko kudin takalmi da

jakarta ba su kai ba? Ka da ka kuma furta mini

ko kala, fice ka bani guri tun ranka bai kai ga

baci ba." Ya gallawa Zainabu harara wacce ta

rama sannan ya fice, yana yiwa Karimatu

magana, "Ki lura da yanda za'a shiga da kayan

kada fentin su ya goge." Tana daga can zaune

gefen kicin tana yanka Salad da zasu ci abincin

rana da shi tace masa "To." kawai. Ai sai bala'in

Sala ya koma kanta, ina wuta ta jefa ta, zagi ta

uwa ta uba da gori tana fadin, "Dadin abin dai

da abincin da Abula ke ciyar da ke kika rayu ke

da shi din." Ita kam ko kala bata ce ba, dan

idan da sabo ta saba, ita kam aikin ta ma ta

cigaba da yi ko a jikinta. Zainabu ta ce, "Haba

Sala, ki yi shiru haka mana ka da muyi bakin

kunya." Ai kuwa tamkar ta ji wahayi daga

mala'ika ta yi shiru. Ita dai Karimatu dariya ma

abin ya bata ta ce, "Idan ka ki sharar masallaci

kayi ta rumfar kasuwa ai."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

CALIFONIA: 30/9/2003

Yana tsaye jikin window hannuwansa nannade a

kirjinsa, dogo ne ba sosai ba yana da dan jiki

irin na maza majiya karfi, jikin nasa a murde

yake, yana da kyau irin na gogaggun maza da

suka san duniya, bai cika fari ba amman ba

zaka sanya shi a layin bakake ba, yana da irin

gashin nan da samari ke ajiyewa a fuskarsu, ya

iya daukar kwalliya irin ta namijin duniya. Bai

fiye hayaniya ba, miskili ne ga wanda bai san

shaidancinsa ba, ma'abocin farin jini ga shan

yabo ga jama'a saboda faran-faran din sa da

sakin hannu (kyauta), amman a badini mutum

ne mai tsananin son holewa, sai dai yana da

matukar taka tsantsan don yana gudun bacin

ran iyayensa. Ransa a cunkushe yake, lokuta da

dama idan abin ya motsa masa sai ya ji kamar

ya zama tsuntsu ya bar garin, ya dade yana

tausar zuciyarsa a kan abinda yake gani ba

komai ba ne, sai dai yanzu abin yana neman fin

karfinsa da shallake iyakacin dauriyarsa. Abin da

ya faru dashi tsahon wasu shekaru da yake

ganin a can baya mara amfani da muhimmanci,

har idan ya tuno abin yakan kira shi da tsuntsu

daga sama gasashshe, sai dai tunda ya yi nisa

abin ya fara damunsa, da farko yakan ga kamar

abin nan ne da Hausawa kan kira 'Sabo tirken

wawa' sai dai da yaga duk kwanan duniya abin

yana kuma tsiro a zuciyarsa har ya kai matsayin

da ya cika zuciyar tasa babu sauran wani gurbi

na tirjiya da dauriya. Ya yi kwafa a karo da

dama ya juyo yana kallon kayataccen falonsa

wanda ya sha kayan alatu kamar ba za'a mutu

ba, ya isa dan gurbin shan lemo, ya zuba lemo

a kofi ya hada da shandy ya cilla kankara ya

daga ya shanye wai ko zai ji sanyi a zuciyarsa,

sai dai har lokacin abin yana nan, sai yaga

kamar ma karuwa ya yi saboda mutuwa da

jikinsa ya yi sabon tunani ya shige shi. "Me ya

sa haka ne?" Yayi wa kansa tambaya, wadda

tsawon lokaci yake yiwa kansa, ya dauko taba ya

kunna ta ya bata wuta a hankali yana lumshe

idanuwansa amman har lokacin bai ji sanyi a

ransa ba. Ya jawo takardar da ya bayar da irinta

a Ofis dinsu jiya ta barin aiki yana kuma

dubawa, wayarsa ta fara kara ya dauka da kyar

yake magana, abinda aka gaya masa kamar kara

hasala shi aka yi don haka da zafin rai yake

magana cikin harshen nasara. "Eh! Ni ne na

rubuta dan na yanke shawarar barin aikin nan

don jama'ar kasata na bukatar gudummawa ta,

sannan iyaye na sun damu da su ganni,haba

Mustafa kada ka yi mana haka, idan albashinka

ne ya maka kadan zamu iya kara maka mu." A

ransa yace, "A wannan karon babu wanda zai

hana ni tafiya dan zan biyawa raina bukatarsa

ne, dan idan na cigaba da zama a haka zan iya

asarar farin ciki da kwanciyar hankalina."

Amman a fili sai yace, "Oga kuyi hakuri ba zan

iya janye kudirina ba a wannan karon na tafiya

ko da nawa zaku kara mini, nayi muku alkawarin

dai duk sanda na sami dama zan dawo muku

gaba daya, amman yanzu hankalina ya yi

kasata." Dan Baturen da suke maganar ya sare,

dan 'dan zaman da suka yi sun san Mustafa

mutum ne kaifi daya, idan ya sanya abu a

gabansa babu wanda ya isa ya hana shi

aiwatarwa, dan haka ma ya rike aikinsa da

gaskiya da amana, dan haka suke masifar ji

dashi, shine zai bare inji ba tare da ya tsaya ya

kalli 'yar takardar bayani ba ya maida ya hada

shi kuma ya tashi tsaf, ba kamar sauran

Turawan da sai sun duba ba a rubuce, ya dai

daure yace, "Shike nan Mustafa muna maka

fatan alkhairi, sai mun hadu a Ofis din. Ya yi

ajiyar zuciya ya ce, "Shike nan Oga sai mun

hadun." Ya kashe wayar tasa gami da lumshe

idanuwansa, wata rayuwa ta dinga bijiro masa

wacce ta wuce shekarun baya wacce a da can

yake daukarta shirme, sai dai yanzu ya tabbatar

ita ce rayuwarsa mai cike da ainihin farin ciki da

sanya shi nishadi da dariya, sai dai duk sanda

yake tunanin wani abin mai fadar da gaba kan

fado masa, sai dai yana addu'ar Allah kada ya

tabbatar da wancan abinda ke fadar masa da

gaban. Washegari jikinsa babu kwari ya fito daga

Ofis din nasu dan alhinin rabuwa da abokan

aiki, sai dai daman haka rayuwa ta gada dole

wata rana za'a rabu, walau ta gurin zama ko

aiki ko kuma ta har abada ma (mutuwa). Daga

nan kai tsaye gurin neman Visa ya nufa ta

komawa kasarsa ta haihuwa wacce rabonsa da

ita tsahon shekaru.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

KANO-NIGERIA: 15/10/2003.

Bayan ya sauka ya dauki shatar mota tun daga

filin jirgi har gidan Mahaifinsa. Maigadi ne ya

fara ganinsa don haka ya zuro da gudu cike da

murna da doki yana fadin, "A'a Alhaji Mustafa

yau kake tafe? Marhabun lale, sannu da zuwa."

Mustafa yana murmushi yake amsawa ya

sallami mai tasin, sannan ya dubi maigadin ya

ce, "Malam Bala a shigar da kayan ko?" Daga

nan ya shige cikin gidan kai tsaye, ya yi sa'a

kuwa jama'ar gidan duk suna nan domin la'asar

ce. Da Mominsa ya fara cin karo tana zaune a

falo tana karatun jaridar Leadership Hausa, tana

sanye da (Medicated glass), ya shiga da sallama

bakinsa a washe. Ta daga kai cike da tsananin

mamaki, suna hada ido dai ta tabbatar da lallai

shine, ta mike cike da murna tana fadin,

"Babana! Da gaske kai ne ka iso garin ba tare da

ka sanar da mu ba?" Ya isa gaban Mahaifiyar

tasa cike da farin cikin ganin Mahaifiyar tasa don

ya kwana da dama bai ganta ba, dan ma wani

lokacin ta kan bi Mahaifinsa suje ganinsa, don

shi tunda ya tafi bai kuma waigo wa Nigeria ba,

wanda shi wai nan dabara ya yi dan ya manta

da abinda ke damunsa a ransa, a cewarsa idan

ya yi nisa da abin zai samu sassauci koma ya

manta gaba daya, sai dai yanzu ya gano

dabararsa ba za ta kai shi ko'ina ba. Ya ce,

"Momi barka da gida, na same ku lafiya?"

"Lafiya kalau muke sai dai mamakin dawowarka

yanzu babu sanarwa, Allah dai ya sanya lafiya."

"Momi Lafiya kalau wallahi, na so kwarai na ba

ku mamaki ne dan na sha sanya rana zan zo

amman bana zuwa, dan haka nace wannan

karon sai dai ku gan ni kwatsam." "Lallai kam ka

ba mu mamakin, bari na je na samo maka dan

abin tabawa." Ta mike ta nufi kicin din gidan.

Tana isa kicin ta tadda 'yan matanta suna ta

faman kacaniyar girkin dare, ta ce, "Albishirin

ku?" Gaba daya suka ce, "Goro Momi." "To

yayanku ya dawo yanzun nan, yana falo dan

haka sai a hado masa abin motsa baki kafin a

kammala girki." Gaba daya suka yi falon da

gudu suna murna suna ihu, sun ma manta da

abinda aka ce su dauka, ta yi murmushi sannan

ta dauka ta tafi da shi.

Yana ganinsu ya ce, "Lallai 'yan matan Momi an

girma, kalle ku don Allah." Suka kalli juna suna

dariya.

Ya so tun daran ya fita ya fara aiwatar da

abinda ya kawo shi garin, sai dai gajiya ta hana

shi dan haka dole ya hakura har gari ya waye.

Washegari ya shirya cikin manyan kaya wadanda

suka kara fito da kimarsa da martabarsa, duk

da zaman da yayi kasar waje bai daina sanya

manyan kaya ba, musamman yakan aiko a yi

masa, idan ya sanya turawan suyi ta sha'awarsa

musamman idan zai je gidan biki ko wani fati,

yawaita sanya manyan kayansa tun yana nan

gida ya kara masa martaba a idanun jama'a har

suke ganinsa wani mai hankali da tsantseni.

Motar Babansa ya hau dan na shi yayo Odarsu

ba su karaso ba, yana tafe yana jin wakar Bob

Marley don mutuminsa ne, sai kada kai yake

cike da nishadi, yau ce ranar da zai cikawa

ransa burinsa, yau ne zai je ga Zainabu Abunsa

karo na biyu da sunan soyayya, idan ya tuno

abinda ya faru a baya sai ya dinga jin wani farin

ciki da nishadi. Sai dai abinda ke fadar masa fa

gaba idan ya tuna anya Zainabun tasa ba tayi

aure ba? Idan aka ce Zainabunsa ta yi aure

kuwa lallai yana cikin tashin hankali da rashin

nutsuwa, dan ya gano yanzu itace rayuwarsa,

sai yake ganin nisan gidan nasu da yake su sun

tashi sun koma cikin G.R.A. Ya isa kofar gidan

yayi fakin yana kallon gidan, kusan yanda ya san

shi haka yake yanzu, sai dai wasu sauye-sauye

da aka samu, mutane ne a kofar gidan can da

can suna cikin kwalliya. Gabansa ya tsananta da

faduwa da ya ga Sadiku sanye da manyan kaya

da gani sababbi ne sai daukar ido suke ya zama

babban mutum mai kamala, sai fito da abinci

yake shi da wasu cikin farantai. Ya zubawa

Sadiku ido har lokacin gabansa na faduwa, ya

zuge gilas din motar a hankali yana kara kallon

jama'ar dake kai kawo kofar gidan. Can ya

hango wani maroki yabi Sadiku yana masa kirari

ya sanya hannu a cikin aljihu ya dauko kudi ya

ba shi, da alama yana cikin farin ciki, daga

ganin alamun babu ko tambaya aure aka daura

sai dai bai san ko na waye ba, ya yafito wani

yaro da yazo wucewa ta kusa da shi yana kallon

motar. Yaron ya karasa yana kallonsa a alamun

rashin sani a fuskar yaron, "Dan Allah yaro

daurin auren wa aka yi a kofar gidan ne?" Ya

nuna kofar gidan da hannunsa. Yaron yace,

"Daurin auren wannan din nan aka yi 'yar gayun

nan mai kwalliya ni na manta sunan ta ma." Ya

rasa gane wacce yaron ke nufi sai dai

hankalinsa yayi kololuwar tashi don yana ganin

kawai Zainabun sa ce ma, ammai sai yayi ta

maza ya ce da yaron, "Na gode ka ji abokina, un

go wannan." Ya mika masa Naira dari biyu,

yaron ya amsa cike da murna ya tafi.

Yana cikin mota yana ta sake-saken yanda zai

yi, shin kundumbala zai yi ya futo ya tambayi

wacce aka daurawa aure ko kuma hakura zai yi

ya koma.Tunaninsa ya tsaya cak sanda ya hango

wasu hadaddun mata sun nufo shi, dayar

doguwa ce sosai fara amman da alama ta dan

kara da na kanti, sai dayar gajera ce amman ba

can ba, tana da wani irin kyau na daukar

hankali, daga shigar ta har tafiyarta sun yi

matukar burge shi, yana hango su suna doso

shi, sai yaga mara tsahon da yawa fuskarta tana

masa gizo kamar ya santa. Suka zo suka gota shi

suna taku sannu a hankali, gaba daya sun tafi

da hankalinsa, wani irin kamshi ya ji ya bigi

hancinsa san da suka wuce, ya lumshe idonsa

saboda kamshin da ya ji

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

"Anti Abu ga wayarki in ji Sala ta ce kin manta

ta." Wata 'yar yarinya da ta fallo da gudu ce ke

fadin haka. Mustafa ya bude idonsa da sauri.

Wacce tafi tafiya da hankalinsa yaga an mikawa

wayar, ta amsa ta sanya a jaka, yayi wata

sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da rudani yana

fadi a ransa, "Yanzu wannan Abu ce da ya sani

a can baya 'yar mitsitsiya da ko kwalliya bata iya

ba, 'yar tallan abinci da ya wayar da ita, ita ce

ta zama wata irin tauraruwar mata ta wuce

yanda duk yake tunanin zai gan ta?" "Ya Salam"

Ya fadi a fili. Ko da wasa ko a mafarki bai taba

zaton Abunsa zata yi irin wannan wayewar ba,

ya daukarwa kansa zai dawo Kano na Nigeria ya

auri Zainabu, ba don tsananin kyau, ilmi ko

dukiya ba sai dai dan tsananin sonta kawai da

Allah ya jarabce shi, sai dai abun mamaki da

tsoro sai ya ga Zainabu ta sauya ta wuce

iyakacin tunaninsa gaba daya. Tashin motar da

yaga sun dosa ne ya farkar da shi daga dogon

tunanin da ya fada, ya tada ta shi ya bi bayan

ta sun sai dai ina sun riga sun yi masa nisa, dan

haka ko hangosu baya iya yi, dan hala dole ya

dauki hanyar komawa gidan su dan ya ji kiran

wayar Dadin su. Karfe takwas na dare ya kuma

dawowa kofar gidan su Zainabu, don yinin ranar

haka ya yi shi sukuku, ya dinga tuno yanda ya

ga Zainabu na tafiya da kamshinta na yanzu,

musamman yau Babansa bayan sun gaisa sai

yayi masa maganar aure dan sun jima suna

masa maganar yana cewa suyi hakuri har yanzu

baiga wacce ta yi masa ba ne. Cikin wata shigar

ya iso ya yi kyau matuka, shaddar har wani kara

take yi saboda tsabar bugu da ta sha, sai dai ya

tarar da cincirindon mata a kofar gidan, sai

motoci ne ke diban su, sai dai addu'arsa Allah

ya sanya ba Zainabunsa aka daurawa aure za'a

kai dakin miji ba. Yayi fakin ya fito ya jingina da

motar yana kallon matan dake kaiwa da

komowa cikin hasken fitilar da ya haske kofar

gidan. Har ya gama kalle-kallen sa bai hango

Zainabu ba, wata budurwa mai shegen yangar

tsiya da take ta wucewa ta gaban sa ko zai taya

ya daure ya yafito, babu musu ta nufe shi kanta

ya kuma fasuwa don ga dan gayu mai

hadaddiyar mota yayi kiran ta zata buda gurin

'yan matan gurin, ta nufe shi tana kara salon

tafiya tana wani girgiza, duk da ba wani kyau ta

cika ba amman daga gani tana ji da kanta.

"Barka da yamma adon gari." Ya fadi da wata

mayaudariyar muryarsa, yayi mata kuri da

idanuwansa wadanda ke ruda 'yan mata. Tayi

wani far da idon ta da kyar kamar bata son

magana ta ce, "Yauwa ya kake?" Yayi dan

murmushi yace, "Kalau nake. Na ce banga

amarya Abu ba ko har sun wuce ne?" Ya shirya

hakan ne don ya tabbatar da gaskiyar abin. Ta

yi masa wani kallo mai cike da mamaki sannan

ta ce, "Hala dai mantuwa ka yi naji kana cewa

Abu, dan dai na san Karimatu ce amarya ba

Abu ba, yaushe Abu zata yi aure ita da ta

daurewa bariki gindi?" Ta karasa maganar tata

tana yatsina fuska da alamun kishi a muryarta

jin ya ambaci Zainabu don ta zaci cewa zai yi

yana son ta. Ransa yayi wani wasai cike da farin

ciki da yaji ba Zainabunsa ce aka yiwa aure ba,

duk da bai ji dadin abinda ta ce din ba amman

sai ya dake ya ce, "Kai na shafa'a ne, yi hakuri

Karimatu nake so na ce miki na manta." Ta dan

saki ranta tace, "Babu damuwa idan gurin fatin

za ka mu zo ka rage mana hanya mana ni da

kawayena?" "Me zai hana, ki shigo na kai ki

mana." Ya yi haka ne dan yayi amfani da

wannan damar ya ga Abun a can.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347



Zaharaddeen Shomar

whatsapp 08168575100




Idan zuciya tagyaru 1-04

Posted by ANaM Dorayi on 01:13 PM, 30-Jan-16

Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU

_______IDAN ZUCIYA TA GYARU_____

_____________ Na

_______Fauziyya D Sulaiman______

Dadi ya cika ta ta yafito kawayenta da ke can

tsaye suna kallon su da mamaki da sha'awar ina

ma ace su yace yana so. Ta shiga motar tana

fadin, "Ga kawaye na nan zaka rage musu

hanya." Yace, "Su shigo mana." Dadi ya kuma cika

ta tace musu, "Ku shiga baya mana." Ta umurce

su sanda suka iso jikin motar. Ta so ya dan ja ta

da hira sanda suka hau kan kwalta don ta kara

budawa a gurin kawayen nata, sai dai shi kaset

kawai ya kunnan na mutumin na sa, yana gyada

kai zuciyarsa na can ga Zainabu Abu yana

kwadayin yanda zai ganta ko da sau daya ne. A

haka suka isa har inda za'a gabatar da fatin,

hotel ne hadadde, tun daga waje za ka san fatin

na manya ne dan manyan motoci ne a gurin.

Sisters night aka rubuta da kyalli baro-baro

wanda ke haske a gurin. Fatin Abu ce ta shirya

shin don taya kanwarta murnar biki, Malam ne

ya daura auren sannan 'ya'yansa suka shige

gaba gurin bikin dan duk yawancinsu suna auran

masu hali ne suna tukinsu, don haka a motocinsu

aka dinga dauko mata ma. Bayan yayi fakin

sauran 'yan matan suka fice da saurin su, ita

kuwa 'yar gwallin ta tsaya tana wani yauki da

fari, har zai ce ta fita mana sai ya tuna yanda

take masa wani yauki da yanga. Dan haka yayi

murmushi ya ce, "Ga shi har zamu rabu ban san

sunan Hajiyar ba." Tayi dariya mai cike da nishadi

ta ce, "Sunan ai ba wani na ku zo mu gani ba ne,

sunana Salimat." Yace, "Lallai nice name, suna

mai dadi." Ya zaro kudi a aljihunsa ya mika mata

ya ce, "Ga wannan kya yi liki kafin na shigo zan

ga wani abokin da bai karaso ba, idan na shigo

zan gan ki." Yayi mata haka ne dan ta rabu da

shi. Ta yi wani fari da idonta don ta yi zaton da

gaske yake musamman da taga ya bata kudi

masu yawa, dan haka ta ce, "Babu damuwa,

amman fa ban ji sunanka ba." Da sauri yace,

"Sunana Mustafa." Don ya gaji da ganin ta ya

matsu ta bashi guri ya shiga ya ga rabin ransa.

Ta ce, "Shi kenan na gode Mustafa sai ka shigo."

Ta fita tana wata yanga. Ya bita da kallo har ta

kule sannan ya yi tsaki yana fadin, "Ki ga mace

kamar an zana one amman sai wani firirita da

iyayi take, ita wannan ko a kafa aka daura mini

ita ai zan yage ta na zura da gudu ne." Ya kuma

gyara fakin ya kwantar da kujera gami da kara

sautin wakar da yake ji, ya kunna taba yana sha

yana kada kai kamar kadangare, ta cikin hasken

gurin yake karewa matan da ke shige da fice

kallo. Ya dan jima a haka sannan ya bude motar

ya fice ya kukkullo ko ina, sannan ya nufi inda ya

ji kida yana tashi na Mahmud Nagudu don shine

yake taya su shakatawa. Gurin ya tsaru matuka,

mawakin ya dage yana ta rera wakarsa cikin

tattausan lafazi, amarya da ango suna tsakiyar

makeken filin suna takawa a hankali, yana daga

inda yake tsaye ya gane Karimatu dan ya santa

tun tana karama, sai dai daman can ita tafi

Zainabu hankali da nutsuwa. Ya sakale hannuwa

a kirji yana ta waige-waige, bai kula da matan

dake ta kallon sa wasu ma har sukan yi masa

sigina. Can ya hangota ta shiga filin rawar tana

sanye da wani irin material golden anyi masa

wani matsiyacin dinki da ya kama jikin ta tsaf

kamar a jikin ta aka kera shi, ta daura wani nadi

mai kyalli shima, wani dan ziririn gyale a kafadar

ta, sai wani katon takalmi da ta sanya mai kama

da tsani dan tsaho, ta yi kyau matuka, ta zaro

kudi daga jakar dake hannunta ta fara watsa

musu.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Tana yi itama tana taka rawa a hankali, da yake

gwana ce gurin rawa sai abun ya kayatar da

jama'a da dama. Sai mawakin ya koma kanta da

waka, "An gaishe ki yayar amarya karkada tsiwar

ango, magajiyar uwa, manyan matan da duniya

ke yayinsu, Zainabu tauraruwar zamani mai

haske duniya, kin dade kina tashe har gobe ke ce

tauraruwa farin wata sha kallo." Kanta ya kuma

fasuwa ta dinga zaro kudi tana zuba masa, Asma

ta shigo filin da irin kayan Zainabun komai da

komai, ita ma tana shiga ta hau yiwa Zainabu

likin kudin. Ango ya kama hannun amaryar suka

fice yana dariya yana fadin, "Kada ta gaji ta isa

haka rawar." Suna fita ya kuma mai da kidan

kansu yana wakesu su kuwa sai rawa suke yi ta

burgewa. Mustafa dake gefe a tsaye bai san

sanda ya kutsa filin rawar ba don Zainabu ta

tsumo shi da yawa, yana shiga ya zura hannu a

aljihu ya dinga debo daloli yana manna mata, ta

dinga dubansa da mamaki sai dai tana ganin

kamar gizo idonta ke mata ko kuma mai kama da

shi ne, amman da yake miskilar kanta ce sai ta

dake kawai ta yi kamar bata gane shi ba, sai da

ta gaji don kanta da rawar sannan ta fice daga

filin, yana ganin ta fita shima ya bi bayanta, duk

wanda ke shirin yiwa Zainabu liki sai jikinsu ya yi

sanyi dan sun ga mai liki da daloli, gurin ya

kacame da ihi da tafi na burgewa. Ita kam can

wani tebur ta nufa dake can baya da jama'a,

Asma ta bita da gudu har suka zauna. Asma ta

dube ta tana fadin, "Shegiyar ina kika sami

wannan hadadden gayen ga kyau kuma ga

'ya'yan banki? Ya yarfawa 'yan mazan gurin nan

wallahi." Zainabu tayi mata wani kallon banza

sannan ta sanya hannu cikin jakarta ta dauko

tabar shaidan ta kunna ta, ta jingina da kujera

tana fesar da hayakin ranta ya dauki zafi. Lallai

ko a duhu taga Mustafa ba zata manta shi ba,

shine mutumin da ya fara lalata mata rayuwarta

kuma ya gudu ya barta a lokacin da take matukar

bukatarsa, ba ta taba son wani mutum kamar

Mustafa ba sanda ya nuna mata kulawa da

soyayyar da sai daga baya ta gane tsananin

yaudara ce, sannan a yanzu bata da wanda ta

tsana a mutane sama da shi din. Asma kam sai

maganar Mustafa take mata ita kuma zafi take ji

a ranta dan haka ta kulle idonta kam har Asma

din ta gaji ta yi shiru, a tunaninta ko ta bar gurin

ne don haka ta bude idon ta. Tsaye ta gan shi a

kansu ya nannade hannuwansa a kirji yana

kallonsu, babu wani abu da ya sauya na daga

kamanninsa sai kiba da haske da ya kara, yana

nan har yanzu a dan gayunsa, yanda ya kura

mata ido itama haka ta kura masa har lokacin

tana cigaba da shan tabarta ta shaidan, Asma ta

dinga kallonta tana kallon sa ta gaza gane abun

da suke nufi, ta dai tabbatar da lallai yau

kawarta ta hadu da daidai ita.

Ya jawo kujera dake kusa da su ya zauna sannan

ya jawo jakarta dake ajiya, ba ta ko motsa ba

balle ta yi masa wani abu, ya dauko tabar

shaidan shima ya kunnata, a hankali ya dinga

fesar da hayakin sannan ya kai dubansa ga

Zainabu wacce ke wurga masa wata uwar harara

kamar idon ta zai fadi kasa. Yayi wani murmushi

wanda ya kuma futo da haibarsa ya ce, "Zainabu

Abun Musty!" Ta ja tsaki kana ta mike a fusace ta

rike kugu bayan ta kashe tabar ta ce, "Malam

lafiya dai ko? Don ni ban sanka ba ko don ka ga

na kyale ka kayi mini liki kake neman zakewa da

yawa?" Ya yi murmushi ya ce, "Zainabu kenan,

kina tsammani ko a buge kike zan yadda baki

gane ni ba? Na san na yi laifi amman na san zaki

yafe mini dan Mustafa naki ne." "Ka ga Malam ni

fa ban sanka ba, ban san daga inda ka futo ba,

ka je can ka nemi wacce kaka nema, idan kuma

buguwa ka yi kwakwalwarka ke gaya maka

karyane to ka bari ka nutsu ka dawo hayyacin ka

sai ka nemi wacce kake nema." Yayi dariya sosai

wacce ta kara kular da Zainabu sannan ya dora

da cewar, "Haba Zainabu, ai kinfi kowa sanin giya

ko taba basa bugar dani, sai dai ke farin shiga

balle yanzu ma na daina shan giya dan haka ya

dace kema ki daina." Ta doki tebur gami da

fadin, "Karya kake yi wallahi karamin kwaro, ka

dube ni da kyau ban yi maka kama da wacce ka

sani ba a da, dan kuma baka bar gurin nan ba

zan sanya yanzu a yi maka rashin mutunci

wallahi." Asma dake kallon su ta zunguri Zainabu

wai tayi shiru, amman kamar ta kuma zigata sai

cewa ta yi, "Dalla Malama ki kyale ni, ba irin

wadannan ake saurarawa ba, wannan da kike

gani cikakken dan iska ne da bai dace a dagawa

kafa ba." Maganar tayi masa zafi a ransa amman

da ya tabbatar dai ta gane shi din tsiya ce kawai

sai yayi murmushi ya ce, "Ni dai na sani Zainabu

ko giyar wake kika sha ba zaki manta dani ba,

dan haka na dawo rayuwar ki bada wasa ba, ina

fatan zaki manta da duk abinda ya faru a baya."

"Wallahi karyarka ta sha karya, ka dube ni da

kyau, sama da kasa zaka ga ba Abun da ka sani

da can bace, wannan Zainabu ce, dan haka ka ja

tsummar rayuwarka ka bar nan gurin idan ba

haka ba zan rotsa maka kanka da kwabar nan."

Ta nuna masa wata kwalba da ke kan tebur din

da suke zaune ta lemo.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ya yi murmushi gami da gyara zama har lokacin

yana zukar tabar sa yana kallonta babu ko

kyaftawa. Ta san halinsa mutum ne mara tsoro

sannan duk abin da ya sanya kansa babu mai

hana shi, dan haka tasan babu wata barazanar

ta da zata bashi tsoro, idan har ta yadda suka

cigaba da zama guri daya komai zai iya faruwa,

dan haka ta ga barin gurin kawai shine mafita a

gare ta, dan haka ta dauki Jakarta ta bar gurin

tana huci. Ya bita da kallo har ta bace wa

ganinsa, yayi murmushi sannan ya dawo da

dubansa ga Asma wacce ta zuba masa ido kawai

tana kallonsa, ta san lallai kawarta ta debo mai

zafi dan barazanar da takewa maza suna tsorata

shi tayi masa amman ko gezau bai yi ba. Ya yi

dariya ya ce, "Kawarmu yaya gida?" Ta yi wata

wawiyar ajiyar zuciya dan maganar ta zo mata a

bazata, sannan ta ce, "Lafiya kalau." "Kinga

yanda muka yi da kawarki ko? Na san halin

Zainabu muguwar 'yar buyagi ce zata iya yin

abinda ya fi haka ma, sai dai ban damu ba ko

dar ma banji ba, don na gano tsagwaron sona a

cikin idon Abu" Ya nuna kirjinsa da yatsansa yana

cigaba da fadin, "Ni ne mutum na farko da ya

san wacece Zainabu, duk wani iskanci da Zainabu

ke takama da shi nine na koyar da ita, ba wai ina

alfahari da haka bane, a'a zuwa yanzu ma duk

sanda na tina ni ne silar lalacewarta na kan ji

takaici kuma na ji haushin kaina, don haka nayi

alkawari yanda na zama sanadiyyar lalacewar

rayuwar Zainabu zan kuma zama jagora gurin

ganin na shiryar da ita." Ya manta Allah shi ne ke

shiryar da wanda ya so, ga shi ya yi hasashe ba

tare da ya nemi yardar Allah ba. "Amman ki bar

ni da Zainabu ni da ita kar ta san kar ne, na san

na yi mata laifi amman zata yafe mini komai

dadewa tunda nine mutum na farko da ta fara so

a rayuwarta." Gaba daya ya gama burge Asma

har ma take ganin inama ace itace ke da wannan

hadaddan gayen, amman ta san tunda Zainabu

ce a gabansa ba zai kalli kowa da daraja ba

musamman da yace shine masoyin ta na farko,

dan haka da wuya ya kalli wata mace da daraja.

Don haka ta share wannan tunanin ma a ranta

dan ta san ba mai yuwuwa bane, yanda kuma

suke da Zainabu ma ba zata iya yi mata zagon

kasa ba, dan haka ta fara jan sa da hira ta

Zainabu kawai, ya ma manta da Zainabu 'yar

buyagi ya zauna suna ta hirarsu har aka tashi

daga fatin, sannan ya nufi gurin Zainabu wacce

ke ta hada kayan su na fatin da ta san nasu ne,

ya isa gabanta yana dariya ya ce, "Yaya dai uwar

dakina ko za'a taya ni kwana ne yau dan ina tare

da gajiya wallahi na yo doguwar tafiya mai nisa."

Ba ta kalli inda yake bama balle ya sanya ran

zata kula shi, ya cigaba da surutunsa don a

ganinsa dole zata bi shi don yanda dare yayi

kuma kowa ya watse a gurin har amarya da ango

dole ta bishi dan babu wanda zai dauke ta, don

haka nema ya share guri ya zauna yana ta cigaba

da surutunsa. Can wata dankareriyar mota ta

kutso kai harabar da suke zaune, Zainabu ta

mike tsaye gami da kallonsa sama da kasa ta ja

tsaki sannan ta ce, "Malam ina gargadinka karo

na biyu da ka fita daga rayuwar Zainabu, ka

kuma gane yanzu Zainabu nake ba Abu ba."

Tana gama fadin haka ta nufi motar da salon

tafiyarta na yanga da jan hankalin maza. Ransa

ya yi masifar baci har yana ganin ba zai dauki

wannan raini wayon ba, don yana da masifar

kishin tsiya. Don haka ya nufi motar da sauri cike

da bacin rai, amman ina tuni ta riga ta shiga,

bayan ta zauna ta kalle shi yana wani huci kamar

tsohon zaki, ta yi wata mayaudariyar dariya mai

kularwa sannan ta rufe murfin motar, yana kallo

suka fice a guje, ya ji kamar ya rufa musu baya a

guje amman ina sun yi masa nisa. Ya doki iska

yana huci gami da fadin, "Ba zan taba daukar

wannan rainin hankalin ba wallahi, zamu gauraya

ne." Ku ji fa karfin hali namiji da suna Hajara

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

. Suna daukar hanya DPM ya kalle ta yana wani

lasar lebe yace, "Yaya dai gimbiya za'a taya ni

kwanan ne mu wuce gidan shakatawa ta?" Ta

galla masa harara ta ce, "Au abinda kake yiwa

kenan shiya sanya ka nace daman zaka dawo ka

dauke ni? Tsaya ka saukeni dan ka san kuna da

yawa 'yan iskan garin zan sami mai kai ni gida,

dan ni na gaji babu wani abinda zan iya yi." Ya

ce, "Kai Zainabu ke fa 'yar buyagi ce wallahi,

daga dan tayi sai jidali, shi kenan na hakura muje

kawai." Bata kuma cewa komai ba ta jingina da

kujera ta lumshe idonta tana tuno abinda ya

faru, wani ciwo mai zafi da ya dade yana damun

zuciyarta ya fara taso mata, tsigar jikinta ta fara

tashi yar-yar kamar mai jin sanyi "Mustafa!

Mustafa!" Ta fadi a cikin ranta gami da girgiza

kai. Lallai ta sani abu ne gingimeme a gabanta,

dan Mustafa da ban ne a cikin maza a gurinta,

kuma tayi wa kanta alkawarin a can baya duk

sanda Allah ya hada su ko a hanya ne sai tayi

masa rashin mutunci, amman sai ga shi a

gabanta amman ta kasa aiwatar da komai a

kansa, sai ma wani abu da yake neman ya dawo

mata da shi. Har suka isa kofar gidan su bata san

sun iso ba don tayi nisa a tunani, sai da ya kai

hannunsa yana shafarta tamkar wani maye

sannan ta farga, ta yunkura da masifa ta

hambare hannunsa gami da dalla masa harara.

Ya kama sosa keya yana dariya ya ce, "Tuba nake

yi, ai na zaci ko kinyi bacci ne, Allah Zainabu sam

ba na gajiya da ke, ke din ta daban ce, kamshin

ki kawai kan tayar mini da hanlaki, yanzu ji yanda

kamshin ki ya cika motar nan tamkar ni ban

sanya turare ba, wai ni da wane turare ki ke

amfani ne ma?" Ta yamutsa fuska ta ce, "Su

kuma wadanda ka ajiye a gidan fa meye amfanin

su? Dan haka wallahi nake tsoron aure, sai ku

baro matan ku a gida kuzo kuna hurewa

kadangarun bariki kunne da naira, yanzu haka

matan ka suna can suna jiranka kana nan kana

gantali da wannan daran." "Ke rabu da

wadannan matan, babu wani abu da suka iya sai

jarababban kishi da shegen bin Malaman Banza,

burin su kawai su tara kudi, da kun hau gado su

yi maka wani sumbukaka kamar jakai, babu wani

salo da suka iya wai su kunya, sau da dama idan

nayi niyyar daina bin matan titi na zauna da su

idan suka gaza gamsar da ni sai kiga na dawo

ruwa, balle ke Zainbau daban ce wallahi kin san

kan da namiji matuka, ko makarantar kika yi ne

na kawo matan nawa ki koyar da su?" Ta yi

dariya sannan ta ce, "Matsalarka ce wannan,

wata kila kai ma da laifinka, kana shigar musu

gida ne tamkar mala'ikan tsaron wuta babu

fara'a shi ya sanya suke kasa sakin jikinsu, ni dai

yau duk jarabar ka nan gani nan bari, ka ga fitata

ma.

Ta bude kofar ta fice tana fadin, "Asuba ta gari."

Ya bita da kallo har ta shige cikin gidan na su,

yayi tsaki da damuwa gamida kifa kansa bisa

sitiyarin motar tasa, Zainabu ta zame masa

masifa a rayuwarsa, muguwar hatsabibiya ce,

muddin ka yarda ta lasa maka zumar ta a baki to

lallai ka shiga uku, idan ba kana da kwararriyar

mace mai iya salo-salo ba sai ka ji ka rainawa

matan ka.Ya figi motar tasa ya bar kofar gidan

tamkar mai tsere da iska, ita kuwa tana isa gida

ta tadda gidan shiru kowa ya gaji da kacaniya ya

yi bacci, ta shiga ban daki ta dauro alwala ta

sanya kayan ta na sallah, ta shimfida sallayar ta

wacce ke ta kamshin turare ta haye ta fara

gabatar da Sallah. Idan ka ga yanda take

nutsuwa idan tana Sallah zaka rantse idan aka

sanya mata hannu a baki ba zata iya cizawa ba,

dan duk iskancin ta bata wasa da Sallah, tunda ta

taba jin wa'azi akan Sallah da irin azabar da

mara yinta ke sha ta nutsu da yin sallah, wannan

shine kadai abinda zaka daga a rayuwar Zainabu

ta yi tutiya da shi. Mu dai bi ta a sannu don

duniya ai takaitacciya ce.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Mustafa kam da kyar ya iya komawa gida, ya

dade a dakin sa yana sintiri hannuwansa sakale a

bayansa, wani masifaffan kishi da zafin Zainabu

ke addabarsa, lallai yau da yana da hali da sai

yayi wa Zainabu da wanda ya dauketa dan

banzan duka, gaskiya ba zai iya lamuntar wannan

halin nata ba na kula kowa, lallai dole ta daina

harka da kowa indai tana son kanta da zaman

lafiya, ya dade yana sintiri da kyar ya iya

daurewa ya dan kishingida har bacci ya dauke

shi. Da safe ya so yaje amman ya san da kyar zai

sami ganin ta don hidimar bikin da sukeyi dan ya

ji suna cewa yau din ne yinin biki, dan haka ya

yanke shawarar sai dare sannan zai shiga. Karfe

tara na dare ya isa gidan nasu ya rasa ta yanda

zai yi ya ganta, sai can ya sami wata budurwa

yace ta kira masa ita. Ta dube shi ta ce, "Ai Anti

Abu tun da aka yi Sallar Magariba suka fice da

kawarta Asma." Ya yi mata godiya ya koma motar

sa ya zauna, Allah ya sanya jiya ya amshi lambar

wayar Asma din, dan haka bayan ya shiga motar

ya zauna ya fara neman layin Asma din. Da

yanga ta dauka a yauki take maganar sanda taji

kira, "Hello wa ke magana?" Ya yi ajiyar zuciya

sannan ya ce, "Mustafa ne, don Allah ina son ki

bani kwatancen inda kuke, amman kada ki sanar

da kawarki yanzu zan zo." Ta dubi Zainabu da ke

zaune tana zukar tabar shaidan ta dora kafa

daya kan daya, tunda suka iso gidan abun da

take yi kenan dan cewa ta yi ba zata je kai

amarya ba don ranta a bace yake su wuce gidan

ta ta sami hutu, amman tun da suka karaso din

ta gaza tabuka komai baya ga busa taba, dan

haka ta riga ta gano kawar tata tunanin Mustafa

ne kawai don bata taba dora hankalin ta ga

namiji kamar haka ba. Sai ta ce, "Shike nan zan

yo maka text." Daga haka suka yi sallama. Minti

talatin da biyar kacal ya kwashe ya iso gidan ya

danna kararrawar kofa, Asma ta mike da sauri

don ta san Mustafa ne. Zainabu ta bita da kallo

ta ja tsaki tana fadin, "Banza, kin gayyato mana

wani kwarton ko? Ni da nazo dan na huta zaku

dame ni, daman tunda naji kina magana kasa-

kasa a waya na san jarabarki ta motsa." Bata ce

mata komai ba sai dariya kawai da tayi ta nufi

kofar, yana tsaye sanye da kananan kaya, wando

ne na jeans bulu da shet fara tas mai taswirar

birnin London, da silifas na fata a kafarsa dan

gasken, sai agogo na azurfa da wani kwalelen

zobe shima na azurfar, ya yi kyau matuka. Suna

hada ido da Asma ta yi ajiyar zuciya sai taga yau

yafi kyau ma fiye da jiya, dan ta kuma yadda irin

gogaggun mazan nan ne ma, ta kwantar da

murya tana fadin, "Yallabai barka da isowa." Ya yi

murmushi gami da fadin, "Yauwa kawarmu ya

gida?" Tana amsawa ta bashi hanya ya wuce ciki,

sannan ta kulle. 'Yar buyagin tashi tana zaune

tana ta busa hayakinta bata ko kalli inda suke ba

balle ma ta gane waye ba. Ita ma Asma tana

shigowa kiran wayar Alhaji Buba ya shigo wayar

ta, yace ga direba nan ya turo su taho, dan shi

baya zuwa da kansa dan kada masu ganin sa da

daraja su ganshi girma ya fadi, dan haka sai dai

duk sanda ya bukace ta ya turo direbansa a kaita

can gidan sa ta kwana, dan haka dakin ta ta

wuce ta hado 'yan kayanta. Har ya isa kusa da

ita ya zauna bata san ya zo ba, dan tabar

shaidan din ta fara gaya mata karya, ta jingina

da kujera ta lumshe idanuwanta tabar tana

tsakanin hannunta.A hankali ya zare tabar dake

tsakanin hannunta, kamar wacce ya tsikarawa

allura ta bude idonta firgigit ta ware manyan

idanuwanta a kansa suka yi ido hudu, sai ta yi

zaton ko gizo yake mata kamar yanda yake mata

tun dazu. dan haka ta mai da idanuwanta ta

lumshe wai ta daina ganin gizon sa, sannan ta kai

tabar ta bakin ta da zummar ta kuma zuka,

amman sai taji wayam babu komai, ta bude

idonta da sauri a kansa, shine din dai da gaske

yana taya ta shan tabar tata. Haushi da takaici

ya cika ta tama rasa yaya za tayi masa, amman

ta san ba kowa ne yayi mata wannan iskancin ba

illah Asma, dan haka ta mike da bala'inta ta nufi

dakin kwanan Asma din, sai gata sun ci karo a

hanya, ta ci uwar kwalliya sai kamshi take zubawa

rataye da jaka a jikin ta. Ta rike kugu tana

harararta, ita dai Asma dariya ta sanya sannan ta

nufi Mustafa ta cilla masa makullin tana fadi cikin

harshen turanci "Take care, good night." "Wai

Asma wannan wane irin iskanci ne?" Zainabu ta

tambaya a kule. Asma ta daga kafada alamar Oho

sannan ta fice da saurinta tana dariya. Ta kulu

matuka, ta mai da kallonta ga Mustafa dake

kallonta yana murmushi ta ce, "Wai kai kana gani

kayi mini dabara ne, to ka sani a yanzu na girmi

wayo da dabararka, sanda ka yi kaci nasara dai

ka yi amman ban da yanzu, don haka sai ka

zauna ka jire mata gida." Ta dauki dan yalolon

gyalenta da jakarta ta nufi kofa. Sai dai ina ya

rigata dan mikewa yayi da azamarsa ya sanyawa

kofar makulli ya cilla makullin cikin aljihun

wandonsa. Ta yi tsaye tana kallonsa cike da

takaici da masifa, ya isa gaban ta ya tsaya cak ya

zira hannuwa cikin aljuhunsa ya ce, "Ga ni

gabanki kiyi mini hukunci daidai da laifina zan iya

dauka, amman ki yi mini alfarma ki daina gudu

na sannan ki dai na mini kallon kiyayyar nan dan

yana bakanta mini raina, domin Allah ya

jarabceni da son ki Zainabu, na gaza kallon

kowace mace da daraja a rayuwata, ki taimaka ki

yafe mini laifin da nayi miki nasan mai girma ne,

amman na yi ne ba da son raina ba." Ta rike

kugu tana kallonsa idanuwanta sun sauya launi

zuwa jawur, duk wannan farin da kyallin babu

saboda tsabar dacin ran da take ciki, tayi wani

yake wanda yafi kuka ciwo sannan tace, "Mustafa

na sanka tuntuni gwani ne kai gurin iya yaudara,

da irin wadannan kalaman ka sami nasara a

kaina a wancan lokacin hadi da kuruciya da

talauci da son kudi irin na Mahaifiya ta, sai dai ka

sani a yanzu Zainabu Abu ta wuce duk iyakacin

tunanun ka, baka da sauran kalmar da zaka iya

yaudararta da ita, baka da kudin da zaka iya

yaudararta dasu, domin ina mu'amala da

wadanda suka fika kama daga Gwabnoni sai

Sanatoci da Ministoci zuwa manyan 'yan kasuwa

dake rike da akalar Nigeria, dan haka yanzu ina

da kudi da farin jikin da nafi karfinka, a yanzu

idan na buga waya kadai duk abinda nake nema

zan samu, dan haka kaga baka da makamin da

zaka yaudari zuciyata a yanzu, duk da kana

takamar kaine silar fadawa ta a wannan muguwar

harkar da kullum nake tsinewa mara albarka."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ya kuma kwantar da murya ya ce, "Zainabu

tunda na diro garin nan na ganki nasan lallai ba

Abun da na sani da can bace, kuma ban dawo

rayuwarki dan na nuna miki kudi ko kyau ko

mukami ba, na zo ne da sunana Mustafa

masoyin ki nida zuciya ta kadai ina fata zaki yafe

mini abinda nayi miki can baya, sannan na mai

da matsayina da martaba ta a zuciyarki kamar

da, koma yafi haka don a yanzu Mustafa bai zo

da zummar fasikanci ba sai dai da zummar auran

Zainabu, domin a yanzu Ubangiji ya jarabi zuciyar

Mustafa da tsananin son Zainabu." Ta kalleshi a

lalace tamkar ta ga mahaukaci sabon kamu tace,

"So! So! Lallai ka hadu da mugun ciwo idan har

da gaske kake, balle na san karya kake yi, domin

kai mutum ne mai yaudara da karya, don haka

ka bude mini kofa na fice kawai, dan bana son ko

kallon fuskar ka domin kai ne mutumin da ya

sanya rayuwata a cikin fargaba da tashin hankali,

nasha azabar da har abada ba zan manta da ita

ba dan haka bude mini kofa na fita ko na daina

ganin azzalumar fuskarka!" Ta karasa maganar

tana hargowa. Ya hadiyi wani miyau mai daci,

maganganunta suna yi masa zafi da suya a cikin

zuciyarsa, dan haka da kyar ya iya buda baki

yace, "Zainabu ba zan bude miki kofar nan ba

har sai kin amince dani kin yarda yanzu ni ba

mayaudari ba ne..." "Ba zan taba yadda da kai

ba, ka bude mini kofa kawai na fita tun ban

maka rashin mutunci ba wallahi." Yana tsaye

kyam babu alamun zai ko motsa, ranta ya kuma

baci matuka, ta ga lallai da gaske yake dan haka

ta nufe shi da azama ta kama kokarin kwatar

makullin, nan fa suka fara kokawa amman ina

namijin duniya ne maji karfi dan haka ta gaza kai

hannunta balle ta iya dauka har karfinta ya kare,

tayi kokarin janye jikinta amman ya hana ta

hakan dan ta tuno masa da wani lokaci da wasu

al'amura da ke masa dadi da sanya shi nishadi a

duk sanda ya tuno. Tayi kokarin ta kwace amman

ta gaza sai ma wani abu da yake shirin jawo

mata dan shin din daban ne a zuciyarta ya san

kanta da yanda yake samun ta a sama, daman

haka yake so ta shiga jikinsa dole sai ta sakko

don dai shine ya santa ya san wacece ita, tayi luf

a faffadan kirjinsa mai kirar zaki ta gaza kasa

aiwatar da komai. Ya sami yanda yake so dan

haka yake da salon yaudarar da sace zuciya,

yanzu kam ya soma nasara a kanta dan tana jin

zafinsa a ranta amman tana matukar son sa, dan

haka komai ya kwance mata, Mustafa ne namiji

daya tal da idan tana tare da shi take manta

kowa, amman duk sanda take tare da wani sai ta

tuno shi da soyayyarsa, don haka bata da karfin

halin da zata kwaci kanta duk da haushinsa da

take ji, dan haka sai ta fashe da kuka kawai.

Jikinsa ya dauki rawa don yasan ba karamin abu

ke san ya Zainabu kuka ba, don tana da taurin

zuciya, dan haka cikin tausasa murya da rada ya

ce, "Zainabu don Allah ki yi hakuri ki yafe mini na

tuba....."."Me ya sanya ka tafi ka bar ni sanda

nake tsananin bukatar ka a rayuwa ta eye?" Ta

tambaye shi tana kuka. "Ki yi hakuri na san nayi

miki lafi, sai dai na yi miki alkawarin ba zan kuma

barinki ba har abada, ni din naki ne ke kadai, ba

zan iya kuma barinki ba Zainbau, ni kaina na sha

wuya, na yi miki alkawari." Ta yi luf ta gaza cewa

komai dan yayi mata yanda ba zata iya kuma

musa masa ba, anan suka baje suna shashancin

su. Sai karfe goma na safe suka sami sukunin

tashi suka fada wanka sannan suka yi sallah,

sannan Zainabu ta fada kicin da sauri don ta

samar musu abin da zasu karya dan yunwa suke

ji matuka. Ya bita kicin din tana sanye da wani

dan guntun siket, tare suka yi aikin suna ta

dariyarsu. San da suke karyawa yayi mata kuri da

ido yana kallo don Zainabu ta bashi mamaki, ta

wuce duk yanda ya santa, gaba daya ta gama

haukata shi a daran jiya, yanzu abu daya ya rage

masa ya auri Zainabunsa ya huta, kullum yana

manne a jikin ta shi kadai, sai ya ji wani kishi ya

kama shi mai tsanani dan bai san iyakacin adadin

mazan da ta yi mu'amala ba, sai yake da na

sanin tafiya da yayi ya bar ta, da shi kadai ya san

abarsa. Ita ma wani irin farin ciki take ji a cikin

zuciyarta, dan ta sha karo da maza kala-kala a

yawon iskancinta, amma bata ji wanda ya taba yi

mata dai-dai da Mustafa ba, don haka tana yin

bariki ne bawai dan dadi ba sai don neman abun

duniya(Allah ya kyauta), Zainabu hatsabibiya ce

ta kin karawa, dan haka maza da dama ke shan

wahala a kanta, yanzu ma mikewa tayi tsam ta

isa inda yake ta zauna cinyarsa, ta sakala

hannuwanta a wuyansa ta mika masa bakinta wai

ya sammata abin da yake taunawa (wainar kwai),

bai yi mata gardama ba dan shima gwani ne, dan

haka ya hada bakinsa da nata yana ciyar da ita

abinda ke bakinsa, da haka ta dinga kara susuta

shi tamkar wani karamin yaro ta mai da shi.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Bayan sun kammala cin abincin suka yi masauki a

doguwar kujera mai cin mutum uku. Ta kwanta

lamo a kirjin sa tana shafar sa tamkar mage,

cikin kunnensa ta ce, "Musty wai me ya sanya ka

tafi ka bar ni sanda nake tsaka da bukatarka?"

Yace, "Sai kin sanar da ni irin wahalar da kika ce

kin sha sannan zan sanar dake nima." Ta yi kwafa

tana fadin, "Labarina mai cike da abun tausayi ne

da takaici, domin daga ranar da na nemeka na

rasa na shiga tashin hankali, naje har gidanku

aka ce mini daman hutu kazo wai a kasar waje

kake karatu, na shiga tashin hankali da ciwo mara

misali, abu fa kamar wasa sai ciwo ya dinga yin

gaba, da farko na zaci ciwon soyayya ne, sai da

abu yaci tura aka gano ashe ciki ne dani....." "Ciki

da gaske Zainabu ko na wasa?" Ya tambaya da

sauri. Ta yi dariya tana fadin, "Da gaske Musty

wallahi ciki ne na gaske, kai ai munga tashin

hankali ni da Sala a wannan lokacin." "To yanzu

ina abun da kika haifa din?" Ya kuma tambaya.

Ta tabe baki tana fadin, "Cabdijam, ai tuni muka

zubar da shi." Ya dafe kai yana fadin, "Ya salam,

ai sam ban san kina da ciki ba, har na ji ina son

abuna wallahi Zainabu." Ta warware masa duk

abin da ya faru sannan ta dora da cewar, "Bayan

mun gama da wannan muna murna mun dawo

gida da kwanaki kuma sai ciwon ciki ya balle mini

ga zubar jini kamar jinina zai kare, amman da

muka je gurin shegen likitan da ya zubar mini da

cikin ya caje mu kudi masu yawa gashi a lokacin

bamu da komai duk mun saida 'yan

kadarorinmu, don haka yace ba zai taba ni ba,

sai nurse din da tayi mana hanya ce tace muje

asibitin kuroda tun da dai yanzu ba zubar da ciki

bane zasu karbeni, gahi an kwana biyu da zubar

da cikin sai nace ina da aure bari na yi, sai ta

shige mana gaba da sunan ni 'yar uwarta ce daga

kauye aka kawo ni. Amman duk da na Gwabnatin

ne ma sai da aka rubuta mana magunguna masu

tsada ga karin jini, sai yaya na ne ya bada jininsa

aka diba, sannan Sala ta je ta ciwo bashi aka sayi

magunguna, lokacin adadin kudin kusan dari

shida ne. Bayan na warke muka fara tunanin

inda zamu samu kudin da zamu biya dan daman

irin kayan nan na bashin watan nan ta amsa ta

karyar da su ta saida sannan aka sami kudin, don

ma matar tana shakkar Sala ba tayi magana ba,

da na samu sauki sosai Sister din nan ta bani

shawarar na dinga fita good evening (karuwanci),

cikin kankanin lokaci komai ya sauya domin dai

kasan ni ta daban ce." Suka yi dariya gaba

dayansu sannan ta cigaba da maganar, "Yaya

Sadiku kamar zai shake ni ya kashe ni don tsabar

tsana da yayi mini, don har cewa yayi da ya san

ci gaba zanyi da iskanci da bai yadda an kara

mini jininsa ba, gwara na mutu kowa ma ya huta,

sai da Sala ta tsawatar masa harda barazanar

zata tsine masa idan bai fita harka ta ba sannan

ya saurara mini. Sister ce tace na koma karatu

domin rayuwa babu ilmi tana tawaya don haka

Sadiku na komawa ya maidani makaranta wacce

na yi kusan wata shida banje ba, da farko yace

ba zai maida ni ba sai da nayi masa alkawarin ba

zan kuma yawo ba sannan ya yadda ya kwashi

katina da zai tabbatar da bani da lafiya ne

sannan muka wuce makarantar. Sanda muka isa

Principal dinmu ta ce ba za ta amshe ni ba

domin dai nayi wajen wata shida ban zo ba 'yan

ajinmu har sun zana jarabawar sake aji . Sadiku

ya marairaice yana bata hakuri, ji nake kamar na

harbe shi don haushi, daga karshe ya dauko kati

ya bata don ta tabbatar bani da lafiya ne. Ta

ware idanuwa domin dai duk da bata fahimci

abinda likitan ya rubuta ba ta fahimci kalmar

(bleeding after abortion), wato zubar jini bayan

bari, ta daga katin cike da tsana da takaici take

kallona sannan ta fara magana.

"Lallai yarinyar nan kin cika tantiriyar 'yar iska,

bayan iskancin da rashin kunya har karuwanci

kike tabawa, kamar ki ace an zubar miki da ciki?

Kai tir da halinki, Allah ya wadaran halinki." Sai

ta jefeni da katin akan fuska ta. Sadiku ya mike

jikinsa yana rawa domin bai san likitocin da

suka yi mini karin jini sun rubuta bari nayi ba

don bai san karyar da muka shirya ba, sannan

bai tsaya ya duba katin ba duk da ba komai zai

gane ba ma, ya fara magana da rawar jiki, "Don

Allah Hajiya kiyi hakuri kaddara ce da

tsautsayi....." "Da kuma sakaci da rashin

tarbiyya." Ta karbe daga bakinsa, sannan ta

dora da cewa, "Wallahi ka ji na rantse yarinyar

nan ta gama zama a makarantar nan, alfarma

daya zan iya yi maka na rubuta maka takardar

(transfer) canji zuwa wata makarantar, don ban

ga amfanin zama da daliba irin ta ba, ita ba

kokari ba sannan ga shegen iskanci ta addabi

dalibai da malamai tun yanzu tana matsayin

kwaila, ina ga ta zama babbar mace? (No i

can't) ina ba zan iya ba." ta karasa maganar a

hasale. Ni kuwa ina gefe na cika nayi fam,

domin Sadiku ya gaza rama mini cin mutuncin

da matar nan take mini, don haka na mike daga

tsugun nan da nake yi na dole, domin tun a

gida ya gargade ni na durkusa da munje kuma

na gaida ta don ta san na yi hankali. Ke! Ma ya

ishe ki haka, haka kawai zaki sanya ni a gaba

kina zagina kamar wata uwata? Ko abun da yafi

ciki nayi ina ruwanki, idan ba zaki karbe ni a

makarantar ki ba kawai kice ba zaki karbeni ba

amman kin saka ni a gaba kina zagina, ke

wayasan iskancin da 'ya'yanki suke..... Marin da

Sadiku ya dauke ni dashi ne ya sanya ni yin

shirun dole, na dinga dubansa da jin haushi

kamar nayi masa Allah ya isa, amman tunda

lallabashi nake yi ya sanya na hakura ina ta

kunkune dai. Kana ji a gabanka tana zagina ma

ko? To maza ku bar mini Ofis dina tun ban hada

ku da (security) ba, ta fadi a hasale. Ya dauki

katin da yake a kasa yace, Malama nagode, kiyi

hakuri hali ne kowa da irin nasa, sannan ya

dubeni yace idan kin ga dama sai ki taho mu

tafi. Bai jira abinda zan ce ba ya fice daga Ofis

din. Na dalla mata harara ina fadin, "Allah ya

sanya ba kece kika kawo ilimin boko duniya ba,

sannan Mangwafak ba dan gidanku ba ne, don

haka zanyi karatu a wata makarantar ko kina so

ko baki so....." "Ki fitar mini daga Ofis dan

ubanki ko na sanya a zane mini ke ko na hada

ki da 'yan sanda su kulle mini ke wallahi

shegiyar yarinya mara kunya kawai karuwa.....

Na ce, "Kin ga karuwa dai a gidanki ba niba."

Ina gama fadin haka na ficewata ina hangota

sanda ta zauna a kujera cike da bacin rai da

bakin ciki mara misaltuwa, na dai ji dadi don na

rama wulakacin da tayi mini. Bayan mun dawo

gida Sadiku ya yi kamar ya cinye ni don bala'i,

yace kuma babu ruwansa da ni, don haka na

rasa yanda zan yi na koma karatun, don na

gane idan mutum yana zuwa makaranta yakan

rage 'yan sa ido. Daga karshe dai Sister Asibi ce

ta yi mini hanya na koma Sheka da karatuna,

acan dai na kammala Secondary dina, bayan

sakamako ya fito babu lafi na samu admission a

FCE, domin a wancan lokacin ba'a tsaurarawa

gurin makin jarabawa, don haka da 2 credits 2

passes na sami admission. A wannan lokacin ne

na kuma wayewa na san lallai da kai na a duhu

yake, duk da dai ba wani karatun ne a gabana

ba, na hadu da malamai 'yan ban gishiri na

baka manda da taimakonsu na kammala. Dai-

dai lokacin da na kammala karatuna na hadu da

wani dattijo ma'abocin son holewa DPM ne a

wata karamar hukuma. don haka tunda ya

kyalla idon sa a kaina ya makale mini, shine dai

ya kawo min takardar fara aiki (upper) har gida

tun sakamako na bai fito ba, don haka na fara

aiki na, amman fa a kanyi wata banje Ofis ba

domin dai ina da manya a sama, sun ajiye ni a

cikin Sakateriya bangaren (Accountant), mai raba

kudi, don haka Salary bana wasa nake samu ba,

duk da ba abinda na karanta kenan ba kasan

Nigeria jaga-jaga inji wani mawaki, don wallahi

wadanda muka yi karatu dasu da dama basu

sami aiki ba har yau, kuma yawancinsu sune

masu kokarin sun fito da first class amman da

yake basu da wani a sama suna zaune, kai

Nigeria sai a slow wallahi." Ya yi dariya yana

fadin, "Wallahi ke din nan 'yar buyagi ce, ni

kaina wani lokacin tsoro kike bani, barin ma

yanzu, don haka ne ma na dinga jin tsoron

dawowa don kada kiyi mini buyagin naki." Ta yi

dariya gami da kai masa bugu na wasa, suka

kama dariya gaba dayan su, sannan ya gyara

zama yana kuma shinshinarta kamar wata diyar

mage sannan ya fara bata labari kamar

haka.Kamar yanda kika sani daran da yayanki

Sadiku ya yi mini wannan wulakancin na tafine

raina a tsananin bace, domin tun da nake ba'a

taba mini wulakanci kwatankwacin wannan ba,

don haka na kudirta a raina na hakura dake

tunda daman yace duk randa ya kuma ganina a

kofar gidan ku sai ya sanya an jefe ni, ni kuwa

bana son iyayena su san halin da nake ciki sam.

Sai da na koma gida ne ma sannan na tuna da

abinda ya kaini gurin ki, don muyi sallama ne ni

zan koma makaranta duk da na san ban taba

gaya miki hutu nazo ba. Sai da tafiyar ta kama

gadan-gadan sannan na ji wani irin masifaffan

son ki yana bijiro mini da kewar ki, amman na

dake don ina ganin da zarar na bar garin duk

zan daina ji, don haka na bar Kano da zummar

na bar Zainabu Abu na nufi birnin Califonia. Sai

dai tunda na isa garin na jini kamar wani mara

lafiya, surarki da kamar ki ta dinga bijiro mini

don haka na yi zaton ko kewar ki ce, don haka

na fara mu'amala da mata kala-kala masu kyau

masu ilimi har ma da masu dukiya, amman sun

gaza gamsar dani kamar 'yar kwaila Zainabu,

amman na dinga yaudarar kai na da lallai sai na

manta Zainabu, duk macen da na kalla sai naji

na raina ta burin yana ga Zainabu, na ki na

dawo hutu don ina ganin idan na dage zan

manta dake din, sai dai iyayena suzo mini hutun

can, har na kammala karatuna kina nan a raina

na kuma baiwa kai na wani lokacin na mantawa

da ke, don haka na fara aiki a can duk da ba

haka iyayena suka so ba, sai dai shi Mahaifina

mutum ne mai saukin kai da baiwa mutum

damar sa inda yaga babu cutarwa a kanta. Dare

daya na ji duk iyakacin dauriyata ta kare,

musamman da nake ta fama da yawan ciwon

kai da aka auna ni akace na rage sanya damuwa

a raina, na yadda muddin na cigaba da zama a

can ciwon zuciya yana gan da kamani saboda

yawan tunani, na yanke shawarar zan dawo

Nigeria na neme ki amman a wannan karon

auranki zan yi, don na gane kece kadai nake so

a rayuwa ta, na kuma yi kokarin jifan tsuntsu

biyu da dutse daya don daman iyaye na sun

damu da lallai na dawo nayi aure.Sai dai idan

na tuno ki sai naga kamar na rasa ki ko kin yi

aure, da zarar na tuno hakan sai naji duk

hankalina ya tashi, na yawaita sallah da rokon

Allah ya sanya baki yi aure ba, da wannan

shawarar na dawo gidan Nigeria, da zummar ko

a yaya na sameki zan aure ki, don ban yi zaton

Abun da na sani zata koma mace mai girma da

daraja da aji kamar haka ba, don dai a yanzu so

ne tsagwaransa a raina ba wata sha'awa ba. Sai

dai na sha mamaki a yanda na ganki a yanzu,

nasan tun a can baya kina da kyau don yana

daya daga cikin abunda ya sanya nayi mu'amala

dake, ga tsabta koda yaushe zaki wuce ta gaba

na sai na ganki tsaf dake, takalminki kamar ba

kya sakawa.Don haka Zainabu ba da wasa na

dawo ba da zummar na aure ki na dawo, don

haka bana son a dauki wani lokaci mai tsaho,

sannan dole ki daina kula 'yan iskan samarin

nan naki don ina da kishi mai tsanani, shi ya

sanya a wancan lokacin ma nayi kokarin ganin

baki kula kowa ba, don haka Zainabu gani

gabanki da kokon barata ina fata zaki amince da

bukata ta." Tayi dariya cike da jin dadi ta ce,

"Lallai Mustafa ka debo ruwan dafa kanka, ta

yaya zaka ce kai kadai zan dinga kulawa bayan

ba mijina kake ba? Ai hakan ba mai yiwuwa

bane ba." Ya mike zaune yana mata wani duba

idonsa fal da masifa ya ce, "Wallahi kina so ne

na fara rotse a kofar gidanku, don duk dan

iskan da yayi mini rainin wayo a kanki zan yi

maganinsa, da can sun yi yanda suke so, yanzu

kuwa mai guri ya zo kowa sai ya matsa ya bashi

gurin sa, duk mai neman kansa da arziki.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta makalkale shi tana dariya ganin yanda yake

masifa kamar zai rufe ta da duka, suka kama

dariya don tana masa irin salon ta da take siye

masa zuciyarsa. Bugun kofar da akeyi ne ya

fargar da su, Zainabu ta mike da sauri tana

fadin, "Ina zaton shegiyar nan ce ta dawo." Ta

dubi agogo sha daya da minti uku, sannan ta

nufi kofar da sauri tana kokarin budewa. Asma

ta shigo da gudu tana ihu da dariya tana fadin,

"Shegiyar ashe akwai mai maganin iskancinki,

gaskiya Mustafa ka ci a baka na daya, ya ci a

sara maka wallahi, don kayi mana maganin mai

shegen taurin kan nan." Mustafa ya mike tsaye

yana dariya sannan ya ce, "Daman ke muke jira

mu wuce." Ya mika mata makullin sannan ya

dubi Zainabu ya ce, "Ke madam sai ki shirya na

sauke ki a gida ko, don na san idan na tafi

wannan dan iskan ne zai zo ya dauke ki." Suka

fashe da dariya ita da Asma har da tafawa, yayi

murmushi yana fadin, "Lallai kwa yi mini dariya

don kun san kun kama wuya na, ni kam na

wuce mota kya tadda ni a can." Har ya kusa

kaiwa kofa sannan ya tsaya yana fadin, "Ahaf!

Hajiya Asma na gode kuwa zan gan ki." Tayi

dariya tana fadin, "A'a don ni kada ka damu

babu damuwa ai duk yiwa kai ne, don bani da

kamar Zainabu duk Kano." Yayi murmushi ya

ce, "Na dai gode din sai mun sake haduwa."

Sannan ya fice. Asma ta kalle ta gami da

fashewa da dariya su dukan sannan suka tafa

Asma ta ce, "Wallahi kawata kin iya iskanci, ki

dubi yanda kika juyar da zuciyar dan talikin nan

a lokaci kankani don Allah, don Allah yaushe ne

zaki sanar da ni sirrin nan ne?" Zainabu ta tafi

tana fadin, "Sirri ne abin." Asma ta bita da gudu

tana fadin, "Haba kawar, ki taimaka mini don

Allah." Zainabun tayi dariya sannan ta ce, "Ki

bari sai mun hadu kinga yanzu lokaci ya kure,

don zumana yana jirana a mota." Suka kuma

fashewa da dariya, sannan Asma tace, "Lallai

Mustafa ya ciri tuta don ban taba jin kin ambaci

wani namiji da ko sunan da iyayansa suke gaya

masa ba, daga shashasha sai dan wahala ko dan

akuyan can, amman Mustafa yaci Zuma gaba

daya ma." Zainabu ta zame da sauri ta falla da

gudu tana fadin, "Malama ki kyale ni haka nan,

kina bata mini lokaci." Sanda suka isa gida duk

'yan biki sun gama watsewa sai dai sauran

kwadayayyu, sun jima a mota suna sallama

sannan ta fita tana takawa da tafiyarta ta

daukar hankalin 'yan maza, sai da yaga shigarta

gida sannan ya ja motar tasa cike da tsananin

sonta, da wani nishadi da farin ciki.

Tana shiga Sala ta kama yi mata sannu da

zuwa, ta sami kujera 'yar tsugunne ta zauna

don cike take da nishadi. Sala din ta kama

murmushu don ganin diyar tata a cikin farin ciki

sannan ta ce, "Hala yau diyar tawa ta hadu da

mai barin dala ne naga bakin naki ya ki

rufuwa." Ta yi 'yar dariya sannan ta ce, "Sala

kin san abun mamakin da ya faru kuwa tun

daran jiya?" Bata bari ta bata amsa ba ta dora

da cewar "Mustafa ya dawo." Da mamaki Sala

din tace, "Mustafa kuma? Waye me wannan

sunan, ba dan dan banzan yaron nan da ya

cuce mu shekarun baya ba can?." Zainabu ta

bata rai matuka kamar zata yi kuka, ganin haka

ya sanya Sala din ta tsuke bakin ta, don ta yi

zaton zata yiwa Zainabun gwaninta ne, don ta

san irin alwashin da taci akan Mustafa. Ita kam

mikewa tayi tana fadin "Ashe daukar hakkinsa

muka yi daman, don ba laifin sa ba ne." Ta sha

ruwa a randa sannan ta dawo ta gaya mata duk

yanda suka yi da Mustafan. Sala din tayi dan

murmushi tana fadin, "A'a lallai bashi da laifi to

mun yafe masa." Zainabu ta ji dadin abunda

Sala din ta fadi, don haka ta mike tana dariya

sannan ta ajiye mata damin 'yan dari dari na

dubu ashirin tace, "Sala gashi nan kya kashe."

Sala din ta dauka tana dariya sannan ta ce, "Ke

Zainabu ba kya gajiya? Na ga fa kin sha

kacaniyar biki kwanan nan." Zainabu tayi dariya

tace, "Ai Mustafan ne ya bada ya ce a baki kya

sha ruwa kafin yazo bada hakuri da kansa." Sala

ta fashe da wata wawiyar dariya sannan ta ce,

"Kayya ki gaya masa ya kwantar da hankalin sa

komai ai ya wuce gashi kin ce daman ba laifinsa

ba ne." Ita dai Zainabu daki ta shige domin tayi

baccin gajiyar kwanakin da bata yi ba can baya,

kafin yamma tayi su hadu da zuman nata

************

Cikin kwanaki kalilan soyayya da shakuwa ta

kuma shiga tsakanin su, duk da suna rikici duk

lokacin da Mustafa ya ga Zainabu da wasu

Musamman Alhaji.... Dan haka duk inda tasan

zata gamu da samarin ta kan guje masa don

bata son ace kullum suna samun sabani da

Mustafa dan yana da matukar kishi, su kuma

sun gaza hakuri dan duk kusan namijin da ya

fara mu'amala da Zainabu bai iya daina wa dan

ta fiye fitina da yawa, sai dai idan Allah ne ya

kwato shi daga hannunta. Shi kam Mustafa

kullum hankalin sa a tashe yake dan bai kaunar

ya ga Zainabu da wani, dan haka nema suka

yanke shawarar yin aure a wannan lokacin. Shi

kam yana shakkar tinkarar Momin sa da

maganar auren nasa don ya san ta bata san

wargi sam ita, ga shi daman kullum tana masa

maganar ya zabo mace cikin 'yan matan gidan

ko kuma ya duba cikin 'yan uwa masu tarbiyya

dan bata son yayi zaben tumin dare, sai dai shi

a iyakacin ganinsa daga 'yan matan dake cikin

danginsu har na waje bai ga wacce tayi masa

kamar Zainabunsa ba. Yau ya tadda Momin

nasa a karamin falo, 'yan matan ta suna

karamin falo suna kallo sai musu a keyi tsakanin

'yan matan, don gidan nasu bai rabo da 'yan

mata na 'yan uwa dan su basu da yawa su biyu

ne kacal, gashi Momin su tana da son jama'a

dan haka koda yaushe gidan a cike yake banda

masu zama dindindin, banda kuma wadanda

aka aurar, dan haka tunda ya ga take-taken

Momin na su na son ta hadashi da wata a

cikinsu shi ya sanya ba ko da yaushe yake sakar

musu fuska ba. Ya shiga falon da sallama, ita

kadai ce don ya baro Alhajinsu a falo da baki, ya

isa gaban ta ya gaishe ta, sannan ya koma

babbar kujera ya zauna, ya dubi tibin inda yaga

hankalinta ya karkata. Yakin Falastinawa ne dai

da Isra'ilawa wadanda kanwa uwar gami

America ke daurewa gindi, ana nunowa a tashar

C.N.N. "Kai wadannan mutanen wallahi

azzalumai ne, ka dubi yanda suke kashe farar

hula da basu ji ba basu gani ba, sannan su yi

farofagandar basa taba farar hula, Allah dai ya

bi musu hakkinsu kuma ya nuna musu karshen

su, Amin." Hajiya Kubra ke fada da bacin rai.

Mustafa ya ce, "Haka ne Momi, sai dai idan kika

duba daman can zaki ga abun nasu bawai suna

yi bane don wani abu sai don su yaki addinin

musulunci kawai, yanzu fa idan kika shiga

kasashen turawa da gemu sai kaga an mai da

kai wani abin tsoro saboda sunyi farofagandar

batawa musulmi suna a idon duniya, dan ma

yanzu Allah yana nuna musu ishara mutanan su

turawa sai musulunta suke, musamman

matansu kamar su Kristian Barkeu da 'yar uwar

tsohon shugaban kasar Birtaniya Tony Blair,

Laurent Bothh wacce ma'aikaciyar jarida ce, da

sauransu, shine fa muke dan samun sassauci a

gurinsu, abun nasu dai sai addu'a." Ta amsa da

"Amin, ina wai ka shiga ne?, tun da safe nake

saka rai da shigowarka amman shiru." Gabansa

ya fadi, don yanzu sam bai zama a gida kullum

suna makale da Zainabunsa, amman sai ya

dake ya ce, "Momi kin san ina fafutukar fara

aikin tun da sun bani (offer), takardar daukar

aiki, shi ya sanya yanzu bana zama." Ta ce,

"Lallai kam haka ne, Allah dai ya taimaka ya

sanya a fara a sa'a." Ya ce, "Amin." Sannan ya

kama inda-inda don ya rasa ta yanda zai gaya

mata. Hajiya Kubra ta dube shi tana dariya tace,

"Babana duk yanda aka yi da magana a bakin

nan naka." Da yake sunan Baban ta ne da shi.

Ya yi murmushi yana sosa keya ya ce, "Momi

sirika na yi miki shine nake kunyar sanar da

ke."tayi dan murmushi dan ba hakan taso ba

taso ace anyi 'yar gida, amman sai ta danne

dan tana son yayi auren, dan haka tace, "Lallai

kam kace yau zanyi kwanan farin ciki, a ina ka

samo matar taka ko a can American ne?" Yayi

dariya ya ce, "A'a Momi a can dai unguwar da

muka taso take, can kasan layinmu na da,

sunan ta Zainabu." Ta ce, "Lallai kam, Allah ya

tabbatar mana. Waye kuma Babanta, a wane

gida take ne ma?" Da sauri ya ce, "Sunansa

Malam Abubakar." Tace, ai shike nan bari Alhaji

ya shigo sai a sanar da shi, amman dani na so

ace cikin 'yan uwanka da suke gidan nan ka

zaba, amman tunda Allah ya kaddara matar

taka a waje take ba zamu ja da ikon Allah ba,

sai dai muyi addu'a Allah ya tabbatar mana da

alkhairi kawai. Ya ji dadin abunda ta ce, yayi

mamakin kuma saurin shawo kanta da ya yi,

duk da saurin daukar zafin ta. Daga nan suka

cigaba da hirar su a cikin hirar nema take cewa

tana fatan zainabun tasa mai hankali ce da

nutsuwa. Ya ce, "Momi ko ke kika ga Zainabu sai

kinyi sha'awarta, ta kammala diplomarta yanzu

haka tana aiki ne." Tace, "To ai shike nan, na

san dai sai Baban ku ya sanya anyi masa bincike

don kada ayi zaban tumun dare." Kirjinsa ya

bada ras-ras, amman dai ya dake yace, "Na san

ma babu wani aibu da zai tadda ga Zainabu in

dai ya sanya mutanan kirki a binciken ba

munafukai ba." Tun daga sannan ya ji hirar ta

fita daga ransa gaba daya, don bai san irin

abinda za'a ce akan Zainabunsa ba, shi kam yaji

ya gani dan haka koma me zai faru sai dai ya

faru amman shi dai da ikon Allah sai ya aure ta.

Da haka yabar dakin mahaifiyar tasa ya nufi na

shi, amman yana cike da tunanin abunda zai

biyo baya idan suka san wacece Zainabu.

Kwanaki biyu shiru babu wanda yace masa ko

kala akan maganar, shi kam ya damu kwarai ya

ji anyi masa zancan, dan Baban sa ma da suka

yi maganar da Hajiya Kubran abinda ta fadi ya

maimaita, cewar zai sanya ayi masa bincike

sosai. Ya sami wani tsohon abokinsa acan

unguwar da suka taso ya ce don Allah ya bashi

amana ya binciko masa labarin wata yarinya

Zainabu diyar Malam Abubakar kamar yanda

aka ce masa, sai dai abokin nasa ya dan sami

matsala da farko dan duk wanda yace wa sun

san Zainabu diyar Malam Abubakar sai suce

gaskiya basu san taba, mutum hudu ya tambaya

amman duk ba'a dace ba. Sai da ya isa

majalisar da yake zama ya fara kawo maganar

neman Zainabu da yake yi, sai wani cikin

abokan hirar tashi yace, "Ko dai Zainabu diyar

Baba Abbakar mutumin Sudan din nan ake nufi,

in dai itace kuwa bai yi mata ba, domin dai

kowa yasan karuwar gida ce, duk da babu kyau

suka akan maganar aure amman tunda dai

amana ya baka sai ka sanar da shi gaskiya in

dai ita ce din, da dai kanwarta da aka yiwa aure

kwanaki ce ma da sauki dan ba halinsu daya

ba." Nan suka hau sanar dashi irin halinta dan

gaskiya shi ma'aikacine bai fiye zama ba sai

karshen sati kuma yawanci hirar siyasa suke yi

da matsalar da kasar ke ciki. Ba shi da wani ja

Zainabu diyar Baba Abbakar ce dai dan abokinsa

yake nema, dan haka ya je ya sanar dashi

yanda suka yi, daga karshe har kofar gidan su

Zainabun suka zo tare ya nuna masa. Haka nan

Alhaji Abdullahi ya koma gida jikin sa sanyi

kalau, domin dai ya tabbatar da lallai itace

wacce dansa ke so, shi kuwa duniya sam bai san

ya takurawa dan sa, yaso ace Zainabu da dan

sa yake so ta kasance kamila ce ba lalatacciya

ba, kafin ya shiga sallar Magariba ya kirawo

wayar Mustafa yace lallai idan an idar da sallah

yana son ganinsa,babu bata lokaci Mustafa ya

iso gidan dan kusan tare ma suka yi sallar Isha'i

da Baban nasa, ya dade a raka'ar karshe yana

addu'ar Allah ya sanya Zainabu ta zama

rabonsa, don yaji muryar Mahaifinsa kamar da

zafi shi ya sanya duk ya kidime. Ya riga Baban

nasa shiga gida, Momin nasa ta zuba masa

abinci amman ya gaza ci duk da uwar yunwar

dake addabarsa, dan kada ma Momi ta zargi

wani abu ya sanya ya dinga tsakurar kadan

yana ci har ma taso ta gane. Ta dubeshi da

kulawa ta ce, "Baba anya wani abu baya damun

ka? Na ga kwana biyu duk ka wani shiririce,

balle yanzu ka gaza cin abinci sai tunani." Ya

kakalo murmushi yana fadin, "Laaa! Momi me

kika gani? Babu komai gajiya ce dai kawai."

Ganin tana son ta gano shine ya sanya ya saki

jikinsa yaci abincin sosai, har Baban nasa ya

shigo, ya shige sashinsa ya kira Hajiya Kubra ta

wayar gida (land line) ya ce, "Baba ya shigo ne?

Idan ya shigo kuzo tare ke da shi." Ta amsa da

"Ya shigo, ga munan zuwa." Bayan ta ajiye

wayar ta dube shi duk ya sha jinin jikinsa ta ce,

"Alhaji yana kiranka." Sannan ta mike ta nufi

sashin Maigidan nata yana biye da ita a baya

har suka isa. Mustafa bai zauna akan kujera ba

a kasa ya zauna ya sunkuyar da kansa yana

gaida Baban nasa, fuskar sa babu annuri yake

amsawa, ba kamar yanda ya saba amsa masa

da sakin fuska ba, hakan ne ma ya sanya gaban

Mustafa ya cigaba da faduwa dan yana ganin

lallai wani abu yana shirin faruwa. Sun jima a

haka yana cigaba da duba jaridar leadership da

suka taddashi yana dubawa, labarin ya dauke

masa hankali wanda aka ce wai waye ya haifi

Obasanjo, sai da ya karasa shafin da yake

sannan ya daga kai yana duban Mustafa kur da

idonsa, abinda ya kuma fadar da gaban

Mustafa. Can ya daure ya ce, "Baba ka ce

yarinyar da kake nema acan kasan layin da

muka taso take har ma ta kammala karatunra a

F.C.E ko?" Bakinsa yana rawa yace, "Haka ne

Baba." Alhaji Abdullahi ya kuma gyara zama ya

ce, "To nayi bincike kamar yadda addini ya

umurci muyi a duk sanda aka tashi neman aure,

sai dai abun takaici duk mutanen da aka

tambaya wadanda ba zasu yi karya ba sun

sanar dani ko wacece Zainabu, dan haka sam

ban yarda da tarbiyyar ta ba da ta gidansu ba

ma gaba daya, don haka kaje ka nemo wata, ba

zan maka auren dole ba amman ya dace ace ka

samo mace mai mutunci da daraja a idon

duniya." Hankalin Mustafa ya yi mugun tashi

ransa ya baci, makwallaton sa sai kaiwa da

komowa yake yi, duk da sanyin A.C da fankar

dake dakin basu hana shi yin gumi ba, da kyar

ya iya bude bakin sa yace, "Baba kayi hakuri

bawai zan maka musu bane, ni na san Zainabu

diyar kirki ce, ka san halin mutanan yanzu ba

duka ne ke fadar gaskiya ba, dan haka ma

yanzu idan za'a yi aure ba'a cika zuwa a

tambayi mutanen unguwa ba, dan basu kaunar

wani ya cigaba, dan haka nasan zasu iya yiwa

Zainabu sharri dan haka ina neman yardarka

akan na auri Zainabu, watakilama ba wacce

nake so aka gaya maka ba." Alhaji Abdullahi yayi

dariya dan shi yana da hakuri da bin komai a

sannu ba kamar Hajiya Kubra ba mai saurin

daukar zafi ba da saurin fushi, sannan ya ce,

"Baba bana shakkar ba Zainabun da kake nema

aka sanar dani ba, amman bari nayi maka wasu

tambayoyi idan har ba ita bace shike nan." Ya

goge zufar dake tsats-tsafo masa ba tare da ya

iya cewa komai ba Baban nasa ya fara jeho

masa tambaya"Asali Abu ake ce mata sanda

tana yarinya, yanzu ne ake ce mata Zainabu

ko?" Ya ce, "Haka ne." "Kuma da can tana tallar

abinci da gyada da dai sauransu ko?" Ya hadiyi

wani yawu dan dai ya san lallai Baban nasa ita

ya gano, da kyar ya iya cewa, "Haka ne." "Tana

da wani Yaya mai suna Sadiku wanda shi ba irin

halinta gare shi ba, da kuma wata kanwarta da

aka yi mata aure kwanaki ba ko?" Yayi shiru bai

bada wannan amsar ba dan dai ya san Babansa

yayi bincike matuka akan Zainabu. Alhaji

Abdullahi ya cigaba da bayanin sa duk da bai

bashi amsa ba, "Babanta mutumin Sudan ne,

sunan shi Baba Abbakar, kuma ana kiran

Babarta da Sala....." "La'ilaha Illallahu! Yanzu

wannan karuwar yarinyar kake so Baba?" Hajiya

Kubra ta amshe zancen tun bai kai ga bada

amsa ba. Jikin sa ya kama rawa da rawar murya

ya ce, "Momi ba karuwa bace, don dai tana

aikine a (Local Govt.) ne shi ya sanya ake mata

kallon 'yar iska, wallahi ina sonta Baba kayi

hakuri don Allah, sharri kawai aka yi mata."

Hajiya Kubra ta amshe, "Sharrin gidan Uwar wa?

Ai ni sai yanzu ma na gane da ka fadi sunan

Mahaifinta Abbakar da sunan Babarta, yarinyar

da tun tana 'yar labubuwarta take iskanci, har

ciki aka zubar mata tana da shekara sha hudu a

duniya." Mustafa ya ce, "Kin ji ba Momi, sharri

ne aka yi mata dan ana....." "Sharrin Uwarka? to

tsaya ka ji na sanar da kai, na san Zainabu

shekarun da suka wuce, yarinya ce mara

mutunci kuma mara kunya dakikiya, ta addabi

kowa, duk wannan lami ne ma akan iskancin da

take yi." Ta dubi mijin nata tana magana, "Alhaji

idan baka manta ba na taba baka labarin wata

'yar iskar yarinya shekarun baya da tayi mini

rashin kunya har cikin Ofis dina, lokacin ina

makarantar 'yan mata ta Dala (G.G.C DALA), dan

ranar da tayi mini rashin mutuncin nan kasa

bacci nayi, don har sai da jinina ya hau, har yau

ina addu'ar Allah ya hadani da yarinyar nan

nayi mata rashin mutunci amman har yau Allah

bai hada mu ba, sai daga baya ma na ji 'yar

unguwar da muka baro ce a bakin wata 'yar

ajinsu, sai yanzu zaka ce kana son ta wai kuma

da aure ma? Ai ko da ku biyu kuka rage a

duniyar nan ba zaka aure ta ba muddin ina

raye." Ya dafe kansa idonsa ya kada yayi jajir

yana fadin, "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."

Dan ya riga ya gano Momi ta san komai, ta san

Zainabu farin sani, ashe ita ce wacce take bashi

labari din nan, sai dai ya rasa ta yaya zai sanar

da su wannan cikin da take tsanar Zainabu

saboda shi dan ta ne yayi shi, ta yaya zai ganar

da su shine ya fara lalata Zainabu tun a wancan

lokacin da take zarginta, duk da ya tadda

Zainabu da wasu muggan halaye amman shine

ya koyar da ita kashi saba'in cikin dari. Ya yi

tsamo-tsamo da shi kamar wanda kaza ta

fashewa a cikin sa, bashi da damar da zai kuma

musa musu abinda suka fadi, don idan yace na

Babansa sharri ne to na Momin sa fa wanda

Zainabu da bakin ta ma ta bashi labari, a sanda

take bashi labarin bai yi zaton Mahaifiyarsa bace

dan shi ko tambayar ta makarantar da take bai

taba yi ba balle har ya gano hakan ba. Alhaji

Abdllahi ya katse masa tunaninsa ta hanyar

fadin, "Baba ka sani ba wai muna kin Zainabi

akan kanta bane, A'a muna kin Zainabu saboda

halinta, don babu wanda zai so ace yau ya hada

zuri'a da lalatacce, da ace irin halin kanwarta

gareta babu abinda zai hana mu kyaleka ka

aure ta, dan haka ina baka shawara da lallai ka

koma ka sake nemo matar aure dan wannan

bata yi ba."

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347


Zaharaddeen Shomar

Whatsapp 08168575100




Idan Zuciya Tagyaru1-05

Posted by ANaM Dorayi on 08:00 PM, 03-Feb-16

Under: IDAN ZUCIYA TA GYRU

_____________ Na

________Fauziyya D Sulaiman_____

"Yo to banda abunsa ma a gidan nan wacce irin

mace ce babu kuma masu tarbiyya da kyau idan

ma shine ya rufe masa ido, don haka ka kwantar

da hankalinka ka zabi wacce ta dace da kai duk

'yan uwanka ne." Alhaji Abdullahi ya amshe, "Ki

na ji Kubra, ba wai dole sai anan gidan zai zabi

mata ba don zai iya yiwuwa bai ga wacce ta dace

da ra'ayinsa ba, ya je ko ina ya samo mata in dai

diyar musulunci ce kuma mai tarbiyya." Shi kam

duk bai fahimtar duk abinda suke fada don sam

hankalinsa baya jikin sa, ji yake kamar ya dora

hannu a kansa yayi ta zunduma ihu kawai ko ya

ji sanyi a ransa. Alhajin na sa ya ce, "Ka tashi ka

tafi Allah ya zaba maka abinda yafi zama

alkhairi." Ya mike da kyar yake iya daga kafarsa

yana hada hanya tamkar wanda ya sha giya ko

kwayar sanya maye, idanuwansa sun kada sun yi

jajir da su kamar gauta, har ya fice basu ce

komai ba illa binsa kawai da suka yi da kallo.

Hajiya Kubra ta ja tsaki tana fadin, "'Ya'yan yau

ba'a iya musu, banda haka daga ganin yarinya

baka san halin ta ba ka dage sai ka aure ta, ni

abun ma mamaki yake ba ni, yaushe har ya

dawo garin nan suka kulla soyayya da

hatsabibiyar yarinyar nan har ta dauke masa

hankali haka? Duka baiyi ko cikakkaken wata

guda a garin nan ba, ni ko bayan raina ba zan so

ya auri diyar nan ba, Wallahi Alhaji dan baka san

ta bane sam bata da kunya da ladabi ko miskala

zarratin, tuntuni na tsaneta wallahi." Alhaji

Abdullahi ya kuma gyara zama cike da tashin

hankali dan dai yana tausayin dan sa, don ya

gane ba karamin so yake yiwa Zainabu ba ya ce,

"Ai haka Allah yake ikonsa, shi kadai yasan a inda

suka hadu, sai dai muyi masa addu'ar samun

mace ta gari, da addu'ar ita kuma Allah ya shirya

ta." Hajiya Kubra ta ce, "Amin dai." Shi kam

Mustafa da kyar ya iya kai kansa sashinsa saboda

tsananin tashin hankalin da yake ciki, dan Allah

ya sani duk duniya baya ga iyayansa babu

abinda yake so sama da Zainabu, ya sani

Zainabu wata tsoka ce a cikin jikinsa mai yawo da

jininsa, a da can baya yana daukar son Zainabu

shirme kuma shiririta a zuciyarsa, sai dai a yanzu

ya sani muddin bai auri Zainabu ba lallai kam

rayuwarsa tana tare da hatsari. Ya kwanta

rigingine a gadonsa ya rintse idonsa, ina ma zai

iya kuka da lallai yayi ko ya sami sassauci a cikin

zuciyarsa. "Zainabu! Zainabu!" Ya fadi a hankali

ko ya ji sanyi a zuciyarsa, ya sani hakkin Zainabu

da sauran matan da ya cuta ne Allah ya saka

musu ya jarabce shi da son macen da ya raina a

da can, lallai da iyayansa sun san irin yanda yake

son Zainabu da sun barshi ya aure ta ko yaya

take. Haka nan ya dinga juyi a gadonsa bai san

sanda bacci barawo ya silalo ya dauke shi ba,

don yana cikin tsananin tashin hankali. Da asuba

da kyar ya iya tashi dan jikinsa duk ya masa

nauyi, a masallaci ya jima yana addu'ar Allah ya

karyo da zuciyar iyayansa su amince ya auri

Zainabu, har gari ya waye yana ta lazimi, sam ya

manta da zuwa Ofis dan haka sai da ya makara.

Ko da ya isa dinma kasa tsinana komai ya yi,

banda kallon hoton Zainabu dake bisa tebur

dinsa babu abinda yake yi, ya sani muddin

iyayansa suka hana shi ya auri Zainabu to kuwa

lallai zai jima bai yi aure ba, kai babu ma rana.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ya nufi kujerar da ke Ofis din doguwa ya kwanta

yana neman layin wayarta, bugu daya ta dauka.

Ita ce ta fara magana, "Hello My honey, Zuma

ta."Ta fadi da wata irin murya mai tsananin fisgar

hankalinsa, wacce ta ke siye zuciyar 'yan maza da

ita. Ya yi ajiyar zuciya sannan ya ce, "Zainabu ina

tare da matsala mai girma, na rasa yanda zanyi

da rayuwata ba ni cikin hayyacina da walwala ta."

Ta ji gabanta ya fadi amman sai ta dake ta ce,

"Ayya Zumana ka kwantar da hankalinka komai

zai zamo da sauki Insha Allah, ka na ina ne

yanzu?" Ya lumshe idon sa kana ya bude ya ce,

"Ina Ofis yanzu amman na gaza komai, ji nake

kamar bani da lafiya ma." Ta kuma kwantar da

murya ta ce, "Kana jina ko zumana, ka kwantar

da hankalinka gani nan zan zo yanzu Ofis din

naka don bani son bacin ranka....." "A me zaki zo

ne?" Ya tambaye ta da sauri. Ta yi murmushi don

ta san Mustafan ta da shegen kishii ta ce, "Ka

kwantar da hankalinka zan zo a shatar tasi ne,

don nima ina Ofis yau." Ya ce, "Yayi kyau, ina

jiranki kada ki jima." Ta dubi abokin aikin nata da

yake kallonta tamkar maye sai dai duk iyakacin

jarabarsa da gulmarsa ya gaza jin abinda take

cewa, ta galla masa harara kana tace, "Wallahi

Oga kai mugun dan saka ido ne, wannan kallon

da kake mini fa kamar maye?" Yayi dariya yana

sosa keya ya ce, "Ke din Zainabu da tsokano

mutum kike, banda ni waye zai daure zama da

zukekiyar mace irinki yana kallonta..... yanzu dai

ina zaki naga kina shirin fita bayan yanzu D.P.M

yayo waya zai zo." Ta yamutsa fuksa tana fadin,

"Idan yazo kace masa na fita idan da dama zan

dawo." "Zainabu ki yiwa Allah ki tsaya idan

ba....." Ko kuma bi ta kansa bata yi ba ta fice

abunta ya bita da kallo yana girgiza kai sannan

ya ce, "'Yar jidali, yarinyar nan kina gara zama

wallahi, ko da yake kin isa ne." Ta isa Ofis din

nasu cikin wani ubansu leshi, zanin ya zauna

dam a kugunta rafa ne,rigar bata fiye girma ba

don da kadan ta iya wuce cibiyarta, sai dai

hannunta dogo ne, yanayin kirarta ta kalangu ya

fito sosai duk wanda ya kalleta sai ya kara sai dai

mai karfin zuciya, kamshinta ka dai zai iya sanya

ka kalle ta balle kyau da tsarin tafiyarta.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ta murda kofar Ofis din ta yi sa'a kuwa a bude

take don yasan zata zo, ta san Ofis din dan kusan

tare suka tare ma, ta shiga da sallama, yana bisa

kujera yayi tagumi, har ta isa inda yake bai motsa

ba sai dai idonsa yana kanta har lokacin. Matuka

kwalliyar ta burge shi, ta isa ta zauna bisa

cinyarsa ta janye hannunsa daga tagumin da ya

yi, ta shafi gurin tana magana kasa-kasa,

"Zumana waye ya taba mini kai?, hankalina a

tashe na iso Ofis din nan." Ya daga idonsa yana

dubanta, abinda ya kuma bata tsoro don ganin

idon yayi jajir da alamar tashin hankali, ta kuma

shafar fuskar sa abinda ke sanya shi jin sanyi a

ran nasa ta ce, "Zumana ka sanar da ni abinda

ke faruwa wallahi hankalina a tashe yake." Ya

lumshe idonsa sannan ya fara magana har

lokacin tana shafar fuskarsa yace, "Hajiya Kubra

tsohuwar Shugabar makarantar ku ta G.G.C Dala

wacce kika yiwa rashin kunya itace Mahaifiya

ta....." Ta mike a zabure gami da dafe kirji tana

fadin, "Innalillahi wa inna ilahihi raji'un, na shiga

uku, Mustafa yanzu Hajiya Kubra Mominka ce?

Wayyo Allah na yanzu ya ya zan yi? Ina fatan

baka sanar da ita ko ni wacece ba?"Ya ware

idanuwansa wadanda suke jawur yana fadin,

"Zainabu babu hanyar fita, Momi ta sanki farin

sani kuma tasan kece Zainabun da nake so yanzu

a raina, Baba na ya sanya anyi masa bincike a

kanki matuka, ina sonki Zainabu amman iyayena

sun hanani auranki, abunda basu sani na yanda

Zainabu take haka ma dan su yake, amman na

rasa ta yanda zan sanar dasu abinda suke gudun

Zainabu saboda shi na dansu ne." Jikinta ya

dauki rawa dan ta shiga tsahin hankali matuka,

ya kamo ta ya tallafe ta a jikinsa yana shafar ta,

ta yi lamo a jikinsa tana ajiyar zuciya tamkar

diyar mage, ta ayyana a ranta wannan wace irin

masifa ce ta doso su, yanda suke son juna ace an

haramta musu auran juna, don dai duniya bata

da abin so kamar Mustafa, ta gama sallamawa

kanta a yanzu shine bango majinginarta, don ta

gaji da walagigin yawon iskanci da shan bakar

azaba ta saida mutunci a gurin maza, domin dai

ta lura yanzu ta sani babu abinda ke tattare da

bin maza sai bata da sai da mutuncin kai,

amman gashi wani katon abu na neman ruguza

mata wannan burin nata. Ta san halin Hajiya

Kubra mace ce mai kafiya da dagewa bisa duk

abinda ta sanya a gaba, wuya da dadi basa

sanyawa ta sauya daga kan ra'ayinta, bata manta

kirarin da malamansu ke mata lokacin tana

makaranta, "Mace mai kamar maza kwari ne da

babu." Sun yi shiru na tsahon lokaci kowa da

abinda yake sakawa a zuciyarsa, sun gaza sanya

kansu farin ciki kamar yanda suka saba a duk

lokacin da suka hadu don basu gundurar

junansu. Ita ce tayi karfin hali tace, "Musty

zumana yanzu yaya zamu yi, ko shike nan mun

rabu babu mafita?" Ya kuma rungumar ta tamkar

zai maida ta cikin sa kada wani ya kuma ganinta

sannan ya ce, "Zainabu abinda nake tunani

kenan tun daga daran jiya har zuwa yanzu

amman na gaza samun mafita, sai dai na sani

ruwa ko iska da duk wata azaba basu raba ni da

sonki, ko da an rabani dake a fili ba za'a iya cire

sonki a raina ba, son ki shine so na gaskiya mai

wahalar da ruhin Mustafa da zuciyarsa." Tayi

sanyayyar ajiyar zuciya mai cike da jin dadin

kalamansa, sannan tace, "Shike nan zumana kada

ka damu ka kwantar da hankalinka mu cigaba da

addu'a, sannan mu tsaya kan ra'ayinmu na son

juna duk wuya da dadi ina ganin zamu yi nasara

komai dadewa." Yace, "Hakane Zainabu kin kawo

shawara mai kyau, har naji raina yayi fari." Ta

kuma kwantar da murya tana fadin, "Kada ka

damu ka kwantar da hankalinka ni din taka ce

har abada." Ta fara masa salon nata na jan

hankali a cikin kunnensa take fadin, "Musty

zumana (I love you so much) Ina sonka da yawa."

Bai iya hakuri da Zainabunsa musamman idan

tana masa salonta na kauna dan haka sai ya

shiga maida mata martaninta, ya ma manta inda

suke.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

**************

Abubuwa sun hadu sun jagulewa Mustafa har ma

da Zainabun kanta, don dai yanzu ba ta iya

kallon kowanne da namiji da gashin arziki idan ba

Mustafa ba, wadanda take watsewarta dasu a da

can ma ta kisu yanzu, kawarta Asma tayi mata

lallashin duniya akan ta cigaba da harkarta ko da

a boye ne amman ta gaza, dan sai dai tayi mata

wani kallon ta ce, "Asma baki san Mustafa ba ne,

shine namijin da idan ya baki zumarsa baki iya jin

dadin ta kowa, shine namijin da ya iya soyayya

mai kwantar da zuciya, shine mai kula da duk

wasu bukatu na macen da yake matukar so,

shine ya sadaukar da kansa ga Zainabu, shin kina

tunanin yana gabana da ransa zan iya kula wani

da namiji? Ki barni kawai baki san Mustafa ba

kina kallonsa ne kawai." Don haka Asma sai dai

ta zuba mata ido kawai don ita da kanta ta san

Mustafa daban ne a cikin maza kamar yanda

kawarta ke fadi. Samarin ta da dama sun damu

da wannan sabon halin da ta bullo musu da shi

musamman Alhaji Jamilu da kuma D.P.M, don

haka ma ta kashe duk wayoyinta, idan kaga ta

kunnasu lallai Mustafa zata kirawo. Hankalin Sala

idan yayi dubu ya tashi, domin dai tana ganin

kamar ana son kashe mata jin dadin diyar tane

da walwalarta, dan da farko ma fada ta kama yi

mata tana fadin, "Haba maitsada yaushe zaki

zauna namiji kwaya daya yayi ta gare-gare da

rayuwarki a banza, ki dubi irin wahalar da kika

sha a baya, amman yanzu duk kin daga

hankalinki don uwarsa tace ba zai aure ki ba, ga

maza nan kala-kala suna binki wadanda suka

fishi komai kamar su cinye ki amman kin makale

masa, dan haka ki rabu dashi kawai tunda dai

yanzu ba da bace." Ita dai shiru kawai tayi tana

ayyanawa a ranta, "Sala baki san so bane shiya

sanya kike fadin haka, da kin san irin abunda

nake ji akan son Mustafa da kin tausaya mini, zan

iya jure rashin komai amman banda Mustafa,

wannan wata jarabta ce da Allah ya doro mini."

Da dai Sala taga fada da mita ba zasu yi magani

ba sai ta koma lallashi, amman duk a banza wai

talaka ya girmi Sarki, su kuwa abokan watsewar

ta sai kyauta ta bajinta suke mata wai ko zasu

shawo kanta, amman idan an aiko ma sai dai

Sala ta karbe tana godiya tace bata jin dadi ne

shiya sanya bata fito ba. Idan mutum ya fiye

matsa mata da aike kuwa fita take yi tayi masa

rashin mutunci, don dai muguwar 'yar buyagi

ce.Haka zaka tadda ta tayi dif da tabar shaidan

ko shandy din ta a gidan Asma dan can Mustafa

ke tadda ta suyi watsewarsu acan da lallashin

juna, don ma dai shi yanzu Mustafa bai son

shaye-shayen da take yi don shi kam baya ga

taba yanzu bai shan komai sai dai idan wani yana

shan tabar shaidan a kusa dashi ya amsa yayi ja

uku ko hudu, amman giya kam tuntini ya daina

sha, don haka take rage shan su don su kan yi

fada idan ya tadda ta tana sha. Al'amura sun

kuma tsauri a gare su, don Momi ta kama shi da

hoton Zainabu wacce tayi tunanin ya rabu da ita

tuntuni ya fara neman wata ma, ta yi matukar

girgiza musamman da taji kalaman da yake

furtawa akan Zainabu din. Ta yi neman wayar sa

ne ta sanar dashi sallahun da Babansa ya bari ya

kaiwa kanin sa Kawu Sale, amman duk wayoyin

nasa a kulle suke, gashi kuma ta ga motar sa a

kofar gida abun da ya tabbatar mata yana ciki

kuma dai lokacin babu yara a gidan don haka ta

nufi sashin nasa da kanta don ta sanar dashi

sakon Baban nasa. Ta tadda shi zaune bisa

kujera ya dora (laptop) akan cinyar sa ya kura

mata idanu wadanda suke rine saboda tsabar

tashin hankali, a fili yake fadin, "Zainabu yaya

zanyi da son ki a zuciyata, ni kadai na san irin

azabar da nake sha saboda raba mu da ake

shirin yi, na gaza ganin ko wace mace da kima da

daraja don kece kadai kika san Mustafa, ba zan

iya auran wata mace ba muddin kina raye a

duniyar nan ba, san yani a kafadarki ko naji sanyi

a raina, na zama mutum-mutumi sai yanda kika

yi dani Zainabu." Hankalin Hajiya Kubra yayi

mugun tashi da jin kalaman da Mustafa ke

furtawa, ta kuma jin tsanar Zainabu ta lunku a

ranta don sai taga kamar yanzu yafi son Zainabu

sama da ita ma daga yanda take jin kalamansa,

kai ita tana ganin wannan son da yake wa

Zainabu ma bana Allah bane asiri kawai tayi

masa, banda haka meye hadin shi da ita, don ya

fita komai a ganinta, ta nufe shi da sauri dan ta

bayansa take baiga shigowarta ba, sai ta tsaya

turus tana kallon abinda ya dauke masa hankali

har bai ji shigowar ta ba. Wani katon hoton

Zainabu ne ta dauka da wani yadin material (light

purple), mai yarfin fulawowi jajaye da ruwan

zaiba, tana sanye da wani dankunne na fashion

mai kyau, ta tallafe habarta da tafin hannunta

tana dariya, (dimple) dinta ya fito sosai, fuskar ta

yi fayau, gashin idonta ya tashi gazar-gazar,

girarta ta kwanta luf-luf, labbanta sun sha

jambaki kalar kayanta sai walkiya suke yi tamkar

ba a hoto ba, hoton ya dauko matuka don an

futo da ainihin kyan Zainabu. Lallai ba Zainabun

da ta sani da ba ci, don ta goge matuka tana

kuma da kyan da lallai zata iya yaudarar Mustafa

ya sota, sai dai ita kyanta baya gabanta tunda

bata da kyan hali. Zuciya ta dauke ta don ganin

wai har lokacin bai san ta shigo ba hankalinsa

yana ga Zainabu ne kawai, ta fisge laptop din ta

kwadata da kasa, ai kuwa sai gashi ta bare gida

biyu, da alama da kyar zata kuma moruwa gashi

mai kyau ce dan daga kasar waje ya taho da

ita.ya daga kansa a gigice dan yaga wanda yayi

masa wannan yankan kaunar sai yaga Momin sa

a tsaye tana ta huci ta cika fam, nan da nan gumi

ya fara karyo masa don yasan Momi babu wargi

ba iri Babansa bane mai sanyi ba. "Mustafa! (ta

kirawo sunan sa yau babu sayawa saboda bacin

rai), wato dama baka rabu da wannan karuwar

ba ko? to tsaya kaji na gaya maka ko mutuwa

zaka yi akan sonta ba zaka auro mana jaraba ka

kawo mana gida ba, da mun sakankance ka rabu

da ita, ashe 'yar jarabar tana tare da kai. Shin

wai ni me ka gani a jikinta da har tafi sauran

mata da ka kasa kalla da daraja ne eye? Kai

yanzu ba zaka ji kunya ba ace matarka tsohuwar

'yar tallan goro bace mara tarbiyya ba? Bata gaji

tarbiyya daga uwa ko uba ba sam?, to tsaya kaji

na gaya maka ta mahaukaci, ko bayan raina ka

auri Zainabu ban yafe maka ba, sannan daga yau

idan ka kuma zuwa gidansu ko inda zaku hadu

ban yafe maka ba." Ya runtse idonsa gami da

dafe kai hankalinsa yayi mugun tashi, babu

abinda yake fadi sai, "Innalillahi....." Ta kuma

kufula tana fadin, "Kai ko mutuwa zaka yi babu

kai babu Zainabu na gaya maka in dai nice na

haifeka dan halak." Tana gama fadin haka ta juya

ta fice sam ta manta da abinda ya kawo tama

sashin nasa. Ya zauna jabar a kujera har lokacin

bai cikin hayyacinsa, ya kuma fadin, "Ya Salam!

Ya Salam!" Har lokacin zufa tana karyo masa duk

da sanyin A.C da fankar dake dakin. Maganar

Momin ta dunga masa amsa kuwwa a kunnensa

sai yake ji kamar har lokacin tana tsaye a kansa

tana ta maimaitawa ne, don haka ya sanya

hannuwansa ya toshe kunnuwansa wai ko ya

daina ji, amman da yake abin daga zuciyarsa

yake fita sai ya cigaba da ji kamar ma karuwa ya

yi. Lallai ko yaki ko ya so yasan rabuwar sa da

Zainabu ta zo kenan, idan har ya kasance da mai

albarka, don dai ya san duniya bai hada

Mahaifiyar shi da kowa ba, ko da kuwa zai mutu

din kamar yanda Momin nasa ta fada din ya rabu

da Zainabu har abada.

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

WAI WACECE ZAINABU-ABU MAI TAGWAYEN SUNA

NE?

Asalin Salamatu mahaifiyar Zainabu 'yar cikin

birnin Kano ce, ta tashi babu arabi balle boko,

bata da aiki sai dai ta dauki tallan soye (dan tayi

da ake cirowa daga dabbar da aka yanka na kasa

mata a kokuna sannan a jera a cikin faranti). Don

haka kullum da sassafe zata yi sammako ta tafi

Mayanka ta siyo dan tayin wanda zama suke

kusa da dabbar da ake yankawa da zarar an

hango da dantayi sai a kwasa da gudu, wacce ta

fara kamawa nata ne sai ta saka a kwanonta ayi

ciniki sannan su kuma matsawa gaba da haka har

ka tara na iyakacin kudinka, sannan sai ta tafi

gida a yayyanka shi a soya, a zuzzuba a kokuna

sannan a tafi tallanshi kasuwanni. Idan ta dauki

tallan tun safe sai yamma likis take komawa gida,

don haka bata da lokacin karatu, sai dai ran da

taso sai ta tafi makarantar dare ita ma bata

fahimtar komai dan banda gyan-gydi babu

abinda take yi, don an sha yawo an gaji, idan

kuma ranar alhamis da Juma'a ce a tafi gidan

amare a yita wasan 'yar carafke ko lido da

sauransu. Mahaifinta yana so tayi karatu sai dai

bai isa ba dan matar sa tafi karfinsa, don haka

yana ji yana gani 'yarsa ke wannan rayuwar babu

kwaba balle harara, sannan idan dare yayi wani

lokacin zaka ga samari sun cika kofar gidan anata

zance da shewa da kawayenta kuma bana aure

bane illah ayi shashanci da zancen batsa a watse,

amman babu na aure a cikinsu. A gurin da take

sai da soye wani mutumin Sudan sunansa

Abbakar, shayi yake saidawa irin na babbar butar

nan wanda ake dauka a hannu da biredi da

kofuna a faranti, Abbakar mutum ne mai kirki da

hakuri dan kullum Salamatu sai ta tsokane shi

dan hausar sa bata fita sosai, gashi kuma da

shegen surutu da son tsegumi. Duk danginsa

suna can Sudan, yaki ne ya sanya suka watsu

suka yo Nigeria da 'yan uwansa, sai dai tun da

suka zo kowa ya nemi masauki, shi kam yayi sa'a

ya fada hannun wani Malami Malam Nadabo

mutumin kirkine ya bashi gida inda yake saukar

baki ya zauna cikin almajiransa, yana fita neman

abincinsa don shine ma ya bashi jarin da ya fara

sana'a tun yana zagaye cikin unguwar har ya

koma yana shiga kasuwanni.Da yake ya iya

shayin sai ya samu kwastomomi dan irin na

larabawan nan yake yi, a haka suka hadu da

Salamatu ma, don Allah yayi shi mutum ne mai

shegen surutu da son gulma dan haka duk

abinda ya gani sai ya nuna mata ko ya tambaye

ta da haka har soyayya ta shiga tsakaninsu. Abu

kamar wasa sai gashi sun saba matuka, sai dai

tun a wancan lokacin tayi mugun raina shi tayi ta

masa masifa bai damuwa, domin yana da

matukar hakuri sai dai zancan gulama amman

sam baida abokin fada, sai dai mutane da dama

suna ganin abun nasu kamar ba zai yiuw ba don

shi fari ne tasa kamar balarabe gashinsa ma a

nannade yake sai dai wahala ta sanya shi ya dan

dafe, yayin da Salamatu take baka, amman bata

da muni, sai dai bata da tsawo gajera ce sosai

mai jiki. Malam Nadabo dai shine kamar matsayin

mahaifinsa don haka shine ya tsaya masa har aka

yi wannan auren, suka tare a nan gidan Malam

din da yake zaune da almajirai, wasu suka koma

shagon gidan wasu kuma suka koma daya gidan.

Ta addabi kowa a gidan don gidan kusan a hade

yake da na Malam kasancewarta masifaffiya ce,

su dai matan malam bata yi da su don sun ja

girman su haka malam, sai dai duk 'ya'yan gidan

'yan dakinta ne musamman matan, amman duk

kusan almajiran malam tayi fada da su don ma

malam yakan yi mata fada, don haka babu

wanda take shakka kamar malam don babu

wargi, a nan gidan ta haifi dan ta na fari Sadiku

wanda aka haifa rana daya da dan Malam Zaidu,

don haka rana daya aka yi suna Malam ne ma ya

rada musu sunansu duka. Sun tashe tare da

Zaidu da yake Sala bata wani damu dashi ba don

ita ta fi son ta haifi mace wai itace abokiyar

neman kudi, don haka kullum a cikin watangariri

yake a cikin gidan musamman da ta yaye shi sai

ta bar musu a can, don haka kusan a gidan nasu

ya taso.Tare Malam ya sanya su a makaranta Ma,

sannan ta kuma samun wani cikin tayi ta tanadin

kayan mata har su dankunne da awarwaro

amman sai gashi ta kuma haifar namijin, shima

din haka ya taso a gidan malam din, sai dai daga

kansa bata kuma samun haihuwa ba har ya

shekara biyar, sai wata annoba ta zo ta kyanda

shima yana ciki, ai kuwa dai wannan kyanda itace

ta yi ajalin Sabitu. Rashin samun cikin nata ya

sanyata fara tunanin wai matan Malam ne sukayi

mata asiri don ta fara haihuwar da namiji, su a

kan Zaidu suka fara haihuwar namiji duk mata

suke haifa, ita fadi take banzaye ni da ana

musanye da munyi don nafi son matan, sai dai

bai ya wata goma ba da rasuwa Sala ta kuma

samun wani cikin. Ai kuwa dai wannan karon tayi

sa'a a wannan karon ta samu abinda take so din,

don haka murna ba'a magana, sai da dauki son

duniya ta dora akan Zainabu sunan Mahaifiyar

malam din ya sanya mata kenan, da farko tace

bata yarda ba sunan Sima take son a sanyawa

diyarta, shi kuwa malan sunan matarsa ta fari ne

da ta rasu yana son sunan, sai da Abbakar yayi

ta lallaba ta sannan ta amince, akan Zainabu sai

tayi fada da uban kowa a kuma sannan ne

Abbakar ya kammala ginin gidansa da taimakon

malam, don haka suka tattara ya nasu-ya nasa

suka koma, amman banda Sadiku wanda sai dai

yaje gidan nasu ya koma gidan malam don

kamar ba Sala dince ta haife shi ba musamman

idan Zainabu tana kin ji yana mata fada, dan

haka shima bai fiye zuwa gidan ba sai da ya

shiga sakandire ne ma yake zuwa sosai.Sala kam

sana'a ta kafa sosai a gidan ta, don daman tun

tana gidan malam jarabar neman kudi ne da ita,

don haka ba ta zama kullum cikin neman kudi

take. Tun daga wannan lokacin shike nan

haihuwa ta bude a gidan nasu, sai dai yaran

suna tashi babu tarbiyya, da farko malam ya fara

kiran Baba Abbakar akan halin da yaransa suka

tashi da shi, don haka yayi masa nasiha mai

shiga jiki, sai dai idan aka ce namiji bashi da

katabus a gidansa babu tarbiyya, don haka san

da Baba Abbakar yaje mata da abinda Malam din

ya ce, tsalle tayi ta dire tana fadin, "Wallahi baka

isa ba, wacce tsiyar kake tsinana mana da har

zaka yi mini wannan tsarin (don a lokacin babu

ciniki a sana'ar ta shi sai dai yayi ta yawo bai

samun ciniki sosai, daga karseh sai ya koma

kame-kame)." Malam Nadabo yana ji yana gani

gidan Baba Abbakar ya koma yanda yake don dai

yayi har ya gaji, sai dai shifa duk wani abu na

tsawatarwa yana musu dan haka shi kadai suke

shakka a rayuwarsu, don duk wanda ya doki

Zainabu sai inda karfin Sala ya kare, amman idan

Malam ne sai ta ce, "Sai kiyi hakuri na gaya miki

ki daina zuwa gidansa mana." Shi kam Sadiku ya

sami karatu mai kyau don ya sami makarantar

firamare mai kyau da sakandire, daga nan ya

wuce kwalegin share fagen shiga jami'a, shi kuma

Zaidu da yake bangaren Arabic ya dauka yana

Jami'atu Ummul Qura dake birnin Makkah yana

karantar harshen larabci, wannan shine mafarin

komawar Sadiku gidansu don dai babu abokinsa.

Da kyar da sidin goshi Sala ta bar 'ya'yanta suke

makarantar boko da ta allo don Malam yana fada

ne da kuma Sadiku, sai dai duk da haka Zainabu

ba kullum take zuwa ba sai jefi-jefi. Sai dai da

yake ba karatun ne a gabanta ba sam bata yi,

Zainabu ta taso da hali irin na Babarta don haka

bata da wargi duk wanda ya taba ta sai ta rama,

don dai Sala ta bata ta tun tana yarinyarta, ga

fadan ta baya mutuwa kamar fadan kurma, don

sai tayi wata tana fada sai dai idan iyayen yaran

sun gaji su zo gidan a baiwa Sala hakuri sannan

za ta hakura, idan mutum yafi karfinta ba ta raga

masa don da cizo da yakushi zata kwaci kanta, ko

kuma idan ka doke ta tayi ta jifanku ko duk inda

kuka hadu sai fadan ya tashi. Wannan halin nata

ya sanya duk unguwar kowa yake shakkarta,

abinda ke farantawa Sala rai kenan don takan ce,

Abulata da na kai kararki gwara a kawo mini

wallahi, don haka duk wanda ya taba ki koda

gemunsa yana jan kasa kada ki kyale shi ki rama,

daga nan har ofishin kwamishinan 'yan sanda zan

iya zuwa a kanki Abulata. Don haka har siyan

fada take yi, duk wanda bashi da karfi Zainabu

kan sayi fadan ta casa wanda ake fadan da shi

don akwai ta da karfi, idan kayi gulmarta za ta

sanya a kama ka a tura ka lungun ka-ci-uwaka a

tura maka kashi a baki ko bara-gurbin kwai, don

haka ta addabi kowa a unguwar tasu. Ko fakin

din mota aka yi bai gamshe ta ba sai tayiwa

mutum faci a motar tasa, don haka duk kofar

gidan masu hali na unguwar da an gan ta masu

gadi zasu bita da gudu tana dariya. Idan aka tura

ta makarantar firamare kuwa masu kosai da 'yar

tsala na sadaka take bi da waina wadanda ke

yawo da almajirai mutane na siya suce su raba

wa almajirai sai an fita tara take tafiya

makarantar. Yawo kuwa ko kare ya gan ta ya

kyale, don kullum za ta hada zugar yara suna

shiga karkashin manyan motoci da ke fakin a nan

kan tudu, dan haka duk wanda baiga dan sa ba

yana tare da Zainabu, yawo bola-bola sun iya

shi, gashi babu dama kayi magana sai Sala ta

hau bala'i tana fadin, "Kun ga kada ku sanya

mini diya a gaba, waye Abula ta daurawa igiya a

wuya kowa na ga da kafarsa ya bi ta, don haka

duk matar da ta kara cewa Abula ta ja mata

'ya'ya yawo wallahi sai na dirji bakinta, duk

wacce ba ta son 'ya'yanta su je yawo ta daure a

kofar gida, kurwar Abula kur! Na gaya muku."

Wannan shine kadan daga cikin labarin Zainabu

Abu mai tagwayen suna.

**********Ku ziyarci blog dinmu domin karanta

Littatafai masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.com

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347

Ubangiji babu ruwansa yakan bar bawa ya sakata

ya wala ya yi sabo son ransa ba tare da ya matsa

maka ba a duniya, amman abu kalilan zai jarabce

ka dashi duk sai ka gigice ka ga ashe kai din ba

komai bane, ka koma abin tausayi. To, Lallai kam

hakan ce ta faru ga Mustafa, don bai taba zaton

zai shiga ko da kwatankwacin wannan matsalar a

rayuwarsa ba, Allah ya jarabce shi da son

Zainabu wacce ita kuma mahaifiyarsa ta tsana

kamar mutuwarta, Zainabun da ya raina a baya,

sai ga shi son ta yana neman raba shi da duk jin

dadin rayuwarsa, don wacce ta kawo shi duniya

ta yi musu katangar karfe a tsakaninsu. A da can

da suka hana shi auran ta bai damu kamar

yanzu ba, don yaka je gurinta ya kwanta a

kafadarta ta lallashe shi, amman yanzu babu

dama don haka abubuwa suka masa yawa, yanza

haka yana ofis ya hada tagumi da hannuwa biyu-

biyu kamar wani karamin yaro, wani inji aka ce ya

je ya duba amman ya gaza tashi, gashi yafi kowa

iya gyara a sashen nasu, yanda kasan maye haka

yake idan ya sanya gyara a gabansa sai ya ga ya

gyaru, don haka suke ji da shi.Yana nan zaune ya

ji kiran wayarta ya shigo, ya zabura da sauri ya

dauka ya kara a kunnensa. Da kashe murya da

shagwaba ta ce, "Zumana shiru kwana biyu babu

kai babu wayarka, ko Zainabu ta yi laifi ne bata

sani ba?" Ya lumshe idonsa gami da kwanciya

jikin kujera, ransa ya yi fari tas saboda jin muryar

Zainabu kawai da yayi, sai dai ya gaza bude

bakinsa ma balle yace wani abu. Hankalin ta ya

kuma tashi da jin shirun da ya yi mata, ta kuma

duban wayar ta ga lallai a kunne take, da tashin

hankali ta ce, "Mustafa ka ce wani abu mana, ko

dai ka manta da Zainabunka ne?" Hankalinsa ya

kara tashi don jin muryarta kamar za ta yi kuka,

ya daure ya bude bakinsa da kyar ya ce,

"Zainabu baki yi mini komai ba, illah dai

Mahaifiya ta ta kafa mini mummunan sharadi a

kan idan na kuma zuwa inda kike ko duk inda na

san zamu hadu, to lallai ba ta yafe mini ba....."

"Me ka ce Mustafa? Yanzu kana nufin shi kenan

mun rabu har abada? Yanzu yaya zan yi da

sonka a raina Mustafa na? Anya zan iya rayuwa

babu kai, Zumana?" Yayi kokarin jawo dauriya ya

sanyawa ransa ya kwantar da murya da lallashi

ya ce, "Kin ga Zainabu kwantar da hankalinki, ni

din naki ne har abada ba zan iya rabuwa da son

ki ba, sai dai dole zanyi biyayya ga maganar

Mahaifiyata don ina son na rabauta duniya da

lahira, na yi miki alkawari ni naki ne har abada,

sai mu cigaba da addu'a komai ya zo da sauki,

don ina ji a jikina ke matata ce da zan rayu da ita

cikin ni'ima da soyayya." Hankalinta ya dan

kwanta ta yi ajiyar zuciya tana fadin, "Zumana

yanzu yaya za muyi kenan? Don na san zan sha

walahar rashin ganinka matuka." Ya lumshe

idanuwansa wadanda yake jin suna masa nauyi

ya ce, "Ki bari zan ga Babana idan ya dawo zan

sanya shi ya lallasar mana Momi din, ina ganin

shi zai tausaya mini idan ya ga halin da nake ciki,

don yafi Momi saukin kai." Ta ce, "Shike nan

zumana, amman zan dinga jinka a waya ko?" Ya

ce, "Dole ne ai Zainabu na kiraki a waya, idan ba

haka ba zuciyata ai bugawa zata yi." Ta yi

murmushi gami da fadin, "Ina sonka matuka

zumana." Ya yi dariya ya ce, "Nima haka Zainabu,

sai dai ina son don Allah ki yi mini alkawarin kin

bar hulda da maza kamar kina ganina, don na

danka miki amanar kanki, ina jin kamar zuciya ta

zata babbake idan na ganki da wani, shin zaki iya

rike mini kanki da alkawari har komai ya lafa?."

Ta yi murmushi gami da fadin, "Mustafa ko da ba

kace ka ba ni amanar kaina ba ba zan iya hulda

da kowanne namiji ba, don kai din kayi mini

yanda ba zan iya kallon kowa da gashi ba, ka

kwantar da hankalinka a yanzu Zainabu taka ce

kai kadai." Da kyar suka iya rabuwa a wayar don

suna ta sanar da kawunansu irin son da suke

yiwa junansu ne kawai. Sai a sannan ya sami

karfin gwiwar da zai iya tunkarar aikin da ke

gabansa, don haka ya shiga dan wani daki ya

sauya kayansa daga na gida zuwa na aiki ya nufi

inda injin da zai gyara yake. Ita kuwa Sala ce a

kanta a tsaye tana rike da kugu jira kawai take ta

kammala amsa wayar, ai kuwa tana ganin ta

gama wayar din ta dirar mata da jaraba. "Yanzu

Abula shi kenan zaki zauna namiji daya tal yana

miki yawo da hankali? Ga wadanda ke son ki

kuma sai wahalar da su kike yi? Yanzu jiya Alhaji

Hayatu Tumbin kudi sai da ya kashe kunyarsa ya

zo ya sameni ya ce don Allah ki fito ko gaisawa

ne ku yi, shi da gaske yake auranki zai yi ma, ya

cake mini dubu hamsin a hannuna ke kuma ya ce

idan kin fita zai baki duk abinda kike so, amman

yarinyar nan kika bada mini kasa a idona, har

mutumin ya gaji da jiranki ya yi zuciya ya tafi, kin

kwallafa ranki a kan shegen mayaudarin yaron

nan, kin ki ki saki zuciyarki ki ci arziki ki bar arziki

a mazauninsa? Wallahi kin bani mamaki Abula

ban taba zaton zaki koma sokuwa a hannun

namiji ba, su da kike juya su kamar waina?."

Zainabu ta dinga duban Sala da mamaki da

takaici da kyar ta iya buda bakinta ta ce, "Sala

kin san So kuwa?" "Ban san shi ba sai ke diyar

zamani, ba kuma na fatan na san shi tunda shi

din masifa ne da jaraba, ki dubi yanda ya maida

mini ke, wallahi da zan gan shi shi So din dana

rade masa kai don Ubansa, tunda ya hana ki ki

zauna lafiya." Ta dafe kirji gami da jingina da

kujera tana fadin, "Sala ki kyale ni kawai tunda

dai kin ce baki san So ba, yanzu haka kirjina ciwo

yake mini, lallai idan na rasa Mustafa na san

mutuwa zan yi don Allah ya jarabce ni da

tsananin son sa, zan iya yin komai don na same

shi Sala, yanzu kam na gane so yana gaba da

kudi da komai, ki rabu dani kawai don na yiwa

Mustafa alkawarin ba zan kuma kula kowa ba zan

yi ta jiransa har ranar da Allah ya sanya iyayansa

suka amince ya aure ni din." Sala tayi Salati tana

tafa hannu tana fadin, "Shike nan an sammace

mini ke Zainabu, don in dai ba asiri ba babu

abinda zai sanya ki gaza hulda da kowa sai shi

kadai, kuma yanzu ba ya nan baya ganinki ba kya

ganinsa ma, amman kin ce ba zaki iya kula kowa

ba, to wallahi ya yi a banza, don ni ma ai ba'a

zaune nake ba, duk neman sa'ar da nake miki a

ce ya tashi a banza, bari na tafi gurin boka na

kan tudu zan sanya ya raba min ku, idan ya so

sai na ga karshen shegen So din, tunda dai shi

ciwon masifa ne." Zainabu ta riko hannun Sala

da ke shirin fita daga dakin nata tana fadin, "Sala

kada ki rabani da Mustafa idan dai ba so kike na

mutu ba, shin wai kin san abinda ya sanya iyayan

Mustafa ma suka hana ni aurensa? To ba wani

abu bane illa yawon da nake yi na bin maza

tamkar karya, kowa ya zo ya dauke ni a mota ya

je yayi abinda ya ga dama da ni kan kudi, sun ce

ni karuwar gida ce, yanzu me ye amfanin irin

rayuwar iskancin da na yi? Ni kam zuciyata ta

gyaru don haka na bar abinda kike so na yi." Sala

ta kuma shiga rudu ta ce, "Ahaf! Kinji ba? Ai na

sani asiri yayi miki, banda asiri ke da bakinki ki

dinga kiran kanki 'yar iska, yanzu kin yarda ke

din 'yar iska ce? Kalmar da da idan aka gaya miki

sai inda karfinki ya kare amman yanzu kike gaya

wa kanki, to ba karuwa ba ko ke mecece kinfi

karfin danta wallahi, idan tace kuma ke karuwa

ce shi dan nata ai karuwi ne tunda dai shine ya

watsa miki rayuwa, sai nayi maganinsu shi da

uwar tasa in dai sunana Sala." Ta warce

hannunta daga rikon da Zainabun tayi mata ta

nufi waje tana cigaba da bala'inta.... To, masu

karatu, mu hadu a littafi na biyu don jin yadda

Sala zata aiwatar da wannan mataki.

Take cewa kar ku damu na dayan tare suka fito

da na biyun,Mai kaunarku da yi muku fatan

alkhairi a kullum: FAUZANKU CE! Mrs Q for Q,

Ku ziyarci blog dinmu domin karanta Littatafai

masu nishadantarwa

Anamdorayi.mywapblog.co

Kokuma ku kasance taredamu a facebook

https://mbasic.facebook.com/HAUSA-

Novels-389304544597988/?_e_pi_=7%2CPAGE_

ID10%2C737012347


0 Response to "Idan zuciya ta gyaru Hausa Novel"

Post a Comment