Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Grow Fund domin ba da tallafi ga matasa masu son yin kasuwanci
Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Grow Fund domin ba da tallafi ga matasa masu son yin kasuwanci
Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Grow Fund domin ba da tallafi ga matasa masu son yin kasuwanci, wadanda suka samu horo a shirin Inspire Create Start and Scale (ICSS). Wannan tallafi zai taimaka wajen samar da kudade masu saukin biya ga matasa sama da dubu shida (6,000) da aka horar domin rage gibin da ake fuskanta a cikin samun kudaden jari ga kanana da matsakaitan kamfanoni a Najeriya.
Shirin Grow Fund na gudanar da shi ne ta hanyar Cibiyar Cigaban Kanana da Matsakaitan Kamfanoni ta Najeriya (SMEDAN), kuma an kaddamar da shi a Abuja tare da hadin guiwar Deutsche Gesellschaft für Internationale Zusammenarbeit (GIZ) da kuma Society for Organisation, Planning and Training da Kaduna Business School.
A lokacin kaddamarwar, Ministan Harkokin Matasa, Ayodele Olawande, ya bayyana cewa gwamnatin tana da niyyar tabbatar da cewa shirye-shiryen horaswa ga matasa sun kai ga samar da dama a cikin tattalin arziki. Ya bayyana cewa matsalar rashin samun kudade na daga cikin manyan kalubale da kasuwancin matasa ke fuskanta, wanda shirin Grow Fund zai magance.
Shirin ya maida hankali ne wajen samar da kudaden jari a fannonin noma, masana'antu, harkokin kirkire-kirkire da fasaha, da kuma fadada shirin a dukkanin jihohin Najeriya. Za a ba da tallafi ga kamfanoni da suka samu horo a cikin shirin ICSS, wanda ya hada da dabarun samun kudade da kuma tsarin kasuwanci.
Don yin rijista da kuma nema wannan damar, ziyarci wannan hanyar haɗi:
https://smedan.gov.ng/icss/icss-registration/
Ranar ƙarshe domin aikawa da aikace-aikace yana tafe, don haka kada ku bari wannan damar ta wuce!
0 Response to "Gwamnatin Tarayya ta kaddamar da Grow Fund domin ba da tallafi ga matasa masu son yin kasuwanci"
Post a Comment