Ma'aikatar Ilimi ta Tarayya (Federal Ministry of Education) na sanar da neman kwararrun masu horarwa da su nemi gurbin aiki a matsayin Technical Facilitators (Masu Gudanar da Horon Fasaha) a dukkan Kwalejojin Fasaha na Gwamnatin Tarayya (Federal Technical Colleges) da ke fadin Najeriya.
Wannan dama ce ga kwararrun da ke son bayar da tasu gudunmawar a karkashin shirin bunkasa ilimin sana'a da fasaha na TVET (Technical and Vocational Education Training), wanda ma'aikatar ke gudanarwa a halin yanzu.
Muhimman Bayanai:
Matsayin Aiki: Technical Facilitator.
Wurin Aiki: Dukkan Kwalejojin Fasaha na Gwamnatin Tarayya (FSTCs).
Ranar Rufe Aikace-aikace: 16 ga watan Maris, 2026.
Yadda Za A Cika:
Ga masu sha'awar neman wannan gurbin, ana bukatar su cika fom din neman aiki ta yanar gizo ta hanyar amfani da adireshin da ke kasa:
Hanyar Cika Form: https://forms.gle/Cjoq5YeuUASqyAqF7
Kada ku bari wannan damar ta wuce ku!
0 Response to "AYI RIJISTA YANZU: Ma'aikatar Ilimi Ta Tarayya Na Neman Masu Horarwa (Technical Facilitators)"
Post a Comment