-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Kalaman Bada hakuri a soyayya 2023

Kalaman Bada hakuri a soyayya 2023

Kalaman Bada hakuri a soyayya 2023

Amincin Allah ya tabbata a gare ki ya ke wacce ta fi tauraro da duk wani haske. Haske a idanuwa na, Ina fatan dai ba fushi kike da ni ba. Zan iya manta komai amma ka sani ba zan iya mantaka ba haka kuma zan iya jure rashin komai amma ba zan iya jure rashinka ba, hakika daga jiya zuwa yau ina cikin kunci mara misaltuwa, bakin ciki y ziyarci zuciya ta wanda har kawo i-yanzu ba na jin zan iya kula wani cikin walwala.

Idan har na ce zan iya na yi karya domin ni kadai na san irin halin da nake ciki na rashin jin dadin tafiyarka.   Zuciyata na tafasa har nakan ji tamkar na fashe da kuka ka sani cewa, wannan sakon duciyata na sanar da kai, hannu aikinsa rubutawa ba wai ina fada ne don tsari ko don ka ji dadi ba.

Daga lokacin da ka hada yanaka-yanaka ka yi gaba ni ma daga wannan lokacin na tattara duk wani walwala na da farin ciki na na ajjiye su a can gefe barin da ba za su taba kusanto ni ba. Don haka ina sanar da kai ban yi fushi da abin da ka aikata ba kuma ban kiraka don ka bar abin da kake ba, illah na kira ka na ji laifin ba daga gare ni yake ba. Ka kasance cikin farin ciki ka huta lafiya. Na gode da kulawa, amma  ina ga ba ki kai ni shiga kewa da zullumi ba, dama an ce ba a sanin muhimmancin mutum sosai sai a lokacin da ya yi nisa da kai.Hakika jiya na kara gasgata wannan maganar.

Domin nisanta da na yi da ke na yini daya sai na ji kamar shekaru dubu ne, Kin riga kin zama fatar jikina duk wanda ya raba ni da ke kamar ya raba ni da kyauna kwarjini na hade da suturata. Ke garkuwa ce a gare ni mai kare ni daga abubuwa da dama, Hasken zuciyata farin cikin raina, annashuwa da jin dadi na. Ina sonki ina kaunar ki, ba zan iya nisa da ke ba. Ba zan bar ki ba duk rintsi duk wuya, Sai dai in ke kika bar ni  zuciya kuwa ba ta fatan ko mafarkin hakan balle a gaske. Ina so ki sani cewa soyayyarki ta yi nisa cikin zuciyata.

A hankali – a hankali ina ta ba ki filayen zuciyata ina so in rasa kaina a garin yin hakan ta yadda ba zan taba samuwa ba da sannu sannu dai ina ta mika rayuwata izuwa gareki ya masoyiyata kinzama abar kaunata wannan duk saboda karamcin kine a gare ni a yayin da nake kara kusantuwa dake duk tunane-tunane na suka fara bayyana ya masoyiyata kin zama abar kaunata kamar giza-gizai haka kika zamo inuwa a gare ni kamar ruwan sama haka kika jike ni da farin ciki kamar iska haka kika tafi da tunani na kin sabunta kaddarata ta hanyar samar da sabuwar safiya a rayuwata.

Dake kawai nake son kare rayuwata ya masoyiyata kin zama abar kaunata Kada ki taba mantawa da cewar wani na rayuwa ne kawai saboda ke ko ina zaki je ki tuna da hakan wani na rayuwa ne kawai saboda ke a duk inda kike ina miki fatan aminci addu’ar da zuciyata keyi kenan tamkar kyakkyawar abokiyar alaka haka rayuwa take idan kina tare dani a duk lokacin da kika yi nesa dani rayuwar sai ta zame mun ba dadi irin son da nake miki ta yaya zan iya bayyana shi wadannan idanuwan nawa tsahon dare suna tsayawa cur! kuma sunayin kuka duk da kasancewar ina tare dake me yasa nake jin kewarki? na kasa fahimtar miye hakan ki fada mun har na same ki duk da haka ina nesa da ke.

 Yayin da kika iso bakin kofar zuciyata na sadaukar da rayuwata ga sunanki na koyi yadda zan rayu masoyiyata ada ban taba koyon yaya zan rayu ba ban taba koyon yadda zan rayu ba tare dake ba, masoyiyata wadannan yabo ne na gaskiya nake miki da zuciyata yayin da na same ki sai duniyata ta kawatu matuka duniyata ta cika burinta duk kanmu ba a ciki muke ba yanzu ne da muka hadu muka zama daya.

Ina ma a ce na kasance da ke a duk bugun numfashina, kaunarki ce take kara tasiri a ruhina, babban burina na ga bayyanar fitar murmushinki a kan wannan kyakykyawar fuskarki, ya kuma zamana ni ne sanadin hakan. Bana son Allah ya kawo lokacin da za ki fushi da ni sosai kaina ba zai dauka ba, hakika Allah ya wadata ki da abin da mata da yawa suke nema sun rasa ke kanki kin san a cikin jinsinku, mata irinku kadan ne da a ce na iya rubuta labari da a kan fuskarki zan rubuta littafi mai suna kyauta daga Allah, kuma na san zan samu bayanan rubutu kamar guda uku 1,2 da 3.

Sararin samaniya na cike da taurari, teku na cike da ruwa, doran kasa na cike da ciyayi, amma ni zuciyata cike take da soyayyarki ba ta gushewa kamar yadda taurari ba sa gushewa a sararin samaniya, ba ta kafe wa kamar yadda teku ba ta kafe wa, haka zalika ba ta bushe wa kamar yadda ciyayi ba kamar sukan bushe, soyayyarki dauwamammiya ce a farfajiyar madinan zuciyata da akwai wanda zai tsaga jikina da ya ga jininki yana gudana, a kan kaunarki na manta kaina, kikan hau ingarman doki domin ki taho mafarkina, wannan sunan da kika boye a tafin hannunki idan dare ya yi, ki duba sararin samaniya kin ga mai wannan sunan yana haska duniya masoyiyata, hakika na kasance mai bayyana a mafarkinki kin kasance a fatar lebena. Duk wani taku da na yi a doran duniya sai inji takun na iso ni zuwa gare ki. So marurun zuciya ya yi min saka tun asali so ya shige zuciyata yana min suka.

Ganinki burina, idanuwana ko bacci na farka ki amshi soyayyata abadan kada na koka ba ni barinki cikin kunci yaki zo na yi miki tarba. Daga motsin numfashina kika ziyarci rayuwata a matsayin abokiyar rayuwa a duk zantukana sai na ambace ki. Damuwarki kullum tana cikin tinanina ke ce jin dadina kuma ke ce bacin raina ke kadai ce a zuciyata kalamaina, zabina jin dadina, bacin raina, saboda da ke kawai nake rayuwata, kaunarki ce ke kula da ni take kuma kau da duk wata damuwa daga raina koda a ce babu ni ka san tuwata zan zamana a tare da ke har abada. Kamar yanda baki bai isa ya furta ba haka jiki bai isa ya nuna ba, sannan zuciya ta yi kadan ta kwatanta ruhinki ne kadai ya san yadda nake jinki a sakamakon ziyartar da yake yi wa ruhina a kowane dare ina sonki ba zan daina ba har abada saboda ban isa na daina ba.


Soyayyata da ke ba ta mutuwa kuma ba ta tsoran mutuwa koda za a yi mana kwace, ko da za mu mutu ko za mu lalace to soyayyar mu za ta kasance a raye na bayar da zuciyata na karbi ta ki na kamu da sonki. Ki tallafi rayuwata da ta tsunduma a kan tsananin soyayyarki, ki tausayawa zuciyar da ta shagala a kan tsananin soyayyarki ka da rintsi ko zugar mahassada ya sa ki guje ni ko kuma ki rage son da kike min, sonki yana dankare a zuciyata kamar yadda kwakwalwa ke dankare a kan dan’adam da a ce zan samu ikon fito miki da shi da na yi domin ki kara gazgata tsananin kaunar da nake miki.  

Labarin Zainab Da Mubarak (7)

Har zuciyarsa ta burge ta sosai don ya iya tsari sai dai kuma ta san ba zai yiyu ta aure shi ba, cikin sauri ta kawar da wannan tunani ta ce “ai na za ta ba zuwa za kai ba, sai dai shi har yanzu ya kasa daina kallonta, shi ma kwalliyar da ta yi ta dauke hankalinsa gaba daya. Wani Material ta saka (Purple) wanda aka ratsa masa (pink colour) a jiki, dinkin riga da siket sai kuma ta dauko (pink) din mayafi ta dora a kai shi ma takalmin ya dace da mayafin jikinta, a hankali ya saki ajjiyar zuciya tare da murmushi ya ce “ Ni na Isa?, kin san ganinki ya fiye min komai” Sai fa ya zuba wa Zeey ido da colour da ke gefen precious wani irin wanda ya sa duk ta bi ta tsargu don kunya, ta sunkuyar da kanta ya ce “’yan mata adon gari, kin yi shiru, ko rowar muryar ake mana?” Ita dai Zeey colour ji take tamkar mafarki take yi, don ta tabbata duk wanda ya ga Seif dole ne ya yaba tsarinsa, precious ta yi gaskiya Saif yana da kyau sosai kuma gashi ya iya kwalliya don duk ya hada komai na kyau wanda ake bukatar a ga da namiji da shi, fari ne kyakkyawa na kin karawa, gashi dogo, hancinsa dogo, bakinsa dai-dai misali, idanuwansa gwanin ban sha’awa, gashin kansa akwance yake irin na Fulani.

Hasali ma ga iya furta zance sai dai kuma abin da ta lura da shi akwai jiji da kai hakan kuwa ba ya daga cikin tsarinta. Ta kale shi ta yi shiru na dan wasu dakiku kanar ba za ta yi magana ba, daga bisani kuma ta ce “Uhm..! Ya kake?, ya kuma hanya?”, Saif ya ce “ Lafiya lau, ina fatan dai kina kula min da baby na ko?” Ita dai Zeey colour har ta kagu tabar wajen ta koma ciki, a ganinta ya fiya kallo, a hankali ta danyi murmushi ta ce “Kamar ka sani, kullum ni nake kula da ita”, Precious kuwa har zuciyarta ji take kamar tafi kowa farin ciki don ganin gata ga Saif , cikin fara’a precious ta ce “ Wannan ita ce kawata Zainab ana kiranta da Zeey colour wadda nake ba ka labari ba ni da Aminiya kamar ta” Saif ya tsura mata idanu yanayin yanda take magana yana burge shi hakan ya sa ya ci gaba da saurarenta tare da bin kallon bakinta da yake motsi…

M asoyiyata abar kaunata ki sani ina sonki ina kaunarki son da nake miki har ya kai ga…..ko da idanuwana a rife suke ke nake gani idan na bude su ke nake son gani. Ko da ba na tare da ke ina jin motsinki a cikin jikina Lokachin da nake tinaninki, kadaici shi ya fiye min komai dadi. Me ya sa kina rayuwa a cikin jikina ni ma ina rayuwa a cikin jikinki amma duk da haka nake jin tsakaninmu da nisa?

Sarauniyata taho gare ni ki kama hannuna ki furtamin kalmar kauna a cikin kunnuwana…na rayu saboda ke ki zo ki mutu a kai na…ki sani ni fa ko a lahira idan an tashe mu to ke nake so a matsayin matata….na samu biyayyarki me kuma ya rage zan roka a wajen ubangiji?


kawai numfashi nake so ga ubangiji don mu yi soyayya mai dorewa ni da ke….fatana Allah.ya tsawaita mana rayuwa ya ke abar kaunata…wacce nake ganin sunan ‘ya’yan da zan haifa a cikin idanuwanki….fakina da idanuwana ba za su iya fada miki ko kwatanta miki adadin son da nake miki ba don tuni na shide a cikin sonki, na zama ke…. 

Ke dai taho gare ni dauke da kauna za ki gane ni ne na ki..ba ni da ta cewa sai godia ga Allah da ya ba ni yar fara mai fararen idanuwan da suka dace da kyakkyawan hancinta wanda ya yi daidai da kyakkywan kumatunki…wanda ya sa kika zarce sauran mata a kyau.

Ya ke mai kyakkyawar kirar jikin da babu irinki..mai iya kwalliya tamkar dawisu..mai zakin murya kamar kanari..takawarki lafiya mai tafiyar aasaita tamkar jimina kin isa ne dole ki yi domin duniya ban ga kamar ki ba ko kusa babu ba aiba kuma ba za ai ba

Ya ke rayuwata na dauki amanarki daga nan har izuwa ranar tashin alkiyama, ya ke wadda saboda tsananin kyauta idan tana tafiya ba takalmi samaniya ke ji kamar ta sakko kasa ki takata don ta ji me doran kasa ke ji.

Ke dai bari kawai ki sha kuriminki ni na ki ne ke tawa c,e kuma mun riga mun yi alkawari…ni da ke ke da ni jiki biyu ne muka zama rai daya zuciya daya…ba rabuwa har abada wannan shi ne alkawarina fatana ga mahalichchinmu ya cika mana burinmu. Sarauniya rife bakinki ba sai kin ce komai ba zuciyarki da gangar jikinki da kyawawan fararen idanuwanki su riga sun sanar da ni irin tsananin son da kike min don haka kwantar da hankalinki ba sai kin fada ba na san ba zai kwatantu ba ke dai samu guri mai kyau a cikin zuciyarki ki kara boye ni kawai domin ni na ki ne ke kadai

Hanya daya da zan bi na kwantar miki da hankali ita ce abin da kin riga kin sani kuma zan kara jaddada miki shi ne…..idan ba ke ba ni idan ba soyayyarki ba nimfashina duk wata ya budurwa a idanuwana fanko ne domin ke kadai nake gani na san na ga ‘ya mace kin ga idan ba ke a tare da ni ba zan iya gane ni da namiji ba ne don haka ni na ki ne mai sonki har abada soyayyarki ce jagorar rayuwata matukar ba soyayyarki to ba zan amfana ba kidai rike ni amana, ni ne dai na ki wanda ya zama ke, kika zama shi.

Kasan cuwar mu na ‘yan adam a doran ƙasa, Allah ya halicce mu ne don mu bauta masa kuma shi ne ya sanya soyayya da sha’awa a tsakaninmu. Saboda haka samarin da suke ƙoƙarin ganin mallakan zuciyar ‘ya mace ko kuma samun zuciyarta ba tare da wata mishkila ba, ga wasu hanyoyin guda takwas da ake bi don sace zuciyar budurwa.


1. TSARI: Duk wata ‘ya mace tana son ta ga namiji mai tsari, ba wai tsari irin na magana ba. Abin da nake nufi da haka shi ne, namiji ya kasance yana da tsarin rayuwa mai kyau, ba mutum ya zama shashasha maras kan gado ba.


2. KYAU DA KWALLIYA: Wasu matan suna son mutum mai kyau da kwalliya ba irin su wancan nanka ba, sau da yawa za ka ga mata suna soyayya da saurayi saboda tsabar kyau da Allah ya ba shi, da kuma iya kwalliya kamar ɗawisu.


3. KALAMAI: Yana da kyau namiji ya zama ya iya kalaman da za su janyo hankalin duk wata ‘ya mace, rashin iya kalami kan janyo rashin masoyi. Maimakon haka sai ka zama tamkar ɗan bora a soyayya. Dole ne ka kasance ka iya kalaman da zaka birge budurwa.


4. KIRKI DA KULAWA: Namiji yakan tafiyar da zuciyar ya mace dalilin kasancewa mai kulawa da kirki. Misali duk bayan wani lokaci ko sa’ar da ba ta fi rana ɗaya ba, ko kwana biyu a ce kana zuwa ganin ta ko kuma kana kiran ta, idan ya yi yawa ne a ce kun haɗu sau uku. Musamman ma a irin wanan lokacin da wayar hannu ta zama ruwan dare. Wani lokacin idan haɗuwa ta yi ƙaranci sai ka kirata a waya. Amma fa ka sani yawan zuwa gun mace ko masoyiyarka ce wani zubin nasa gundura. Ma’ana za ta ji duk ta gaji da ganin ka, musamman idan ya zama soyayyar taku ba ta yi ƙarfi ba.


5. KAR KA RIƘA YAWAN YI MATA MAGANA GABAN ƘAWAYE: Ka guji yawan kula yarinya cikin sahun ƙawayenta ko kuma cikin jama’a. Hakan zai karama kima, sannan da nesan ta kanka ga barin wulakanci. Wata kila lokacin da ka je mata cikin jama’a ko ƙawayen ta, ta ji tana son ka. To amma watakila a lokacin shigar da ka yi bai yi mata ba. Hakan zai sa ta guje ka, wanda yin haka a soyayya wulakanci ne ga masoyi.


Mafi kyawu shi ne ka jira ta keɓance ko kuma ta koma gida. Idan ba haka ba, to sai dai idan sun kai koda su biyar ne, to kuma ya zama dole ku kasance ku biyar koda sauran ba sa san ‘yan matan. Saboda su kasance masu ɗauke masu hankali a lokacin da kuke hira kuma suma sauran ‘yan matan yin haka zai nuna cewa wadda kake so ba ta fita daban a cikin su ba. Duk abin da sauran ƙawayenta suka ce a kanka da shi za ta yi amfani.


6. BARKWANCI: Idan ka kasance mai raha ga masoyiyarka to nan da nan za ka sace zuciyarta. Misali ka riƙa ce mata a duk lokacin da ka zo hira da ita, amincin so gareki ya tauraruwan zuciyata, ɗaya tamkar da goma cikin sahun mataye, a do da kyau siffarki ce, murmushinki ke sanya zukata fara’a. gimbiya adon ‘yan mata. Da sauran su. Kana mai ambaton haka cikin murmushi da shauƙi irin na soyaya kuma dole ne hirarku ta kasance mai amfani ba ka yi ta zuba ba, har sai ka gundure ta. Yawan magana ba shi da tasiri a soyayya muddin ba magana ne masu ɗauke hankali da san ji ko rashin gundura ba.

7. KUƊI DA KULAWA: Mata suna son samun saurayi mai tashen kudi da kulawa cikin bukatunsu a koyaushe. Idan ta samu wanda ya haɗa waɗannan abubuwa kuma ya tafiyar da su yadda ya kamata, to abu ne mai sauƙi ya sace zuciyar budurwa. Akwai mazan da suke roƙon ‘yan matansu kuɗi; wannan ba soyayya ba ce, sai a kira shi a kwaɗayi.

8. KYAUTATAWA: Sai dai kuma duk da na yi bayani kan cewa kwaɗayi bashi da kyau a soyayya, hakan ba shi yake nuna ba za ka kyautatawa masoyiyarka ba. Hasali ma idan kai haka, to za ka ƙara ƙarfin shaƙuwa ne tsakanin ku da juna. Sai dai idan za a yi kyautaa duba me masoyiya take da buƙata a daidai wannan lokaci. Misali, kar ka kawo mata hoda a lokacin da take buƙatar turare, atamfa, yayin da ita kuma leshi take so.

Sanin haƙiƙanin abin da budurwa ke so, ko da ku fara soyayya da ita, ko ba ku fara ba, yana taimakawa ƙwarai wajen sace zuciyarta.

3 Responses to "Kalaman Bada hakuri a soyayya 2023"