-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Abakin Aurenki HausHausa Novel

Abakin Aurenki HausHausa Novel

 A BAK'IN AUREN KI...

漏Feenat Ja'afar.


1_Sauri take tamkar taci da k'a, kai daga ganinta

ka ga marar gaskiya, a d'ai d'ai layin da zai

sadata da gidanta ta t'saya tamkar munafuka ta

d'an leka, da sauri ta komar da kai tare da dafe

kirjinta mai barazanar fashe mata... "Na

shigesu.. Ja'afar? Ta fad'a tana mai sake

lekawa, sai karaf sukai ido hud'u dashi,tuni

buguwar zuciyar ta ya k'aru, bata ta6a ganin shi

a irin wannan yanayin ba.

"Mey yasa kika fita bayan yace ka'rki fita?...

Bak'in g'yalenta tasa tana t'sane gumin dake

t'sat'safo mata, cikin jihadi ta fito daga inda ta

boye harda d'aure fuskarta tamkar bata ganshi

ba.

Kanta na k'allon gefe tazo d'ai d'ai kofar gidan

zata shige ba tare da ta k'alli yanayin nashi ba..

Turus taja ta t'saya, ganin yadda ya d'aura wani

mukulli kan wanda ta rufe gidan dashi, cikin

k'arfin hali fuskarta na gefe tace "ya haka?

Wanda bai nan ma yafita,hakan yasa ta kara

fad'in "Ya Ja'afar ya haka?.. Tamkar kububuwa

yake cika, ji yake tamkar ya rufeta da duka dan

takaici, Ashe d'uk uban rat'suwar Salma ta mai

kan ta d'aina a fatar baki ya t'saya?..

Mota ya bud'e yana ko'k'arin shiga ta mot'so da

sauri, "Ja'afar magana nake fa... A tunzure ya

juyo da nufin kifa mata mari tai baya da sauri

gabanta na fad'uwa.

Lalle yau ta ta6o ran y'an maza, cikin bacin rai

yai mata k'allon banza, "kin za6i gidan suna

sama da sharad'i na koh? Toh mey kika dawo yi

min gida? Koh kin manta da sharad'in da na baki

na in kin fita toh kin fita "A BAK'IN AURENKI?...

Ido ta zaro tana dubenshi, kawai sai ta dake,

cikin k'arfin hali tace "A BAK'IN AURENA fa kace

Ja'afar? Daga gidan sunan shine har kake

wannan kumfar bak'in?.. Ta karasa tana y'atsine

mishi fuska,kawai sai ya k'ada kai ya shige mota.

Ganin da gaske tafiya zai yasa da sauri t ajiye

t'siwar ta fara kiranshi, ina,tuni ya juya a kalar

motarahi cikin zafin nama, da sauri ta mat'sa

ganin sai ya iya bi ta kanta..

Tana ganin da gaske yake hakan yasa tuni ta

t'sure, hannu ta aza bisa kanta cikin nadamar

fitar da tai sunan da ba'a ma gaiyace ta ba, "na

shiga uku ni Salma.. Na ja ma kaina wani bala'in..

"Yanzu igiyar Aure na biyu ta t'sinke kenan?..

Tuni zufa ta kara zubo mata dan tunawa da

kalaman Babanta, "d'uk randa zaki kara maimaita

haka Salma sai na 6alla kafarki in kin doso

gidana.... Fad'uwar gabanta ta t'sananta,t'saf

Baba zai aikata mata hakan,

ta k'alli gabar,da yamma, ta ma rasa ta ina zata

fara? Gefen dakalin gidan ta d'an dosana, da

d'ukkan hannunta biyu ta dafe kai,tuni kalaman

Ja'afar ya dawo mata, "in kin fita kin fita A

BAK'IN AURENKI....

Ku biyoni Bayan sallah dan jin yadda zata kaya...

By

Feenat

Ja'afar.

9/29/16, 8:46 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. *3*-

Kai ya k'ada mishi, _"aure ba shine mafita ba

Ja'afar,ka g'yara wacce ke hannunka tukun,bana

tunanin wannan shawara ce_. Murmushi yai tare

da k'ada mishi kai _("I know)_.. _"Amma ka gane

ba dan dad'i zanyi ba,nasan d'uk duniya ba

abinda Salma taki jini irin nace zan kara

aure,dole na d'andana mata mad'acin da ta

d'andana min nima_. Murmushi Garba yai yana

K'allonshi,wai yau Ja'afar ke maganar zai

d'andanawa Salman sa mad'aci?.. Kai ya girgiza,

lalle Salma tai wasa da damarta, dan yasan irin

dimbin son da Ja'afar ke mata, sai dai gashi za a

kaita a baro,dan ta fara sane ma abokinshi..

_"Bana tofa tawa ba nikam,nasan da kai da

Salma sai Allah,ni d'ai kai tunani abokina,kar ka

yanke hukunci cikin fushi azo daga baya ai

nadama_... Baki ya ta6e, kan ya ciro mukulli a

aljihunshi ya mika mishi, _"k'ar6i mukullin

motarka,dan aure kam nayi na ma gama,kuma

*Bintu* zan aura kasa ido_.. Ido waje Garba yake

k'allonshi,kan ya k'yalk'yale da dariya, _"lalle ka

d'ebo aiki..za kuma ka dasa ma Salma zargin ka

cikin ranta tunda kasan komai_... T'saki yai kan

yace _"zanso hakan ya kasance, dan zata fi jin

haushi sosai_.. Kai Garban ya k'ada yana kunshe

dariya, _"muje na sauke ka toh na Salma da

Bintu,kai (scene) din nan zai dad'in k'allo

wallahi_.. Ya karasa da dariyar keta. Murmushi

kawai yai suka shiga mota,har suka isa gida

Garba na mishi t'siya..da ya had'o shi da Salma

zai kicin-kicin. ************************ A wajen

Salma kuwa,sai da dare yai tana k'wance

d'akinsu na da sai juyi take,wanda ita kanta ta

rasa dalili,har yanzun haushin Ja'afar na kasan

ranta na ya mata wulakanci, sai dai da ta tuna

rabuwar igiyarta d'aya sai taji fad'uwar gaba. Yau

gata a katifa ba ta ita da Ja'afar d'inta ba?..yau

d'aya ta raba alakar matashin kanta(kafad'ar

Ja'afar) sai pillow... Hannu takai kuncinta,da

mamakinta hawaye take,kawai sai ta ida

karasawa ta fashe da kuka.. Wanda kai da gani

na k'ewar Jafaririn ta ne da t'sant'sar

nadama,amma ina,zuciya taki amsar hakan.. Ga

uban sauro da ya damu k'unnenta da ihu duk da

da Katanga a t'sakaninta dasu(net), ga uban zafi

ba wuta ba (Gen), d'uk t'siya tasan da a gidanta

ne da yanzu tana shan iskar injin da Ja'afar ke

k'unna mata d'uk dare ta k'wanta dan bata bidar

zafi.. Ga mama tace ba mai tada mata inji

Babanta baya gari, kuma bata kud'in mai... ***""*

Shima hakan take ga Ja'afar, kusan a hali d'aya

suke,sai dai shi kawai ya kura ma fankar d'akin

da ke kad'awa a saman d'akin ido. Tabbas har

yanzun baida sama da Salma koh a kasan

zuciyarshi.. Yana sonta, so marar misali,duba ga

yadda suka gina soyayyar tasu kamin aure.. Da

za'a ce mishi a da Salma zata sauya hali gaba

d'aya musamman akanshi da zai mu sa... Juyi

yai ya jawo filo,d'uk t'siya tanan yai k'ewar

Salma.. Dan karamin t'saki yai kamin ya tashi yai

waje dan kashe inji. *By* *Feenat Ja'afar*

9/29/16, 8:48 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 4-

Salma Umar Y'a ce ta biyu gun Mama(Haj Rabi'a)

da Baba(Malam Umar),y'an asalin Yobe

ne,kasuwanci ya kawo kakansu Kano da rabon su

Salma. Su biyu kawai ne a gun kakan su Malam

Bukar Mai buhu,baban su Salma ne karami, sai

yayanshi Baba Aji, yaranshi a kallah za suyi

(16),yayin da Baban Salma ke da uku,Aisha

(Aunty A'i)dan tafi Salma sosai,Salma,sai Ummi.

Kasuwanci ne gadon su Baba,dan koh bayan

rasuwar kakan su Salma sun cigaba da juya

abinda ya rage musu. Suna taimakon juna

sosai,hakan yasa kansu yake a had'e, duk da

rufin asiri ne kawai na Allah. Sannan d'ai-d'ai

iyawa sun bama yaran su karatu da tarbiya,suna

da t'sanani musamman Baban su Salma. Sai dai

fa ita Maman su gani take kakarsu ta yanke

saka,tunda Allah ya hore mata yara mata uku

setin samira ta zuba jari,shi yasa d'ukkan wani

abu akan A'i yake karewa dan ita tasa a lokacin.

Ba lefi,ak'wai dan k'yau irin na ainashin mutan

kanuri,sai kuma Maman dake asalin Shuwa,ba

farare bane,za dai mu iya kiransu da _"black

beauties"_sirrin su kuwa,diri ne da yalwar gashin

ka da _"beauty point"_ _(dimples)_.. Wanda

tamkar kowa diga mata ake. Hakan yasa kasuwar

Aunty A'i ta daga da sauri,tuni k'wa Mama abin

nema sai ya samu,hakan yasa ta kara sa ma

sauran Burin da yafi na Aunty A'in.. Barin Salma

dake doguwa ce cikin su. Ita kam Salma bata san

ma ana yi ba. Kasantuwar shagonsu Baba ya

zama biyu sai ya zamana aiki yai musu yawa,

har bai samun damar dawo wa gida cin abinci sai

d'ai Ummi koh Salma su kai mishi. Ranar kaiwar

Salma ne,tai shirin Islamiya ta doshi shagon su

Baba. Tunda ta ajiye abinci taki gaba taki

baya,kamar dai da alamun an mata abu daga

gida. Murmushi Baban yai kan yace tazo.. _"mey

aka miki uwata?_ Hawaye ta dan matso halamar

6aci. _"Mama ce ta hana ni kud'in tara_. Kai

Abban ya k'ada yana murmushi kan ya sa hannu

a aljihu ba chanji,gudar naira dari ya fitar kan ya

nuna mata shagon kusa dasu taje tai chanji. Da

sallamarta ta shiga,ta gaida shi,shago ne na

kayan k'yallin mata na sawa, attamfofi da

laces,ga materials kala kala,d'uk zuwanta bata

ta6a shiga shagon ba sai yau. _"Salamatu y'an

mata,ina su Ummi?_ Murmushi tai mishi,dan tana

ganin shi gun su Baba, dattijon na da kirki da

fara'a, banda yaron shagon shi da koh k'allo bai

mata ba, _"suna gida,Baba ne yace aban chanji_.

Kai ya k'ada, kan ya k'allo na zaune a acikin

shagon rike da littafi halamar yana dubawa.

_"amm *Ja'afar*_.. Kai ya dago karon farko,

_"Na'am Abba_,, sai lokacin ya kula da Salma,

_"Ba wa Salma naira ashirin ta tafi kar tai latti_.

Kai ya k'ada kan ya kara k'allo Salman wacce sai

hange take koh za taga wani dan islamiyar su

tana mika hannu. _"k'ar6i man_.. Juyo wa tai

taga yana miko mata kud'i fuska ba fara'a, da

sauri ta k'ar6a tana tafiya tana fad'in _"na gode

Abba_. Da k'allo Ja'afar ya bita,yana ganin Ummi

ce mai rawar kai ashe sauran ma haka suke.

_customers_ ne suka tada shi ya shiga shagon.

Washegari ma sai ga Salma,wannan karan koh

shagon su Baba bata je ba tai shagon su Ja'afar.

Da mutane da kusan d'uk y'an mata ne suna

siyayya, yana ganin Salma ya had'e rai, sam yaki

jinin a 6ata yaro da kud'i, ita kam Salma harda

mishi murmushi tana dago mishi hannu da kamar

abu aciki. T'saki yai,kan ya cigaba da abinda ya

ke,sai da ya sallami kowa kan ya ganta tana

gaida Abban shi da ya fita yana nuna mata cikin

shagon. Da dan gudinta ta shigo,a tunanin shi

kud'i Abban yace ta kara k'ar6a gun shi,dan da

zumudinta ta gaida shi. _"dama Abba ne yace

in_..... Cikin fad'a-fad'a ya katseta, _"bani da

chanji nima yau,jiya an baki kinji dad'i shin_....

Shiru yai sakamakon idonta da yaga ya cika da

k'walla tana k'allonshi. D'uk kuma sai jikinshi yai

sanyi.. A hankali ta ajiye masa gudar naira

ashirin akan benci ta juya tana goge hawaye. Ba

dai kud'in shi ta biya shi ba dan ya mata fad'a?

Da sauri ya d'auka da niyar k'wada mata kira ya

mayar mata sai dai tuni tai nisa sosai. D'uk

kuma sai yaji bai k'yauta ba. Yana nan zaune har

Abba ya dawo, _"kaga Salamatu wai kud'in ka na

jiya ya hau shine ta dawo ma dashi ba"_.. K'allon

Abban yai da sauri, _"Abba kud'i kuma?_

K'allonshi yai kan ya k'ada mishi kai, _"sai da

nace ta tafi wai A'a tana da wani,Salma ak'wai

hankali, ashe batai ma magana ba?_ Shi dai

Ja'afar yai shiru yana jin Abba,sai ya kara jin

wani iri. *By* *Feenat Ja'afar*.

9/29/16, 8:50 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAK'IN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. *5*-

Washegari sai zuba ido yake yaga Salma

shiru,dan d'uk jiya ji yake bai k'yauta mata ba.

Sai d'ai Salma har k'wana biyu shiru ba koh kalar

ta sai Ummi ke zuwa kawo abinci. Ranar Ummi

ta kawo zata tafi ya t'sayar ta da tambayar ina

Salma k'wana biyu? "tana gida Yace "ya bata

kawo abinci sai ke?.. Tana zungura baki tace

"sai gobe ne nata kawowar. Dan koh ita Ummi

Ja'afar ke hanata zuwa gun Abba mai k'yautar

naira biyar goma.. Sam baida fuska,shi yasa taki

jinin shi. Washegari kuwa tun da ya ga lokacin

kawo abinci yayi yake k'allon shagon su

Baba,yau ga k'ananan shi a shagon baida

mat'sala. Kamar ance ya dago,sai gata kuwa

sanye da kayan islamiya,sai dai duk tai kicin

kicin fuska ba walwala. Yana k'allon yadda ta

t'suguna ta gaida su Abba kamar kullum, tana da

nut'suwa ba kamar Ummi uwar bankaura ba.

Tashi yai kamar mai tafiya wani gun,dai dai

k'wanar da take bi gida ya t'saya,sai gata

kuwa,har zata wuce ya kira ta,suna had'a ido ta

had'e rai,sai ta bashi ma dariya. Hannu yasa ya

ciro naira ashirin d'in ya mika mata yana

murmushi, a dan sace ta k'allo shi kan ta kawar

da kai tare da girgiza mishi kai. *"Salma*..K'all

onshi ta kara,ganin yana murmushi sai abin ya

bata mamaki,bata t'sinke da lamarin ba sai ji tai

yace tai hakuri, kai ta kawar kawai, kin huce?

tana wasa da hijab d'inta ta daga mishi kai, "toh

ki k'ar6a in kin huce,na bar miki.. Kai ta kara

girgiza mishi,kan tace "A'a ka barshi fa.. "baki

hakura ba kenan Salma?.. Kai ta k'ada mishi,

yace "toh ki k'alle ni ki amsa maza kar kiyi latti

kinji K'anwata.. Da lallami yasa ta sakko harda

dariya,har kusan makaranta ya rakata ya

dawo,yana mai mamakin fara'ar shi yau ga

yarinya Salma,sam shi baida sakin fuska

musamman ga mace d'uk k'ank'antar ta k'wa.

Tun daga ranar ya zamo in Salma ta kawo abinci

sai Ja'afar ya rakata ya kuma bata ashirin d'uk

bayan k'wana biyunta. Sosai sun saba,har in

batazo ba baya jin dad'i, har su Abba suka kula

da sabon kawancan Ja'afar da Salma,ana haka

Baba yasa ya dinga ma wa su Salma _lesson_

tare da kannenshi tunda ya gama _secondary_

_admission_ yake jira. Koh a gun _lesson_ misalin

Ja'afar a Salma yake t'sayawa, in k'wa duka ne

koh t'sawa Salma bata ciki,sai dai yai ma

k'annenshi, hakan yasa tun tana karama yaran

suke ce mata Salma budurwar Ya Ja'afar. A

lokacin takanyi bori kan bata so,har takai da ta

kai kara gunshi,sai dai mamakinta dariya ma yai

mata,yau da gobe har Salma ta saba da tsokanar

k'annen Ja'afar . Karatu ake sosai za ai _coming

interest_, sai dai ba Ja'afar dan ya tafi Zaria

sakamakon _admission nashi da ya fito. Sosai

Salma tai k'ewar shi,har hakan yasa ta d'aina kai

abinci shago sai almajiri,a hankali har k'ewar ta

sake ta suka gama jarabawa sai zaman jiran

sakamako... Sai dai Ya Jaafar na chan k'wance

kasan zuciyar ta. Yau ga Salma a _boarding_

babban burunta kenan makarntar k'wana.

************************** Lokaci ya shud'e,

kamar wasa yau ga nan Salma an zana

_J.S.C.E_, hutun mai dan nisa ne na yau. Mai

nut'suwa ce a d'uk y'an gidan su,a layin su,dama

unguwar gaba d'aya, Salma abar k'watance

ce,musamman rashin yawanta,kullum kaje in tana

hutu toh za ka samu Salma a gida. Batta

k'warafniya irin ta y'an mata masu tashen

tashi,asalima fitar ta in tai yawa toh islamiya ce

ta yamma, sa6anin su Ummi da tuni tun kar ta

far ta kone, dan wanka iya wanka Ummi ta

iya,hakan yasa Mama ta kara d'aure mata gun

siyan kayan k'arya. Dan a ganinta ta gama da

kason Aunty A'i tunda har an kawo sadaki, kuma

irin wanda mama ke da muradi. Ita kam Salma

zai wuya ka ga tama sanya g'yale bare har ta

zauna k'yali. Gata dai mama ita tafi sawa buri,

ga ta kuma y'ar _boarding_. *By* *Feenat

Ja'afar*.

9/29/16, 8:52 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A

dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga

islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan

kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar

littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_

nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan

kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin

jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a

nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum

ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar

kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai,

sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar

ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin

nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar

da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a

zuciyarta lokacin da ya taso yana mata

murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take

ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi

ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama

Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce

ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta

muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa

ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta

gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake

yana murmushi, kamar mai mamakin kara

girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta.

D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun

yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya

halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta

sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar

gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai

duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada

da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe

gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun

bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai

kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida

ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda

suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan

dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha

zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da

Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar

d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai

gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa

wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar

d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da

kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har

Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata

gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai

kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale,

"da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada

kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar

yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari

muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma

koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi..

"Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni

Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma

K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi,

toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken

shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A

tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji

Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan

koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu?

Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin

tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da

kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare

ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan

uban d'acin ran kike wannan kumfar

bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama

abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son

fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki

ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki..

Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta

bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen

bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma

ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar*

Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 20

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 6-A

dai-dai k'wanar su Ja'afar take,dawo warta daga

islamiya kenan,sanye take da dogon hijab ruwan

kasa mai yashi har kusan kasa,rataye da jakar

littafai da Qur'ani a hannu,sai dan asirin _skirt_

nata na attamfa da ya fito _green_ da ruwan

kasa, duguwa ce,ba zangal ba,tana da kaurin

jiki,dan ta fita sahun ramammu,tafiyarta a

nut'sue tafi komai d'aukar hankali. Kamar kullum

ta daga kai dan k'allon gidan su Ya Ja'afar

kamar yadda ta saba k'ewar shi ta kawar da kai,

sai dai taku biyu taja ta t'saya tamkar an t'sayar

ta. Kanta duk'e dauke da murmushi,cikin

nut'suwa ta kara k'allon kofar gidan dan tabbatar

da wanda ta gani.. *"Ya Ja'afar*?...ta fad'a a

zuciyarta lokacin da ya taso yana mata

murmushi. Ikon Allah,wai kunyarshi kuma take

ji,cikin nut'suwa ta d'auke kanta daga gareshi

ganin ya karaso. "Assalam Alaikum Malama

Salma.... Wani irin buguwar zuciya taji ya ziyarce

ta,shekara uku da wani abin ba wasa ba,hatta

muryar Ya Ja'afar ta sauya mata. Cikin nut'suwa

ta dago da murmushi ta amsa mishi,kamin ta

gaida shi a kunya ce, shi dai kawai k'allonta yake

yana murmushi, kamar mai mamakin kara

girmanta,ga wata nut'suwa da ta kara shigarta.

D'uk sai ya kara yaba Salman nashi,ganin shirun

yai yawa yasa da hannu ya nuna mata hanya

halamar su wuce. Dan satar K'allonshi tai kan ta

sunne kai suka fara tafiya. "Salma koh murnar

gani baki yi,ba koh tambayar yaushe nazo? Kai

duk'e tace "yi hakuri,yaushe kazo?.. Kai ya k'ada

da murmushi,kan yace "jiya. Tambayar yaushe

gamo yake mata, yadda take kunyar tata gun

bashi amsa d'uk sai ya ji shi wani iri,mace mai

kunya itace muradinsa. Da haka har kofar gida

ya rakata yana mata tad'in makaranta da yadda

suka juma basu gamo ba. Ummi ya k'allo achan

dan nesa dasu tana tad'i, sai ya tuna mata yasha

zuwa ai. Ita dai daga murmushi sai k'ada kai da

Umm,a'a,d'uk ta takure yau a gaban Ja'afar

d'inta. Ganin haka yasa yai mata sallama tai

gida.. A katifa ta zauna tana cire hijabi,ta rasa

wani irin farin ciki take ciki na ganin Ya Ja'afar

d'inta yau. Sai murmushi take saka cike da

kunya ita kad'ai kamar yana ganinta. A haka har

Ummi ta cimmata, dan harara ta sakar mata

gami da had'a rai. "Yanzu Ummi kinyi dai dai

kenan? A y'atsine ta k'allo ta tana ninke g'yale,

"da nai miki mey? Iya jaraba.. Kai Salma ta k'ada

kan tace "dan t'sabar wulakanci ashe Ya Ja'afar

yasha zuwa gidan nan nema na in yazo gari

muna sa6ani sau biyu yana fad'a miki amma

koda wasa baki fad'an ba? Allah kin ban haushi..

"Mtsww.. T'saki Ummin tai kan ta ta6e baki,tuni

Salma ta kule,sam ta t'sani t'saki, bare ga Salma

K'anwar ta. "Na zata wani abin kirkin ne wallahi,

toh meye nawa dashi da zai mayarni y'ar aiken

shi?.. Anki a fad'a miki d'in ki d'au mataki toh.. A

tunzure Salma ta tashi tayo kan Ummin sukaji

Mama na magana a kofar d'aki, "Kun fara cin kan

koh? Yara kamar masu ganin hanjin junansu?

Baya Salma tai tana harar Ummi, "Mama kimin

tsakani da ita toh,ta fita harkata dan bata da

kunya sam wallahi.. A y'atsine Ummi ta harare

ta,"ka ga kunya manya,akan wannan mai dan

uban d'acin ran kike wannan kumfar

bak'in?...baki ta ta6e kan tace "Kin k'wa kama

abga in dai Ja'afar ne.... "Ke Ummi... Bana son

fit'sara fa,kullum ina sanarki Salma yayarki

ce,dole ki bata girma, koh nai mugun sa6a miki..

Maza bata hakuri. Tana chunno baki ciki ciki ta

bawa Salma hakuri,ita kam har ta fara hawayen

bak'in ciki. "Toh fito ki biyoni.. Mama ta nuna ma

ummin kofa da hannu.. *By* *Feenat Ja'afar*

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 20

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

7_Washegari ma ta fito zata makaranta sai gashi

shi da abokinshi Garba suna tafiya. Ido ya kura

mata ganin tai kasa da kai tana murmushi. Sai

ya k'ada kai suka karasa,cikin sanyin murya ta

gaida su,Garba kad'ai ya amsa,shikam Ja'afar

k'allonta kawai yake yana murmushi, kamar mai

son sai sun had'a ido. "Malama Salma fa kar tai

latti a mata bulala abokina.. Kasa ta kara da kai

tana dan dariya, shikam gogan sai binta yake

kawai da k'allo,kan ya nuna mata hanya kan wai

su rakata hanya. Ba musu ta wuce suka

jera,Garba sai shakiyanci yake zuba

musu,murmushi kad'ai ne nasu har suka zo bakin

_gate_ d'in islamiyar. Ka'ro na farko suka k'alli

juna cikin ido,da sauri ta K'awar da kanta tana

murmushi, shikam harda k'ada kai, tuni Garba ya

harbo jirgin nasu,sai ya hau shafa ha6a yana

k'allonsu,musamman abokinshi da yace bai san

so ba.. Hannu Ja'afar ya kai aljihu yana lalube,ita

kam sai ta hau satar k'allon shi ganin mey zai yi.

Da mamakinta k'wa sai gashi ya fito da naira

ashirin yana mika mata. K'alloshi tai tana kunshe

dariya,sai ta k'ada mishi kai, "Kud'in tara ne fa

Salma, ki k'ar6a ki sai hambididi... Dariya Garba

ya fara harda rike ciki,itama wacce take rikewa

ta fito fili, sai ta sa hannu a baki dan rufe sautin

ta.. Shikam Ja'afar kawai sai ya hard'e hannu

yana K'allonsu, musamman Garba yadda yake

k'yak'yata dariya. Shikam ba kasafai ya iya

dariyar keta ba irin ta Garba,shi yasa wataran

yakan kularshi a abu. "La Malam Ja'afar......

Gaba d'ayan su suka juya k'allon mey magana.

Ja'afar take k'allo tana murmushi halamar jin

dad'in ganin shi, shikam tuni ya had'e rai yana

k'allon ina ma ya santa. Kamar tasan mey yake

tunani tace *"Bintu*(Na Rufaida Omar) ce,dalibar

ka a day... Salma ya k'alla wacce itama ke kallon

Bintu,kan ya k'ada kai, "toh Bintu.. Salma Bintun

ta k'alla jiki a sanyaye ganin ko in kulan da

Ja'afar ya mata,"shiga za kiyi ne Salma? kai ta

kada mata, jiki a sanyaye tai gaba Salma ta daga

musu hannu halamar sai anjima tana murmushi.

Da k'allo ya bita cikin wani yanayi, da ko shi

kanshi bazai iya fassara wa ba. Kai ya k'ada kan

ya k'allo Garba wanda k'wachokam ya maida

K'allonshi kan abokin yana dariya kasa-kasa.

Harara ya maka mishi kan ya juya,sai k'wa

Garban ya kara sa dariya yabi bayanshi. "An

fad'a tarko makal ana hura mana hanci,sai anyi

magana kace wani "mey nene so? Ni ban sanshi

ba.. Karyan kawai,koh makaho ya laluba yaji ka

afka so ai yanzu kam. Chak! Ja'afar ya t'saya

tare da juyo wa gun Garba. "Mey kenan haka ke

nufi?.. Harara Garban ya k'wada mishi kan

yace"kar ka maida ni yaro fa malam,kana nufin

baka san kana son Salma ba ko mey?.. K'allonshi

kawai Ja'afar ke yi cike da mamaki,a hankali ya

furta *"SO"*?... Hararar shi Ja'afar ya kara,gani

yake kamar ya raina mishi hankali ne. "Kaga

Malam kawai kai saranda haka,tuni tun yadda ka

ke ta yawan fad'in Salma nasan a rina,ka bar

wani k'wane-k'wane. Shi dai Ja'afar ya

t'sunduma tunani maganar Garba,wai So? Salma

kuma?. *By* *Feenat Ja'afar* 庐NWA.

9/29/16, 8:56 AM - Queen Safiyyert馃憫: [7/21, 12:28 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

8-Har Ja'afar yazo k'wanciya yana tunanin

kalaman Garba,tabbas biri yaso kama da mutum,

dan yana jin sauyi tun ranar farko da ya dora

idonshi a Salma bayan dawowar shi.

"So"... Ya furta a hankali, murmushi yai kan ya

k'ada kai,dan yana da aiki a gaba,dan bai san

kom ba game da lamarin.

Tun daga ranar ya zamto kusan kullum da

yamma yakan raka Salma islamiya,koh da yana

shago zai zo ya ganta kawai,hakan na sashi

nishad'i, yau da gobe har ta fara sakin jiki dashi

a karo na biyu.

Sai ya zamana itama in bata ga Ya Ja'afar a

ranar ba batajin dad'i sam,haka zata k'wana

sukuku.

Shirye-shiryen bikin Aunty A'i suke,duk sun shiga

_busy_.

Da yamma sun fito bak'in shagunan su Abba

siyayyan kayan fitar biki, tasan kuma d'uk layin

ba inda ya kai shagon su Ya Ja'afar kawo kayan

k'yali, amma da tayi magana Ummi sai ta tanka.

Kai duk'e yana duba takaddu,kamar

_papers_,chak ya t'saya da abinda ya yake yana

murmushi kai duk'e, ajikinshi ya ji kamar Salma

na kusan shi,itama dai satar k'allon shi take,tana

ganin zai dago tai sauri ta juyar da kai tana

murmushi.

Fara'ar shi ta karu dan hango Salman.

A hankali ta dan kara K'alloshi,sai k'wa suka

had'a ido,da azama tai kasa da kai tana

murmushi har suka karaso.

Tuni Ummi ta had'e rai ganin Ja'afar a shagon,a

takaice ta dan harari Salman ganin sai wani

munafukin murmushi suke sakar ma juna,baki ta

ta6e kan a ciki ta gaidashi tai cikin shago ta

barsu nan.

_"My_ kanwa,.. Kai ta kara duk'ar wa tana

gaidashi,sai ya k'ada kai,ya rasa irin kunyar

Salma gare shi yanzu,abu kad'an duk'ar da kai.

"Biki ya karato ba? Kai ta daga mishi tana dan

k'allon _net_ d'in gefenshi da murmushi.

Tashi yai zuwa gun inda take k'alla ya fara

saukar mata dasu.

A hankali ta tako gun dan zabi,d'uk sun mata

k'yau.

Sai ta dan kallo shi, "malam Garba fa? Murmushi

yai yana k'allonta, "yaje inda aka tura shi

_service_ nashi yaga gun,gobe zaki ganshi.

Kai ta k'ada, d'uk sai taji ta kasa za6a ganinshi

kusa da ita.

Kamar ya sani ya kara s'akko mata da wasu.

"Bari na tayaki za6a.

Kai kawai ta k'ada mishi tana k'allon kayan,kan

wani _purple_ idonta ya kai,a hankali ta kai

hannu zata ja shima ya kai zai d'akko shi yana

fad'in

_"purple_ zai miki k'y... Shiru yai ganin itama shi

ta rike,ya rike rabi ta rike rabi.

D'uk sai suka k'alli juna ba koh kiftawa da wani

yanayi...

Tamkar wanda aka lika _poster_ a gun haka suka

kame da k'allon juna.

Ummi ce ta kat'se su da fad'in

"Ga nan wasu materials y'an leda Salma masu

kaman _lace_....

Shiru tai ganin wani ikon Allah,baki sake take

k'allon su,tuni Salman ta sakar mishi tai baya

tana sunke kai da murmushi tare da amsar kayan

hannun Ummin tana sunyi k'yau ba dan ta gani

ba.

Murmushi ya sakar mata shima,har yanzu yana

rike da _net_,ya rasa mey ke damun

K'wak'walwar shi akan Salma.

*By*

*Feenat Ja'afar*

[7/21, 8:05 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

9_Baki ta dan ta6e,kan a y'atsine tace ma Jafaar

d'in "mun zabi wannan, zamu nuna ma Baba sai

ya bada kud'in.

Murmushi yai yana k'allon gun Salma,itama

idonta na kusan hannunshi.

"Koh na tafi ne Salma? K'allo Ummin tai,kan ta

k'ada kan suka yi hanyar fita a shagon,a hankali

ta dago mishi hannu halamar _bye_.

Kai ya k'ada mata shima ya dago mata nashi.

Tai k'walli da Ja'afar ta ji dad'i,har aka je gida

bata umm ba um um,sai Ummi ke ta zuba kamar

kanya, yadda zata zuba wanka a bikin Aunty A'i

har ta kule.

Da dare sai ga yaro wai ana kiran Salma.

Rai had'e ta k'allo yaron, "je kace bana nan...

Shiru tai ganin yadda mama ke mako mata

harara, "anya yarinyar nan kalau kike kuwa? Wato

sai dai ai ta min asarar hoda da kazal a banza

ina tufka kina min warwara koh?

"Farin jini Allah ya bayar kina ma kanki bak'in

ciki? Haka zan ta barar miki ni baki ban bare na

maida g'urbin abinda na fitar Salma?..

Maman ta k'allo da mamaki,toh rokon samari

mama take so ta fara komai? Allah yaga ta t'sani

fita zance.

Amma ganin yadda mama ke wanke ta yasa ba

shiri tace ma yaron "yace ma waye?.. Kai ya

daga mata,"wai ince inji

"Ja'afar in kin tambaya... Ai koh karasa wa nai

ba ta mike,tuni murmushi ya maye g'urbin 6acin

rai, da k'allo mama ta bita, kamar ba ita ce

yanzu ba.

Yau kam ga su Salma harda mit'sika hoda da

_lips stick_ har ta d'au hijab ta kara k'allon

madubi,kawai sai ta janyi g'yalen Ummi tai waje.

Shine kuwa yana jingine da gidan,wani murmushi

ta saka na farin cikin kara ganinshi a daren.

Da sallama ta karasa d'uk da ba wani haske gun

sosai,amma sai dan sinke kai take kamar rana.

Bayan sun gaisa kowa yai shiru kamar basu abin

fad'a.

Chan dai ya nisa ya miko mata ledar hannunshi.

Kamar mai neman ba'asi ta t'saya bata k'ar6a

ba.

"Ajiya na kawo kimin zuwa gobe ne,ba wani abun

ba naga kina tsoro.

Murmushi tai kan ta amsa tana k'allon Ummi

zata wuce,koh ci kanku bata ce ba ta shige gida.

D'uk sai Salman taji wani iri,Ummi sam taki jinin

Ja'afar ta rasa dalili.

Ba jimawa yai mata sallama dan ya rasa abin

fad'i shima.

Dama da Garba ne yau kam da zai iya fad'in

komai ga Salma.

***

Tunda daga lokacin Ja'afar ke zuwa gun Salma

jefi-jefi,d'uk da har yanzun bai furta mata so

ba,amma ita a ganinta d'uk acikin so ne.

A k'wan a tashi gashi har ta kammala secondary,

wannan itace tafiya mafi tsawo da Salma tai bata

ga Ja'afar ba,kusan wata bakwai.

Tun tana damuwa har ta hakura ta rungumi

karatun ta na fita.

Gasu yau sune a gida,d'uk an rame anyi baki.

By

Feenat Ja'afar.

[7/21, 10:10 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

10_Babban tunaninta bai wuce d'uk t'sawan

lokacin nan da aka diba ba Ja'afar ba labarin shi

ba,tasan yakan je mata ziyara makaranta koh a

t'satt'saye ne,ga ita ba waya ba balle ta neme

shi koh lafiya?

K'wana biyu da dawo wa yau d'ai ta kudiri niyar

fita jin ba'asi,koh Garba in ta gani.

Hijab d'in _mss_ d'inta har kasa ta sa harda

nikaf.

Sai d'ai har ta gama zagayen layin ba wanda ta

gani ciki,kawai burinta ganin Ja'afar ne.

Iyanzu kam tasan tai nisa kan sonshi ba kad'an

ba,sai d'ai ita yanzu ta fara tantama.

Har zata juya ta tuna da shago,d'uk da tasan

yanzu ba kasafai yake zama ba tunda ya samu

g'urbin koyarwa.

Sai dai tai chan d'uk bata tunanin ganin nashi.

Daga d'an nesa ta t'saya kusa da wata bishiya ta

d'an kare ba mai ganinta, da sauri ta juya tare da

dafe kirji,zuciyar ta sai bugawa take da k'arfi.

Yanzu ta samo amsarta da kuma kokwantan ta

da ya zama gaskiya... Bata aune ba sai jin

hawaye tai na bin kuncinta cikin nikaf d'in.

A hankali ta fito daga bayan bishiyar tare da kara

k'allo shagon.

Murmushi yake harda darawa, ita kuma budurwar

sai washe mai baki take tana ta mai zuba,rike

yake da hannun wata y'ar k'yak'yawar yarinya

fara kamar yayarta.

Ji tai wani abu ya tokare mata kirji,da sauri tasa

hannu ta dafe gun,ga hawaye yaki ya d'aina

malala.

Lalle tai wautar kin kula kowa sai Ya Ja'afar da

bai furta mata so ba.

Ido ta rint'se ganin ya d'akko mata wani

had'adan net purple yana bata,wato har kalar da

yasha sanar mata yana so ya bata?

Tai imani mai irin wannan zankadediyar budurwar

fara ba abinda zai da ita Salma baka.

Hannu tasa ta cikin nikaf d'in tana goge hawayen

dake zuba mata.

K'allo sun da zatai taga Ja'afar ya zuba ma inda

take ido,har budurwar na k'allo itama,da sauri ta

juya gabanta na fad'uwa, kar dai ace ya gane ta?

Tab,da k'wa ta bada kanta wallahi.

Juyo wa ta kara,sai karaf suka kara had'a ido da

Ja'afar. Ba shiri ta tare mai adaidaita ta

shige,tana k'allo ya bi napep d'in da k'allo yana

girgiza ma budurwar kai.

Kawai sai ta sa kuka mara sauti tare da cire

nikaf d'in.

Lalle tai wautar zurmuwa ga soyayyar Ja'afar,

soyayyar da ba'a ma bayyana mata ita ba... Ya

Ilahii.

**************************

"Oh! Man Ja'afar, dama kana k'allon mata har

haka? Bafa koh kiftawa?

Murmushi yai mata tare da girgiza kai, "Hala tai

kama da Salma ne? Danma da hijab ga kuma

nikaf..

"Kusan hakan ne, jikina ya bani kamar Salman ce

kam..amma nasan ba ita ba ce ma.

Dariya ta danyi har hakorinta farare suka

baiyana,kan tace "sannu _Romeo_ toh, ni

sallameni kan Amal ta fara neman mamanta,

amma ina mamakin yadda ka iya zaben kaya da

color, halama kana son _purple_? Murmushi

kawai yai mata,kan ya k'ada mata kai halamar

eh.

Ita kam Salma tana zuwa gida ta taho da yaro a

kofa ya kaima mai Napep kud'in shi.

Allah yaso ba kowa t'sakar gidan mama na d'aki.

A katifa kawai ta zube ta sau kuka,sai da tai mai

isarta tai shiru tana maida numfashi.

Chan kuma kamar wacce aka t'sikara ta mike

zaune.

Tabbas Ja'afar bai ta6a nuna yana sonta ba

kam,d'uk zuciya ke yaudarar ta.

Asalima da "K'anwata" yake kiranta, kila hakan

ne tun da,ita kad'ai ke kidanta, gaba d'aya ta

gama kore masu sonta ita a dole ta riki Ja'afar.

Hawaye ne ya kara zubo mata tunawa da yadda

yake washe ma budurwar nan baki.

Tasan yadda Ja'afar yake a gaban mata baya

wargi,baya sake fuska ma bare har yai musu irin

wannan tad'in.

"Tabbas budurwar sa ce,nai wauta ni Salma...

"Lafiyar ki kuwa kike maganganu ke kad'ai ya

sabuwar kamu?

Kai ta dago jin batun Ummi tana wannan y'atsine

matan.

Sai dai ganin irin yadda idon salman yadda yai

ja,ga kuma hawaye yasa ta mat'so

"Mey ya faru kike kuka haka?.. Ai kamar mai jira

a ta6ota ta kara sa wani kukan mai sauti.

Tuni kuma sai Ummin ta zauna tana lallashi da

fad'in lafiya?

Ita de sai kukanta take baji ba gani.

Tashi Ummin tayi,"bari na fad'o ki da mama

toh,kila k'ya fad'a mata ita... Da sauri ta rike

mata riga, "ni ba komai.. Marata ke ciwo da

bayana kawai.

T'saki Ummin tayi, "Allah kina da aiki a gaban ki

Salma,kukan jinya sai kace wata yarinya.

Ita dai tana jinta ta karaci kardinta tai waje,a

hankali ta zame ta k'wanta,sai sauke ajiyar

zuciya take.

*By*

*Feenat Ja'afar*

庐*NWA*

[7/22, 12:02 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

11_Kan safiya har ta gama tunanin abin da zai

fisshe ta.

Hakan yasa t'saf ta tashi kamar ba ita taci kukan

nan ba. Aunty A'i yau za'a kaima wuni,tun (12)

suka fice ita da Ummi.

Chan suka yini har dare,a kafa ta ratso ita kad'ai

sakamakon Ummi da ta biya kar6an _style_.

Tunda tazo layin su Ja'afar d'in taji gabanta na

fad'uwa, duk da bata koh k'alli hanyar gidan ba.

"Abokina ina ka tafi ne daga lissafi kai shiru?

"Ba kaga kamar Salma ba waccan mey tafiyar?

Ido Garba ya k'wara, da mutum,amma a duhun

nan bazai tantance ba,kawai sai ya k'ada mishi

kai,

"A cikin duhun daren nan ne har zaka gane wake

tafi.... Shiru yai ganin Ja'afar d'in yai gaba,da

sauri yace "wai mey ke damunka ne? Ina za

ka?.. Binshi yake shi kuma yana bin mai tafiya a

duhun.

"Salma"... Chak! Ta t'saya dan jin kamar an kira

ta,a hankali ta juya,da dan tazara a tsakanin su

kad'an, amma hakan bazai sa ta kasa gane ya

Ja'afar ba koh a cikin dubu,hakan yasa cikin

sauri ta juya ta chigaba da tafiya,har dan gudu-

gudu sauri-sauri take.

"Mey zai fad'a min kuma? Ta fad'a cikin ranta.

Har kusan layinsu ya bita, tsammanin shi koh

tsorata tayi,amma tabbas wannan Salma

ce,kawai sai ya t'saya a dai-dai layin nasu yadda

bazata ganshi ba,da hasken inji a layin, yana gani

ta t'saya ta waiga,kan da sauri ta shige gida.

"Amma fa baka aiki sam Jaa, wai har nan ka

biyota kage ma koh aljana ce a daren nan?

Juyawa yai yana girgiza mishi kai,"Allah Salma

ce,toh yaushe ta dawo?.. Baki sake Garba yace

"hadda rantsuwa? In Aljana ce fa mai siffar ta?.

Harara ya sakar mishi kan ya juya suka tafi.

Ita kam tana zuwa gida Abba da Mama suna

t'sakar gida ta shigo sai haki,tuni k'wa Abba

fad'a ya karu, kan mey yasa sukai dare?

Tuni tai zuru zuru,fad'a sosai tasha,saura

Ummi,d'uk da laifin Ummin har sukai daren.

Washegari kusan yamma sai ga nan yaro kan ana

kiran Ummi da Salma inji su isma'il.

Harara Salman ta k'wada ma Ummi, kan tace

"yanzu sai da kika fad'i ma mutanan gidan mu

kika huta koh? Allah ban san yayi6e ni.

Hararar itama Ummin tai mata,"arziki na binki

kina guduwa,kowa yazo kice bai miki ba,ki mayi

karatun ta nut'su wallahi,dan aure zanyi ni ba

jira..

"Keai Kowanne dan chaburos ma yazo Ummi a

shirye kike, toh ba dani ba.

Yankan farcen Ummin ta bari tai hanyar d'aki

tana fad'in"sai kiyi ta zama kar kiyi aure,har

mahadi ya baiyana.

Cikin kuluwa zatai magana sai ga Mama ta fito a

d'aki, ashe d'uk tana jin su, "toh k'wa maza ki

wuce ki je tun kan na sa6a miki,daga yau na

d'aina zuba miki ido ba fus bare ass Salma...

Yarinya sai taurin kai,ace koh kishin yadda y'ar

uwarki take shiga take fita da y'an k'wabai ba

kiyi? Toh na gaji da gafara sa dan ban hangi

kaho ba... Maza ki shiga daga ciki ki g'yara ki

wuce...

Kai kasa Salma tace "toh.. Ita kam tana

mamakin halin Mama har kullum akan su,sai dai

tana tuna Ja'afar tuni taji tana da muradin

fita,tunda wanda take danshi bai ma san tana yi

ba.

G'walo Ummi tai mata,kan tai waje tana sai ta

fito.

Bata aune ba taji mama a d'akin nasu, bani waje

ki ga,da kaina sai na g'yara ki...

Baki sake take k'allon Maman,aikwa ta zage ta

hau cha6a ma Salma k'walliya irin wacce bata

ma san mama ta iya ba.

Fad'i take "na rasa gane wace iri ce ke

Salma,arziki na binmu kina zura da gudu,d'uk

wani buri da na sa kanki kin rushe shi, in banda

haka a jiya kad'ai kina ga irin bajintar da Ummi ta

shigo dashi daga gun isma'il yake ko wa?

"Haba k'alle ki a madubi man,san kowa kin

wanda ya rasa... Tana yi tana g'yara mata

d'aurin dank'wali.

"Maza ki fita kan Abban ku ya dawo ya hana

ruwa gudu..

Kai ta daga zata d'au hijabi,da sauri Mama ta

warce, "g'yale zaki sa matar Malam,koh a

Shari'ar a haka ake son a ganki,ta ina za'a yaba

in kin maka hijabin? Toh ba walima nace kije ba..

Kai ta k'ada, ta zama tamkar rakumi da akala,sai

yadda mama tace.

"A'a, ko ke fa,k'alli kanki a madubi ki ga man,ai

da banbanci, maza je ki... Kai ta kara k'ada

mata, har zatai waje da sauri Mama ta kara

kiranta.

Turare ta fesa mata,kamar tace ba k'yau

mama,sai dai taja tai shiru.

"Ki murmusa man Salma,haba..murmushi ma ado

ne ga fuskar Y'a mace...

A yadda maman take yi bata ma san sanda abin

ya bata dariya ba.

Allah ya gama su da uwa "LASHE MONEY", har

ta fita kuwa tana murmushi, mama sai barta.

Suna t'saye gaban wata jar _CRV_ tare da

Ummi,d'uk dinsu sun zubo mata ido.

Ita kanta tasan tayi ne, fari da manyan ido kawai

budurwar Ja'afar zata fad'a mata tasan.

Doguwa ce ita dai dai misali,farin jinin samarin

zamani,fatarta a goge take mai launin Wankan

Tarwada(black beauty), tana gashi ga gashin

ido,gata fuska doguwa,gata tana da diri dai dai

so,d'uk komai ya ji ba bau ba.

Ya dace kam tai amfani da lokacinta tun yanzun.

Cikin takun da ba irin na Salma ta da ba ta

karasa gun su Ummi,ga murmushin nan dan

_beauty point_ din nan sai lot'sa wa yake.

Tuni ta kara tafiya da imanin Muzammil,har yake

ji kamar ya taro ta kan ta iso.

By

Feenat Ja'afar.

[7/22, 4:57 PM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

12_Ita kanta Ummi tai mamakin Salma da

sakewar ta.

Sun gaisa da isma'il saurayin Ummin su kuma

suka zaga dayan bangaren motar,

Kusan kawai d'aurewa take tana mishi yake,

amma ita sam taki jinin saurayi mai shegen

surutun t'siya.

Hakan yasa d'uk taji ta gagu su k'auce, ga tasan

Abba gaf yake da zuwa da magriba tayi.

Kamar ance daga kanki, Ja'afar tagani kusan su

kad'an, tamkar gunki yaja ya t'saya, ga nan

wannan budurwar da ta ta6a ganin su itama tana

k'allo su,sai ta k'alli Ja'afar, kawai sai ta d'auke

kai kamar bata gansu ba.

Harda kara bawa Muzammil wani _attention_ na

daban tana murmushi.

Cikin sanyin jiki ya juya,tana dan satar k'allon

shi,a baya budurwar tabi shi tana waiwayen

Salman,ji tai kamar ta k'wada mai kira,So ba

k'arya bane Salma.

Da k'allo Ummi ta bisu lokacin da suka zago ita

da isma'il, sallama sukayi,suna kokarin jan mota

sai ga wata bakar mota ta _parker_.

Ganin su Garba yasa da sauri Salma ta daga ma

muzammil hannu tana mishi murmushi.

Ja'afar dake k'allonta ta glass din ya rint'se ido

da sauri.

Ganin zata juya yasa Garba fad'in "Salma" da

sauri.

Juyo wa tai lokacin da yake yafito Jafar da

hannu halamar ya fito.

Koh ta kansu Ummi bata bi ba tai gida.

Yake tai mishi lokacin da suke karasowa,sai dai

koh inda Ja'afar yake bata k'alla ba shi da

budurwar shi.

Cikin barkwanci Garba yace "duniya da alkawari

kuwa Malama Salma?.. Murmushi tai mishi iya

le6e, "ashe kin dawo amma koh mu sani..

Karon farko ta k'allo gun Ja'afar, idonshi k'wa a

kanta girrr...ba koh kiftawa.

Da sauri ta d'auke kai daga kanshi.

Gaidasu tayi,budurwar na mata an dawo. Lafiya?

A ciki ciki ta amsa,Garba yace "yaushe a gari?

An gama lafiya _hope_?

Da mamaki take k'allon shi,yanzu dama da

wanda zai ce bai san y'an makaranta sun dawo

ba?

Kawai dai sai ta maze, "yau kusan satin mu da

dawo wa.

K'allo Ja'afar d'in Garba yayi,kan ya dawo da

K'allonshi ga Salman.

Ba wannan dawowar ba,yau k'wana uku da

zuwan mu K'anwarki tace mana kinyi tafiya...

Da sauri ta dago kai da mamaki,tana k'allo gun

Ja'afar d'in ya d'auke kai.

Garba yaci gaba, "zuwan mutumin kenan daga

Zaria yace sai ya zo ya ganki ya miki murna,ashe

ke har kin ma fice a garin.

Batta bakin magana,dan bata san amsar basu

ba,amma Ummi tana mata daya a rayuwa..wai tai

tafiya?

"Ga nan mutumin jiya har sururu yake yaganki da

dare ina mishi t'siya, ashe ke ce.

Kai ta daga,kan ta kara k'allon Ja'afar, d'anna

wayarshi yake kamar bai wajen.

Cikin wasa Garba yace "toh ni zan gabatar mata

da ita ko mey da kai mikis?..kasan ba kunya zan

ba ni.

Murmushi budurwar tayi kai duk'e, dan sam bata

ga fuska gun Salman ba.

K'allon Ja'afar din take,yayin da yake k'allon

Garba yai shiru.

"Toh,mu bama sanya, sai ya juyo gun Salman,

"Salma ga nan budurwa,kuma matar... Da sauri

ta rint'se ido,kan ta karasa da "Ja'afar"... Na

sani Malam Garba...

D'uk ido suka zuba mata har Ja'afar baki sake,jin

shirun yasa ta bud'e ido akansu,yadda suke

k'allonta tasan tai su6ul da baka...

Cije le6e tai,amma ta bada kanta wallahi....

Dariyar keta Garba yasa harda k'yak'yatawa, sai

ta dago tana k'allonshi.

Sai da yai mai isarshi kan ya k'allo Billy,

"Haba,Yanzu na ji batu,ni fa naga kowa yana

sassahan kamshi,ashe-ashe...uhm uhm

_Jealousy_...

"Toh wannan Matar Garba ce bata Ja'afar

ba,sassauto madam.

Wani irin sanyi taji ya ziyarci zuciyar ta,har

batasan sanda murmushi ya su6uce mata ba.

A kunya ce ta k'allo Billy,sai ta mat'sa kusan da

ita kan tace "sannu da zuwa...

Dariya suka sa mata banda Ja'afar da ya dan

dara,idonshi kir a kanta,bazai iya fassara mey

hakan yake nufi ba, shin Salma na son sa da

kishin sa ne koh mey?

Ita dey sai dan satar K'allonshi take,amma

bazata iya fassara ina ya dosa ba.

Mota su Billy sukai suka barsu,ga nan magriba ta

gabato,gaidashi ta kara yi itama ciki

ciki,t'sayuwa ya g'yara kan ya amsa,tare da mata

murnar kammala karatu,shiru ba mai cewa

uffan,kowa miskilin kanshi,kawai sai sukai

sallama kan gobe zai zo.

Tana shiga gida dan takaici kasa ma Ummi

magana ta cikin fad'a."yanzu Ummi kina k'yauta

min kenan a rayuwa? Mey Ya Ja'afar ya t'sare

miki ne ki ka ki jinin shi?

Rai ta had'e, kan tace "oho,kawai bai min bane...

Ga nan sakon daga Muzammil,kinga in da ake

harka ai...

Kai ta k'ada dan takaici tai d'aki batabi koh ta

kayan ba.

Washegari dan kalata sai ga su sun dawo, ana

la'asar, mama ta fita unguwa.

Ado Ummi ta ciwo da tafi na jiya,sakare tai ganin

Salma koh mot'sawa batai ba.

"Koh ba zaki bane Salma?

A tunzure tace "ba zani ba..

Baki Ummin ta ta6e,kan ta daga kafada,

"mat'salar ki ce wannan kuma... Sai tai waje.

Aiko yaro sau biyu ana yi daga waje daga

Muzammil amma fur taki fita.

A ka'ro na uku ne yaron suka shigo da Mama da

ta dawo daga unguwa.

Dole ta tashi badan rai naso ba,sai dan ganin

Ummi ta shigo ta had'a ta da Mama kan taki

zuwa gun Muzammil.

Tana had'a rai ta fito,sai dai da mamakinta taga

Ya Ja'afar t'saye yana aiken yaro kan tazo. Da

sauri ta koma cikin zauren kan ya ganta.

Jim tai kad'an bayan fitar yaron kan ta fito,kanta

t'saye tai gun Ya Ja'afar, kan tace ya bata minti

biyu dan Allah.

Kai kawai ya k'ada mata,sai tai gun su Ummi,a

mutunce suka gaisa,kan tace da Muzammil

sakon shi sai gobe.. Bata jira amsa ba tai gaba.

Shi kam Ja'afar k'allonta kawai yake,amma tuni

har yazo wuya.

Tabbas dole ya bayyanawa Salma yau ranshi ba

sai an k'wana ba,dan wannan samarin tsaf sai su

iya kasa shi yana k'allo.

"Bissmillah, muje zaure... Bai yi musu ba yabi

bayanta.

Har ya dan saki fuska, dan sam ba kaunar zaman

ta a layi yake ba.

Bayan sun gaisa yake bata labarin abinda yasa

bai je mata ba.

"Kinsan Mamana tana a Zaria ne,sun rabu da

Abba tun ina dan shekara biyar,hakan ya zamana

Abba ya k'ar6e ni a dalilin tai aure,nakan kai

mata ziyara haka,sannan dan ita na zabi zuwa

Zaria karatu.

A _time_ d'in da za ai _visiting_ aka aiko bata

lafiya,chan naje har t'sawan wata uku.

"Taji sauki sosai,har tana ta fad'an na koma

bak'in aiki na,ana haka y'arta K'anwata ta dawo

sun gama makaranta,hakan yasa na tuna da

Salma.. Nan nai shiri na dawo,duk dan na

ganki,sai aka samu akasi, Ummi tace kinyi

tafiya... Shiru yai kai duk'e, itama tai tsam tana

sauraren shi.

"Salma"...kai ta dago ta dan k'alleshi, shima

idonshi a kanta. "Yanzu kam lokaci yayi da zan

sanar ki wani sirri,sai d'ai ina fatan wani bai

rigani yad'awa ba...

"Salma"... Cikin wata siga ya fad'i, kan yace "na

jima ina dakon son ki azuciyata,tun ma kan

Salman tasan itace...

K'allonshi take baki sake,shikam ya zage sai

tona sirrin ranshi yake a gare ta ido bud'e..

Dad'i, farin ciki har ya kasa misaltuwa a gun

Salma,So d'aya ne, tasan Ya Ja'afar tai ma.

By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 8:59 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 13_Har

yai shiru ita kam idonta na kanshi,kan dafa bisani

tai kasa da kai cike da kunya,kawai shima sai ya

zuba mata na mujiya yana murmushi. Magana

suke jiyo wa kasa-kasa,duk sai suka zuba ma

kofar ido. "Ba mutunci ace kowa yana wuce wa

yana ganin ku a t'saye a titi, gaba na fad'a miki

ki nemi koh zaure ne koh cikin gid... Shiru Abban

yai dan ganin Ja'afar a zauren da Salma.

D'ukawa ya danyi kan yai ma Abban sannu da

zuwa. Cikin sakin fuska Abban ya amsa,Salma

ma ta mai kai duk'e. Sim-sim Ummi tazo ta

wuce,dan duk iskancin ta tana bala'in tsoron

Abban su sosai. Yana shiga gida shima yai mata

sallama da alkawarin gobe zai zo dan jin amsar

shi. Da t'sananin farin ciki ta shiga yau, haka

dashi ta tashi. Tun jiyan Ummi ke ci mata kunu,

tasan kuma d'uk akan Muzammil ne,shi yasa koh

bi takanta batai ba. Washegari tun kan Ummi ta

shiga wankan yamman ta na kullum Salma ke

gaban mudubi, sosai take k'yali, yau d'aya ta

bata lokaci dan Ja'afar d'inta. Ummi da tun dazu

ta fito tana jira ta ta6e baki, ''kiyi kare ni ki ban

waje na zauna Malama... Juyo wa tai da tana

yage mata baki, "dan Allah Ummi nayi k'yau?..

Bar zancen wasa. Baki ta ta6e kan ta juyar da

kai gefe, "oho miki ni kar ki daman. Murmushi tai

kan ta tashi ta bata gu. Bincike ta fara,a babu

babu Mama kala 5-5 ta musu kayan _candy_ na

ke ce sa'a, ciki masu ruwan _purple_ ne kusan

duk. Cikin nishad'i ta ciro attamfa wata mai

_purple_ da rat'sin _yellow_ riga da siket,

murmushi tai dan tuna wa da kalar da Ja'afar

yafi so kenan. Tunda ta zura kayan ta nad'a

d'auri take bin kanta da k'allo a mudubi ta gefen

Ummi. MashaAllah tai k'yau, gashin da ya fito ta

kasa take turawa cikin dank'wali,ta kai dubenta

ga Ummi wacce sai ko'k'arin fiddo nata take tabi

dank'wali ta kansu. Murmushi kawai ta

mata,tasan da tace ta mayar su ciki ma a iska.

Sai dai tana d'akko turare ta hau feeeee ba ko

kakkautawa. "Haba Ummi,turaren nan kinsan

haramun ne sashi ki fita koh?.. Ga gashi kullum

sai ance ki alkinta shi.. Allah kina *TABARRUJ*

da yawa.... Galala take k'allonta, kan ta ja t'saki

tai waje. Iya wuya Salma tazo, ta bala'in t'sanar

t'saki. Ba'a jima ba Ja'afar yazo.. Tabarma yau

ta d'aukar musu,shima yasha wankan farin kaya

da farin takalmi _half cover_ sosai yai mata

k'yau. Yadda yake fara'a da bin k'allonta tasan

itama ta wanke shi. Suna t'saka da gaisawa

cikin nishad'i yaro yazo,wai tazo a waje inji

Ummi. Tuni ya sauya,dan yaga zuwan su

Muzammil. "Minti biyu kawai.. Kai ya k'ada mata

da dan yake. Tana fita suka ware gefe,tsakani da

Allah ta fad'a mishi yai hakuri. Baki sake yake

binta dashi har ta kule cikin gida. Amma Ja'afar

ya bala'in k'wada shi da kasa,dan haushi koh

isma'il bai jira ba yai gaba. Ita kam tana zuwa ta

bashi amsa gamshasshiya, wanda tasa fara'ar

Jafaririn ta dad'u ba shiri. Tad'i suke kamar ba

gobe, mot'si kad'an yace "kinyi k'yau..... Itama

cikin kunya tace yayi shima. ***************

************** "Naga sai zarmewa kike fa akan

Ja'afar salma,sam kinfi k'arfin shi kima ji da

wai,gaba ake son ci ba baya ba wallahi,d'uk da

ban san wacce iriyar amsa kika bawa Muzammil

ba... Da harara Salma ta bita, kan tai k'wafa, "ina

ruwan ki da sha'anina? Ke har kin isa ki fad'a

min wanda ya dace dani Ummi? Baki Ummin ta

ta6e, "ke dai kika sani,dama ni meye nawa? Ni

koh ana saurayi mey zanyi da Ja'afar mai shegen

dacin ran t'siya... "Wai ku baku zama inuwa

d'aya ne da juna Salma? Mey yasa baki iya daga

ma Ummi K'afa sai kin tanka mata kullum kuna

sa makota na jin ina daga murya.. Kasa Salma

tai da kai kawai,tasan yanzu in mama taji ta

kad'e.. Kamar k'wa wacce Ummi ta karanci

zuciyarta ta amshe.. "Wai fa mama daga

shawara ta tsaya min masifa,yau akan wannan

dan gidan Malam Kabiru mai shago ta kori

Muzammil,daga fad'a mata gaskiya ta hau ni da

masifa.. Dan Mama daga ganin yadda Muzammil

ya tafi rai 6ace nasan cewa tai bata son shi...

"Eh bana son shi,koh ana son dole?.. Ja'afar d'in

da kika rena ni shi ya min ki ji da wai.... "Kunga

ku min a hankali,koh yanzun nan na sa6awa

mutum... Shiru sukai,yayinda Salma taci ka tai

dam. "Ke ummi wani dan wajen Malam Kabirun

kike fad'a? Da harara Ummin ta k'allo Salma kan

tai ma Mama bayani,"yanzu haka mama Malamin

makaranta ne wallahi yana chan yana kokawa da

alli.. Jim Maman tayi kamar mai tunani,chan ta

nisa tace "Ikon Allah..anya yarinyar nan Salma

ba'a min misanye dake ba a layin jarirai a

haihuwa ba?... Mutum arziki na binshi yana

ki?...Ina laifin yaran nan?har kasa suka gaida

ni,ga mota ga boko..amma in banda abinki mey

na sama yaci bare ya bawa na kasa? Da shagon

uban zaku dogara koh da kud'in malami?.....

Shiru Maman tayi ganin yadda Salman ke

hawaye... "Au,au,Salma kuka? Daga fad'an

gaskiyar? Kai ta k'ada ma Maman. "A ni tawa

mai sauki ne Salma,ina d'ai hanga miki gaba ne

kawai... Amma banga abin kuka.... "Wa ke

kuka?... Assalamu Alaikum. Shiru sukai salman

na goge ido,sai Mama da ta amsa mishi sallama.

"Sannu da zuwa Abba. Kai ya daga musu kan ya

amsa. D'uk suka tashi sim-sim sukai d'aki. Sai da

Abban ya gama komai yasa Mama ta kira su.

Kowa tai ladab kai kasa suna saurarar Abba. "Ni

ke Ummi na ma kasa gane alkiblar da ki ka kama

sam,kullum da wanda za'a ga yazo gunki,sai

aukin shegen zance a titi ba wanda ya iya yazo

ya samu iyayen ki.. "Ga nan yayarki yau d'in nan

yaron nan na wajen Alhaji Kabiru yasa Baban shi

yazo muka zanta kan yana son Salma da

aure,kuma har sun sasanta da ita.. "Koh ba ai

haka ba Salma?... Kai duk'e cike da kunya ta

daga kai halamar anyi. "Haka shine musulunci, ta

haka kuma ake gane da'ar yaron da zai auri

y'arka... Shiru kake ji Ummi anyi lakwas. Nan ya

kara ja ma Ummi k'unne kan tara samari da

zancen waje,ya kuma ja mata k'unne kan ta

fidda na aure koh ya fiddawa mutum. ***** ***

Zancen aure dai ya kank'ama tsakanin Ya Ja'afar

da Salma. Itama Ummi Isma'il yace da gaske

yake.. Mat'sala d'aya tafi damun Salma,yadda

komai Ja'afar ya bata na alheri a rene yake gun

su Mama, barin Ummi. Dan ita fachaka isma'il

yake mata kamar ba gobe. Tun abin bai damunta

yau da gobe har ta fara ganin kamar Ja'afar

mammako yake mata. Zuciya bata kashi. By

Feenat Ja'afar. 庐NWA.

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 24

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

14_Anyi bikin su Garba. Ana haka saurayin Ummi

ya d'allo mata wata sabuwar waya,ita kam tun

wata Zain da ya bata,nan habaici ya karu gun

Ummi. Biki ya kusa sukai shirin zuwa Borno

dangin Abban su. Sunyi sallama da Ja'afar ta

shigo gida rike da farar ambalan,d'uk suna zaune

t'sakar gida har Aunty A'i da yaronta. Hannunta

Ummi ta k'alla, kan cike da shakiyanci tace "ta

Ja'afar mey aka samu ne haka har a farar

takadda?.. Harara ta dan mata kan ta mikawa

Mama. Kai Maman ta k'ada, kan tace "a rabani

da kayan haushi,rike abinki kawai ki kirga...

Dariya Ummi ta sa,wanda tuni ta kara kular da

Salma. "Mama ba ma sai ta kirga ba,dan wallahi

ba kaffara nasan kud'in nan bai fi dubu biyu ba...

Kanta Salma ta yiwo a tunzure mama tai musu

iyaka. "Meye na jin haushi?.. K'yautar tashi tana

wuce nan ne?... Ba dai d'an d'an kasuwa zaki

aura ba? K'wafa tai,kan tace "baki fara ganin

komai ba ma Salma. Aunty A'i ce ta k'ar6a ta

kirga,ai kam sabbin hamsin hamsin ne ta dubu

biyu. Mama tace "Ahab,na sani ai. D'aki Salman

tai tana hawaye,sam bata kaunar abinda ake ma

Ja'afar,amma shima da laifin shi,dubu biyu ina

zata kaita? ****************************** Biki

kam yazo,gashi yau har anje jere, k'warai sunyi

mamakin gidan Ja'afar da gina kuma da kanshi.

D'uk da ba wani babba bane,dan koh t'sakar

gidan karama ce,babban _parlour_ ne sai _bed

room_ da band'aki aciki,ga _kitchen_ a ciki

karami,sai d'aki d'aya daban a waje, d'ai d'ai

zaman mutum d'aya de,rufin asiri dai ak'wai

shi,Alli da shago sunyi rana. Sa6anin Ummi mai

tafkeken gida da mai gate yasha alatu. Yanzu

lefe ake wat'sa ido aga na Ja'afar, dan tuni na

Ummi yazo san barka,sai zuzutawa ake. Salma in

ta tuno gabanta har fad'uwa yake,fatan ta Ya

Ja'afar ya fitar ta a magana. Dan tun a kud'in

anko taga tasku,dan isma'il ankon k'yauta yai ma

k'awayen Ummi da dubu ashirin nata na fitar

biki. Shikam sai hakuri yake bata,kan shi bai

d'aura ma kanshi abinda bazai iya ba,bare daga

baya ya dame shi. Kawai sai ta toshe k'unnenta

gun su mama,komai ta samu ta samu,wanda ta

rasa tasan bai da hali. Mamaki kam Ja'afar ya

bama su mama, dan ak'wati shidan nan y'ar yayi

sai da aka bat'se ta da kaya, ga uban

_cosmetics_ har a jakar Ghana must go. Aciki da

swiss d'aya, holland biyu,engla biyu,sai su code

dav'ior,sauran kam duk kana na ne su dangin

material. Salma baki har k'unne jin ba wanda ya

kushe a dangin sai d'ai ace na Ummi yafi t'sada.

Anyi biki lafiya kowa ya wat'se an bar amare da

halin su a gidan su. Kauna ziryarta taga gun

Ja'afar mai t'sayawa a rai,sosai sukai amarcin su

cikin kula da tarairayar juna,musamman ga

Ja'afar d'in. _kitchen_ tare,wanki tare,shara

tare,duk aiki in dai ba ya fita bane yana a makale

da Salman sa, d'uk wata kulawa tana ganinta a

gun Ja'afar,shi yasa sai abinda yace take

aiwatarwa matukar bai sa6a Shari'a ba. Yadda ta

fuskanta ma kamar bai kaunar tai nesa dashi,koh

dan ganin har wata biyu kenan da bikinsu amma

ba inda taje sai barkar Aunty A'i da makotansu

da taje tun tana sati daya da zuwa. Sai dai tai ta

jiyo shewar su ta katangar gidan halamar ana ta

_chapter_. *Farin Bacin komai* Yau tun tashinta

sallar asuba ta kasa komawa bacci,sakamakon

tun dare da yace yau ta shirya da wuri zata gida.

Dan farin ciki ji take kamar a wani garin zata je

musu. Waya tai da Ummi kan zata fito yau gida.

Gaban madubi take tana yi tana k'allon agogo

har sha d'aya saura. Karar _machine_ d'in Ya

Ja'afar taji a kofar gidan,sai ta cigaba da

shiryawa. Sallamar shi taji,daga d'akin ta amsa

tana fara'a. Yana shiga ya jingina da kofar d'akin

yana mata murmushi,ta mudubin ta mishi tana

d'auri. Kan ya tako gaban madubin ya t'saya ta

bayanta. "Sannu da dawo wa.. Kai ya daga

mata,sai kare mata k'allo yake, kayan sun mata

k'yau, "Kinyi k'yau... Tashi tai da jin dad'in

kalaman shi,sai ta dan ja mishi kumatu kan tace

"na gode... Muje koh?.. Ta fara nad'a lifaya. Sai

ya rike mata daya gefen tana nad'a dayan da

murmushi. Da kanshi ya yafa mata akai ya rufe

ko'ina ruf. "Ba dan kin nace sa abar nan ba da

hijab d'inki za ki sa zai fi min k'wanciyar

hankali.. Murmushi tayi kan ta lang'wa6e kai, "ai

ba g'yale bane Ya Ja'afar, Allah ina son lifaya.

Kai ya k'ada mata yana d'aukar mata jaka. "Toh

naji,amma ni banga maraba ba. Murmushi kawai

tai tana d'aukan mukulli. Machine d'in ya karkata

mata kirar lifan,a hankali take ko'k'arin hawa sai

ya dan girgiza machine din,da sauri k'wa ta dafa

kafad'arshi suna dariya. In kagansu g'wanin k'yau

suna ta nishad'i har suka zo gida. Tana g'yara

lifaya tace "bazaka shiga ba?.. Kai ya girgiza

mata da murmushi,"ki gaida su Mama, anjima in

nazo d'aukan ki zan shiga, yanzun makaranta zan

koma. Kai ta k'ada mishi,kan ta bashi hannu,sai

ya bata suka gaisa suna dariya. "Abincin ka yana

a kitchen a bisa faranti,na had'a komai, a dawo

lafiya... Kai ya daga yana mata murmushi,jin yaki

tafiya tace "kaje man.. Kafad'a ya make yana

nuna mata gefen fuskanshi, kai ta k'ada mishi

cikin kunya. "A layi muke fa... Shima sai ya kada

kan tukun ya tada sukai sallama. Har ya kule

tana daga mishi hannu,kan tai cikin gida. Da dan

gudunta ta shiga tana kiran Mama. D'uk suna

d'aki, Ummi an hakimce a kujera ana d'anna

waya. "Har kun rigani ashe d'uk saurin nan

nawa?.. K'allonta Ummi take ganin tana since

lifaya,ga flasks da jaka an ajiye. "A ina zaki zo

da wuri,ke dad'i miji ce ai.. Banza tai da ita tana

gaida Mama, itama Maman a dan ciki ta amsa

mata. D'uk sai taji ba dad'i, jikinta yai sanyi,da

murnar ta tazo amma sun dakushe mata. "Sai ya

barki ki waiwayo mu?.. Maman ta k'alla, kan tai

kasa da kai, "ai na zata irin ta y'an da zai

miki,sai kin shekara koh kin fito yawan arba'in....

Baki Ummi ta ta6e,kan tace "d'uk mai irin halin

Ja'afar ai dole yai k'ulle Mama,in banda haka

wata biyu wai sai yau za kizo gidan ku,ni nazo

yafi a girga,wallahi tun wuri ki mawa tufkar

hanci.. Dan in kika sabar mishi da haka zai mike.

Dagowa tai da niyar yi wa Ummi magana Mama

ta tari numfashinta. "Y'ar uwar ki ce,dole ta fad'a

miki gaskiya, ke zaki nema mana mutunci a gun

miji ki ma ji da k'yau. Kasa tai da kai tana

murmushi, duk da a zuciyarta bataji dad'i ba

sam. "Mama baza'a a sake ba inshaAllah. Da

haka aka ware kuma zancen nawa ta tara a

banki. "Ni fa ba'a ban kud'in cefane Mama, komai

yana kawo min har katin waya,sai dai in ina da

bukata yana cewa na mai magana... Baki Ummin

ta ta6e,kan ta zuge jaka, sai ga nan kud'i tumi.

"Kinga kud'in cefane na,nima ai ba abinda na

rasa,ina ruwana da wani ni kud'in kati? Kawai naji

dumus ni... Gashi nan na banki ne dana sa Mama

ta sai min. Kai Maman ta k'ada, tabbas Ummi

tasan ta kan maza,shi yasa take burgeta sosai.

Itade Salma an sata duhu,dan sun raba

hankalinta biyu. T'saka mai wuya kenan. By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:00 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 15_Sai

dare yazo a dalilin yadda take fad'in bata gama

ba,har cikin gidan ya shiga,kawai kuma sai yake

ma Mama k'warjini, dan fuska sake ta amsa

mishi,kan suka tattara suka tafi. Koh da Salma

tazo k'wanciya maganganun su Ummi take ta

tunawa. Ita babban haushinta ma yadda aka fa

fad'in koh tsoron Ja'afar take. Washegari ma

haka ya yakaita gidan su Abban shi,nan ya wuni

suka biya gidan Garba. Yau tun (7:30) ya fita,

sakamakon an fara jarabawa a makarantu. Sha

d'aya ta gama aiki ta fara jiyo hayaniyar y'an

unguwa a makotanta,halamun sun hallara za'a

fara chapter. D'uk yau sai hankalinta yai

gidan,duk da ba sabawa tai dasu ba. Waya ta

d'auka,ta d'anna kiran Ja'afar _no answer_.. Ji

take kamar ta zaga in ya dawo ta fad'a mishi,sai

dai ta daure. Da yamma kam kamar kullum yazo

fita shago tace zata leka makota. Jim yai ba

amsa,sam tarbiyar matan unguwar bata mishi

ba,baya so Salma tai sabo dasu a samu

mishkila,amma kawai sai ya k'ada mata kai, "Sai

kin dawo. Cike da murna ta rakoshi har bak'in

kofa ta koma d'aki. Da sallamarta ta shiga,tun

daga bak'in kofar gidan zaka fara jiyo karad'in

matan. Da fara'ar su suka amsa,d'uk sun baje a

tabarma, wasu ba koh dank'wali. A dan kunyace

ta gaida su, dan ganin duk sun girme ta,sai wata

mai kamar shekarunta da D'a a goye. Chan hira

taci gaba, zabiyar ciki sai karanta musu makamin

kama wuyan maza take. Salma tai shiru tana jin

su,tabbas babban burinta shine Ja'afar ya so ta

har karshen rayuwa. "Su amarya yanzu ai farin

take gani kan a juya mata bak'in bayan.. K'allo

matar tai,bata gane nufinta ba,sai dai bazata iya

tambaya ba. Haka firar yau ta tashi kan makamin

rike miji har Salma ta fito. Tunda ta zauna a gida

take tariyo firar sun. Tabbas shawarar nan tayi ta

makamin rike miji, ta hakan kam ba yadda

Ja'afar zaiyi ya raina ta... Toh amma Ja'afar

yana sonta,batajin zai mata dabi'a irinta mazajen

sauran Matan da ke fad'i. Nan ta jefar da

dayawa a hudubar da taji a makota tai kitchen

dan k'unna ritio. Sai d'ai Washegari ma da

yamma Salma ta sake tambayar shiga makota.

Karan nan kam kir ya fito yace mata a'a, da ido

kawai take binshi, "Ya Ja'afar yafi zaman kad'aici

ne,ba jimawa zanyi ba ka ji... Ta langwa6e kai.

Ba dan yaso ba ya k'ada mata kai. Minti biyar

bata kara ba tai makota,gidan chapter. Yau kam

a sa'a taje,dan suna a kan firar rashin fitar matar

gidan,sai bata dabaru suke akan yadda zatai mijn

ya rika barinta fita. "Kar ki fara tambayar

unguwa kina fara'a, sosai zaki dake mishi,mud'in

yaga 6acin rai toh jiki na bari zai barki. Ni da

farko haka Salisu ya t'siro min da k'ulle,tun farko

nai ma tufkar hanci,da yace A'a yana fita zan

arce, gashi yanzu har ya saduda yana barina duk

inda na tambaya. T'sam Salma tai,tana tariyo

maganar Ummi da Mama ta ranar,ga nan ta

makotanta. Daga ganinsu sun san takan duniya.

Tabbas ta yarda itace tun yana d'anye ake

tank'wara shi. Tun yanzu ya dace ta takawa

Ja'afar birki koh dan ta t'sira daga zargin wai

tana tsoron shi. *Wasa farin Girki.* Daga ranar

Salma ta tsiri dan hali,fita makota,tambayar fita

gida,ga wani t'sarewa da take in tana tambayar.

Kamar kullum tazo rakiya taja ta t'saya a gefe,

"Ya Ja'afar... Jiyo wa yai shima rai ba dad'i,tare

da zuba mata ido,yasan abu daya zata tambaya.

"Zan leka gidan Maman Ummi gobe suna za ai

k'ulli... K'allonta kawai yake, yadda tasha mur

tamkar wanda take bashi umarni. "Anya Salma

wani abu bai shiga kanta ba kuwa?.. Gaba daya

ta sauya mishi hali k'wana biyu in dai akan fita

ne.. G'wara tun wuri ya taka mata burki dan yaki

jinin yawan fita sam shi. "Kiyi hakuri Salma,ki

bari ki leka goben tunda suna ne... Tuni ta

k'ank'ance ido, "gaskiya kar ka maidani saniyar

ware a unguwa ya Ja'afar, yau k'ulli kowa ya je

sai ni ce bazani ba?.. Ai sai a chake ni gobe

dama suna fad'in ni dad'i miji... "Kuma ma ba

wannan ba,nima sai ina zuwa za'a zo min in

nawa yazo ai.... Shiru tai ganin yadda ya zuba

mata ido yana kallo, chan ya nisa "amma Salma

kin fuskanci kin fara sauya hali kuwa?... Kin koyi

ja dani,kin koyi gantali k'arfi da yaji.. K'alloshi tai

a wani iri, "au gantali ma nake Ya Ja'afar?..

Fisabilillahi wace fita ce nake yi ba dalili? A satin

nan sau biyu koh uku ne fa na fita kuma dubiyar

Ummi ne ba wani waje ba, koh shi ka ke nufi da

gantalin? Kai ya k'ada,"kar mu rika ja in ja dake

Salma,kiyi hakuri kawai gobe ki je... Juyawa yai

ganin tana neman wata maganar yai waje, baki

ta ta6e,kan tai cikin d'aki. Tana jin tashin

machine d'inshi ta zaro hijabi ta k'ulle gida tai

cikin gidan k'ulli. "Ai na zata bazaki zo ba,da har

zanyi aike naga machine din maigidan. Hijab ta

cire ta jawo jarka, "bari ke dai Maman

Ummi,dak'yar na fito fa.. Murmushi tai kan ta

d'akko wani abu a bakar leda,"yanzu saratu ta

fita an kawo sabbin kaya dakakku wallahi,tai ta

jira baki zo ba zata tafi na dau miki wannan...

K'ar6a tai tana dubenshi kan ta kunce ledar,roba

ce karama da wani abu mai d'anko. "Takalmin

Kaza ake fad'a miki,nasan yafi haka,kawai ta

mana sauki ne.. Amma abin ba magana,sai an

g'wada akan san na k'warai... Dariya suka sa aka

tafa harda shewa. "Wannan ne kawai makamin

wulakancin D'a namiji,tunda kuka d'aurani kan

_network_ nake son raina Allah. "Dari biyu ai ma

yai araha... Bari yazo dari biyar zan tat'sa, dan

asusu nake kan zuwa watan haihuwar Ummi na

tara da yawa... Sai da aka gama k'ulli ana firar

duniya,a debo gulma har aka gama,ana kiran

magriba ta tuna Ja'afar, da sauri-sauri tai gida

dan yau abinci ta zarce tayi. Kamar kullum ya

dawo bayan magriba ana kiran isha'i, sai dai sam

ranshi ba dad'i,nan tasha jinin jikinta,koh ya

dawo bata gida ne? Har yaje masallaci akai isha'i

bai dawo ba har ta gaji da jiranshi ta k'unna inji.

Sai chan kusan tara ya shigo,har yanzu jiya

iyau,sam kuma sai taji ba dad'i, tun kan ya fad'i

lefin da tayi,amma de sai ta dake. Komai

yayi,dan har abinci ya ci,sai dai fur yaki sakar

mata. "Wai Ya Ja'afar mey nai ne ka ke ta shan

kanshi?.. K'allonta yake da mamakin anya

Salman shi ce wannan?.. Bai da amsa,sai a

gunta kawai,saboda haka ya tashi yai hanyar

d'aki. By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:03 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 16-Ya

fito a band'aki ya ganta zaune a gad'o,kai ya

dauke yana goge jiki da _towel_,d'uk sai jikinta

yai sanyi,tabbas tasan Ja'afar kila zuciya

yayi,har ya gama shirin bacci uffan bai ce mata

ba,tuni ta fara kuluwa ganin ya ja filo bai bi

takanta ba. "Wai mey in ma ina ta maka magana

tun dazun?.. Kai ya dago ya k'alleta da tuhuma,

"mey kika ce ban amsa miki ba?... Baki ta turo

gaba kad'an, kai ya kada,tukun yace "Salma!...

Salma!!.. Dagowa tai ta bashi hankalinta dan jin

kiran da yawa. "Na'am.. Ido ya tsura mata,sai tai

gefe da nata. "Ina kika fita dazu har magriba?..

Jin tambayar tai ta bazata,hakan yasa ta kasa

K'allonshi, sai da ya maimaita tukun ta amsa a

hankali da "gidan k'ulli... "Gidan k'ulli?.. Mey

mukai dake toh kan na fita?... Duk t'siya ta ki

jinin kuma taga ran Ja'afar ya 6aci, sai dai an

rinjayi zuciyarta. "Kai hakuri... Itace Kalmar da ta

fad'i. Tashi yai ya jingina da pillow,kan cikin

nut'suwa ya fara mata magana. "Ba wannan ne

ba karon farko da ki ke fita ba'a son raina ba

Salma,nasha aiko yaro da sako yace gida a k'ulle

yake,amma nai ta daga miki kafa. Duk gantalin

da take bada yardar shi ba sai da ya sanarta,ga

t'sinuwar mala'iku dake binta har ta dawo...

"Sam wannan ba Salman da nasani a wata 5 d'in

baya ba... Wannan cikin wata d'aya ta sauya,bata

jin magana ta,duk abinda tasa kanta take ganin

shine d'ai dai shi take... Sosai ya kasheta da

kalamai,har ta fara hawayen wai bata jin

magana. Murmushi yai kawai,kan ya dan taso ya

janyo ta ya hau kuma lallashi,da alkawarin

bazata kara ba,sosai ya ji dad'i,dan yana son

mutum mai gane kuskure in ya yi. Washegari

_week end_suna ma haka tai shiru,sai dai kasan

ranta ji take kamar tai filfilwa taje gidan. Tasan

iyanzu an kusa sauke abinci ana ta cin chapter

ba ita. Sai dai tai ko'k'arin ganin bata tambaya

ba. Shi kuma ganin haka yasa yaji dad'i,fatanshi

yasa Salma ta g'yara ne. Ce mata yai yana

zuwa,yana fita ta kasa zaune ta kasa t'saye.

Anya bazata leka ba kan ya dawo?.. Dan tasan

yanzu ana chan an kafa da ita uwar son miji. Sau

biyu tana k'wata fita tana dawo wa,a na ukun taji

dirin machine d'in Ja'afar ta koma. Sai gashi da

leda baka a hannu. Sannu da zuwa ta

mishi,burinta ya fita ta fice, amma fur yaki. A

jima kadan ta k'alli agogo,kafarta har kaikayi

take,da ya k'allota ta sai ta sau mai murmushin

dole. Kamar ya kula sai yace bari yai wanka,yau

sha biyu yake son yaje shago. Ita dai ta samu ya

fice,Allah koh satar hanya sai taje gidan sunan

Maman Abba. Toh sai ma ya barta harda mika

mata ledar riga ta barka. Abu kamar gaske

Salma kamar anyi hankali, sai hali ya dawo sabo.

Shiga makota kam Ja'afar har yai hakuri ya zuba

ma Salma ido, Gashi yanzu su Salma har ketare

ana t'sallakawa,kusan duk yanzu unguwar sun

san da Salma,ga surutu da t'sabar manyance da

ta koya zama cikin manya. Ranar Garba suka zo

gidan a 6ame da mukull,sai ya d'au waya ya kira

Ja'afar din. "Ba kowa fa a gidan nan Aboki,dan

da mukulli a 6ame.. Daga chan Ja'afar yai t'sam,

kan yace "oh,sorry pls,na manta tace zata je

dubiya, ga wayanta ba chargy... Kai Garban ya

kada "toh dai mun fita,dama ita ke mitar madam

shiru,yanzu kam ma had'u suna. Murmushin dole

ya k'akalo,yana cewa ace Billy tai hakuri. Bayan

sun gama ya ajiye waya,Salma tasa ya tafka

karya,dan da abin kunya ace yana mai gida

amma bai san matar gida bata nan ba... Toh mey

zai wa Salma ne?.. Ya mata d'ukkan nasiha,yayi

fad'a, yai lallami,amma tamkar a iska yake

zubawa. Sai tayi kamar ta d'aina, gobe ta fidda

sabon hali. "Assalam Alaikum... Kai ya

dago,ganin mey sallama yasa ya fad'ada

murmushin shi, cikin girmamawa yace "a

Abba,sannu, yana sunne kai, murmushi Abban

yayi,kan yace ''yauwa Ja'afar,ka ga na dawo,zan

dan zaga ne, baya,dayan shagon nan ba kowa ne,

nazo arar Sadi minti biyu.. Kai kasa yace "Bari

na zauna kan ka dawo nan bana komai. Yasan

zai samu ma damar yau amar da abin da ke

ranshi. Yana shagon Baban ya k'wance ya

d'aure, ya fad'a ya je gida ya shiga uku gun

Salma.. Shawara d'aya ya yanke, gun Mama, dan

yaga ita batta zafin Baban. Tun yamma ya

tashi,bayan sun gaisa da Maman faran faran

yake sanarta halin da Salma ta t'suro mishi.

Kamar abin kirki harda bashi hakuri,da fad'in zata

t'sawatar mata. Sai d'ai tana fita Ummi da tun

shigowarshi tai zamanta a d'aki ta fito. "Kai

amma mama mutumin dan rainin hankali ne,wai

kinji fitar Salma tai yawa? Matar da sai tai sati

biyu wataran ba tazo gidan nan bama bare har

fitar ta tai yawa.... K'wafa Maman tai,kan tace

"ke lefin shi ki ka ga?.. Ai lefi na gun Salma da

ta zauna yake juyata kamar waina... A zamanin

y'ancin kai ake yanzu, bana tsawalawa dana..

Kaza kaza,har Abba ya shigo zaure ya dan t'sinci

wani zancen,amma bai gane kanshi ba. Kullum

Ja'afar na sa ran yaga Salma ta sauya,sai dai

shiru,sai yai tunanin fad'an Maman ma bai shige

ta ba. Ranar Garba yace a gidanshi zai magriba

yace Salma tai musu irin gurasar nan tun tana

amarya. A gabanshi ya kirata, a lokacin an zube

ana ta firar kashe wando a makota bayan

layinsu, Koh da ta sauke waya ta cigaba hirarta.

Chan kusan magriba ta kusa ta tuna da zancen

Ja'afar,kusan ma d'uk y'an firar an wat'se amma

Salma matar gida ta riketa wai suna firar su zata

tafi? Yaron gidan tasa yai gudu bayan layinsu ya

siyo mata gurasa mai siga ta karbi kud'i gun

matar gidan. Cikin nishad'i suka zo sai dai gida a

6ame,ga yau ta bar mukullin shi a ciki. Ranshi in

yayi dubu ya 6aci,basu jima ba sai gata

tanan,duk tabi ta burkice, duk da koh k'allon inda

take Ja'afar bai ba. Sai da Garba take magana

tana ko'k'arin bude gida. By Feenat Ja'afar.

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 25

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 17_Shi

dai Garba har suka shiga gida yana zungurar

abokinshi kan ya saki fuska. D'aki ta shiga tana

mai adu'ar Allah yasa a samu gurasar nan,in ba

haka ba yau ta kad'e har ganyenta a gun Ja'afar.

Suna t'sakar gida suna alwalar magriba sai ga

yaro yai sallama rike da k'wano,da sauri ta fito ta

amsa,har ta shiga Ja'afar na bin bayanta da

ido,k'wafa yai kamin yai ciki, shi dai Garba duk

ya gane da wata a kasa. Kitchen ta sameta tana

jera su a faranti. Tasan shine amma fur taki daga

ido ta k'alleshi. "Nagode Salma, kinji? Na

gode,amma ba zanci gurasar titi ba ki sani...

Kofar kitchen din ya rufo sukai waje. Ita kam koh

a jikinta,tunda de ta t'sallake fad'a ai shikenan.

Yau dai ya kasa d'aurewa, har sai da ya sanar da

Garba halin Salma ba ragi. Sosai yai mamaki,wai

Salma ce da halin nan? Sai dai kawai ya bawa

abokinshi hakuri, da kuma ya rage saurin fushi...

Haka ya wuce gida ba tare da shima yaci ba. Da

dare ya d'au pillown shi ya koma parlour,baki ta

ta6e tai k'wanciyar ta. Sai dai koh minti ashirin

ba ai ba ta hau juyi,ta ture pillow,dan Allah yaga

bata saba k'wanciya ba'a hakarkarin Ja'afar

ba,duk fad'a kuwa. Ba shiri tazo bada hakuri dan

tasan ya bala'in jin haushi. Shi kuma haushin shi

d'aya da hakurin Salma,tunda ba wai zata g'yara

bane. Kuka ta fara mishi harda shura kafa kan

wai ya juya mata baya yaki kulata. Juyo wa yai

yana k'allonta, duk da a kule yake da ita amma

har kusan dariya yaso saka. "Ba nace kai hakuri

ba,Allah kasan ban ta6a kin yi maka abinci ba da

gangan... Tashi yai ya zauna a kusa da ita. "Toh

naji na hakura,bar borin...ya sa hannu zai goge

mata hawaye sai dai kamas... "Au kukan ma na

karya ne ashe?... Dariya ta fara ta d'au mishi

pillow sukai d'aki. "Ina a gidan nan Allah ba kai

ba k'wanan parlour. Murmushi yai yana mai

tausayin kanshi, ina ma Salman shi ta da ta

dawo mishi... Ina ma zai yuwu ace kullum yaso

ganin Salma zai sameta a gida haka?... Ya sani

da yana son Salma,so ba na wasa ba,amma k'arfi

da yaji so take tafi k'arfin shi,ga ko kadan bai

kaunar yaga fushin ta. Ina ma itama haka take

nannan da nasa fushin... Yasani da *Mai Hali

Baya fasawa* **************************** Sauri

take tayi,dan yau gidan mai gumama suka

je,tasan kuma tabbas Ja'afar yana hanya. Aikwa

tana zuwa ga nan machine d'inshi a kofa

halamun yana ciki. Duk da tana jin dan shayin

shiga su ar'ba, haka ta d'aure ta shiga. Takaddu

yake nema, da sallama ta shiga, a chan ciki ya

amsa yana cigaba da abinda yake. "Sannu da

zuwa... "Uhmm.. Kawai yace, sai ta ta6e baki.

"Gidan fa mai gumamar nan da na fad'a ma jiya

ta aiko mana za'a kawo muka je..kaga zuwan

banza mukai ma wai sai gobe. A dirare ya

k'alleta lokacin da yake tashi, ganin yai banza

yasa tace "ni fa nan kad'ai naje,sai gidan Maman

Ummi dana biya mata muka tafi.. Kai ya k'ada,

kan yace "yayi k'yau... Maman Ummin ce mijin ki

koh mai gumamar?... Ido ta zaro,sai ya kada kai,

"no ba wannan ba ma, wai d'uk inda kike

azarbabin zuwan nan wa kike gani yana zuwa

gidan ki yafi minti goma aciki?... Koh d'uk suna

da aikin yi sai ke kad'ai ce bakki shi?.. Salma ki

nemi mutuncinki da hannunki,a ganina zai fi

mu.... "Ka ga malam,ba sai ka zage ni ba zan

san dama kana kule dani ba,daga fita nan da nan

din shine har zaka na cemin wata gantalalliya?...

Haka kawai,in ma kayan ne naga kai zan sawa

ba wani ba,toh meye abin zafi aciki?. Kai ya

k'ada kan yace "babu... Amma wallahi kar gobe

ki sake ki kara fita gun wata mai gumama,in ba

haka ba zan mugun sa6a miki... Waje yai rai

6ace, "Ja'afar?... Ni zaka sa6awa?... Chak! Ya

t'saya ya kasa gaba, a hankali ya juyo fuskarshi

d'auke da mamaki. "Salma... Yau ni kike kama

sunana garangatsai ba koh rufi?... K'ugu ta rike

tana girgiza, "ai sunan ka ne naga.. Kuma muna

kama sunan Allah ma bare wani chan... Na gaji

ne da hancini. Kai ya k'ada yana murmushi,

tabbas ba abinda yai saura da gantalin Salma bai

gur6ata ba,ciki kuwa harda iya fit'sara. Sai ya

k'ada kai ya fice,dan yasan komai zai iya faruwa

in ya tanka. ~~~~~~ Washegari haka aka tashi

kowa rai ba dad'i, yau ce ranar farko da har aka

waye gari ba'a shirya ba. Ga yau week end,yana

gida yaki fita shago. Har yamma ba bayani, sai

dai yai bacci,ya je masallaci ya dawo. A sama

take,dan gani take da gayya yaki fita dan ai ba

ita gidan gumama. Ya dawo daga masallacin

la'asar ya shiga wanka. Maman Ummi ta turo

tazo suje kan a za6e,yana jin lokacin da tace dan

aiken yace tana zuwa. Yazo fita ta biyo shi,dan

tambaya a ganinta ta wanke lefin jiya ya barta.

"Ya Ja'afar zamu gidan wannan mai kayan

Maman Ummi na jirana. Ja yai ya t'saya, kan ya

juyo ya koma parlour,ba musu ta bishi ai wacce

za ai. "Tun jiya ai mun gama magana dake,babu

fita... "A gaskiya sai na je, gashi nan ai kai ka ke

jawo komai, da lallami na tambaya ba zaka barni

ba,sai na fita cibi ya zama kari... Haka kurum

yanzu haka jirana ake ka ce wani bazani ba..ta

karasa tana kunkuni. "Sai kinje koh?.. Cikin

fusata tace "eh.. Murmushi yai ya k'ada kai,

"Bazan hanaki ba toh, sai dai wallahi ki sani,

mud'in kika sa kafa kika fita,toh *A BAK'IN

AURENKI*.... Bai jira komai ba yai waje,yana

jiyota tana ai wallahi bazaka sani kaffara ba,fita

kam nayi na gama. By Feenat Ja'afar. 庐NWA.

Like 路 6 路 Reply 路 Report 路 Jul 25

Ummu Maryam Tahir

Sannu da qoqari 6ter

Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 25

Kareema Wakeeli

Tnx

Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 25

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 18

_Kitchen_ kawai ta leka,ta d'aura guntun ruwa a

tukunyar silver a _hot plate_ nata karama nepa

suka d'auke wuta. Kamar zata kashe,kawai ta

bari,a ganinta ba komai. Kan su kai gidan

gumama kuwa 5 tayi,fatansu Allah sa ba'a za6e

ba. Kaya kam gasu masu k'yau, tuni ta fara

daddagawa tana ware na wara. "NEPA"... Cewar

yaran gidan, sai dai da halamun su Salma hankali

yayi kan gumama. Suna nan a gidan har kusan

k'arfe 6,amma basu gama da mai kaya ba.

Kamar ance daga kai sama,sai ga nan dan

hayaki na yin sama halamar daga nesa ana

gobara a wani gu. "Ina ga wutar dazu tai ma

wasu aiki,hayakin nan gobara ce duk yadda

akayi.. Kai Salma ta k'ada, "koh taya ake konawa

ba... Sai dai kan su farga ihun gobara har kusan

layin da suke. Maman Ummi tace suzo su je,in

yaso daga baya sa dawo suyi bayanin. Da sauri

Salma ta tare, "A'a Manan Ummi,nasan yanzu Ya

Ja'afar na hanya 6 saura. "Muje dai koh gobe

tunda ta kirga wanda muka d'auka ma dawo ai

sabon lissa... "Umma!..Umma!!... Da gudu yaron

mai gumama ya shigo, matar tace "lafiya irin

wannan gudu? Ince dai ba daga gun gobarar ka

ke ba? Yana haki yace "a gidan Aunty Salma ne

fa Umma.. Ana ta neman inda za'a shiga a k'ulle,

yanzu aka kira Malam Jaaf... "Na shiga uku... Ni

Salman koh wa?.. Kai yaron ya daga,ai ina,da

gudu ta fice ta wat'sar da kayan a nan ta bar

Maman Ummi da kira. Kamar wata sabuwar

kamu haka ta iso wajen,kofar gidan cike da

jama'a wasu na kok'arin sanya t'sani su haura. A

ka ta d'aura hannayenta d'uk biyun,tama rasa ihu

zata kurma koh kuka. Baban Ummi ne yace ina

mukullin gidan?.. Nan ta fara tunanin mukulli?..

Innalillahi, ta barshi shima gidan gumama... Baya

ta fara yi ganin Ja'afar da Garba sun faka mota a

chan gefe, a gigice suka karaso, "Innalillahi

Wa'ina Ilaihirraji'un"... Itace kalmar da Jaafar ya

iya fad'i. Ina kan ta farga sai ga hawaye na zuba

tana girgiza mishi kai,mukulli Garba ya tambaya,

kan cikin azama ya lalubo a aljihu ya bashi.

Salman ya k'allo cikin tausayin kanshi, har yanzu

hannu na ka tana k'ada kai tana kuka. "Shikenan

kin zaunar mu Salma... Burin ki ya cika sai ki

zuba ruwa a kasa ki sha.... Tuni ta kara fashewa

da kuka. Fad'in "A kashe meter... Ne yasa yai

cikin gidan da sauri. Ba ka ganin koh ina sai

dusu-dusu dan hayaki. Da taimakon Maman

Ummi ta bar kofar suka shiga daga cikin gida.

Sai dai har yanzu kuka take baji ba gani. Yau

tasan ta kad'e har ganyenta. Motar kashe wuta

ce ta iso,da taimakon dak'yar wuta ta mutu.

Ilahirin kitchen da bedroom ya kone ya laso

parlour ta silin Allah ya t'sayarta. Fito wa tai

bayan taji komai ya dan lafa ta leka gidan,sai ga

nan Ja'afar din sun fito rike da barbadin

_documents_ nasa a hannu. Kamar munafuka ta

dan ra6a ta shigo kai duk'e tana jan hanci. Sai da

yazo dai dai ita ya t'saya. Kanta kasa tana

sharar hawaye,a hankali ya saki burbudin

takaddun ya fice jiki duk yayi sanyi.

**************************** Zaune suke a bak'in

masallaci shi da Garba bayan komai ya lafa yana

tausarshi,yan unguwa sai jajanta mishi suke suna

tafiya. "Dan Allah ka'r ka ce zaka d'au

mummunan mataki akan Salma, kai

hakuri,ubangiji ya mayar ma da alkairin da ka

rasa. Shiru Ja'afar d'in yai,zuciyar shi sai tafasa

take,dan ma yana ta kok'arin neman kariya daga

zugar shedan. Zuwa chan dai ya nesa, "Babban

ni takaici na Garba Takaddu na ne,tun jiya ake

_verification_ gobe ne namu,ni bana ta

Salma,dan a bakin aurenta ta fita... "Ni ga nan

d'akin waje zan iya maleji. Kafad'arshi Garban ya

dafa,lalle kowa da jarabawar shi a rayuwa,shi

kuma abokinshi ta mata Allah ya bashi. "Yanzu

toh ya za ai?... Murmushi Ja'afar d'in yai wanda

yafi kuka ciwo... "Ya k'wa zanyi Garba?.. Kana

sane da gamnatin nan tamu, wa zai k'ar6i uziri

na gobe?.. Shiru yai mishi,dan tabbas yasan bai

da abin fad'a ma abokin. Gida suka koma,tana

nan inda suka barta a durkushe ta tasa takaddun

a gaba tana shesshekar kuka. Ja yai ya t'saya

yana k'allonta, muryar ta har ta dashe. Abin

haushi wai kuma zuciyarshi ta fara tausayinta.

Da sauri ya d'auke kai daga k'allonta dan jin

zuciya na ingiza shi yaje ya lallaso ta, Salma ce

fa... Dake wa yai ya daure tukun yace "toh meye

ne na kuka kuma Salma?..ki tashi kawai kije gida

dan sharad'in dazu yana kan ki.... Da sauri ta

dago ta k'alleshi, tuni taji kukan ya kafe,sai ido

da ta kafe shi dashi, shaf ta manta wani sharad'i

ne ma? Tuni ta tafi duniyar tuna abinda ya afku

ka ta fita. Garba ne ya katse mata tunani da

fad'in "haba dai dan Allah? Wannan sharad'in bai

k'yautu a gun ka ba Ja'afar.. Aure ya fice wasa

fa.. Ka janye sharad'in nan tun kan kowa ya ji ku

koma auren ku.... Da sauri ta k'allo Garba,duk ta

kasa ta6uka komai, Mey Garba yake nufi da su

koma auren su? Yaushe Ja'afar ya sake ta?....

Bai furta ba sai dai in yanzu.. Cikin muryar kuka

tana ka'rkarwa tace "bai sake ni ba Garba, auren

mu na nan... Koh yanzu ya furta?.. Banji ba

Allah... Ni bai sake ni ba...bai sake ni ba.. Sai ta

karasa tare da fashewa da wani kukan mai ban

tausayi. Ido kawai suka zuba mata, tamkar

zararriya haka take magana. Duk sai ta karya

musu zuciya, barin gogan,har bai san ya je

gareta ba,da zummar dago ta yaje ya lallashi

abarshi,sai dai kamar wanda aka t'sayar ya

d'auke hannunshi, baya ya koma yana rint'se

ido... Tabbas yanzu saki ya gifta a tsakani,bai da

_right_ na ta6ata,tabbas bai dashi. A hankali ya

furta "Salma kin cuce mu... Kin fara dasa

katanga a tsakanin mu... Ban san da abinda na

rage ki ba Salma...ban sani ba, dazu a yadda

nake jin zuciya ta,wallahi dan banzan doka naso

na miki,Allah ya kareni da yin kuskure. Baya ya

juya mata,kan ya k'allo Garba. "Dan Allah ka

kaita gida gani nan zuwa... Waje yai ya barsu

nan,Shikenan ta tabbata,ba makawa Ya Ja'afar

ya sallama ta.. Ai tuni ta kara jiniyar

kuka,dak'yar ta tashi sukai waje da Garban. Sai

duba Yayan nata take koh zata ganshi. "Muje

Salma,InshaAllah komai zai daidaita,.. Juyowa tai

ta sadakar da yai nisa... Yana k'allon su har

suka kule kan ya fito a inda ya 6oye a bayan

bishiya. Harda goge y'ar k'walarshi... Salma kinyi

aiki. By Feenat Ja'afar

9/29/16, 9:06 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

19_"Toh a garin yaya haka ta faru? Fita kukai?...

Tambayar da baba ya jeho musu kenan bayan

Garba ya kawo ta ya dakko Jaafar shima.

Kukanta kawai take,ita burinta ya kara maimaita

sakin, kuma yaushe ya mata?. "Salma komai

mukaddarine fa daga Allah,ba kuka zakiyi ba, kiyi

adu'ar Allah maida muku alkairi kinji... Kai ta

dago,ido duk yayi luhu-luhu, ta dubi Ja'afar,

kanshi na kasa,cikin muryar kuka tace "Abba

cewa yai fa ya sake ni... Wallahi ba dagangan na

bari haka ta faru ba.... A zabure Mama tace "ya

sake ki?.. Kai ta k'ada tana dan k'allon Abba da

yai shiru yana k'allonta. "Ni dai banji lokacin da

ya saken ba kuma.. Ta karasa da dan kukanta.

Abban ta d'aure mai kai, chan ya k'allo Ja'afar,

"Mey take fad'i ne Ja'afar?... Sam ban gane inda

ta dosa ba.. Kai ya kara d'ukrawa,kan ya

dago,mama in banda harara ba abinda take sakar

mishi. Ya sani da dole su Abba suji. Cikin

nut'suwa ya hau zayyanawa Abba halin da Salma

ta t'sirar mishi,har zuwa kawo kararta gun Mama,

kawo yau da abin ya faru.. Tsananin mamaki

Abba kasa cewa komai yayi,wai Salman sa ce da

wannan d'anyen aikin? Chan dai ya numfasa tare

da fad'in "Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un... Kuma

kin fita d'in Salma?.. Baya ta fara ja tana k'ada

kai, "Abba dan Allah kai hakuri,bazan kara ba...

Murmushi Abban yai na takaici.. Ya ma rasa mey

zai wa Salma ya ji dad'i.. Duka? Kai ya k'ada.

"Ni meye nawa? Ba dai kin fanshi fita sama da

aurenki ba?.. "Wannan shine sakin Salma...

Tunda har kin fice bayan yace *A BAKIN

AURENKI*.... Kai ta dago da sauri.. Saki kuma?

Daga fad'in hakan?... Kawai sai ta sa musu kuka,

"Dan Allah ya Ja'afar kai hakuri, Allah bazan kara

ba,Abba kai hakuri... Cikin t'sawa yace "tashi ki

bar wajen nan kamin nai miki lilis koh na huce...

Kasa motsawa tai,ai da zafin nama Abba yai

kanta da takalmi,Mama ta tare, amma duk da

haka sai da mummuka mata. Dak'yar Ja'afar ya

lallaso shi. "Kin wa kanki toh Salma,dan dole

kizo ki bar gidana, wallahi ba zaki k'wanar min

ba... "Haba wai Malam dan Allah.. Waye baya

kuskure a rayu.... "Kimin shiru kema, dan duk

laifinki ne,tunda kinsan irin shegantakar da take

aikatawa, amma wai ki kasa sanar ni na d'au

mataki.. Jan Salman tai d'aki tana bashi

hakuri,dan sai ya iya had'awa da ita. Sai da ya

gama sababinshi kamin Ja'afar ya hau bashi

hakuri, "InshaAllah bazata kara ba Abba, nima na

rasa abin yi ne shi yasa nai hakan.... "Ni fa

banga lefinka ba Ja'afar, kamin dai dai.. Gaba

nasan bazata kara ba. Shi dai kawai hakuri yake

bama Abba. Abba ya tambaye shi kan saki nawa

ne? Yace daya. Tashi yai yace ya jira shi,sai

yace bari yaje gida shima ya d'au machine

sannan ya sanar musu. D'aki Abban ya shiga

bayan Ja'afar din ya fita. "Amma kin bani

mamaki Allah Rabi... Ashe ba zaki zama mai

g'yara wa ba sai dai kiyi shiru? T'sawan lokaci

yaro yana hakuri da halin yarinya amma kina

sane?... Shiru tai,sai da ya gama chake ta ta hau

bashi hakuri. "Ke kuma tun yanzu har har kin

kone tun kamin ki tafasa koh Salma?... Kai ta

k'ada tana yai hakuri, "A'a, ni ai nawa mai sauki

ne,koh dai ki g'yara halin ki,koh ki shiga hannu

na... Bansan lokacin da kika sauya k'yak'yawar

dabi'ar ki ba Salma?.. Sosai yai mata fad'a cikin

zafi zafi kan ya kara da ta shirya,dan ya rantse

bazata k'wanar mishi a gida ba... "Haba

malam,ina zata toh?... Cikin fad'a yace "gidan

mijinta... Koh da magana?.. Kai ta kada,kan tace

"sakin fa?.. Sannan wane gida bayan ya kone?...

"Eh a konan nan zata zauna akwai daki a waje

yace da bai kone ba,sannan ki sani igiya d'aya

babu a tsakanin ki da shi. "Ki gode Allah kin

samu mai sanki,yau da wani ki kai wa haka sai

ya tabbatar da ya miki shegen duka kan ya baki

saki... Amma shi kok'ari yayi ma a take yace min

ya mayarki. "Abu d'aya zan iya fad'a miki

Salma... Wallahi, duk ranar da zaki maimaita

haka,ki kuma k'waso kafa ki zo min gida sai na

6a66alla kafarki... Baki sake Mama ke K'allonshi,

ita kam yau kad'ai ta kara mugun tsoron

Abba,tasan a yadda yau ya daketa tsaf zai iya

6alla tan. By Feenat Ja'afar.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Zeenat Yakubu

tnx 1st 2 cmmnt

Like 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

19_"Toh a garin yaya haka ta faru? Fita kukai?...

Tambayar da baba ya jeho musu kenan bayan

Garba ya kawo ta ya dakko Jaafar shima.

Kukanta kawai take,ita burinta ya kara maimaita

sakin, kuma yaushe ya mata?. "Salma komai

mukaddarine fa daga Allah,ba kuka zakiyi ba, kiyi

adu'ar Allah maida muku alkairi kinji... Kai ta

dago,ido duk yayi luhu-luhu, ta dubi Ja'afar,

kanshi na kasa,cikin muryar kuka tace "Abba

cewa yai fa ya sake ni... Wallahi ba dagangan na

bari haka ta faru ba.... A zabure Mama tace "ya

sake ki?.. Kai ta k'ada tana dan k'allon Abba da

yai shiru yana k'allonta. "Ni dai banji lokacin da

ya saken ba kuma.. Ta karasa da dan kukanta.

Abban ta d'aure mai kai, chan ya k'allo Ja'afar,

"Mey take fad'i ne Ja'afar?... Sam ban gane inda

ta dosa ba.. Kai ya kara d'ukrawa,kan ya

dago,mama in banda harara ba abinda take sakar

mishi. Ya sani da dole su Abba suji. Cikin

nut'suwa ya hau zayyanawa Abba halin da Salma

ta t'sirar mishi,har zuwa kawo kararta gun Mama,

kawo yau da abin ya faru.. Tsananin mamaki

Abba kasa cewa komai yayi,wai Salman sa ce da

wannan d'anyen aikin? Chan dai ya numfasa tare

da fad'in "Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un... Kuma

kin fita d'in Salma?.. Baya ta fara ja tana k'ada

kai, "Abba dan Allah kai hakuri,bazan kara ba...

Murmushi Abban yai na takaici.. Ya ma rasa mey

zai wa Salma ya ji dad'i.. Duka? Kai ya k'ada.

"Ni meye nawa? Ba dai kin fanshi fita sama da

aurenki ba?.. "Wannan shine sakin Salma...

Tunda har kin fice bayan yace *A BAKIN

AURENKI*.... Kai ta dago da sauri.. Saki kuma?

Daga fad'in hakan?... Kawai sai ta sa musu kuka,

"Dan Allah ya Ja'afar kai hakuri, Allah bazan kara

ba,Abba kai hakuri... Cikin t'sawa yace "tashi ki

bar wajen nan kamin nai miki lilis koh na huce...

Kasa motsawa tai,ai da zafin nama Abba yai

kanta da takalmi,Mama ta tare, amma duk da

haka sai da mummuka mata. Dak'yar Ja'afar ya

lallaso shi. "Kin wa kanki toh Salma,dan dole

kizo ki bar gidana, wallahi ba zaki k'wanar min

ba... "Haba wai Malam dan Allah.. Waye baya

kuskure a rayu.... "Kimin shiru kema, dan duk

laifinki ne,tunda kinsan irin shegantakar da take

aikatawa, amma wai ki kasa sanar ni na d'au

mataki.. Jan Salman tai d'aki tana bashi

hakuri,dan sai ya iya had'awa da ita. Sai da ya

gama sababinshi kamin Ja'afar ya hau bashi

hakuri, "InshaAllah bazata kara ba Abba, nima na

rasa abin yi ne shi yasa nai hakan.... "Ni fa

banga lefinka ba Ja'afar, kamin dai dai.. Gaba

nasan bazata kara ba. Shi dai kawai hakuri yake

bama Abba. Abba ya tambaye shi kan saki nawa

ne? Yace daya. Tashi yai yace ya jira shi,sai

yace bari yaje gida shima ya d'au machine

sannan ya sanar musu. D'aki Abban ya shiga

bayan Ja'afar din ya fita. "Amma kin bani

mamaki Allah Rabi... Ashe ba zaki zama mai

g'yara wa ba sai dai kiyi shiru? T'sawan lokaci

yaro yana hakuri da halin yarinya amma kina

sane?... Shiru tai,sai da ya gama chake ta ta hau

bashi hakuri. "Ke kuma tun yanzu har har kin

kone tun kamin ki tafasa koh Salma?... Kai ta

k'ada tana yai hakuri, "A'a, ni ai nawa mai sauki

ne,koh dai ki g'yara halin ki,koh ki shiga hannu

na... Bansan lokacin da kika sauya k'yak'yawar

dabi'ar ki ba Salma?.. Sosai yai mata fad'a cikin

zafi zafi kan ya kara da ta shirya,dan ya rantse

bazata k'wanar mishi a gida ba... "Haba

malam,ina zata toh?... Cikin fad'a yace "gidan

mijinta... Koh da magana?.. Kai ta kada,kan tace

"sakin fa?.. Sannan wane gida bayan ya kone?...

"Eh a konan nan zata zauna akwai daki a waje

yace da bai kone ba,sannan ki sani igiya d'aya

babu a tsakanin ki da shi. "Ki gode Allah kin

samu mai sanki,yau da wani ki kai wa haka sai

ya tabbatar da ya miki shegen duka kan ya baki

saki... Amma shi kok'ari yayi ma a take yace min

ya mayarki. "Abu d'aya zan iya fad'a miki

Salma... Wallahi, duk ranar da zaki maimaita

haka,ki kuma k'waso kafa ki zo min gida sai na

6a66alla kafarki... Baki sake Mama ke K'allonshi,

ita kam yau kad'ai ta kara mugun tsoron

Abba,tasan a yadda yau ya daketa tsaf zai iya

6alla tan. By Feenat Ja'afar.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 20_Koh

da Ja'afar din yazo haka ya kara bashi hakuri kan

suka d'au hanya. Zaune take a d'akin da ya rage

musu,duk ta dawo kalar tausayi. Waya yake

amma yana k'allon yadda ya takure kanta tana

K'allonshi. D'anna wayar ya cigaba bayan ya

gama, cikin nut'suwa ta hau bashi hakuri, kan

Allah bazata kara ba. Sannan bazata kara fita ba

izinin shi ba. Shiru yayi,hakan yasa ta fara kuka

tana rantsuwa kan haka. Sauka yayi akan 1sittern

dake a d'akin ita kad'ai sai karamar katifa da filo

daya da ledar t'sakar d'aki. Yasan dan so yana

ma Salma,sannan yana matukar ganin darajar

Abba cikin idonshi, sannan yana mutunta

soyayyar da ta mishi a da chan baya. "Salma kin

d'aina so na yanzu sam,shi yasa ki ke ganin

damata a yanzu... Ki duba kiga abinda yawan ki

ya wanzar mana...nayi imani a garin saurin ki

fita ne har kika manta wani abu a k'unne a

kitchen... Ki duba irin kinjin magana ta abinda ya

jawo... Salma takadduna sun kone kaf...sai

guntu, sanin kanki gobe muna da _verification_

da za'a gunar mana. "Ba wanda zan je ma hannu

Rabbana ya k'alle ni... Kinga meyiwa na rasa

aiki,dan zan shiga _miss call_... Kinga kin zaunar

mu... Ba gida ba aiki.. Cikin kuka ta mat'so tana

bashi hakuri, "kai hakuri banzan kara ba Allah..

Murmushi yayi kamin ya janyota da sigar lallashi.

"Ina sonki Salma,kisa a ranki komai zanyi zanyi

ne _for your own good_... Bazan ta6a miki abu

dan tuzarci ba... _cos I love you_... Kank'ameshi

ta kara cikin jin dad'i... Tabbas tana son mijinta,

zata jure komai dan 6acin rana irin wannan. Koh

da yazo k'wanciya ita tana gefe yaga bata niyar

k'wanciyar tunda ta fito a bayan gidan waje.

Daga k'wancen ya mika mata hannu halamar

tazo. Har wata kunyarshi ce ta da tazo mata

yanzu. Da rarrafe ta isa gareshi,sai ya nuna

mata kafad'arshi kamar kullum,nufunshi ta sa

kanta. Da murmushi ta g'yara, kan cikin nut'suwa

ta zame ta k'wanta. Duk kusan tare suka sau

ajiyar zuciya, bata ta6a saba bacci a kafad'ar Ya

Ja'afar ba... Haka shima bai ta6a sa6a bacci,ba

tare da Salma na hakarkarinshi ba. A daren ta

tabbatar mishi da lalle har yanzu tana son

nashi,har ma tai kok'arin mantarshi wasu

abubuwan. *Hmmm..Allah sa da gaske ne

Salma*... *************************** "Haba dai?

Yaushe?.. T'salle ta doka lokacin da ta sauke

wayar a k'unnenta... "Ya Ja'afar.... Da sauri ya

katseta da "Ummi ta haihu... Yana murmushi.

Hannunshi ta kamo,sosai tana a farin ciki.

"Yaushe zamu ganin baby?.. Murmushi yayi,kan

ya k'alli agogo, shida da rabi,harda wasu y'an

mintuna. "Yanzu kam dare kinga ya gabato...

Gobe da safe kan ma an sallamota sai kije koh?..

Kai ta k'ada tana wani tunani... Jin ya kai hannu

cikinshi yasa ta dan murmusa.. Gira ya daga

mata,kamin yace "saura mu koh?... Murmushi tai

mishi ta k'ada kai. "Mun kusa ai...k'wantar da

hankalin ka sarkin son yara... Dariya sukai,kan

yace "sosai ina son su kam...in naje yaron Garba

kamar nace su bamu aro... Kai ta k'ada, "lalle a

gaishe ka.. Ni kam nafi son mu shekara kan na

haihu da... Murmushi yai yana kada kai kawai.

~~~~~~~~~~~~~~~~~~ "MashaAllah, ganshi

kamar dan larabawa... Ta g'yara mishi hular

kanshi... Dagowa tai cikin wasa tana"um um,su

Ummi an iya haihuwa... Shiru tai ganin yadda

Ummin ta 6ata rai. "Mey akai kuma ki ke wani

6ata rai ina magana?.. Baki ta ta6e,kan ta ja

k'wanon namanta ta fara ci. A y'atsine tace "ya

bazan bata rai ba?... Saboda t'sabar wulakanci

tun jiya na haihu amma sai yau zaki wani zo kina

nad'e taburmar kunya?... K'allonta take ba

kiftawa, sam Ummi batta kunya.. Sai dai kawai

ta basar. "Dadina dake Ummi baki bada uziri a

koman ki.. Yanzu ina laifin kin haihu da magariba

nazo da sassafen nan?... Baki ta ta6e kan ta

had'iye naman bakinta. "Ki ce kinbi order mijinki

dai Malama, amma bare nawa ne suka zo tun a

jiyan?.. Karara tsoron mutumin yaci k'arfin ki

k'wana biyu na fuskanta... Shiru tai dan bakin

ciki, ba abinda ta t'sana irin a dinga cewa tana

tsoron Ja'afar...K'wafa tai cikin ranta. Zuwan

Aunty A'i ne yasa aka dawo mutunci kuma.

Kullum tana gidan Ummi,duk dan gudun magana.

Yau kam Ja'afar yace ta hakura gobe tunda aiki

jibi kuma suna,yau masu g'yaran gida zasu zo.

Ba tace toh ba,haka bata ce a'a ba. Sai dai duk

ta sauya,tunaninta muddin yau take zuwa gidan

Ummi,toh ba makawa sai sunce chaketa,hakan

ya tabbata kenan ita mai tsoron Ja'afar ce.

Tabbas lokaci yayi da zata nuna musu bata

tsoron Ja'afar. Hakan yasa da k'warin g'wiwarta

ta tashi ta bishi d'akin waje. Shiri yake yana son

fita wajen ciciku cikun neman takaddun shi da ya

kone. Yanayin da ya ganta ta dan kama kai

yasan yau abin ya mot'so. Kawai sai ya kau da

kai. Zama tai gefen gado tana k'allon shi ta gefe,

"Haba Ya Ja'afar dan Allah... Yau daya kar kamin

haka dan Allah, ka barni naje tunda an g'yara

kitchen ga kuma d'aki muna dashi a waje bayan

suna suyi aikin.... Ido kawai ya zuba mata,sai da

ta kai Aya tukun yai magana. "Ke mey yau din

zata miki in baki fita ba?.. Kullum fa tun

haihuwar nan kina fita Salma,dan yau kad'ai nace

ki hakura sai gobe shine ba zaki iya ba Salma?

Fuska ta y'atsine, kan tace ita dai kawai ya barta

ta fita toh. K'allonta yake,abu yai sauki yanzu

tana son dawo da hali? "Son ranki za'a bi yanzu

koh nawa Salma?... A gida na ban isa nace ga

abinda za ai ba sai ace a'a?.. Meye haka kike

son kawo wa kuma da ya wuce?.... Hawaye ta

fara mishi,tabbas yau in bata fita ba,toh gobe fa

sai dai ta toshe kunne. Haushi tai bala'in

bashi,akan wannan shine harda kuka?.. Sam bai

son abin da ya wuce a dawo dashi. Nan ta zaune

mishi tana mishi kukan gardamar sai ya batta.

Haka yanaji yana gani sai shi ya sauke ya barta

yace ta shirya su je. Da murnarta ta shirya suka

fita ya sauke ta. Sai dai shi sam baida walwala.

Haka tai ta fita har ran suyar nama,washegari

ma wai zata wanke gida,anan suka hau suka

fad'o.. Ya ja ta ja,harda fad'in dama ance

tsoronshi take ji. Ya rant'se da in har ta fita,toh

zai maimaita mata abin ranar,wato ta fita a bakin

aurenta. Tuni ta nut'su ta dawo hankalin ta. Tuni

ya kashe bakin t'sanya,har ya fice ya barta tana

kuka,harda dariyar mugunta... Ya k'wa gano lago

ai. By Feenat Ja'afar.

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

21_Ranar ta fita a Napep ta layin su Ja'afar taga

wani kamar shi tare da wata, har zasu wuce ta

gane Bintu ce,da sauri tace mai Napep ya t'saya.

Sam a yadda suke ba kace ba masoya bane,dan

sai wani sunne kai take kasa halamar kunya.

Tuni zuciyarta ta hau tafasa,ba shiri tai wajen

gadan-gadan,dai dai suyi sallama harda dago

mishi hannu. Kan ta karasa har ya juyo itama ta

tafi... Ganin yanayinta shima ya dan

tsorata,amma sai ya maze. "A'a, har kin fito?..

Harara ta sakar mishi kan ta k'allo Bintun da har

tai mata nisa. "Ban sani ba... Ashe dama zance

ka fito shine kace na hau adaidata koh?.. Kuma

da Bintu?.. Har kana wani yage mata baki...

Hannu ya kai kan bakinshi halamar tai shiru yana

duba layin, "Haba Salma,a titi fa muke,kiyi hakuri

ba abinda ki ke zata bane ba... Harara ta kara

sakar mishi,kan ta farga har ido ya ciko da

hawaye. Tabbas yau ya tabo jaraba... Dan sarai

yasan Bintu kam sonshi take,kuma Salma ta

sani. Akan kishiya k'wa, yasan sai Salma taki ci

taki sha. Tuni ya hau lallami harda rantse rantse

kamin ta yarda bayan anje gida. Wataran yakan

yi tunanin koh Salma na da Aljanu,in ta tashi

sauya hali tafard daya ne,sai dai in ya bud'e

mata wuta su shirya. ~~~~~~~~~~ "Shiru ake

jinki makociya,koh dan ziyarar yamman nan an

daina zuwar mana sai jefi-jefi, koh mutumin har

yau yana nan da kullen?... Baki ta dan ta6e,kan

ta bawa maman Ummi amsa. "Ai sai abinda yai

gaba, yanzu tunda akai abinnan na farko abu

kadan sai ya kafan sharad'i kan in na t'sallaka a

bakin aurena, ina gudun rabuwar mu,yanzu ma

minti goma ya ban na dawo. Baki Maman Ummin

ta ta6e, "lalle kina da aiki in dai mazan nan ne,

saf zasu mayarka marar y'anci in bakai ma

tufkar hanci ba,harda lokaci? Tab aiki.. Ga gobe

sunan _nurse_ din layin chan (Maman

Nuwaira),ke koh barka baki je ba, ke kinsan za'a

watsa karya kiyi kok'ari ya barki muje. Kai ta

k'ada, "Ai dole,dan wallahi baza ai bani ba,ko bai

bari ba naje koh minti ashirin ne a wat'sa

warishan nan dani. Hannu Maman Ummi ta bata

suka tafa harda shewar su,ana haka Ummi tai

sallama,kan tunda ta shiga Jafar yace tana nan

ta fito,wai sai had'a rai yake,shi yasa ta bar

mishi gidan, nan ta daura kan na Maman Ummi,

Zuwa chan Maman ummin tace "Kiyi kok'ari hudu

ki biyo min zuwa 5 dawo. Da wannan suka baje

har ta wuce ka'idar Ja'afar. *Washegari*. "Wai

dan Allah Salma na tambaye ki zaki ban amsa?

Y'atsine fuska tai kan tace "ina ji.. "Shin dad'i ki

ke ji in kin t'saya muna musayarya magana

dake?.. "Mey yasa in na ce ki bar abu sai dai nai

son ranki,amma ni ban isa ba? "Ita maijegon ta

ta6a tako kafarta cikin gidan nan da sunan tazo

gunki?.. Ki ban amsa? Baki ta saka,kan tace

"oho,kana nufin gyaiyar sod'i zani kenan?.. Tunda

ga areni muje biki koh?.. Kai ya kada, "Ke ki ka

kira kanki haka,ba Ja'afar ba,abu daya na sani,ko

na fita ba jimawa zanyi ba, saboda in ma kin

fita,toh kisan inda dare ya miki... "Mey ka ke

nufi? Kana nufin yau ma zaka ce a bakin auren

nawa Ja'afar?.. Da sauri ya kada kai,

"K'warai,tunda abinki naga na yanzu har so yake

yafi na da, in har kam kin fitan,toh kisani,kin fita

*A BAKIN AURENKI*... Sai ki zabi wanda ya fi

miki, aure? Koh gidan suna?... Kofar ya bugo

mata yai waje tare da barinta baki sake. "Eh lalle

yau zan nuna ma tabbas ba tsoron ka nake ba

Ja'afar... Wannan kurin bakin wallahi bazai

hanani fita sunan ba,daga yau kalmar nan ta *A

BAKIN AURENKI* tabar bakinka. Daki tai tana

balbalin masifa ita kadai kamar yana k'allonta.

Kaya ta fito dasu tana duba wanda zata sa,

_lace_ din sunan Ummi ta dakko wani karamin

_swiss_ da aka sashi siyanshi dan dole. Sunan na

manya ne, dan haka sai da kure adaka. Ba koh

shakku ta fice, yau tun dazu taji gidan su Maman

Ummi t'sit kamar ruwa ya shanye su,halamar mai

gidan yana nan kenan,amma tunda ta fara jiyo

hayaniya tasan yai waje. Gidan suna kam ya

kayatu, sun samu abinda ake so tuni aka baje a

faranti ana ci ana kora wa gulmar wata. Kan ta

farga har 5 da yan mintina. Haka kawai taji

gabanta na fad'uwa hankalinta yayi gida. Tashi

tai ana fad'in ta t'saya k'ulli ya kare a k'ulla

mata tana a bawa Maman Ummi. Sauri take ta

zubawa, dan da y'ar tazara a t'sakanin su.

Adu'ar ta daya,Allah sa Ja'afar bai dawo ganin

koh ta fitan ba. Ta rasa dalilin da ya sa

hankalinta ya tashi,bayan ita ta zabi hakan.

Lekawar da zatai shine taci ka'ro da Ja'afar suka

had'a ido. *WAIWAYE*... ***************

************** Haka yai ta juyi har kusan k'arfe

biyu. Washegari haka ta tashi sukuku, ga

fargabar Abba yau zai dawo,ga wani mugun

mak'on Ja'afar da yake taso mata. Kai in ma ba

wai bata kula bane gani take zazzabi ne a jikinta.

"Salma... Dagowa tayi ganin mama a kofa,da

mamaki fal fuska ta karaso ciki. "Wai har yau

kukan nan ki ke Salma?.. Mey yaron nan yai miki

ne haka?.. Hannu ta kai kan fuskrta,sam ba

tasan tana kuka ba, da sauri ta goge tana

k'ak'alo murmushin dole. "Mama ina k'wana.. Kai

kawai ta kada mata. "Haba Salma,kar fa ki rako

mata duniyar nan...kar ki zamo mace mai

kulafucin D'a namiji duk k'wa wulakancin da ya

mata man... Ashe ni ina chan jiya nai baccin

farin ciki da aka rabu lafiya ba rabo bare ya kawo

cikas a zawarci ashe ke kina nan kina kukan an

rabu? Haba Salma, karan nan ne fa ki ke da

dama ta biyu,tunda har ya sallame ki. "Maza

goge hawayenki ki biyoni daki yanzu. Kai ta

kada,a gaskiya ta fara mamakin irin kiyayyar

dasu mama suke ma Ja'afar, wato har ma godiya

ake ta rabu da alakakai?... Allah yaga tafi jin

haushin kanta sama da haushin Ja'afar, in ma

taji haushin shi toh bai wuce yadda ya k'ulle

mata gida ya kuma tafi koh ajikinshi. By Feenat

Ja'afar.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

22_"Toh wa ya jawo?... T'sam tai yayin da zuciya

ta tambaye ta, "Ni ce... Tabbas ni najawo, amma

ba laifi na bane. Kuka ta fashe dashi,tabbas anci

k'arfinta,ta ko'ina an mata dabaibayi da huduba

gur6atacciya. "Gashi na jawo wa kaina saki biyu

ba tare da na samo kan ba(kan Ja'afar).. "Oh ni

Salma.. Ina tunani na yake da har na aikata

wannan wautar?.. Ina son da nake ikirarin ina ma

Ja'afar?.. Ina ya je... "Salma... Mama ce ta

kat'se mata tunanin gaskiya da kira. Hannu tasa

ta share hawayen ta,ta daga kai tare da fitar da

iska dan daidaita nut'suwar ta. "Na'am.. Ta amsa

kan ta tashi tai waje. "Gani mama, Kan gado ta

nuna mata kan tazo ta zauna. Ba musu ta

karaso. Kafad'arta ta dafa kan ta numfasa, "Kina

ji koh Salma? Kai ta daga mata. "Baban ki yau

nasan zai dawo,tabbas ya rit'saki nasan zai cid'a

ki ne a banza. "Yanzu abinda nake so kiyi

shine,ki je gidan A'i,dan mijinta baya gari ya tafi

sari,ki barni in na gama lalla6a shi sai ki

dawo,dan karan nan kam sai dai ai wacce za ayi,

amma aure kin gama... G'wara a chanja

hannu,tunda wannan d'in ba fus, bare ass,sai dan

banzan dacin rai ba koh gidan kai... Hawaye ne

ya zubo mata,ba da ban suna matukar kama da

Mama ba,da tayi shakkun akan haihuwar ta...

Mama na da kamasho a ta6ar6arewar aurenta

kashi 70 acikin dari... Tabbas uwa uwa ce,

amma su kam tasu uwar sai g'yaran Allah..

"Au,au,kuka ki ke? Dan nace baida gidan

kanshi?.. Koh shi ya siya ya gina da gumin ajin?..

Yarinya ki duba yadda ake harka,y'an uwanki na

shiga ta alfarma amma ke kin zama y'ar k'allo..

Ki farka a bacci Salma,dan rayuwar nan ta zo mu

fafata ce. Kai ta k'ada tana goge ido,sai ta mike

tai hanyar waje, "Bari na shirya zuwa gidan

Aunty A'in, naga 10 tayi. Kai Maman ta daga

harda washe baki, "Yauwa,ko ke fa.. Maza aje a

shirya,ga nan abincinki a kitchen. Kai ta k'ada

kan tai waje, da kallo Maman ta bita, ba abinda

y'arta ya gaza a gareta,wa ma zai ce ta ta6a

aure in ta fito da ita gari?.. Dole kud'in da ba taci

ba da yanzu taci gun Salma. ***************

************** A k'wance take kan _3sittern_

Aunty A'i,in banda ciwan kai ba abinda take,

"Tashi ga maganin kisha... Kai ta dago,Aunty A'i

rike da kofi da _paracetamol_. Bayan tasha ta

g'yara zama,d'uk gidan bata jin da wanda bai

ta6a kushe mata Ja'afar ba sai Abba da Aunty

A'i. Hawaye ne ya zubo mata,kan kai duk'e tace

"ban san mey Ya Ja'afar ya t'sarewa su Mama

ba da sam basa kaunarshi... Yanzu ki duba Aunty

A'i Mama yau tace murna take an sake ni..

Harda fad'in g'wara da bamu samu rabo ba...

Kuka ne yaci k'arfinta,tuni ta hau yi ba

kakkautawa. Taso wa Aunty A'in tayi zuwa kusa

da ita ta hau lallashi,chan ta numfasa itama

harda hawaye ta fara fad'in "Kinyi wauta Salma

matuka,samun irin Ja'afar a yanzu wallahi sai kin

tona,irin halin da kika dinga karta mishi duk na

samu gun Abba,kinsan nima ba wai Mama nayi

dani bane sosai,dan ban fiya shiga irin shirgin

nan ba. "A gantali har gida sukutum ki ka kona

mishi Salma.. Naji ance ya kuma shiga cikin y'an

_missed call_..Bana tunanin har yau ya gama

tattare takaddun da ya rasa kuma duk a dalilinki

fa,amma dai dai da rana daya bai ta6a hanaki ci

koh sha ba?.. Duk da baki san ta ina yake samu

ba. "Maimakon ki zama mace ta gari mai

k'wantar mishi da hankali har ya manta bakin

cikin da yake ciki na rasa aikinshi,a'a sai ma

kara hura mishi wutar masifa ki ke a gida.

"Salma kina da ilimi fa,kinsan d'ukkan hukunci a

game da matar da take sa6a umarnin mijinta,

bare ke da kusan kullum cikin shi kike?.. Ina ki

ka bar islamiyar taki Salma?.. Da har kika bari

rudin su Ummi da chan wasu jahilan makotan

suke hure miki k'unne,wanda in zaki titsiye su ba

mai iya rashin mutuncin da ki ke Salma.. "Nayi

imani zaman cikin gidan ki ya fiye miki alkairi

sama da zaga makota yawan gulma da ki ke..

"Ya sanar ni shi sai a shafe wata nawa,baiga

makotan naki na zirya gidan ki ba sai dai aiken

bani taliya bani mai, shin sun fiki sanin ciwan

kansu ne Salma? "K'wanaki haka har gida na

samu yana fad'a kina fad'a, amma dana shiga nai

miki fad'a, sai kika nunan wai maza sai da wuta..

"Kan kiyi aure Salma ni nayi da shekara hudu, ba

zaki fad'an halin maza ba,amma a lokacin na biki

da murmushi ne kawai. "Ki dube ni nan Salma...

Dago tai ido jajir hawaye na zuba. "Wallahi tunda

nake akan fita unguwa ban ta6a sa'inasa da

Abban Aslam ba,kar kara in naja,ya ja,hakura

nake na barshi,wani sa'in sai kiga har ya

fita,amma sai ya dawo yace in shirya ya sauke

ni,ina fara'a za'a gama komai ba bacin rai, duk

wanda zai fad'a miki ana tank'wasa namiji ta

fad'a da bala'i wallahi karya yake miki,sai dai ma

kullum yai ta baud'e ga uwa uba sane mishi da ki

ke. "Zuciya nason d'ukkan mai k'yautata mata

Salma,sannan a kullum tana kara nisa ga wanda

ke munana mata... Ki gane wannan, tunda dama

taki,shine ya koma miki ta hagu, ki fita a bakin

aurenki Salma, tun da kuruciyar ki wai har kin

zama bazawarar k'arfi da yaji? Ranar da kanshi

Ja'afar din yazo gidan nan,akan irin yadda ba

k'ya jin maganarshi,nai mishi alkawarin zanje har

gida na miki fad'a sai gashi Allah ya kawo

wannan. Sosai tai mamakin Aunty A'i,da yau ta

zauna fed'e mata biri har wut'siya.. Tai imani duk

maganganunta ba wanda ba ita ke da laifi ba

tabbas. Wata muguwar nadama ce ta sakko

mata,kuka kam ba kama hannun yaro, har sai da

taji ba dad'i. Bataki koh yanzu ta nemi gafarar

Ja'afar ba kan ya maidata aurenshi,tai alkawarin

d'auwama acikin dakinta har sai yace Salma fito.

Aiya Salma, Ja'afar baya tataki,yanzu ta Bintu

yake.. By Feenat Ja'afar.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 29

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

23_Zazzabi harda amai take,duk zatan Aunty A'i

akan kukan da taki dainawa ne. Washegari ba

zato ba t'sammani Aunty A'i ta t'sinkayi sallamar

Abba a t'sakar gida. Lokacin dawowarta daga

band'aki kenan ta gama zuba ma Salma ruwa a

amai na tun jiya da yaki t'sayawa,sai dai tana jin

Abba ne ta mike tare da yin waje da sauri.

Hannu Aunty A'i ta d'aura aka,ganin zabga-

zabgan bulalin da Abban ya shigo dasu gidan,

fad'i yake "Ina take Aisha?.. Tuni idonta ya raina

fata,fatan ta Salma taji ta buya. Cikin in'ina tace

"Abba wa d'in?.. Hannu daya marar bulala ya

nunota dashi, "Kinci gidan ku... "Bani hanya na

wuce,yau mai rabani da Salma sai Allah a gidan

nan.. Da k'arfi Aunty A'i tace ta gudu,hayaniyar

ce ta fiddota a band'aki ta had'a uban zufa dan

azabar amai, har bata danji sosai, lekawa tai ta

labule jin an ambaci sunanta... Ido waje ta koma

da baya tana neman ma6oya,tuni ta ware tai

bayan kujera tana rufe baki da duk hannunta biyu

jin Abba a parlourn. "Dan Allah Abba kai

hakuri,wallahi bata da l... "Aisha,koh ki fito min

da ita koh bulalinnan su kare a kanki... Ido Salma

ta rint'se da sauri,kirjinta sai d'ukan tara tara

yake. Sai dai mey? Kamshi turaren kayan Abba

ne ta busu hancinta,take taji amai ya taho tai

kokarin ta mat'se sai dai ta kasa,tuni k'ak'arin

aman ya taho sai dai ciki ba komai. Bata zata ba

sai jin magiyar Aunty A'i tai tana dan Allah yai

hakuri... K'wak'waran mot'si batai ba taji saukar

bulali tai ajiki ta ko'ina. Ihu take da iya guntun

k'arfin daya rage mata tana Abba zan mutu,

ina,kawai lafta mata yake,da Aunty A'i ta rike sai

ya cika ya hau zuba mata wata. Makogaro ba

ruwa,duk ya tafi a amai,tuni har muryarta ta

dashe,sai k'ak'arin amai da take. Kamar an hullo

mama sai ganinta sukai a kid'ime,ganin yadda

yake jibgar Salman ta bala'in tsorata, da sauri tai

waje dan kara kiran yayanshi Ganin Abba zai

kisa,yasa da sauri Aunty A'i tai ma Salman rumfa

tana yai hakuri cikin kuka,ganan Salma koh

k'wakkaran mot'si batai,bai bi takanta ba ya hau

zuba musu tare, "Abba ciki ne da ita,wallahi zai

zube.... Chak ya t'saya da bulala a hannu sai

zufa yake, yai dai dai da shigar Mama tai katari

da zancen Aunty A'in. Bulala ya yarda yana

haki,tamkar yasa kuka dan bakin ciki,tunda yake

basshi da fadanshi amma bai ta6a sa hannu ya

dakesu ba sai akan Salma,wannan shine karo na

biyu gareta. So take tafi k'arfin kowa a ganin

shi,toh shi bazata fi karfinshi ba. "Ba mai fin

karfina a gidana ban maganin shi ba... Yau kin

t'sira a dalilin zancen A'i,da na lahira ya fiki jin

dad'i.. Duk da laifin nafi daura ma uwarku data

zuba ido kuna abinda kuke so... "Mun shiga

uku... Da sauri Maman tai kan Aunty A'i mai

magana. Jijjiga salman take tana kira. "Salma!...

Salma!!.. Mama bata mot'si wallahi... Tuni suka

hau jijjigata Aunty A'i na kuka. "Shikenan Malam

ka kashe min Y'a ka huta... Babu yadda banyi da

kai ba akan kai hakuri kar kazo,kar kaje,ga nan

irinta ka... "Ki rufe mana baki, koma meye ke

kika jawo, ruwan k'anin Aslam ya gani a jarka da

sauri kuma ya dakko wai su mat'sa agun,ido duk

hawaye suka mat'sa. A hankali ya dagota tare da

yayyafa mata, a hankali ta kawo numfashi sai dai

ido a rufe. "K'unnen k'ashi gare ki ne Salma,shi

yasa baza mu shirya ba sam sai kin g'yara hali.

Kuka ta fara kad'an kadan lokacin da suke

dagata, sosai ta lillisu,duk jiki ciwo. Wayar Aunty

A'i,da Ja'afar suke magana wai yaji Abban su

yace Mama ta bugo kan Abba zai kashe Salma...

Cikin kuka tace "Kazo gidana suna nan. Duk ya

kuma kid'ime, tabbas ba d'ukkan wasa yasan

Abba yake ma Salma ba,tunda Aunty A'i take

kuka. Garba ya kalla,"dan Allah kaini gidan Aisha

yayar Salma. Da mamaki yake K'allonshi, "amma

dai kasan yanzu _chairman_ zai zo yama signing

koh?.. "In bazaka kaini ba na fita na hau abin

hawa. Kafad'a ya daga, "a muje, ni meye nawa.

Mijin Aunty A'in ya kira koh yana gidan,yace su

shiga kawai,Abba ya sanarshi komai tun dazun.

Abba ya fita lokacin da suka zo,mama ta tafi

nemo abin hawa. Aunty A'in ce ta shiga

dasu,ganin bulalin wajen duk sun kakkarye ji yai

kamar yasa kuka,yanzu duk bulalin nan a jikin

Salman sa ta kare? Jiki a sanyaye suka je

parlourn,duk ta kudindina tana rawar sanyi,da

sauri ya karasa gunta yana kira,tana jinshi ta

kara rushewa da wani kukan. Hijabin ya yaye

mata,yana ko'k'arin cicci6ota ya tuna da sakin

dake t'sakanin su,sai ya zame hannu tare da

zama. Bai san wani irin so yake ma Salma

ba,wanda har yake rawar jiki akanta duk da

abinda ta mishi, gashi har taja jiya ya bada kai

gun Bintu bori ya hau. "Mey yasa Salma?.. Mey

yasa ki ka zabar mana irin rayuwar nan?.. Gashi

yanzu kin dasa min son kara aure koh na samu

maslaha aciki... A zabure ta tashi,duk da yadda

take jin jiki tana cije le6e dan azaba. "Mey kace

Ya Ja'afar?.. Aure?.. Da sauri ya k'allo ta,sam bai

tunanin zancen ba a ciki yai ba. Ganin bai bata

amsa ba yasa ta yarda da abinda taji,hannu tasa

duka biyu ta dafa kan ta zamo kasa tana cije

baki,g'wiwa biyu ta durkusa duk tai kalar tausayi.

"Ka rufamin asiri Ya Ja'afar dan Allah,wallahi, na

rantse bazan kara ba..Dan Allah kar kamin

kishiya.. Dan Allah, wallahi bana sonta.. Allah

zan g'yara..nai alkawari,.. Ido ya rint'se, had'i da

cije le6e,ba yau Salma ta fara mai magiya da

rantsuwa kan ta d'aina ba,amma ba abinda ya

sauya zani.. Yanzu komai ya kare musu,aure

gareshi ya zama dole. By Feenat Ja'afar.

Juma'@ Mubarak.

9/29/16, 9:07 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 24-Kai

ya kada tare da mikewa, "kiyi hakuri Salma.. A

baya na baki d'ukkan wata dama taki kinyi watsi

da ita.. K'arfi da yaji so ki ke ki mayarni wani

iri,dame zanji Salma?.. Na fita waje na samo

6acin rai,sannan na shigo gida nan ma wani

6acin ran ne,maimakon a lallashe ni..A'a ni

kullum ni nake lallashi. "Kiyi hakuri,Allah ya baki

lafiya.. Garba ya k'allo yai mishi halamar su tafi.

A hankali ta mike tana jin wata irin hajijiya na

debarta. "Nasan ni na ja ma kaina komai Ya

Jaafar... Ja yai ya t'saya, jin taci gaba yasa ya

juyo. "Tabbas na chanchanci d'ukkan wani

hukunci da zaka min in dai zaka yafe min.. Kasa

tai da kai,tai matukar zama abin tausayi a

gunshi,sai dai kawai ya kasa gane nadamar

Salma a yau,dan ta saba, ga kafa sai ka'rkarwa

take. "Amma dan Allah wa zaka aura?.. Ba dai

Bintu ba?. A yadda ta t'sareshi da ido yasa ya

kasa magana,sai ya kalli Garba,kafad'arshi ya

daga mishi halamar ba ruwan shi. Sai da ta

maimaita kan ya daga mata kai. Murmushi tai da

yafi kuka ciwo,a hankali take neman juyawa wani

kanta ya sara gami da ganin duhu. "Kar ki min

fassara Salma,ba abinda ya had'ani da Bin... Luu

ta fara halamun zata fad'i, cikin zafin nama yai

taku daya ya taro ta. Gaba d'aya jikinta ya

saki,ga wani irin zafi kamar garwashi. "Salma..

Jijjiga ta ya fara,da sauri Aunty A'i ta shigo,sai

ga Mama na fad'in ta taimaka su sa Salman a

Napep gashi ta nemo.. "Mey zan gani haka... Da

sauri suka juya ganin Mama da tai turus ganin

yadda ya mammakale Salman,ita k'wa k'allonshi

kawai take hawaye nabin gefen idonta. Garba ke

mishi da hannu kan ya saki Salman amma kamar

yana zigashi,sai kara naneta yake. Gaida Maman

sukai da girmamawa tai banza dasu. Sababi

Mama zata fara Aunty A'i ta jata sukai waje.

Garba ne ya tsayarshi ganin yana neman cicci6ar

Salman. "Kasan dai yanzu ba a mat'sayin

matarka Salma take ba,kar ka nemo mana

magana dan Allah.. Harara ya sakar mishi,kan

cikin fusata yace "na mayarta toh.. Koh da

magana? Kai ya k'ada mishi, kan ya bud'e mishi

labule, "Dan Allah kaimu asibiti... "Auntyn mu..

Aunty A'i ya k'wada ma kira, da sauri suka fito

ita da Mama dake huci. "Asibiti zamu kaita, dan

Allah Mama ki yi hakuri na kaita.. Harara ta

sakar musu kamin tabi bayansu ta sallami mai

Napep sai asibiti. Murna ta koma ciki,da d'ukkan

hannu biyu mama ta dafe kai,jin rahoton likita

kan tabbatar da cikin Salma,dan haushi ba tasan

tai waje ba. Shikenan an 6ata mata shiri, ciki?..

Kai amma an sha da ita, sam ta zata fad'in A'in

ne dan a bar Salma. "Mama kiyi hakuri zata

samu lafiya,bari naje na siyo allurori mu dawo.

Kala bata ce musu ba, asalima ji tai kamar ta

rufeshi da duka koh ta huce. A gun Garba ya

k'ar6i kud'i,basu juma da tafiya ba sai ga Ummi

da Aunty A'i sun zo,tuni k'wa ta ware tana

surfawa Ja'afar Ummi na tayata. Kai Aunty A'i ta

k'ada, fatan ta a kullum Allah ya ganar dasu

Mama alkairin Ja'afar, alkairin da batajin koh su

wanda suka auri masu halin suna musu. "Mama

Salma fa matar Ja'afar ce har yanzun,don

musulunci ya mallaka mishi,matukar batai idda

ba,bare da kunne na naji yace ya mayarta

wallahi, dan Allah Mama ki sassauta, in har da

mey lefi aciki toh fa Salma ce.. "Ke dama ina

kika ga kishin kai?.. Ai guntunki ta tsotsa, shi

yasa sam kusan halin ku daya... Aure kuwa in dai

ni nai nakudar Salma toh ya kare ya gama.. Ba

ruwana da wani ya mayarta,sakaryan yaro

kawai,sam bai da zuciya wallahi. Ummi ce ta

amshe tana k'wafa. "Ai wallahi dad'i yake ji dan

yaga Abba na jibgarta,dama garin d'ukan yaja ya

rasa cikin ai da shi ya jiyo... "Ummi mey yasa ke

sam baki da mutunci ne?.. Baki Ummin ta turo,

"Ja'afar fa ba sa'anki bane,in bazaki g'yara ba

toh kar ki 6ata... Salma ita ta chanchanci komai

ba Ja'afar ba,gashi taja yace aure zai kara... A

zabure Mama ta jiyo, "Aure?.. Shine ki ke kuma

fad'a min ya mayarta?.. Kai ta k'ada, "eh lalle

Ja'afar, toh k'wa zama da kishiya ba dai y'ata

ba, karan nan zamu banje da Malam wallahi akan

maganar komen nan,sam naki jinin yaron nan

wallahi.. "Ni kam Mama bana ganin aibun Ja'a..

"Kimin shiru,kar ki gani din,amma aure angama.

****************************** Yau k'wananta

biyu aka sallame ta,fur Mama taki bawa Ja'afar

fuska,daga ina wuni lafiya shikenan. Su Abban su

Ja'afar harda y'an cikin gida sunzo sun jajanta

abinda ya faru. Kowa ya bawa bangarenshi

rashin gaskiya, take Baba yace ya mayarta. Kai

duk'e yace ai tun ranar chan ya mayarta,nan ya

ja mishi kunne kan sarar ki fita A BAKIN

AURENKI. A gaban su Abba ya kara tasa zancen

zai kara aure,cikin fusata Abbanshi yace "Ba mun

gama maganar nan da kai tun jiya?.. Wane aure

kuma bayan wannan da aka mayar? Kai yai kasa

dashi yai shiru, murmushi Abban su Salma

yayi,kamin yace "Kamin dai dai Ja'afar, fatana

Allah yasa auren shi zai zaunar da Salma a

dakinta ta rungumi ibada. Ja in ja sukai tai

t'sakanin Abban Salma da Abban Ja'afar, dak'yar

Abban Ja'afar ya yardewa Ja'afar kara aure. Ana

watse wa koh gama jan mota basuyi ba Mama ta

fara sababi,ita a fafur ba inda Salma zata,bata

zauna da kishiya ba,saboda haka ba mai zama da

ita a yaranta. Itade Salma bata um bata um-

um,sai hawaye kadai ke zuba,ita kad'ai tasan ya

zuciyarta take hautsina mata,ta faru ta

kare,tunda har manya sun amshi magana.

"Ja'afar? kishiya? Kuma da Bintu kawarta?.. Tab

da matsala. By Feenat Ja'afar

9/29/16, 9:10 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

24_Daaga sosai akai da Mama akan komawar

Salma,sai da Abba ya bud'e mata uwata sosai

kamin harda Yayanshi ta saki aka ta koma din.

Ita kanta Salman yanzu ba kaunar komawar take

ba sai ta mot'so mata ga laulayi. Ga Ja'afar

tunda ya ji batun ciki ya kasa sukuni,kullum yana

zaryar dubiya da leda. Shi dai bai mat'sa da sai

ta dawo ba lokacin, dan g'yaran gida sosai yake

wanda Ummanshi ta bashi ya zauna aciki. Har

gida yau Abba yaje gun Abban sun kan lalle yau

Jafar yazo ya dau Salma. Da dare k'wa ta koma

dakinta. G'yaran nan gidan ya t'saya

chak,sakamakon aikinshi da aka mayarshi aka

bashi albashin da ya wuce shi,bai da mat'salar

kud'i yanzu,auren shi kawai yasa a gaba. "Ina

k'wana.. Cikin sanyin murya ta gaida shi kai

duk'e, kai ya daga kamin yace "ya jiki?.. Shiru tai

ba amsa. "Ki tashi ki zauna man.. Kai ta dago ta

k'alleshi kamin ta kada mishi, "A'a magana nake

son muyi da kai. Zama ya g'yara yana

sauraranta. "Mey yasa ka ke son auren Bintu?..

Da ido ta kafeshi tana jiran amsa. Murmushi yai

kan yai baya kad'an harda d'aura kafa daya kan

daya. "Saboda tana so na ne Salma.. Kai ta kada,

''kaima kana sonta?.. A bazata tambayar tazo

mishi,ga takafeshi da ido hawaye taro a idonta.

"Ki gane Salma, ba wai.. "Eh koh A'a?.. Amma

nake son ji kawai. Ba koh shakku yace mata "eh..

Amma.. Hannu ta daga mishi tana hawaye,

"Barni haka dan Allah,amma kasan Bintu k'awata

ce da koh?.. Ya zaka min haka? Kai ya kada

harda dariya, "A sani na banta6a ganin Bintu a

gidan ki ba,asalima... Sallamar Aunty A'i ce ta

kat'se mishi maganarshi,sai ya tashi dan dan

bud'e mata kofar,da kallo ta bishi tana mamakin

kalamanshi,sai kawai ta k'ada kai ta mike tana

goge ido. "Bissmillah mana Auntyn mu.. Yana

gaba ta biyoshi a baya, sosai suke dasawa da

Aisha,dan tasan abinda take sosai,shi yasa baya

6oye mata komai. Bayan sun gaisa ya mike yana

zai fita, kai kawai ta k'ada mishi,sai Aunty A'i ce

tai mishi a dawo lafiya. Zama Aunty A'i ta g'yara

tana ma Salman k'allon tuhuma. "Ashe Salma

baki fara g'yara ba har yanzun?.. Da rashin

fahimta ta k'allo ta tana hawaye, "Fita fa yayi

jiyan nan dawowarki amma har kin fara nuna

mishi baki sauya ba. "Aunty A'i ba abinda na

mishi fa Allah.. Katseta tai da fad'in "Amma zai

fita babu koh a dawo lafiya?.. Haba Salma,nan ki

ka dinga rantsuwar kin shiryu, koh har kin leka

makotar ne yau d'akko sabon darasi?.. Kuka ta

sa mata tana girgiza kai, "Haba Aunty

A'i,k'awata fa zai aura fa,taya bazanji zafinshi

ba?.. Da mamaki tace "wacce kawar taki? Cikin

kuka tace "Bintu,dalibar shi ce a Day school fa.

Ita dai ta hanga bata gano wace Bintu bace a

k'awayen,tasan sarai k'awayen Salma basu fi

biyu ba wanda tasan su. "Wace Bintu kuma cikin

k'awayen naki? Amma basan ta ba koh?.. Kai ta

daga mata, "islamiya mukai tare fa.. "Mtsww,

t'saki Aunty A'in tai tana k'auda kai, "har wata

kawar islamiya K'awa ce?, bana jin ko hanyar

gidan ku ta ta6a zuwa balle ta zama kawarki,

koh ta halarci bikin ki?.. Kai ta kada mata tana

goge hawaye. Cikin lallami ta fara lallashinta.

"Kar fa ki bari tun kamin ta shigo taci galaba

akanki Salma, yanzu ba lokacin t'sayawa kishi

bane a gunki, lokacin g'yaran kuranki na baya ne

Salma... Ki d'auka baki ma ta6a sanin wata Bintu

ba rayuwa,dan ba gaminki da ita sam. "Ki kuma

fidda zancen auren nan a ranki,dan koma meye

ke ce sila Salma. Nasiha tai ta mata tana kuka

har ta gamsu da bayaninta. Ta bata shawara

masu k'yau, ta kuma d'auka. Da ya dawo ya ga

chanji,sannan bata kara mishi maganar Bintu ba.

Yau satin ta daya da dawo wa,amma banda

Maman Abba ba wanda ya leko mata har Maman

Ummin, Ga sai wani kama mata kai Ja'afar din

yake bare tace zata leka,abu daya ta sani,shine

ta daina zuwa gidan kowa sai in ta kama.

Washegari har kofa ta rako shi zai fita tace zata

leka gidan Maman Ummi.. Yana fita yace mata

sai ta dawo kawai. Da k'allo ta bishi,sai ta ga

kamar gat'se ya mata,dan haka ta koma ciki tai

k'wanciyarta. Mukullin gidan da ake g'yara zai

fitar musu dashi sai ya dawo. A k'wance ya

sameta ido rufe a parlour,sai yai jim,ganin bata

fita ba har ya dawo. "Har kin dawo ne?.. Kai ta

girgiza mishi,sai yai d'aki yana tunaninta, haka ta

saba mishi kan gaba ta fand'are mishi,shi dai

yasan yai alkawarin mud'in ta tambaye shi fita

ya d'aina hana ta,yasan duniya makaranta,da

sannu zata gane abinda yake gujar mata. Koh da

zai fita sai ya kara nanata mata kan taje kawai.

Bai jima da fita ba ta fito,tana dan jin hayaniyar

su kasa-kasa. Har zatai Sallama sai ta ja ta

t'saya jin wata gulmar da suke. "Ai yanzu ya

zamarta mai gadinshi, tunda ta dawo ba inda taje

tana d'aka,koh duk sururin zai kara auren ne?..

Tana jin Maman Ummi tace "oho mata,ba ita

areni muje biki ba,mijina baya fad'a.. Muryar

Maman Abba tajiyo tana fad'in ''ni tausayi ma

take bani wallahi, ranar chan dana shiga duk ta

rame tai baki,kana yaronka da kai an ma saki

2.... Baya tai cikin sanda danjin wani na shirin

fitowa. Gida ta koma ta cire hijab tai dabar a

kujera, tun yaushe haka take faruwa da ita?..

Ashe ita k'allon mara wayo suke mata acikinsu?..

Kai ta daga sama, lalle ta gane mey Ja'afar yake

nufi da mutunci yake nemar mata.. Yau ta gane

ashe in an yi gulmar wani da kai yau gobe da kai

za'a kafa ai taka. "Allah na gode maka daka sa

na ji na kuma gani. Tabbas Ya Ja'afar babban

gata yai mata. Toh a ina ma suka samu labarin

za ai mata kishiya?..har dare tana neman amsa.

Ranar har kukan bakin ciki tai na taraiyarta dasu

Maman Ummi. Tuni ta tattare kowa ta wat'sar

shi,duk da ba duka aka taru aka zama daya ba.

Ranar Maman Waleeda da suke kira uwar tsoron

miji ita ta zo mata harda nasiha har gida,matar

da koh gidanta sai tai fita ashirin bata leka

ba,kuma makociya ta kusa,har misali tai mata da

Maman Ummi. "A kaf unguwar nan bana tunanin

da matar da take cikin takura irin na Maman

Ummi Salma, ke shaida ce,in kinji gidan yai shiru

ba koh tarin yaro kasan uban na gida. Sannan in

zai shekara ba taje ko'ina ba shine dai dai a

wajenshi,duk fita in zatai satar hanya take tasan

in ya fita da yamma sai dare,amma a gun kuri

tafi kowa iya dadin magana,da ina cikin su,daga

baya na gane taraiyyata baza tai dasu ba,sai na

zabi zaman gidana ya fiye min alkairi sama da

yawan gulma. "Ka'rkara in abu ya faru in leka a

tsatssaye in dawo, dan Allah ki iya kafarki

Salma,dan zasu kai ki su baro ne kawai. Kai ta

k'ada mata, "Na gode Maman Waleeda,Allah bar

zumunci,kuma InshaAllah naji bayanin ki,duk da

mun kusa tashi a unguwar ma duka InshaAllah.

Anan ta sanarta za ai mata kishiya,k'warai ta

jajanta mata kan ta kara da y'an shawarwari,tun

daga ranar mutunci da Maman Waleeda

suke,kusan duk yamma tana turo mata su

Waleeda taya fira,har lokacin tashinsu yazo.

***************************** Cikinta yana da

wata biyar lokacin auren Ja'afar saura sati. Sam

bazaka zata Salma bace, dan tamkar bai dameta

ba haka tai a auren. Har ranar Ja'afar yana fad'in

wai ta daina sonshi gaba daya,koh kishi bata yi

zai kara aure,murmushi kawai ta masa,dan tsaf

ta kula da rawar kan da yake k'wana biyu. "Ba

k'ya shirye-shiyen komai gashi lokaci ya taho

fa... Tamkar ya choka mata abu makogwaro taji

wani iri,kawai sai ta sa mishi ido tana k'allo.

Tabbas rawar kan Ja'afar karuwa take akan

auran nan,banda haka wani irin tambaya ce

wannan?... Shikam tunani yake yadda Salman ta

g'yaru har kullum,a ganinahi halin ko'in kula da

yake nuna mata ne akan fita. "In da hali zan fita

kar6o wasu kayana unguwar Ummi. Kafad'a ya

daga mata,kan yace "sai kin dawo... Yai waje.

Baki sake ta bishi,tun bayan dawowarta ta kasa

gane inda Ja'afar ya dosa,abu yake mata tamkar

ya kosa da zaman ta a gidan. Gashi tun kamin

amarya ta tare har ya sallamata,wai ko'ina nan

gaba in zata kawai taje,dan yanzu bai son 6acin

rana irinta da. Toh mey yake nufi? By Feenat

Ja'afar.

9/29/16, 9:11 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana

murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi

an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci. Har

yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna

mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh

yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a

gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu. Kuka take

yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya

sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana

ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan

ba mai chazan hawan jini. Kai ta dago tana mishi

k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a

wa matarka baka so na?.. Ni nace ina son ka

koh?.. A haka za ai zaman lafiyan?.. "Ke kinga

bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?.. Da

sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato

harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan

kaina.. "Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki

ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata

fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...

Waje yayi zuwa dakin Salman. Kai Bintu ta k'ada,

"ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a

da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada

mata mari tukuicin sharri. Ita kam tanajin bud'e

kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance

ido. "Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a

gidan nan?.. Yaushe nace miki Bintu ce tai min

tallar kanta na aura?.. Harara ta sakar mishi da

k'allon kar ka rainan hankali. "Ka nad'e taburmar

kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine

ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya

faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura

igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?.. Baki ya

saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi

na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla

mishi a gun y'ar uwarta ashe?.. Bai da tace wa,

kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka

fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba

kai ka fad'i ba... "Idan kuma habaici da iyayi

kake neman matarka ta dinga min dan ka huce

haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana

sa kafar wando daya da kowa a gidan nan

wallahi.. Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki

ta barshi t'saye baki sake. Titi ya fice ko ya

samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin

mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam

yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa. Tun

daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in

Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata

dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har

mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da

gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a

ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya

mata magana ita y'ar dika take,daga shi har

amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.

Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata

kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu

suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe

kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai

ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar

keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi

da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune

kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai... Ta fada

tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk

abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su

aciki... Chak! Taja ta t'saya rike da labule a

hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar

su. "Sai yau Aunty Ladi zaki zo min? Har nayi

fushi ai.. Baki sake Salma take k'allonsu,tana

k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma

Bintun kuskus tai baya da sauri. Ido ta rint'se

tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu

ta gane inda Bintu ta samo duk wasu

_information_ na zaman aure nata ba agun

Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,

har rantsuwa yai mata amma taki yadda. Karshe

har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai

da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya. Zama tai

tana jiyo shewarsu a dakin Bintun. Har kullum

bazata daina nadama akan taraiyarta dasu

Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da

t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta. Har hawayen

bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina

sa6awa mijinta ko da taji haushin shi. T'sakar

gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a

kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya. Ganinta a

t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a

t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai

tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau

inda-inda, "dama kina ciki?.. Sannun ku da gida..

Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar

waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku

hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.

Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai

za tai rakiya waje ya bata izinin fita. Bokiti ta

zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai

waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja

t'saki ta shige band'aki. "A toh na zata koh rafka

mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan

wannan da gani zatai kishin hauka... Dariya suka

sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki

tafiya. Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e

band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin

saukar ruwa sukai akansu har Bintun. Bokitin ta

d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture

suka fita waje da gudu. Tana haki ta leko kofar

gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya

na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon

na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,

InshaAllah kema dubinki ta kusa cika. "Ke kuma

yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai

Allah, yau zaki ga karyar iskanci. Gida ta koma

tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon

ciki. A t'sakar gidan ta zauna tana maida

numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji

tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido

tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh

Salman bata nan sai suka had'a ido. "Wallahi

baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki

bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani

ba hauka ba. Murmushi tai daga inda take, "Lalle

kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da

karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka

yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba

miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31

Feenat Ja'afar Novel's

"Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai

fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu

gabza da hannu in kin is... "Meye hakan ke kuma

Bintu?.. Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta

sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai

Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka

da bokiti bayan ta jika su ita da bakin da zata

raka... Ciki yai gadan-gadan gun Salman,tana

ganinshi ta mike t'saye rike da bokiti,bai

watawataba kawai yai kanta da niyar mari tai

baya. Kunci ta rike har tana halamar yin baya

zata fad'i, "Kin haukace ne Salma ko mey?..

Gidan ki ne da har zaki kafa dokar wa zai shiga

ko ya fita?.. Cike da mamaki ke d'auke a

fuskarta, ganin yadda ya rufe ido yake zazzaga

mata bala'i harda yunkirin mari. "Ni zaka mara da

akan waccan karyar Ya Ja'afar?.. A tuzare yace

"eh wallahi, da da halin duka ma sai na

miki,kuma daga yau kar in sake jin kin kamanta

matata da sunan kare a gidan nan.. Kai ta k'ada,

kan tai baya tana g'yara t'sayuwa tai d'aki. Code

wear ta ciru, a masife ta fito tana mika mishi,

"Amshi waya, yau in ka cika kaine Ja'afar ka

dake a gidan nan sai nasan na ta6a maka y'ar

g'wal dinka Ya Ja'afar, amma ni in naci sunan

Salma,toh wallahi babu mai takani ya k'wana

lafiya,zaman lafiyarta a gidan nan kawai ta fita

harkata... "Bazata fita ba d'in, haba. Wannan

wace irin masifa ce wai?.. Kullum ke kenan cikin

dacin rai?.. Ba wanda yake t'sallake masifarki in

ta motsa.. Haba Salma,yarinyar nan tun tana miki

kawaici har sai kin kaita bango,koh tausayin

yanayin da kike ciki ba k'ya yi?.. G'walo Bintun

ta sakar mata tana a bayan Ja'afar. Kawai sai tai

murmushi tai d'aki ta dakko hijabi da kud'i ta

fito. Cikin sanyin murya tace "kamin izini zan fita

Ya Ja'afar.. Harara ya sau mata!kan yace "Da in

zaki fita ba kina gaban kanki ba?.. Wato ga

shashasha yana magana dole ki fice,toh kije duk

inda zaki ai kin saba... Dak'yar ta iya shanye

kukan dake son subuce mata,ga Bintu sai dariya

take mata a boye,da sauri ta zira hijab dinta tai

waje. K'wafa yayi shima kamin yace Bintu ta

shiga ciki yana zuwa. Waje yayi da sauri,har ta

samu mai Napep ta shige tana hawaye, a tunzure

yai gun mey Napep din, "Kar ka kuskura ka jata

cikin Napep dinnan in kana son kekenka ya tsira..

Sauketa tun wuri.. A masife ta rufe ido tana

mishi balbalin bala'i kan bazata sauka ba din. Shi

dai mai Napep duk ya tsorata,jin ta dawo kanshi

yasa ba shiri ya tada Napep,magana yake mata

amma ina,da sauri ya juya shima yai gun nashi

machine din yabi bayanta. "Hajiya wannan binmu

yake a baya fa,wallahi kar ya tafkan asara..

Murya na rawa tace "Dan Allah ka kara gudu

sabuwar gandu zaka kaini.. Kan ta karasa kukan

har ya taho mata,kawai sai ta jingina kanta ta

hau yi kamar ance mata Mama ta mutu. By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:14 AM - Queen Safiyyert馃憫: *漏 Feenat Ja'afar*.

25_Yau amarya ta taro gidan Ja'afar,suna chan

d'aki yan d'anna kirjin Salma.

Tai kuka yau harta gode Allah,tukun daga baya

taje ta d'au wanka.

Tabbas ba'a iya dake wa kishi,koya sai ya tona

ka,dak'yar ta samu ta saita kanta kamin y'an

kawo amarya suzo kawo amana.

Kowa ya wat'se, daga ita sai amarya, kowa tana

dakinta.

Karadin Garba ta kiyo a parlourn ta,tuni taji

gabanta ya sara, tabbas tasan tare suke da

ango.

A hankali ta yaye labule tana k'allon su har suka

shiga dakin amarya had'i da parlour mai k'allon

nata.

Zama tai ido tuni ya ciko da k'walla, sai tai

ko'k'arin had'iye wa.

Tana jin Garba yana bazai shiga ba yaje tai

tanadin ta6aryar duka, tana suka sa dariya harda

tafawa.

Kwafa tayi,wato ga mahaukaciya sabon kamu.

Tana jin rufe kofar gidan tai sauri ta k'wanta ta

rufe ido.

Da sallama ya shigo parlourn, ba kowa sai

kamshin turaren uwar gida y'ar Borno jikar

Shuwa.

Ko'ina yaji sabon abu,kamar itace amaryar, labule

da kujeru purple da baki, su Mama anga ba sarki

sai Allah,kawai sai aka fito da tsohuwar

ajiya,baba ya cika aka sai mata kayan

parlour,ragowar nata na da suka siyar,gado k'wa

tace bazata siyawa wani gardi ba,harda kukan

Salma.

Sai ma kuma gashi ashe yana da niya,gado

barawan Italian da katifa yai mata a kud'in da

Ummanshi ta turo mai daga Zaria.

D'akin ya shiga,nan ma shiru ba amsa,tai

rigingine kamar mai bacci.

K'allonta ya t'saya yana yi kamin ya ajiye ledar

hannunshi,sosai cikin ya kara fito mishi da k'yan

Salma warai.

Tai k'yau cikin attamfa ruwan purple da

pink,tasha k'walliya sosai gun Ummi,idon nan

yasha (mascara/eyeliner).

Da komai Salman sa ta fi Bintu sau dubu

agunshi,sai dai ta nuna mata hasken fata.

Hannu ya kai kan cikin yana shafawa a hankali,

tana jinshi yana yan surutanshi ma cikin.

Ajiyar zuciya ta yi,sai ya k'allo ta,a tunaninshi

baccinta ne yai nisa.

A tashi yai yana k'allonta,kan a hankali ya duk'o

tare da nufin kai bak'inshi nata,tana jin hucinshi

sai ta juyar da kai da sauri.

Murmushi yayi kamin ya shafo kanta da suka sha

yiriyirin kitso.

"Asbha ta ga Salma.. Ki yafeni kinji...

Bargon kusa da kafarta yaja ya lilli6eta,kamin ya

kashe wutar dakin yai waje.

Ido ta bude tana nanata maganar shi a zuciyarta,

mey yake nufi da ki yafeni?..

Saboda ya tafka miki t'siya mana.. Cewar wata

zuciyar, le6e ta cije,yau gata a gidan Ya

Ja'afar,akan gadon su,amma ba shi ciki,yau zasu

fara raba matashin kafadar Ja'afar da wata

chan.. Tana son Ja'afar, sai ma yanzu ta gano

t'sant'sar son da take mishi,ji take kamar ta

had'iyi zuciya ta mutu dan kishin mijinta,

tuni tasau wani dan marayan kuka a

hankali,kamar tace Ja'afar dawo.

****

Ita k'wa amarya tuni ta mike ta fara zarya a

d'aki, dan a idonta ya shiga bangaren Salma,tuni

ta fara cika tana bat'sewa.

Tana ko'k'arin fito wa a parlourn ya shigo,da

sauri ta koma ciki har tana tuntu6e,duk ba tasan

ya ganta ba.

Ba laifi,tazo da tarikice dayawa,sam sai t'sarin

na Salma yafi burgeshi,dan shi bai son tarkace a

gida da sunan k'walliya,ga wani kala blue da pink

na kayan labule da kujeru,sam bai mishi ba.

"Ki fito da sallaya parlour.. Kawai sai yai waje

dan yin alwala a band'aki.

Assalatun farko ta farka,cike da mafarkin Ja'afar

wai yana ta mata fara'a.

Kasa tashi tai,tabbas da gaske yanzu tasan

bakinshi kamar gonar audiga dan fara'a, tunda

yai k'wanan d'akin amarya.

Hakan ne yasa ko da gari ya waye taje kitchen

ta d'aura abin kari,dan tun asuba taga text din

Aunty A'i kan ta k'auda kishi tai musu kalacin da

safe,dan Allah..

Wannan Kalmar ce tasa ta shiga dan dole.

T'saye take tana juye abincin a flaks,ba abinda

ta tsana irin hada kitchen da band'aki da

kishiya,harar bangaren kayan jeren amarya tai

tana gunguni ciki-ciki,bata nufa ba taji shafo

wuyanta ta baya.

A zabure ta juya dan ganin waye. Murmushi yake

mata kanar dai a mafarkinta,da sauri ta d'auke

kai daga K'allonshi zuwa gefe.

"Kamshi duk ya karad'e gidan nan K'anwata..

Hannunta yake neman kamowa ta mat'sa tana

"An tashi lafiya..

K'allonta yake daga sama har kasa,tana sanye

da rigar banci _sky blue_ nai filawa purple, sai ta

d'aura zani da dank'wali akai, tai mishi k'yau

sosai,ga dan kurcicin cikin ya fito yai d'as.

"Ya gajiyar jiya?.. Na shiga kinyi bacci ban son

tashinki.

Yawu ta had'iya tare da fad'in "ummm.

Fur taki k'allon fuskarshi balle ta fassara mata

bakin ciki.

Dan da ganin yadda ya fara mata zagwadin nan

ta faru ta kare.

"Ga abincin ku,zan wuce..

Hannu yakai zai karbi natan tayi saurin janye wa

ta wuce,kai ya k'ada bayan ya dawo daga

k'allonta.

Dakin amarya ya koma,tana kudindine cikin

bargo, sai baccinta take narka abinta.

Parlour ya dawo ya zauna,Salma nuna mishi halin

ko in kula take tun satin biki, sam bata koh

kishinshi,sabgar gabanta kawai take.

K'wafa yai ya kada kai,dan ba karamin haushi

hakan yake bashi ba.

Motsinta yaji a t'sakar gida,ta window ya dago

yana k'allonta zata wuce band'aki da bokiti da

kwandon wanka,watoh daga shi har amaryar shi

basu isheta ma kallo ba?.. Dan wai koh hanyar

d'akin bata kalla ba,k'wafa yai kan yai waje gun

band'akin ya t'saya kamar maigadinta.

Har ta gama wanka yana t'saye,tana bud'e kofa

sai ganin mutum tai a t'saye ya bake hanya,kai

ta k'auda da nufin ta wuce ya riko bokitin,yaja ta

taja,kawai sai ta sau mishi,k'wandon sabulun

yake neman k'ar6a tai baya dashi.

"Wanka zanyi man Salma.. Wani k'allon ta watsa

mishi kan ta had'e rai,

"Bana _sharing_ din soso.

Baki sake yake k'allonta, cikin fusata yace "da

da wanne muke yi?.. Kanta gefe tace "toh yanzu

na sake t'sari...

A tunzure yace

"Wai Salma meye haka?.. Bana..

"Kai Dear J,ga soso nan kai wankan.

Juyawa sukai gun mai magana, Bintu ce daga ita

sai y'ar yaloluwar rigar bacci ba koh zani balle

dank'wali.

T'saki Salma ta ja,kan tace ''Malam ban waje na

wuce,tuni ya kara kuluwa, shi take ma tsakin?..

Yai mata k'yau,kawai sai ya dungurar mata da

bokitinta ya shige band'aki,da sauri Bintu tai

kitchen ta d'akko mishi nata,koh ta kansu bata

kara bi ba ta zari bokitin ta kara mai,a ranta tana

"karamar y'ar iska kawai.

Sam Salma taki dad'i, dan fur taki bawa kowa

fuska a gidan,dan taga da mugun falli amaryar ta

shigo mata.

Har girkin amarya ya kare ya dawo ga Salma

amma ba sauki.

Zata gaidashi tai komai,amma ba magana

duguwa, sai ma haushin sa dake kara ziyartar ta.

Tuni ya kai kara gun Aunty A'i,wai Salma taki

sake masa fuska.

A ranar tai mata waya ta kare mata tass,tuni ta

hau kuka,wai ai dan ita bata kishiya ne,bazata

gane lamarin ba,ga kusan kullum Bintu na

chakalarta tana kaucewa.

Shiru Aunty A'in tayi,dole wannan ba zancen

waya bane,

"Ki bari zan zo koh zuwa gobe ne.

Ranar girkin Bintu ne,yau tun safe take fallin

fararo a t'sakar gida,sai ya6a mata haibaici take

ita kad'ai kamar sabon kamu.

Salman tana zaune kan taburma a kofar ta tana

yanke farce.

Harara ta sakar mata,kan taja t'saki,

"Wawiya kawai..

Shewa Bintun tayi harda guda.

"Kece babbar wawiya wacce zaman gidanta ke

mintsininta.. Ehee, naji komai ai,saki daya ya

rage miki duk a dalilin gantali gardi.

A masife ta tashi,sai dai nan da nan ta k'auda

bacin rai dan ya6a ma Bintu magana dai-dai ita.

"Ahaiyee,, naji,tunda banyi k'wantai a layi bare

ina bi ina tallan kaina agun d'a namiji ba ehee, ke

har kin isa ki ce kin san komai?. tunda dey ni ba

matar tushe bace ba... Dan tuni akasan da matar

tushe dai bata k'warjini... Karya uwar bin maza

kawai...

"Eh naji ki ce komai,igiya uku ce a kaina kinga na

fiki matsayi a...

"Ke... Bana son shashancin banza wallahi..

Juyawa sukai danjin mai gidan yai shigar bazata.

"Ihu har titi mutanan unguwa ana jinku sai kace

wasu karnika?...

Harara Salma ta sau mishi da t'sabar tuhuma a

k'allonta.

"A ni ba karya bace, dan har gidan mu ka samo

ni..chan ka nemi karya tun wuri..

Jiki ta kad'e tai dakinta ta barshi baki a sake.

Ita kam Bintu lukwas tayi,tabbas Ja'afar kadai

zai iya fad'a ma Salma cewa ita tace tana

sonshi,da kuka tai d'aki dan bakin ciki.

Itama haka take gun Salman,sosai taji zafin

maganar Bintu,tasan kuma babu mai fad'a mata

sai Ja'afar.

Toh fa Ja'afar, ka shiga t'sakiya.

By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:16 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

26_Kowa bin kofar dakinta yai da kallo, yana

murna ba'a rikicin mata biyu a gidanshi yau gashi

an fara,dole ne tun wuri yai ma tufkar hanci. Har

yayi dakin Salman sai ya t'saya, dole ne ya nuna

mata kuranta, in da tai mishi fitsara ya k'yale toh

yanzu bazai d'auka ba,dan ba ita kadai bace a

gidan,kawai sai ya juya dakin Bintu. Kuka take

yana ta fadanshi taki kulashi, chan kuma sai ya

sassauto, "Ni tashin hankali ne bana so a gidana

ne,tun wuri ma in zaku had'a kai ku had'a, dan

ba mai chazan hawan jini. Kai ta dago tana mishi

k'allon tuhuma, "Au shine dalilin da yasa ka fad'a

wa matarka baka so na?.. Ni nace ina son ka

koh?.. A haka za ai zaman lafiyan?.. "Ke kinga

bana son iyayi,dawa nai wannan zancen?.. Da

sauri cikin kuka tace "da matarka man,wato

harda fad'a mata kwantai nayi nai ma tallan

kaina.. "Ban san anyi maganar nan ba Malama,ki

ma cire zargin ni na fad'a mata, bari na je zata

fad'a min yaushe muka fara y'ar sharri da ita...

Waje yayi zuwa dakin Salman. Kai Bintu ta k'ada,

"ashe munafuka karya take dan ta had'ani fad'a

da Miji,toh karyarki taci karya,Allah sa ya k'wada

mata mari tukuicin sharri. Ita kam tanajin bud'e

kofarshi ta mike tare kama k'ugu ta k'ank'ance

ido. "Salma yaushe muka fara y'ar sharri dake a

gidan nan?.. Yaushe nace miki Bintu ce tai min

tallar kanta na aura?.. Harara ta sakar mishi da

k'allon kar ka rainan hankali. "Ka nad'e taburmar

kunyar ka man ta haka,wato kayi amarya shine

ka zabi ka tuzartani agunta,karafkaf abinda ya

faru ta fad'a mini,toh da ka fad'a mata saura

igiya daya ta aurenka a kaina sai mey?.. Baki ya

saka cike da mamaki,lalle ya shiga tarkon kaidi

na mata, wato kowacce sharri take neman k'ulla

mishi a gun y'ar uwarta ashe?.. Bai da tace wa,

kawai sai ya juya zai fice, da sauri tace "a ka

fita man,dan nayi imani bazaka karyata cewar ba

kai ka fad'i ba... "Idan kuma habaici da iyayi

kake neman matarka ta dinga min dan ka huce

haushinka na da toh bissmillah,dai dai nake dana

sa kafar wando daya da kowa a gidan nan

wallahi.. Juyowa yai yana kallonta, sai tai d'aki

ta barshi t'saye baki sake. Titi ya fice ko ya

samu sa'ida, lalle yau ya jinjinawa sharrin

mata,amma kaf yafi jin haushin Salma,dan sam

yanzu ya fuskanci fitsararta tafi ta da yawa. Tun

daga ranar ba jituwa t'sakanin matan, daya in

Bintu ta fad'awa Salma sai ta fad'a mata

dubu,daga karshe ta bige da kukan bakin ciki, har

mai gidan yazo ta kit'sa mai karya da

gaskiya,wani sai dai ya bata hakuri, dan a

ganinshi yanzu Salma tafi karfinshi,dan da ya

mata magana ita y'ar dika take,daga shi har

amaryar zata chake tass, sai dai yai abinda zaiyi.

Shi yasa shi kuma ya t'siri mata t'siya,in dai zata

kona mishi rai,toh shi kuma zai ta biyewa Bintu

suna ta mata feleke a t'sakar gida, daga karshe

kam sai yaci nasara,dan haka zata shiga d'aki tai

ta kukan bakin ciki,a nan zai ta mata dariyar

keta. ***** Sallama taji kamar ta Maman Ummi

da Maman Abba,lekawa tai ta window, sune

kuwa, "munafukan Allah ta'ala kawai... Ta fada

tana kokarin ta fito rai 6ace,dan tai imani duk

abinda take fuskanta yanzu da sa hannun su

aciki... Chak! Taja ta t'saya rike da labule a

hannu ganin Bintu ta fito da gudu danjin sallamar

su. "Sai yau Aunty Ladi zaki zo min? Har nayi

fushi ai.. Baki sake Salma take k'allonsu,tana

k'allon suna nuno kofar dakin da baki suna ma

Bintun kuskus tai baya da sauri. Ido ta rint'se

tare da cije le6e,lalle mutum mugun ice ne,yanzu

ta gane inda Bintu ta samo duk wasu

_information_ na zaman aure nata ba agun

Ja'afar ba,ido ta bud'e, ta d'au alhakin Ja'afar,

har rantsuwa yai mata amma taki yadda. Karshe

har raba shimfida tai dashi akan maganar har sai

da ya gamo ta da Aunty A'i aka shirya. Zama tai

tana jiyo shewarsu a dakin Bintun. Har kullum

bazata daina nadama akan taraiyarta dasu

Maman Ummi ba,tasan duk fushin Ja'afar ne da

t'sinuwar mala'iku ke bibbiyarta. Har hawayen

bakin ciki tayi yau,tai kuma alkawarin daina

sa6awa mijinta ko da taji haushin shi. T'sakar

gida ta fito bayan ta g'yara fuskarta, tai sa'a

kuwa sun fito zasu tafi suna ta dariya. Ganinta a

t'sakar gidan yai bala'in saita nutsuwar su,a

t'saye take k'yam tamkar wata soja ta had'e rai

tam,ido cikin ido take k'allonsu,tuni suka hau

inda-inda, "dama kina ciki?.. Sannun ku da gida..

Harara ta sakar musu,ba shiri sukai hanyar

waje,Bintu ce ta t'sayar su, "bari na raka ku

hanya Aunty,ina zuwa na kira mai gida izinin fita.

Duk tana k'allonsu,har tai ma Ja'afar waya wai

za tai rakiya waje ya bata izinin fita. Bokiti ta

zaburo da sauri tai hanyar fita,da sauri sukai

waje sun zata kansu zata iyo,kawai sai ta ja

t'saki ta shige band'aki. "A toh na zata koh rafka

mana zatayi ai,g'wara muyi ta kai ta kai,dan

wannan da gani zatai kishin hauka... Dariya suka

sa tana jiyo su ta band'aki daga zauren sunki

tafiya. Ruwanta na cika da ta tara ta bud'e

band'akin a hankali tai zaure, basu nufa ba sai jin

saukar ruwa sukai akansu har Bintun. Bokitin ta

d'auka tai kansu dashi a sukwane, da ture ture

suka fita waje da gudu. Tana haki ta leko kofar

gidan ''Ashe karyar munafurci kuke, da ku t'saya

na g'wada muku aikin mahaukaciya, shegu gadon

na aiya,a haka zaki kare Maman Ummi wallahi,

InshaAllah kema dubinki ta kusa cika. "Ke kuma

yau mai rabani dake a gidan nan wallahi sai

Allah, yau zaki ga karyar iskanci. Gida ta koma

tana hakin daga ruwa bucket guda da tsohon

ciki. A t'sakar gidan ta zauna tana maida

numfashi a hankali, ta jima da zama kamin taji

tafiyar Bintu cikin sand'a, kofar ta zubawa ido

tana harara, kai ta leko dashi dan ganin koh

Salman bata nan sai suka had'a ido. "Wallahi

baki isa ki ce zaki hanani shiga ba, in gaske ne ki

bari na shigo na shirya in fad'an ki ke nema dani

ba hauka ba. Murmushi tai daga inda take, "Lalle

kinyi kuskure in kina zatan zan iya had'a jiki da

karya irin Bintu,haukar nake son sauke miki aka

yau ai, gaba kin d'aina irin kuskuren nan ina zuba

miki ido kawai,yau dole na fidda ki cikin gona ta.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31

Feenat Ja'afar Novel's

"Karya ki ke wallahi ki iya koyan hankali Salma,ai

fad'a da makami tsoro ne,ki ajiye bokitin mu

gabza da hannu in kin is... "Meye hakan ke kuma

Bintu?.. Juyawa tai da sauri,tana ganin Ja'afar ta

sau kukan munafurci harda kank'ame shi,wai

Salma tace in ta shigo sai ta kashe ta da duka

da bokiti bayan ta jika su ita da bakin da zata

raka... Ciki yai gadan-gadan gun Salman,tana

ganinshi ta mike t'saye rike da bokiti,bai

watawataba kawai yai kanta da niyar mari tai

baya. Kunci ta rike har tana halamar yin baya

zata fad'i, "Kin haukace ne Salma ko mey?..

Gidan ki ne da har zaki kafa dokar wa zai shiga

ko ya fita?.. Cike da mamaki ke d'auke a

fuskarta, ganin yadda ya rufe ido yake zazzaga

mata bala'i harda yunkirin mari. "Ni zaka mara da

akan waccan karyar Ya Ja'afar?.. A tuzare yace

"eh wallahi, da da halin duka ma sai na

miki,kuma daga yau kar in sake jin kin kamanta

matata da sunan kare a gidan nan.. Kai ta k'ada,

kan tai baya tana g'yara t'sayuwa tai d'aki. Code

wear ta ciru, a masife ta fito tana mika mishi,

"Amshi waya, yau in ka cika kaine Ja'afar ka

dake a gidan nan sai nasan na ta6a maka y'ar

g'wal dinka Ya Ja'afar, amma ni in naci sunan

Salma,toh wallahi babu mai takani ya k'wana

lafiya,zaman lafiyarta a gidan nan kawai ta fita

harkata... "Bazata fita ba d'in, haba. Wannan

wace irin masifa ce wai?.. Kullum ke kenan cikin

dacin rai?.. Ba wanda yake t'sallake masifarki in

ta motsa.. Haba Salma,yarinyar nan tun tana miki

kawaici har sai kin kaita bango,koh tausayin

yanayin da kike ciki ba k'ya yi?.. G'walo Bintun

ta sakar mata tana a bayan Ja'afar. Kawai sai tai

murmushi tai d'aki ta dakko hijabi da kud'i ta

fito. Cikin sanyin murya tace "kamin izini zan fita

Ya Ja'afar.. Harara ya sau mata!kan yace "Da in

zaki fita ba kina gaban kanki ba?.. Wato ga

shashasha yana magana dole ki fice,toh kije duk

inda zaki ai kin saba... Dak'yar ta iya shanye

kukan dake son subuce mata,ga Bintu sai dariya

take mata a boye,da sauri ta zira hijab dinta tai

waje. K'wafa yayi shima kamin yace Bintu ta

shiga ciki yana zuwa. Waje yayi da sauri,har ta

samu mai Napep ta shige tana hawaye, a tunzure

yai gun mey Napep din, "Kar ka kuskura ka jata

cikin Napep dinnan in kana son kekenka ya tsira..

Sauketa tun wuri.. A masife ta rufe ido tana

mishi balbalin bala'i kan bazata sauka ba din. Shi

dai mai Napep duk ya tsorata,jin ta dawo kanshi

yasa ba shiri ya tada Napep,magana yake mata

amma ina,da sauri ya juya shima yai gun nashi

machine din yabi bayanta. "Hajiya wannan binmu

yake a baya fa,wallahi kar ya tafkan asara..

Murya na rawa tace "Dan Allah ka kara gudu

sabuwar gandu zaka kaini.. Kan ta karasa kukan

har ya taho mata,kawai sai ta jingina kanta ta

hau yi kamar ance mata Mama ta mutu. By

Feenat Ja'afar.

Like 路 1 路 Reply 路 Report 路 Jul 31

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 27_Tun

kan Napep ta t'saya ta mika mishi kud'in, da

sauri ta shige gidan Aunty A'i fuska duk hawaye.

"Toh kiyi min bayani man ba kuka ba

Malama,mey aka mi... Wayan Aunty A'in ne ya

hau ruri Aslam ya miko mata. A takaice ta k'alli

Salman sai tai waje dan amsar wayar. Tana ji

tana waya da Abban Aslam kan zata shigo da

Ja'afar. "Dan Allah karki shigo dashi,wallahi ban

san ganinshi,gwara in na huce da kaina zan

koma. Baki sake take k'allonta hijab a hannu,

"Ok,kina nufin yaji kika yi kenan?.. Shiru tai mata

tana ci gaba da goge hawayenta. Bata kara bi ta

kanta ba tai waje. Ba'a jima suka shigo tare,kai

ta kautar gefe, tana jan hanci,ido yayi luhu-luhu

dan kuka. Abinda ya faru ya t'sarawa Aunty A'in,

tuni ganin duk ita ya d'aurawa lefi yasa ta hau

musu bori ba shiri. Ido kawai Aunty A'i ta sa

mata. "Auntyn mu kin gani koh? A gabanki ma

kenan,wallahi na rasa rikicin Salma sam

yanzu,abu kadan yanzu zata hau balbalin bala'i

sai dai ni na bar mata. "Yanzu da banzo ba Allah

kad'ai yasan mey zatai ma y'ar mutane,k'alli a

halin da take fa,amma Salma taki k'wantar da

hankalinta ai zaman lafiya.. "Ni fa kar ma ka

zata kishi nake da kai koh kuma waccan amaryar

taka,sam ba haka bane,ni mud'in za'a tada min

hankali toh lalle na kowa zai tashi... _period_.

Aunty A'i ya k'allo halamar tasa baki.

Tambayarta take mey ya had'a su?.. Amma fur

taki magana a gaban shi,har aka gama sulhu

yace ta taso su koma tace sai dare. Da kai Aunty

A'in tai mishi kawai kan ya k'yaleta. Ba musu ya

tashi kan sai ya zo,yana fita ta mike tai kitchen.

Tana cin abinci Aunty A'i na mata fad'a, kan ta

d'aina fada Ja'afar na fada,dan ta fuskanci Bintu

ta iya bariki. Nan ta fad'a mata ainashin abinda

ya faru,harda irin habaici da sharrin da Bintun ke

mata kullum. Baki ta ta6e. "Ni fa Aunty A'i Bintu

bata gabana, abu daya na sani na tsani a gabana

yana biye mata tana mishi abinda taga dama..

Yana konan rai ne,shi yasa yake rasa kaina.

Murmushi tai mata, "Lalle Salma kina so Bintu ta

kai ki ta baro, kin kuma yi saken da kika bari

kishiya har ta gano lagon ki,dole yai ta ganin

bakin ki ke kadai,dan ke kadai ki ke iya daga

jijiyoyin wuya agabanshi akanta,in sharri ma ta

miki ki barta da Allah kawai,shi zai isar miki,kar

ki manta igiya daya tai saura a t'sakanin ku da

Ja'afar, kuma kince ta sani,toh wallahi ki sani

ingiza mai kantu ruwa kawai zata miki,so take

tai ta tunzuro ki har ki tafka kuskuren da za ai

mai dika, kinga taci galaba kenan. "Gaba koh

abinsu suke kina d'auke kanki a kansu, sannan

abu in kinga zai ja ki fad'i wata magana

musamman kan Ja'afar kiyi shiru kar ki tanka

dan Allah Salma. "Ja'afar na sonki,kiyi amfani da

hakan sai ki ci galaba kan Bintu.. Har ta gama

mata fada tana ta nazarin abin,toh Allah yasa ta

iya k'auda kan. Ita kwa Bintu murna fal rai,dan

tana lekensu ta k'auran zauren, fatan ta Allah

yasa yadda ya figi machine din nan in yaje kawai

ya dankara mata saki. Shi yasa tun kan ya dawo

taje ta t'sant'sar wanka ta hau kananan kaya,

duk da ba ita ke dashi ba. Ita a ganinta an sau

Salma an gama,.. K'warai ta gode da shawarar

su Aunty Ladi ta waya da ta yau,tabbas da

BARIKI kadai zata mallaki Ja'afar ba boka ba

Malam. Sai dai har dare ba Ja'afar ba dalilin

sa,kawai sai ta zata bai gama hucewa

bane,tasan mutumin ak'wai saurin zuciya. Dirin

machine dinshi taji,da sauri ta kara fesa turare

ta haska touch light tai zauren da zummar taro

shi yasha Bariki. Turus taja ta t'saya gabanta na

fad'uwa, ganin ya mike yana fad'in ma Salma

"Dafani man toh,ban san ki fad'i ne garin sauka.

Da kamar kar ta kulashi,amma ganin hasken

fitilar Bintu yasa ta hau shagwaba. "Toh ni kam

tsoron sauka fa nake tunda cikin nan yai girma,in

zaka iya ka sauke ni toh... Ta karasa da kalar

tausayi. "Toh toh,amma ki kokarta,ki rikeni gam,

koh ki bari na fara sauka... Kofar Bintu ta saka

da sauri ta koma ciki dan bakin ciki. Tana jiyo su

a t'sakar gida Salman na fad'in "Wash.. Allah Ya

Ja'afar kafata rikewa take fa.. Tuni gogan ya hau

rikicewa abinda aka jima ba'a mishi ba yau yake

gani,bar zuciya da abinda take so. "T'saya na

d'auke ki toh ai kina ma kok'ari.. Tana jiyo

Salman na fad'in "kai Ya Ja'afar, anya zaka iya

kuwa?.. Nayi nauyi fa yanzu. A zabure ta mike ta

tana lekensu ta window ta cika tai ham. Dariya

suke k'yak'yatawa kan yace"bari ki ga,nawa ki

ke.. Da sauri ta sau labulen ganin ya k'wa daga

Salman ya dauke kamar y'ar tsana suna dariya.

Har d'aki ya dire ta suna nishad'i kamar ba su

bane dazu an bar Bintu da kukan d'aki. Sai yanzu

ya tuna ai koh sallama basuyi ba suka shigo.

Murmushi tai mishi lokacin da yace bari yaje ya

dawo. K'wafa tai tana kada kai, "kowa ya iya

BARIKIN ai,in na baje tawa sai kin ji jiki Bintu.

Yau da sauri-sauri yai ma Bintun sallama yana ta

zumudin sun dinke da ta k'arfen. Kuka wiwi tai

tayi bayan fitarshi. A gaban mudubi ya tarar ta

tana g'yara gashi,kowa farin ciki fal ranshi,ta

baya ya sakalo cikin yana shafawa harda sakar

ajiyar zuciya. Murmushi tai mishi,tare da shafo

siririn sajen shi ta bayan, sai ya k'wanto da

kanshi wuyanta suna ma juna murmushi ta jikin

mudubin. Yaushe rabon su kasance haka shi da

Salman sa?.. Ga y'ar shagwa6ar nan yau yana

shanta,duk sai ta mantarshi komai. A hankali ya

rad'a mata a kunne "I love you... Murmushi tai

kan ta juyo tana lumlumshe ido jin dad'in kalmar,

lafewa tai jikinshi tana fad'in ''Me too.. Sosai

yasha mamakin Salman shi yau,komai yi mishi

take cikin kauna da kulawa, kamar farkon

aurensu kamin komai ya wargaje. Hakan yasa

washegari kowa fuskar nan kamar gonar audiga

dan fara'a, amma banda Bintu Lol. By Feenat

Ja'afar.

9/29/16, 9:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 28_Tun

daga ranar aka dinke da Salma da Ja'afar d'inta,

sam ta d'aina sanya da abinta, shima abin nema

ya samu,wai ! Matar falke ta haifi jaki. Kan kace

k'wabo,tuni tsohuwar soyayya ta dawo d'anya,sai

ya zama kamar kamar yanzu ma tafi yawa. A

cikin wata guda duk sun sauya,takanas zaice su

fito aje siyayyar kayan baby,fur Bintu take kin

zuwa,sai suyi tafiyarsu a kafa suna tadin su,sai

jiran EDD. Kwana biyu Bintu an tsiri zaman

d'aki,sai ta kule ka rasa abinda take aciki ita

daya. Ranar tana bacci da safe wajen k'arfe

goma taji kwkwazon maigidan yana tayi ba

kakkautawa. Tashi tai ta fito parlour. "Na fita ban

karya ba,yanzu ma na dawo ashe baki tashi ba,

bayan tun asubar fari kika fara wannan charting

din danaki jini a rayuwa,na hana kin ki

hanuwa,toh ina gaf da fasa wayarnan a gidan

nan Allah. Baki ta ta6e tare da tashi a hankali

tayi d'aki dan fita wanka. Tana kallo ta fito wai

yai hakuri ta daura mishi indomie,koh ta kanta

bai bi ba yai waje yana huci. Kamar jira take,da

dan gudunta ta koma d'aki ta dane Facebook

cikin group din su na KI G'YARA DA KANKI.

Kusan duk anyi katari masu kishiya sun da yawa,

nan zatai ta samun shawarwari mey kyau da

marar k'yau,dak'yar ta tashi ta d'aura jalof ta

koma. "Wato sai yanzu nake hangen maganar ka

abokina, dan yanzu abinda Bintu take har yafi

mai na gantali ciwo,in ta hau wannan Facebook

din nata,sam bata ji bata gani,abinci a kone, in

ma ta samu d'aurawa kenan,sallah a kure,bacci

sai biyun dare,da asuba ta d'aura a inda ta

tsaya,ga in ka shigo kaji tana dariya ita kad'ai,

Allah zaka zata Bintu sabon kamu ce... Dariya ya

fara mishi harda k'yak'yatawa,har ya fara

k'uluwa,yasan haka zata biyo baya, amma shi

yanzu shawara yake nema ya zai da sabon halin

Bintu?. "In ka gama kai magana sai ka bani

shawarar abin da zanyi. Dak'yar Garba ya takaita

dariyar ya fara magana. "A lokacin chan baya ai

bakaji zance na ba,dake idon ka a rufe yake,na

sanarka baka san mey wani irin hali zaka jajubo

ba,kace kai fa gaji ka gani sai Bintu.. "Malam ni

shawara zaka bani,in babu zanyi gida. Dariya ya

cigaba dayi,kawai sai ya zuciya yai gaba. "Ma

had'u in ka gama,dan hankalina yai kan

Salmatee. "Wash Allah bayana,Bintu!...Bintu!!..

Tamkar ba kowa a gidan ka ke ji sai karar fankar

sama dake kadawa a parlourn wacce bata hana

gumi t'satsafo mata ba. Rarrafo wa tai zuwa

kofa,iya karfinta ta kwalawa Bintun kira,ji take

tamkar zata mutu dan azabar ciwo,tuni ta fara

kuka tana ambatan Allah,tasan koh zata mutu

Bintu bazata taimake ta ba,fatan ta Allah ya

hankad'o mata Ja'afar koh wani ya ceceta.

"Wayyo Ya Ja'afar, Innalillahi.. Bintu.. A razane

ya karaso cikin gidan dan jin ta ambaci Bintu

cikin kuka. "Subhanallah.. Salma.. Ina Bintun

toh?.. Da sauri ta dago,tana ganinshi ta kara

fashewa da kuka tana cije le6e. gaba daya ya

tallafota yana aikin sannu sannu. Waya ya ciro

dan neman Garba ya kaisu asibiti, tana ta ringing

shiru.. Da rigarshi ya goge mata gomin dake

tsatsafo mata, "Bari na ga koh bacci waccan

take na taso ta. Hannunshi ta rike gam tana

girgiza mai kai, Kanta ya shafa, "ki d'aure

Salma,bari na kirata kinji. Dak'yar ta cika shi yai

dakin Bintun, dan ji take yana tafiya zata mutu.

Bata parlourn, sai ya bankad'a daki,tana mike a

kan gado taja rabin bargo tana dariya kasa-kasa

tana charting hankalinta yai gaba. A sukwane yai

kanta,bai wata-wata ya sinketa da mari mai rai

da lafiya,a gigice ta mike tare da dafe

kunci,wayar ya warce, "Lalle haukar nan taki

karuwa take Bintu,yanzu dama kina cikin gidan

nan Salma take ta kakarin kiranki kamar zata

mutu?.. "Toh ki biyoni yanzun nan waje, tana turo

baki ta sakko kan gadon tana gunguni. Nishi take

ta dafe d'ukkan hannunta a kasa, sannu yake

mata da tausayawa,da harara Bintu ta bita da jin

haushin akanta an mare ta. "Ka kira min Iya

Shatu dan Allah Ya Ja'afar kar na mutu.. Bintu

ya kallo dake maka musu harara, "Kizo ki

kamamin ita na kira Iya Shatun, kamar bata so ta

matso kusa,yana fita ta mat'sa tana jan

tsuka,"aikin banza,dan kina wata shegiyar

nakudarki akan hakan kika ja aka mare ni, wallahi

za... "Eh dan Allah kazo yanzu mukaita asibiti..

Shiru tai jin Ja'afar na kokarin shigowa tare da

matsawa gun Salman da sauri zata ta6ata tana

sannu. A hankali ta janye daga hannun Bintun tai

dan ciki kad'an tana nishi, da sauri ya karaso

dakin yana mata sannu. Nishi take iya karfinta

sukaji sallamar Iya shatu,tana dubata tace ai

haihuwa ce tazo gadan-gadan, ya basu waje, ya

siyo reza da sauran abin bukata. Gam hannunta

na cikin nashi,ji yake tana cikawa in ya tafi zata

mutu. Kanta ya tallafo yana ta d'aure, iya shatu

sai k'allon ikon Allah take. "Kai hakuri

Jafaru,zata haihu lafiya dan ina jin kan D'a,

yanzu bazata ji komai naka ba sai adu'a. Kai ya

kada harda guntun hawayenshi yai waje,yana fita

Bintu ta d'aura a bayanshi. Iya shatu tsuhuwar

ingozoma ce mai ritaya, da guntun hand gulf din

zuwa awunta ta karbi haihuwar Salman. Allah ya

taimake tazo mata da sauki inji Iyan,sai shigowa

yai shi da Garba yaji ihun jariri,baki wangale zai

dakin iya shatu ta fito k'ar6ar reza. Ummanshi

ya fara mawa albishir sai Aunty A'i,tuni ya fesa

cikin gidan su,da ance mey ta samu? Sai yace

bai gani ba. Har aka kintsa komai basu kara

ganin keyar Bintu ba,sai da zasu asibiti ta fito,shi

kam baiya ma ta ita. Suna fita su Aunty A'i suka

zo da Ummi,lokacin Bintun na t'sakar gida tana

yankar farce,ita dey Iya sai mamakin karfin hali

irin na Bintu take. Sallama suke ta manna musu

bajon hauka,tuni Ummi taja dogon t'saki, taki

jinin Bintu a rayuwa. "Banza y'ar bakin ciki

kawai,toh sai ki had'iyi zuciya ki mutu ai.. Hannu

Aunty A'i ta daga mata halamar tai shiru,ita k'wa

da harara tabi su har suka shige. Sun dawo an

duba suna lafiya ita da babyn ta,Ja'afar baki har

kusan k'unne dan murna,yana makale da yarshi.

"Um,Baban baby ba koh dan karar nan ma ta

manyan yayu.. Kai ya sosa yana ma Aunty A'in

murmushi, ba dan yaso ba ya mika mata ita. Kan

kace mey gida har ya cike da dangi yan barka da

yan unguwa. Sai dare ta samu tasa hakarkarinta

dan hutu. K'allon babyn take mey kama da

Abbanta, gashi kadai da dan _beauty points_

(dimples) tai gadonta. Murmushi tayi tana kai

hannu kan kumatun babyn, Allah mai halitta.

Murmushi yake musu yayin da ya shigo d'akin,

sai ta daga kai ta k'alleshi, kai ta girgiza tana

dan murmushi. Sallama ta uku yana musu kenan

yana dawo wa,ta rasa wani irin kulafuci yake

musu musamman babyn. Zama yayi yana shafo

sumar babyn da farin ciki. "Oh ni kam,koh zaka je

da ita in tai kuka sai ka kawo ta. Murmushi yayi

yana kai baki kan dimple din babyn yana kissing.

"Ba kinki barina na k'wana anan ba?.. Da kalar

tausayi yace "yau dai daya naji dumin y'ata kinji?

Sai ya marairaice fuska. Dariya ta dan mishi,kan

tai magana ta jiyo Babah mai zamar mata tana

ya fito zata zo ta k'wanta,taga sallamar bata

karewa. Dariya suka sa kamin ya tashi yai waje.

"Maza ki rika biye mishi ki debo ma kanki

magana da kazamin goyo ai. Da rashin fahimta ta

k'allota tana neman karin bayani. ***** ***** Yau

suna,baby taci sunan Mama tun ran huduba

amma ya 6oye mata. Sosai yau daya Ja'afar ya

biya mama,harda mishi waya tana kwarara mishi

godiya ba iyaka. Maijego tai ras abinta da Baby

Miemien ta,sun fito sunyi k'yau sosai. By Feenat

Ja'afar. Ai hakuri da wannan dan zani gidan

Suna Salma.. Zuwa yamma in na dawo zakujini

Lol..

9/29/16, 9:17 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

29_Suna ya wat'se kalau,maijego tai

goshi,ak'wati guda Mama ta mata na suna sai na

baba,ga Umman Ja'afar nata daban da tazo

suna,chan gidan su Ja'afar su ma sun mata

karamci,sai son barka. Wankansu suke cikin

g'yara na musamman da Mama ta zage yi ma

y'arta, albarkacin Miemie mama ta sakko sosai.

Shirya Miemie take tare da taimakon Ja'afar din

suna ta nishad'in su yau za ai yawan arba'in. Ta

chakare sosai kamar yau ne sunan ita da Miemie.

Baya ta juya mishi yana goya mata ita, "D'aure

ta dakyau,dan kinga machine zamu hau.. Kai ta

kad'a tana murmushi, Sai da ya zaga ko'ina yaga

yayi kan ya bata majanyi tana mishi dariya, "A'a

toh in baki iya ba ni sai na goya abata kawai...

Dariya tai kan tace "Da kwa kabar abin fad'i

agari kuwa. Jakar ya d'au mata ta d'au mukulli

sukai waje,shima yasha sabuwar shadda abinshi.

Bintu na t'sakar gida tana d'anne-d'anne a wayar

da dak'yar ya bata. Da harara ta bisu harda dan

t'saki a hankali. "Toh mu zamu fita sarauniyar

charting.. Sai kisa mana mukulli a gida dan

gudun kar a dirko kina sana'ar taki koh.. Tuni ta

kara k'uluwa kuwa,ita dai an mayarta borar karfi

da yaji a cikin gida. Hannu Salman ta dago mata

halamar sai sun dawo,da harara ta bisu har sukai

waje. "Jishi kamar wani dan daudu rike da jakar

mata. K'wafa tai tana tashi t'saye, "Ba dai kin

fara fita ba?.. K'wanan nan zaki yabawa Aya

zakinta wallahi. ** K'wana biyu yau tayi tana fita

yawan arba'in, yau ne na uku,yau kuma aka tafka

t'siya da maigidan,dan fur yace ba inda zata je.

"Bazaki k'waso ma yarinya rana ba fa,kiyi hakuri

kawai. Iya wuya Salma ta kawo dan takaici, tayi

magiyar yaki kuma,kawai sai ta raya mata tunda

dama taki bari ta koma hagu. "Amma gaskiya

baka min daidai ba Abban Miemie in har ka

hanani fita yau. "A ka'ida sati ake fita yawan

arba'in fa,amma ni na yarda zanyi ukun shine har

na gama shiri amma kace bazani ba... Gaskiya

da sake. Gefe tai da kai tana kunkuni,tuni ta

kular dashi shi zuciya kusa. "Toh ban hanaki ba

kije d'in, amma ki ajiye min y'ata ki tafi ke kad'ai.

Baki sake take k'allonshi,ganin yadda ya fidda

waya yasha kunu ya barta. A zuciyarta tace "Eh

lalle,da gani abin Ya Ja'afar yazo da wulakanci...

"Kasan dai ba yadda za ai na tafi na bar Miemie

a gida,dan Allah in wasa ka ke ka bari,dan kam

nasa rai da fita yau.. A tunzure ya mike da niyar

magana cikin masifa,sai yai shiru yana k'allonta.

"Kiyi toh gaban kanki kawai.. Sai yai waje da

zummar barin gidan ma dan haushi. Sai dai

mey?.. T'saye yayi yana binta da k'allo galala,

ganin yadda ta fara kame-kame dan ya kamata

tana musu la6e ta window. "Ke kuma lafiya kike

abu kamar marar gaskiya?.. Dakewa tayi tai

ganin kamar bai ramfota ba. "Dama zuwa nayi

ina son na leka nan na dawo ne... "Ba mai fita

yau acikin gidan nan in dai ni ne mijin, wacce ban

isa ba ta fita nagani.. A fusace ya fice yabar

gidan,duk sai ta Salma tafi zafi. Ita kam Bintu

dariya tasa harda shewa, "Yau karya ta kare,sai

a za6a zaman gidan miji koh fita yawan gantali

gard'i... Tana jiyota tai banza da ita tana

hawayen bakin ciki. Waya ta d'auka ta kira Aunty

A'i kan abinda Ya Ja'afar ya mata. "Salma kiyi

biyayyar aurenki, dan Allah kiyi hakuri da fitar

kawai. "K'wana biyu ai yayi ma,tunda kin zaga

ko'ina ai har gidan su... "Aunty A'i ban fa wuni a

gida ba kullum a ziyara muke wuni. "Ai duk fita

kina zuwa,dan Allah kar ki dawo muku da hannun

k'yauta baya man,kuna cikin zamanku abin

sha'awa. Baki tai ta bata sai da ta tabbatar mata

da ta hakura kamin sukai sallama. Haka tanaji

tana gani ta hakura da fitar tai zamanta a d'aki.

Koh abincin rana kin zuwa yai yaci a gidan sai

gidan Garba yaje. Kawai zuciya ke raya mishi

Salma ta fita,bazai so yaje gida yaga tabbas ta

fitan ba,kawai sai yai zamanshi har yamma tukun

ya koma gida. Dakin Bintu ya nufa har yanzu

baida walwala sai ya tabbatar da Salma bata fita

ba,yasan Bintu kat ce,bata t'sallaka doka akan

fita,in yace A'a, toh ta hakura. Sannu da zuwa tai

mishi tana fara'a, a ranshi yana aiyana da Salma

ce yasan sai ta cika tai fa kan ta mishi sannu da

zuwa duk akan ya hanata unguwa,amma kullum

y'ar uwarta ko ajikinta. "Yau bayan fita ta Salma

ta fita?.. Kai zata girgiza, sai tai saurin kwa6ar

kanta, dole yadda tasa taga bakin ciki har yau

itama ta gani. "Eh,bata jima da dawo wa ba

ai,baka sani bane?.. Hannu ya daga mata,cike da

jin haushi yace "ya isa ni,tambaya na miki kawai.

Waje yayi tana binshi da g'walo, yana yin nisa ta

tuntsire da dariyar mugunta. Kamin cikin sand'a

tai waje jin ya zata kaya. Ba koh sallama ya

shiga parlourn, ganan takalmin a gefen kofa

wanda ta fitar zata sa dazu. Tana zaune tana

_feeding_ din Miemie ya shigo yana binta da

kallo,da fara'arta tai mishi sannu da zuwa.

Kekam yayi yana k'allonta ba koh kiftawa, tabbas

Salma ta fita,dan mud'in bata fita ba bazata tare

shi da wannan fara'ar ba haka,yasan kayarshi.

"Wato kin fita hankalinki ya kwanta koh?.. Ban

isa ba ashe har yau halinki yana nan baki sauya

ba koh Salma?.. Baki sake take K'allonshi da

tsananin mamaki,sai d'aure ta yake da jijiyoyinta.

Cikin nut'suwa tace "Ni fa ba inda naje tun fitar

ka,dan Allah ka d'aina tun.. Malama ki amshi laifi

kawai,kinsan nafi t'sanar musu sama da komai,

koh kina nufin Bintu karya zata miki?. K'allon

mamaki take mishi,a hankali ta maimaita

"Bintu".. Yaki ma bari tai mishi bayani sai

zazzaga mata yake kan bata maidashi abakin

komai ba. Kawai sai ta sau mishi kuka,tama rasa

abin fad'i,wai Bintu ce ta fad'a mishi,wato ita ba

abin yarda bace sai kishiyarta indai kan fita ne.

"Haka ki ke ai,da kukan rashin gaskiya

Salma..sam bana son ki dawo mana da hannun

agogo baya,ina ta murna komai ya wuce ashe

albarkar ciki ne yasa ki zaman dole. Ganin

kukanta na karuwa yasa ya fice ya koma d'akin

Bintu. Har da bawa kura ajiyar nama,wai duk

randa Salma ta fita dan Allah karta 6oye mishi.

Tun daga ranar ya sauya mata,sam in ya shigo

sai dai ya d'au ya'rshi ya fice,itama daga

gaisuwa shikenan ta gama,dan a ganinta

wulakanci ne wannan babba. Ga wani fi'ilin

mutunci da Bintu ta koya da kissa,kullum faram

faram take mata,harda gaisuwa in antashi. Ta

d'au Miemie ta goya a bayanta in Baban ya

d'akko ta. Ba karamin dad'i kwa Ja'afar din yake

ji ba,dan yana karrama mai son Miemien shi,ita

kam Salma nata ido,sai ta dukufa gun kai

kukanta ga Allah. Dan tabbas tasan tai saken da

har mijinta yai mata mummunan tambari. Bintu

kuwa kullum rokon ta Allah duk wani sharrin da

take nemanta dashi Allah ya mayar mata kanta.

By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:20 AM - Queen Safiyyert馃憫: [8/2, 2:29 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

30_Sai ya huce kamar sati ana mutunci da ta

tambayi fita unguwa zai kicin-kicin,yace tai son

ranta,haka zata hakura tanaji tana gani,in ya

dawo kuma tasha fad'an da batasan laifi ba.

Kawai Allah ya d'aura mata wani irin hakuri,daga

Ja'afar din har Bintun ido tasa musu kawai.

A haka har Miemie tai wata hudu Salma na

zaman hakuri, musamman ga saurin fushin

Ja'afar gareta,ga tai alkawarin daina kai kara gun

kowa sai gurin Allah.

Ana haka Maman Abba ta haihu.

Ganin yau y'an mutuncin na kanshi yana zaune

ya shagala da yiwa Miemie wasa tana wage

mishi baki tana dariya.

Da fara'arta ta zauna kusa dasu tana k'allonsu.

"Abban Miemie...

K'allota yayi tare fad'in yana jinta,cigaba yayi da

wasan su.

"Inda hali dan Allah zani barkar Maman Abba yau

kwananta hud'u da haihu banje ba.

Kai ya kad'a, "wace Maman Abba?..

Da zumudin zai batta ta sanarshi makociyarta ta

unguwar su ta da.

Abinda yake ya t'sagaita yana k'allonta ba koh

kiftawa.

Tuni ya zata an rufe babin y'an tsohowar

unguwar su a gidan,ashe har yanzu tana makale

dasu.

Bazai manta dasu ba,dan sune ummul aba'isin

wargaza gidanshi.

Kai ya girgiza mata,

"Kiyi hakuri ba halin zuwa..

Baki ta sake tana K'allonshi, a gaskiya bazata

zuba ido tai ta zaman gida na y'anci ba,da takura

gaskiya.

Amma sai ta bishi da lallami.

"Dan Allah ya Ja'afar ka barni naje,nima dana

haihu fa sau biyu tazo min har suna uku,kaga ba

dad'i ace ni koh sau d'aya banje ba barka ba sai

suna.

"Sunan ma ki fidda a ranki,dan inda mu'amular

dana fi tsana,toh mu'amular ki da y'an unguwar

chan ne,kin gane ai?.

Kasa tai da kai,sosai take d'aure irin halin da Ya

Ja'afar ya tsiro mata,yanzu da ta kara tambaya

zai ce tai gaban kanta,hakan yasa tai shiru.

Shi kuma yadda yaga batai gardama ba yasa yai

tunanin zancen bai shige ta ba ne.

Miemie ya ajiye kusa da ita ya bar mata d'akin.

A hankali ta zame ta kwanta,sai ga hawaye ya

zubo mata.

Zaman gidan nan ya fara isar ta,hakurinta ya

fara karewa.

Tana ji yai ma Bintu sallama ya fice,kawai sai ta

sau kuka a hankali marar sauti.

Wato a dake ka a hanaka kuka?.

****

Tun bayan fitarshi bayan ta gama kukanta

Miemie ta fara,kukan har ya wuce kima, komai

tayi taki shiru,kawai sai ta goyata tasa hijab akai

suka fita t'sakar gida dan sanyin magriba.

Bintun na t'sakar gida tana saita abin fad'i kan

Ja'afar ya dawo tambayar Salma koh ta fita,dan

komai a k'unnenta ya wakana.

Jijjiga ta take tana yawo daga t'sakar gida zuwa

zaure da ita,tasan Miemie ba mai rigima bace,

tabbas da abinda ke damunta yau,yawan kukan ji

take kamar itama tasa kukan koh taji sa'ida.

Dak'yar ta samu tai shiru,sai ajiyar zuciya take

halamar tai bacci.

Buta ta d'auka ta shiga band'aki kenan sai gashi

kamar an hulloshi gidan,fatanshi yau ya rit'sata

garin satar fita.

Bintu ya kalla wacce ke murmushin ganinshi,sai

taunar cingam take tana kas-kas,kai da ganinta

da yanayinta kaga na mai shirin kulla wani

sharrin.

"Sannu da zuwa..

Kai ya daga mata, kamar kullum zai tambayi

Salman sai yaji bud'e band'aki.

A fusace ya kallo Bintu, "bayan fita ta Salma ta

fita?.. Ki fad'an t'sakani da Allah.

Kwai tayi kan ta fasa tare da yin kas dashi,

"Eh ta fita,mey ya faru? Yanzun bud'e dakinta ta

shiga band'aki ka shigo.

Gadan-gadan Salma tayi kanta da butar data cika

zatai alwala anjima,kansu farga ta rot'sa mata

aka tana huci,bai isa ba ta rufeta da duka baji ba

gani,fad'i take

"Sharrin naki ya wuce bayan idona yanzu a

gaban idona ma yi..

Mari ya d'auketa dashi shima yana fad'in ta sake

ta.

A fusace tace bazata saka ba,ita kam tamkar

wawiya ta bari Salman na jibgarta,ganin da gaske

take yasa da sauri ya finciko Bintun tare da kara

mata wani marin.

Kunci ta rike tana K'allonshi, "ki sani na gaji da

halinki a gidan nan, karan nan zan d'au

mummunan mataki akanki wall...

"Ka sallame ni in ka gaji dani Ja'afar.. Dan ni tuni

na gaji da zaman gidan ka, ka sallame ni ka huta

toh..

"Haka ki ka ce?..

A fusace tace "eh haka nace..

Tuni shedan ya shiga cikin zuciyar

kowa,musamman Ja'afar da ya rufe ido tamkar

bashi ba.

"Ki je gida sai na neme ki toh...

Cikin kuka tace

''Ban isa zuwa musu ba sheda ba,dole ka bani

sheda..

Ba tare da jin komai ba mugu(shedan) yasa ya

rufe ido.

"Kije na sake ki toh..

Chak! Taji kukan ya t'saya sai na Miemie data

tashi dan hayaniya.

Baki sake take k'allonshi fuska wanke da

hawaye.

"Ja'afar ka sakeni kace fa?.. Muryarta na

ka'rkarwa ta tambaya.

Da sauri ya bud'e ido ya dawo hankalinshi kanta.

K'allon-k'allo suke ma juna cikin rashin sanin

abin fad'a, musamman Ja'afar dashi ya furta.

Ido ta rufe a hankali, sai ga hawayen da ya

makale sun zubo.

A hankali ta bud'e idon ta k'alli Bintu.

"Allah ya biya ki da dai-dai abinda ki kamin

Bintu.. Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai

dawo gun maishi..

Jiki a sanyaye ta juya gun Ja'afar.

"Shikenan abin nema ya same mu Ja'afar.. Aure

ya kare a t'sakanin mu..igiya uku ka rusheta

Ja'afar.. Ka rushe su..

Hannu tasa ta share idonta.

"Ba ka da bukatar na t'saya maka bayani yanzu

kam,dan ka zuba katanga a t'sakanin mu.

Cikin nut'suwa tai hanyar waje ba tare da ta koh

waiwayi d'aki ba.

Da k'allo ya bita, ilahirin jikinshi ka'rkarwa

yake,ya kasa tattara kalma daya da zai ambata,

har Salma ta 6ace wa ganinshi.

'By

Feenat Ja'afar.

[8/2, 10:40 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

31_"Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'un.. Allahumma

Ajurni fi Musibati,wakhluf li khayran minha...

"Salma ki ce min ba gaskiya ki ke fad'a ba

Salma?.. Dan Allah ki ce wasa ki ke..

Murmushi take,wanda da zatai kukan zai fi mata

alkairi, amma ta kasa,tun zuwanta gidan Aunty

A'i ido ya kafe,tunani ya t'saya.. Dabara ta ka

re,sai kallo da ido da murmushi da yafi kuka

ciwo.

Waya Aunty A'in ta d'auka dan kiran Ja'afar,

tayuwu koh shi ya mata bayanin da zata gamsu

tunda Salma ta zama kurma.

"Ja'afar..

"Bashi bane.. Tsam tayi dan tasan Bintu ce ta

d'auka.

Da karfin hali ta tambayi in yana kusa ta bashi

man, t'saki tai mata kamin ta kashewar.

Kasa tai da wayar tana mai tabbatar da kalaman

Salma na aure babu,ya ka re.

A hankali ta sakko ta t'suguna gaban Salman

tare da dafa kafafunta.

"Salma kimin magana ba shiru ba dan Allah.. A

dunkule kika bani, dan Allah kiyi magana, shin da

gaske ya sake ki cikon na ukun?..

K'allon Aunty A'in take cikin ido,tabbas wannan

kalmar ita ta 6acewa tunaninta.

Kan ta ankara ta sau mata wiwi,baji ba gani.

"Bintu ce... Wallahi itace.. Ban mishi komai

ba..ya raba aurenmu.. Allah banyi komai ba

karan nan Aunty A'i,ki yarda dani dan Allah, koh

su Abba baza su yarda ba...

Kamar karatun yara haka take had'a kalaman

cikin kuka.

Jiki a sanyaye Aunty A'in ta tashi tazo kusa da

ita,sosai ta gane sambatu take,cike da tausayin

y'ar uwartata ta rungumo ta, ta abu daya take

gane gaskiyar Salma tun a yarinta, shine fad'in

abin da batai ba cikin kuka.

"Na yarda Salma,na yarda dake karan nan.. Ki

bar kukan haka, Allahu yasa shi yafi zama muku

alkairi.

Ita dai kukanta take.

Ina Ja'afar ya gano abinda Aunty A'i ta sani

game da rayuwar Salma, da bai bawa CID na fitar

ta ba, da ya fuskanci ta sauya tun sa'ilin da in

yace ta fita take kuka,da ba ayi hakan ba.

*******************

"Innalillahi Wa'ina Ilaihirraji'una... Ja'afar mai ya

kai ka wannan yanke d'anyen hukuncin kan ku?..

Mey ya kai ka?.. Abinda ya faru yake sanar

mishi,gaba daya ya rasa abin yi.

"Shin ka tambayi ta fitan koh bata fitan ba?.. Koh

har yanzu kai baka hango hankalin Salma ba ne..

Kai ya k'ada mishi

"Ba wannan ne karon farko ba,ni nasan Salma

fiye da zaton ka..

"Ka kuma yarda da Bintu fiye da yarda ka bawa

Salma yarda koh ka ke nufi?..

Murmushi yayi na takaici, "Ja'afar bakasan sharri

irin na mata bane.. Da baka ba Bintu amanar

aurenka sukutum ba Allah. Tayu ka tafka babban

kuskure na fahimtar Salma karan nan.. Amma ka

yi bincike, shine t'sarin Shari'a.. Ni na shiga gida.

Da kallo yabi bayan Garban, duk maganar shi

gaskiya ce,kuma ba daya daga ci da ya aiwatar

kamin komai.

Yau daya yaga fushin Garba karara kwance a

fuska,tabbas haushin shi yake ji shima,kamar

yadda shima yake jin haushin kanshi da kanshi.

Jiki ba kwari ya tada machine yai gida.

Dole ya tit'siye Bintu ta sanarshi gaskiya.

Bata d'aki,ga nan wayarshi da ya manta da tata

akan gado halamar tana sana'ar tata ta charting.

A garin ya d'auki tashi ya danno screen na

Bintun, haske ya baiyana halamar tana ma kan

charting din tai wani waje.

Kwanciya yayi da bayanshi jiki duk a

sanyaye,bazai iya bawa wannan ranar suna ba.

Ido ya kura ma wayar Bintun kirar _Techno_, zai

so yau yaga mey ke debe hankalin ta zuwa

Facebook.

*Bintu U*.

_"ke an saki shegiyar fa,ki tayani murna zan

sakata in wataya_..

*Shining star*:

_"Kai matar nan baki da dama,a bani satar amsa

dan yanzu na dawo makarantarki_..

Da azama ya mike zaune dan ganin charting din.

*Binta U*

_"Hhhhh,tuggu dai kamar kullum nayi,sai dai na

yau mai zafi ne,dan jiya an bani sa'a har gida,

take ina fad'in ta fita ya d'anna mata saki,baiwar

Allah harda dan guntun wa'azin ta ta min

hhhhh_..

*Shining star*

_"ina ma zan iya irin wannan sharrin naki dana

huta, sai dai tawa tasan takan duniya,ina mata

take dawo min da abu na_..

*BINTU U*

_"ba gari daya muke ba,da wallahi taci karya,ni

zan baki maganin y'ar banza_...

"Ya Allah... Kai shafo cikin ranar jiki hawaye na

zuba, da sauri ya d'anna _previous chat_

Sai gata kamar an jehota da buta a hannu tana

zare idano na munafukai.

Sam bataji koh dirin machine dinshi ba,sai

arbawa tai da takalmanshi.

Da d'ukkan hannu biyu ya dafe kanshi yana

hawaye,mey zai ma Bintu ya huce da bala'in da

ta jawo mishi?..

A hankali kalaman Salma ya dawo mishi,

_"Allah ya biyaki da dai-dai abinda ki kamin

Bintu..Ki sani,sharri kare ne,ko yayi nisa zai

dawo gun maishi_...

Gashi tun kan a kwana ya dawo ma Bintu bata

shirya ba...

"Ka dawo..yaushe ka shigo..ban banji shigowar

ka ba..

Da in'ina take maganar, ganin yadda hawaye ke

diga a kafafunshi ga kuma wayarta a hannunshi

tasan yau karya ta kare.

Ido ya goge kamin cikin nut'suwa ya ajiye wayar

kan gado ya k'allota.

"Tabbas kinyi nasarar rabani da d'ukkan farin

cikina Bintu.. Kinyi nasara,tanan kam nasan kin

ma Salma fincinkau,dan ita bata sharri..

"Na baki d'ukkan wata amana,ki mayarni

shashasha.. Ki nunan yau abinda Salma take

gudu a kishiya,"makirci"..

"Amma ki sani,wallahi!,wallahi!!.wallahi!!!

Uku,yadda kikai sanadin 6allewar aurenmu da

Salma kinyi naki.

"Kamin nan zaki ji jiki kamar yadda ki ka sa taji

t'sawan zaman ku..

Kan tai kwakwaran mot'si ya hard'o ta, ta ko'ina

mari yake bata iya karfinshi tana ihun jama'a su

ceceta..

Sai da tabbatar ya taga wuta dan mari kamin

yana haki ya nuno ta.

"Kije kema,na yanke igiyar aurena dake kanki har

guda uku... "Tun kan ki kwana maganar Salma ta

kar6u gun Allah...

Ihu ta saka tana bashi hakuri kan ta daina, "dan

Allah karka sake ni...

Hanyar waje yayi yana sa waya a aljihunshi.

"Ki tabbatar baki kara awa d'aya cikin gidana

ba,dan saki uku na furta.

Waje yayi ya ja ya t'saya a zaure,tamkar wani

yaro ya rushe da kuka mai tsanin ciwo..

Yayi kuskuren da dak'yar ya g'yara shi cikin

rayuwarshi.. Yayi kuskuren da ya bari Salma tai

mishi nisa...

Yayi kuskuren kin kar6ar shiryiwar Salman sa..

Tabbas ya tafka babban kuskure a rayuwa.

"Allah ya isa t'sakani na dake Bintu... Ubangiji

yai ma Salma sakayya akanki daga yau har ranar

sakamako... Allah ya isar mata cikin sauri..

Ganin hakan ba mafita bace gareshi yasa ya

d'akko waya hannu na ka'rkarwa zai nemo Garba

yaga kiran Aunty A'i na dazu.

Garban ya kira,dole ayi wacce za ai,Aurenshi da

Salma mutuwa ce kadai zata raba.

Da Allah ya had'ashi cikin muryar kuka kan yazo

gidanshi yanzun nan..

"Isha'i ake kira fa Ja'afar..

"Dan Allah kazo,in bakazo ba komai zai iya

faruwa...

Ba'a fi minti goma ba yazo,fatattakar arziki yai

ma Bintu ta bar gidan ya rufe ya fad'a mota.

Da t'sananin mamaki yake k'allon abokin nashi, a

iya abotarsu bai ta6a ganin koh da hawaye na

Ja'afar ba bare kukanshi mai sauti irin haka.

Dan Ja'afar namijin duniya ne,Jarumi, kuma

jajirtacce, yasan komai ya sashi kuka ayau ba

karami bane.

"Gidan Aisha zaka kai ni yayar Salma..

Baki sake yake k'allonshi,

"Yayar Salma kuma?..

Ido jajir ya kalloshi ba halamar wasa,dole ya tada

mota suka d'au hanya.

Waya yai mata kan ta fito yana kofar gida.

"Malam mijina ya fita..kai hakuri.. Kit ta kashe

wayarta,yau Aunty A'i ta d'au zafi ya sani,tabbas

kuma Salma na gidan..

Murfin motar ya bud'e a fusace ya fice Garba na

kira.. Kofar a bud'e take,kawai ya tura ya shiga,

nufinshi a d'aureshi bayan yaga Salman.

"Salma!,, Salma!!.. A tunzure Aunty A'i ta fito a

parlourn dan tsayarahi shiga mata parlour.

Yadda taganshi bata isa hana shi ba ganin

Salman, dan g'wiwa biyu ya zube gabanta tamkar

yaga Salman.

Hanya ta bashi ba musu,da zafin nama ya mike

ya shiga parlourn, bata zata ba taga mutum a

kanta,da sauri ta zabura ta mike tana kwad'a

kiran Aunty A'i da sauri.

Bata nufa ba taga mutum zube a gabanta kanshi

a kasa.

Ido ta rint'se tare da kawar da kanta,koh kadan

bata son kara ganin Ja'afar a rayuwarta Abadan.

Juyo wa tai da niyar surfa mishi ruwan bala'in da

ba shiri zai bar gidan,sai dai mey?

Da t'sananin mamaki take kallonshi tana k'allon

Aunty A'i.

Hawaye ke malala a idonshi kamar wanda ya

rasa jin dad'in rayuwarshi,abin g'wanin ban

tausayi.

Ja'afar?.. Kuka ma?, a namey toh?.

"Salma gani gabanki, a matsayin wanda ya tafka

miki laifi cikin rashin sani,da kuma sharrin

Bintu..Salma kiyi hakuri,wallahi _am really really

sorry.. Kar ki barni dan Allah.. Zan tagaiyyara

Salma.. Zan zauce.. sharrin Bintu ne,kuma itama

ta amshi hukunci,dan na saketa kamar yadda ta

jawo mana,

_please_ Salma _forgive me_... Wallahi _I can't

live without you anymore_,ki tausaya ma mijinki

uban yaranki...

Baya taja da sauri ganin yana kara kusantota.

Da sauri Aunty A'i tai waje jin kuka zai kubce

mata.. Dole haka zata kasance dasu Salma,ranar

rabuwa, rabuwar da ba a da tabbacin za'a dawo

ta.. Tabbas tausaya wa rayuwar su,dan a irin

soyayyar nan ita ce ake kira *Mutu ka raba*..

Gashi yanzu K'ADDARA ta raba masoyan biyu.

By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:24 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

32_Kuka take yanayi iya karfinsu, tabbas

K'ADDARA ta rigayi fata, duk kuma yadda ka

t'sara rayuwarka sai ka ga ba haka ya tafi

ba,tabbas ta Allah itace daidai. Baya tai ta zube

kan kujera da6ar.. Duk sunyi kuskure, kowa na da

laifi,meyasa ma tace ya saketa?.. Mey yasa?..

Le6e ta cije tana mai sa d'ukkan hannunta biyu

zuwa fuskarta, kuka kam yau har sunji ba dad'i.

A hankali ta dago tana K'allonshi ido yai luhu-

luhu,duk ya marairaice mata hawaye na zuba, tafi

tausayin kanta sama dashi, Kokarin magana take

su Aunty A'i sukai sallama ita da maigidan da

taima waya. Fuska Ja'afar yai saurin gogewa

ganin yadda Abban Aslam ya sau baki yana

kallonsu,bai tunanin abin ya kai haka ba, kuka a

gaban mace da zubewa g'wiwa biyu?.. Lalle

yasan abin babba ne. "Innalillahi Wa'ina

Ilaihirraji'un... Itace kalmar shima da ya fad'i

bayan yaji mai ke faruwa.. "Dole aje gida kowa

ya samu labari,dan wannan ba abin a 6oye bane

koh da za'a nemi sulhu,saki ya cike na uku abin

yafi karfin zama anan Ayush.. Zamu tafi da

Salman kai Ja'afar sai ku taho da abokin ka. Har

kusan goman dare ana abu daya akan zancen

saki. "Ka ce kayi saki,ita tace ya zama uku,

sannan kana zancen ai sulhu koh? Kai ya daga

da sauri, murmushi Abban yayi,abin yaso ma

bashi dariya, "Wato Ja'afar... "Malam Umar

wannan zancen ba zancen da za'ai wa sakwakwa

bane,kan Ja'afar ya dawo. "Kai kuma in dan baka

tashi mun wuce ba zan mugun sa6a maka

yanzun nan.. "Kana hauka ne?.. A wane garin ka

ta6a jin anyi saki d'ai daya har uku kuma ana

neman sulhu?.. "Ai baka fara ganin komai ba

Ja'afar, ba dai zuciya ba?.. Za ta sa ka dana

sani, "Malam Umar ai hakuri bisa wannan

K'ADDARAR da ta sakko mana,zamani ne yanzu

muke ciki da yara basu dauki saki a bakin komai

ba.. Tashi yayi yana bawa Abban Salman

hannu,kan ya kallo Ja'afar,har yanzu sautin

kukan su ke fita shi da Salman. "Muje koh?..

Salma ya dago ya kalla da sunkuyar da kai,

"Salma dan Allah ki basu hakuri kar su

rabamu,kin san bazan iya rayuwa ba ke

ba,Abadan Salma...Please. Kuka ta kara saka

mai karfi, t'saki Abba yayi ya karkade riga yana

nuno shi cikin fad'a. "Hauka kenan wannan, dan

koh a musulunce Salma ta haramta a gare ka..ta

haramta har abada,dan kai kam ka nuna mana

bazaka ta6a iya rike aure ba, saki tamkar wasan

yara? Itama waccan wai ka mata saki uku?.. Toh

koh aure Salma tayi na fad'a maka ta haramta a

gare ka har abada,kaje kaci zuciya. Da gudu

Salman ta tashi tai d'aki tana kuka.. "Haba

Alhaji, abin bai kai haka ba,kuskure ne kowa yana

iya tafkawa a rayuwa.. Anji bai k'yauta ba,amma

kar hakan yasa kai mishi baki,kai hakuri. "Hakuri

shine ya biyo ni yanzun nan.. Wace iriyar

haukace wannan kamar a jahiliya?.. Wani yai

mishi sakin?.. Haka Ja'afar naji na gani yai waje

yana waiwayen dakin da Salma ta shige yana

hawaye. Tun daga ranar duk suka zama sakwa-

sakwa, barin Ja'afar da baida kuzari,ga Abba ya

sako shi gaba ta ko'ina.. Dan har gida iyaye

Bintu suka zo sukai ma Abba rashin k'yauta wa

akan yadda bayan saki uku sai da aka

kumburawa ya'rsu fuska,harda ikirarin

koto,dak'yar aka basu hakuri kan suka debe

kayanta, ranar Abba yayi takaici har yaji ina ma

da ya barma Umman shi Ja'afar,kila da baici

karo da bacin ranshi ba. Sai dai yace kayan

Salma koh sama da kasa zasu had'e ba mai diba,

ashe ma in ya bari aka diba sun rabun kenan...

Ja'afar mat'sala. Anyi ban baki, Abba yayi fad'an

ya dawo lallashin amma Ja'afar ba sauki,kawai

sai Abban Salma yace a rabu dashi,dole in ta

tashi aure zai bari a diba da kanshi. Kullum ta

Allah yana kan jelar gidan su Salma,a wata guda

har kama ya sauya,ba aski,ba g'yaran fuska,ya

zama tamkar zararre. Sosai Abba yake tausaya

mishi,Mama kadai ke shafawa idonta toka ta

hana ya ga Salman,sai dai a bashi Miemie, haka

zai gaji har ya tafi,sai dai tai ta ganin text na ban

hakuri,gobe ma zuciya zai dawo. ***************

*************** Rayuwa irin ta kunci kam sun

ganta a wata hudu da ta gabata. Salma ta

saduda sosai akan Ja'afar,dan har yanzu shi

yana kan bakar shi. Sam in ka ga Salma ta

sauya,ta dawo shiru shiru sosai,kullum zaka

same ta a daki,koh ta dukufa tunani, koh tana

k'allon Miemie tana hawaye. "Salma... Gefe tayi

da sauri da kanta tana goge hawayen jin

maganar Mama akanta. Dole yau ta kawo

karshen matsalar nan. Zama tayi a gefen gadon

tana kare mata kallo. "Rayuwa fa kullum sauyi

take Salma,amma banda taku, ni dai ban ta6a cin

karo da kulafucin D'a namiji irin naki ba, wata

hudu ba kwana hudu bane Salma.. "Lokaci yayi

da za ki cigaba da rayuwarki ki manta da kashin

Ja'afar.. Ki d'auka Rabon Miemie kawai ya had'a

ku,ki manta da rayuwar da,dan ta wuce,ki

fuskanci zahiri a rayuwar gaba Salma.. Fad'a

Mama ke ta mata tana kuka, taya zata mance

Ja'afar?.. Taya zata mance zaman su?..Soyayyar

ta da Ja'afar had'i ne na Allah a ganinta ba wai

wani rabon Miemie ba... In har Ja'afar na bata

haushi bai wuce yadda ya dankara mata saki ba

ba ji ba gani,amma bacin hakan,tabbas bata da

sama da Ja'afar a zuciyarta kawo iyanzu..

"Nasan da kin gama iddar ki sarai... Da sauri ta

k'allo Mama da t'sananin mamaki, kai Maman ta

kad'a mata. "Tunda ki ka zo gidan nan ina

fuskance dake Salma,kin gama iddah tun wata

uku da suka wuce. Kasa tai da kai tana goge

hawaye,tasan Mama gaskiya ta fad'a, dan

shayarwa bai hanata period ba.. "Nasan ma

hakan ne Salma,yanzu abinda nake so dake

shine, "Dole ki fara fita,dan saki ba takaba bace,

bazai yu kiyi ta zama a gida ba kamar matar

kulle,tun yanzu zaki fara fuskantar cigaban

rayuwa,bana son musu koh taurin kai Salma a

zuwan nan daga gunki, dole komai nace kiyi kiyi,

kina jina koh?. Shikenan kuma,ta faru ta kare,wai

an ma mai dami daya sata.. Shikenan ta shiga

sahu,yanzu sai jiran bazawari.. Kuka ta sa mai

sauti,yi take ba kakkautawa,har ta kular da

Mama ta bar lallashi ta hau sababi. Dole kam in

dai ta yadda da K'ADDARA ta maida komai ba

komai bane.. Dole ta daina yaudarar

zuciyarta,tana biya zancen Ja'afar a kullum akan

tashi ce shi kad'ai.. Hannu tasa ta share

hawayenta,kan ta g'yara zama. "Na shirya bin

umarnin ki Mama matukar bai sa6a shari'a ba..

Baki Maman ta washe, "Koh ke fa,yanzu naji

batu,ko ke fa Salma. Kasa tai da kai tana

murmushi, sosai taga farin cikin Mama.

Washegari da dare bayan Abba ya dawo taje

gunshi suna zaune da Mama,yai mamakin

sauyawarta faradd daya,shima sai murmushi

yake mata. "Abba.. Zama ya g'yara da murmushi

ya amsa. "Abba makaranta nake son shiga

dama... Da sauri Mama ta kallota, ji zata kwafsa

musu kuma,wai makaranta? Baki ya washe dan

murna. "Toh Salma,kinyi tunani mai k'yau, Allah

yasa a shiga a sa'a. Kai kasa tace "Amin Abba...

"Anjima ina son zan k'waso akwatina na a gidan

Abban Miemie koh da y'ar makota ne.. Kai ya

kad'a mata "A'a,ki bari zan ma shi Ja'afar din

magana zai kawo miki har gida. Sosai sukai fira

Mama na jinsu bata ce kala ba,tana shiga d'aki

Maman ta bita. "Ya zaki min haka Salma?.. Wace

makaranta kuma ana zaune lafiya?.. Shiru tai sai

da ta gama kan tace ba abinda karatunta zai

tsare mata,tai hakuri tasan zai mantar ta wasu

abubuwan. Ba dan taso ba ta yarda. Ta gama da

Mama, saura Ja'afar. By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:25 AM - Queen Safiyyert馃憫: A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

33_Washegari Abba da kanshi ya samu Jafar din

a shago,duk da yai jim,daga baya ya tuna da

wannan ne damarshi na ganin Salma a yau dan

tuna mata da alkawarin shi. Da yamma k'wa

yasa Garba ya k'waso mata akwatinan ta da

sauran sabbin kayanta marar dinki. Da sallama

ya shigo gidan, ya k'wa taka babbar sa'a Mama

bata nan. T'saye yayi ganin Salman t'saye a

gaban famfo Miemie na mata kukan kunu tana

dauraye murfin feedern. "Sam baki da jimirin

yunwa Miemie,kimin hakuri yanzun zan... Itama

shirun tai dan jin sallamarshi. Da dan rarrafe da

tafiyar da batayi kwari ba ta nufi gun Abban da

murna. Ganin Miemien ne yasa shi dawo da

hankalinshi kanta,sama yai da ita kamar kullum

suna dariya. A hankali ta rufe idonta tanajin

zuciyarta na bugawa da sauri,kusan wata 2

rabonta da ta sashi a idonta,jin takunshi na

kusanto ta yasa ta juya da sauri tare da had'iye

hawayenta. Ya sauya mata,duk ba g'yara, har

wata kasumba ya had'a ta dole ta rashin g'yara

fuska. Da t'sananin murnar ganinta ya karaso sai

washe baki yake,da sauri tai baya ganin abinda

yake shirin yi tai gun taburma ta d'akko,sai ya

bita da kallo baki sake, tabbas Salma batai

kewarshi kamar yadda ya mato a kewarta ba..

Koh irin d'aukin nan na ganinshi t'sawan lokaci

haka bata yi. Dan dukan da Miemie take mishi ne

yasa ya kallo ta,da hannu take nuna mishi kan

feedern dake hannun Salman. Kan taburmar ya

nufa tare da zama,so yake sai ya fassara

yanayin Salman,shi yasa yake ta k'allonta.

Feedern ta mika wa Miemie tana dan satar

kallonshi kan ta kau da kai tace "Ina wuni.. Shiru

yai mata,sai ta dan kalloshi cikin ido,shima ita

yake kallo,bazata iya kallon kwayar idonshi

ba,zata chaza mata matsala,da sauri ta kara

dauke kai tana maimaita gaisuwar. "Mey yasa

kwana biyu ba k'ya d'aukan kira na Salma?.. Ba

k'ya ban amsa koh na miki text?.. Gefe ta kara yi

da kanta tana kallon wani waje, kan tace "Ban

gani ba ne.. Da mamaki yake kallon yadda tai

maganar cikin nuna ko'in kula. "Salma kin daina

so na yanzu koh?.. Yadda yai maganar yasa jin

wani iri da dan tausayinshi,da jihadi ta juyo ido

cike da kwalla. "Ya Ja'afar, ya dace mu fuskanci

zahiri fa yanzu,mu daina yaudarar kan mu dan

komai ya afku..Dole nai aure ka sani,ban maka

alkawarin zama ba aure ba,bazan maka alkawarin

kin kula wani ba.. Yanzu haka karatu zan

koma,ka d'auka rayuwar da ta shud'e a mafarki

muka yi ta, yanzu mun farka... Dole akwai cigaba

a rayuwa.. Kai hakuri, amma bani da alaka da

daukan kiran ka yanzu,ka manta Salma dan

Allah,mu fuskanci rayuwar gaba.. Kai ta kautar

tana goge hawaye, shi kam k'allonta kawai yake

ba koh kiftawa. "Ke nan kina nufin son da nake

miki karya ne?... Soyayyar mu hasashe ce

Salma?.. Zaman mu da rayuwar auren mu wasa

ne?.. Kina nufin Miemie ma mafarki ce?... Da

fusata yake tambayarta,kai kawai take girgiza

mishi tana hawaye. "Ba haka nake nufi ba.. "Toh

mey ki ke nufi?.. Shiru tai tana cigaba da kukan

ta,sai ya kada kai cikin takaici. "Salma kin d'aina

so na kam.. Girgiza mishi kai tai "Ina sonka Ya

Ja'afar, har karshen rayuwata.. Abu daya nake

son ka gane,yanzu komai ya sauya,alakar Mimi

ce kawai ta rike mu... Ka cire son zuciya aciki,

dan bazan iya haramtawa abinda Allah ya

halasta min ba.. "Assalam Alaikum, wannan

akwatunan fa a zau... Tsaye tai ba tare da

karasawa ba, kai kasa ta amsawa Mama

sallama,ciki Maman ta karaso,ya gaida ta kai

kasa,duk shiru sukai ba mai magana, sai muzurai

Mama take ma Salman kan ta shiga daga ciki.

Jiki a sanyaye ta tashi ta shiga ciki,a hankali ta

sa kanta a kan katifa tana hawaye. Ba dan yaso

ba ya tashi yai fita,tare da shigo mata da

akwatunan ta. Har zauren Mama ta bishi ta sa

sakata tana sababi kan tai gun Salman. "Wai ke

baki da hankali ne Salma?.. Meye had'inki da

wannan da har zai shigo cikin gida ki bashi

taburma, har ki zauna a gabanshi kina wannan

shashancin cin?.. Mey fa rabawa(K'ADDARA) ta

raba ku har abada. Shiru tayi har Maman ta

gama tana ta kok'arin shanye kukanta, ta sani da

koh tayi bayani Mama bazata gane inda ta dosa

ba. "Kiyi hakuri bazan sake ba. Kai ta k'ada tuni

har tai laushi. "Ina kuje miki yaudara irin ta D'a

namiji ne Salma,gaba in kina mishi haka sai ai

abin kunya. Shiru tai tanajin wa'azin Maman

kawai. G'yale ne kusan kala 5 had'add'u,tana

washe baki ta fito dasu daga leda. "Ki zabi na

za6a ki darje,dan zawarcin ki sai yafi y'an

matanci a komai Salma, gobe kayan k'walliya

zasu zo dan na bawa Hajiya Jidda kud'in kayan

g'yaran jiki,ga wata yayi nisa da komai kin samu

akan lokaci.. InshaAllah sai mun cike gurbin da

muka rasa.. Ni da zakiji shawarata ma da an

yaye Miemie a satin nan a mikata ga gidan su

chan ya karata... Da sauri ta dago tana kallon

Mama, Kat'seta tai da fadin "Eh man,bashi yake

ikirarin yana kawo shi ba?.. Toh zamu mayar

mishi da abarshi kawai. Kai ta hau girgiza ma

Maman,Allah yaga ba mai rabata da Miemie sai

aure. "Mama Miemie fa karama ce,kawai tai

saurin tashi ne,koh fa wata tara bata cika ba..

Dan Allah kiyi hakuri,dan ba abinda zata t'sare

min koh a makaranta. Harara ta aika mata, "Kina

nufin da ita zakina fita?.. Kallonta take ta rasa

amsar ba Maman. "Toh da sake wallahi, ba

yadda za ai ina tufka kina bin bayana da

warwara.. Zawarci da goyo?.. Toh da sake,dan

ba mai gani ya kulaki alhalin kina sa6e da y'a.

"Aikina fitarshi ta naga dama ce,in ma kince

baza'a mayarta ba ni zan na miki renon,aje a

dawo lafiya. Shiru tai tana jinta kawai. Washegari

sai ga kayan k'walliya jibgi,su mascara, eye

shadows,su sabulun g'yaran fata harda su man

gashi,ga haddun man gyaran jiki,lalle Mama da

gaske take. Shi kam tunda ya koma da yazo

k'wanciya yake tuna dazu,lalle in Salma tasan

wata toh bata san wata ba. Tazo k'wanciya taji

karan wayanta,agogo ta duba, tasan ba mai mata

haka sai mutum daya. Badan taso ba ta d'auka,

sai dan jin dame yazo. "Naji kije makarantar,

amma bisa sharad'i uku.. Baki ta bud'e cike da

mamaki,wai koh ya manta bata karkashin ikon

shi ne yanzun? Dan dai taji sharad'in tace tana ji.

"Good. "Na daya kafarki toh kafar Miemie duk

inda zaki shiga. "Na biyu ba zancen yaye sai

Miemie ta cika shekara biyu kamin kiyi komai.

"Na uku,fitar ki sai da nikaf da hijab,sannan ni

zan sama miki mai kai ki a Napep ya d'akko ki in

kin gama, dan ba ko wanne kato zai na d.. "Ka

ga malam,ka bari ka fad'awa Miemie wannan

dokar taka ba wai ni da nake Salma ba... Dan ba

y'ar ka bace ni,ni nake da damar t'sara rayuwata

yanzu ba kai ba. "Abu daya nasan na yarda zan

iya shi,shima dan hakkin ka ne dole,shine yaye

Miemie,zanyi yadda kace, sauran kuwa ba

huruminka bane... Wayar yabi da kallo baki sake

jin ta kashe kit.. Lalle Salma ba ta so zaman

lafiya ba a garin nan, amma zata jidi mamakin

shi. Dan shi tai mishi daidai ma da zata tafi

makaranta. Tun daga ranar ya daina kiranta a

ganinshi zata damu ta bashi hakuri ayi yadda

yaso,sai dai ta daure ita. Ana haka ranar Abba

yace ya batun makarantar da yace zai koma?..

Kanshi t'saye yace ya ma Abban ai ya fasa. Nan

ya bud'e mishi wuta kan bai isa ba,duk haukar da

yake ranar ya samu labari gun Mama,dan har

gida tace ai mishi t'sakani da Salma,sai dai yazo

za'a bashi Miemie in dan ita ne. Sosai yaji

haushi,yasan aikin Salma ne..shi yasa ya d'auke

mata wuta,sai dai ya tura k'annenshi su dakko

mishi Mimi

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 4

Feenat Ja'afar Novel's

Su Salma an samu gurbi a school of hygiene,da

shawarar baba ta cike ba Polly ba. Ranar da ta

fara fita da personal zata kai takaddun ta. Ba

yadda zaka ga Salma ka gane itace da lokacin

tana budurwa, yanzu Salma ta daban ce,ta gaban

goshin Mama, dan ta dage dole sai tayi kara'i da

zawarci. Kwanar su Ja'afar ta shawo,tasan

yanzu haka yana makaranta dan sha d'aya na

safe. Sosai tai k'yau cikin doguwar riga ruwan

kwai mai duwatsu,da g'yale karami ta nad'a

fari,ta ritaya jaka karama mai (chain),ba wata

k'walliya tayi ba ta azo aga,dan wannan ma

Mama na t'saye tayi ta,ta kuma rantse ita da

hijabi sai a sallah. Zai wuya kace ta ta6a aure

har da rabon Miemie, dan yanzu ne take

shekarunta na (22) a duniya. Kanta kasa take

tafiyarta cikin nut'suwa, sai dai ji take duk ta

tsargu,tamkar Ja'afar na kofar gida yana

kallonta. Dak'yar ta kai kanta bakin kwalta tana

sauke numfashi, ashe feeling take... "Kin k'yauta

Salma kenan?... A razane ta juyo jin mai

maganar.. Rai had'e yake kallonta tamkar bai

ta6a dariya ba. Duk da ta tsorata da ganin

yanayin da yake amma ta cije itama ta ci kunu.

"Da nai mey fa? Rai 6ace yace "Ina Miemie?..

Kai ta k'autar gefe,kan tace "Gida".. A fad'a

fad'a yace "Wato bakiji abinda nace ba koh?..

Kalli shigar ki,kamar wacce zata party,sam baza

mu shirya dake ba in.. "Tafiya ne?.. Wani mai

keke napep ya tambaya, kallo irin na baka isa ba

tamai, kamin tace ma mey keken "Eh tafiya ne.

Tana kokarin shiga tace "ba ruwanka da shiga

ta,cos I know what i'm doing.. And ni ba y'arka

bace, na fad'a ma ka rabu dani. Sam taki k'allon

fuskarshi bare ta sare gun taka mishi burki. Baki

sake yake binta da k'allo har mai napep yaja

kamin ya samu k'warin ya tanka. By Feenat

Ja'afar.

9/29/16, 9:28 AM - Queen Safiyyert馃憫: [8/7, 11:03 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

34_Jingina tai a jikin Napep din tana sauke ajiyar

zuciya.

"Kai hakuri Ya Ja'afar, ya zama dole na koya ma

nisa dani,kai hakuri,ina sonka wallahi..

"Hajiya magana ne?..

Kai ta dago jin mai Napep na tambaya, ashe

maganarta ta fito fili.

Ta gama komai Monday zata fara zuwa,kwarai

taso ta yaye Miemie sai dai ba hali,dole tabi

yadda uban y'ar ya t'sara.

Shikam Ja'afar tun daga wannan ranar kullum

zata makaranta sai yai mata maganar wani

abu,koh yace k'walliya tayi yawa, koh yace

uniform ya d'ame ta.

Wani sa'in har ta wuce tana dariyar zariya irin ta

Ja'afar, tabbas gani take ya zare.

Shima kamar yadda Abba yace haka dole ya fara

_processing_ dan tafiya masters a B.U.K,sai dai

fur Abba yace garin zai bari,a Zaria zai yi,kar ya

damu an ma kusa shirya masa komai ba koh

kwandalar sa.

Tamkar ya aza hannu aka ya kwala ihu yake ji

ranar,yana nan ma ya ya k'are da Salma bare ya

mata nisa?..

Tafe suke ita da wata y'ar makarantar su da

tazo zata rakata bakin kwalta, ta gama shirinta

kenan zata gidan Aunty A'i sai fasawa tayi.

Tai kyau,fatar sai shining take taji mai da

sabulun Mama.

"Allah ba wanda zai ce kin haifi Miemie sis

Salma,kin ganki kuwa?..

Murmushi tai ma kawar tata lokacin da take

t'sayar mata da Napep.

"Haka dai kuke cewa kullum.. Murmushi tai mata

sukai sallama.

Tana kula da wani mai mota yana ta kallonta ya

t'saya siyan Apple.

Kokarin tsallakawa yake ganin zata wuce da

sauri,kai ta kada dan sarai tasan yau ma za'a

tafka dirama irinta ranar chan da Ja'afar, dan

tana kallon yadda yake maka mata harara a kofar

gidan su suna zaune shi da Garba da wani,tasan

darajar kawarta taci da yanzu ya taso bambami

dan tasa g'yale a kafad'a, kai ta girgiza dan

yanzu abin dariya yake bata ma...

"Assalam Alaikum.. Waiga wa tayi jin an mata

sallama.

Da dan sakin fuska ta amsa tana mai cigaba da

tafiya a nut'se.

"Gunki nazo fa y'an mata dan Allah.

Kai ta daga aikwa idon Ja'afar kyar kanta.

Da murmushi ta juya badan taso ba sai dan

yakice dan gudanta, duk da tasan baza a wanye

lafiya ba.

Tuni dad'i ya kama saurayin dan da har ya fara

d'ari-d'arin mata magana,sai ya ga kamar matar

manya ce.

"In bazaki damu ba dan Allah ki ban numbern

ki,wannan ne gani na biyu da na miki a layin nan

yanzu ina sauri zan kira ki...

Ta gefen ido ta sato k'allon Ja'afar ai kwa a

suk'wane yake zuwa gun nasu.

Da sauri ta karbi wayar mutumin da zummar sa

mishi ya iso.

Su dai su Garba ido ne nasu,dan abin Ja'afar ya

daina bashi dariya yanzu tsoro yake bashi.

"Bashi wayarshi ya kauce tun kan na

dagargazata a gun nan..

Banza tai dashi tana cigaba da latsa wayar

karya,bata aune ba taji ya warce da karfi.

"Karbi wayarka ka bar layin nan Malam, koh kaga

tayi sa'ar tsayuwar ka?..

Baki sake saurayi yake kallonshi,shi a tunanin shi

koh yayanta ne ma,dan shima haka yake ma

samarin k'annenshi baraza,dan haka bakin shi

alaikum ya kar6a yana kallon Salman.

Cike da tsiwa ta kallo Ja'afar din,

"Malam wai ina ruwanka da samari na ne

eyeee?..

"Kimin shiru tukunna, kema zan dawo kanki ne ai.

Da hannu ya nuna ma saurayin hanya halamar ya

ware,ba daban yaga Ja'afar din ba na wasa bane

ba da ba yadda za ai ya bar wannan

sankaceciyar budurwar.

Da sauri ganin zai tafi tace "Malam ina zaka

ne?.. Kai ya kad'a mata yana murmushi kan ya

kara gaba.

A fusace ta nuno shi da hannunta

"Wallahi Ya Ja'afar na gaji da wannan abin fa,dan

wallahi na kusa kai karar ka gun Abba ya mana

t'sakani,mey ruwanka dani wai?...

Shiru tai tare da matsawa da sauri ganin ya mika

hannu bayan gyalen ta.

"Wai kai lafiya ka ke?.. Harara ya sau mata kan

yace

"Tun muna sheda juna ki daina sarar nan ta

sauke g'yale a kafad'a Allah...

"Bazan daina ba din, na fad'a ma bani ba kai,

tunda kai har yanzu bakasan Annabi ya faku ba...

Shiru tai ganin Garba.

"Haba Salma,haba,a titi fa ku ke?.. Tunda kinsan

halin kayanki sai ki gaba ki barshi ya karata, dan

Allah ki daina biye mishi.

Harara ya sakar ma Garban, "ina ruwan ka toh

kai ma,kowa dai yasan da matata nake t'saye ba

kowa ba..

"Mtsww... T'saki taja rai 6ace, duk suka kallota..

"Wallahi you are sick..

"Ni matarka ce, amma fa a da, kai istigfari ma

tun wuri,dan wallahi za kayi sa6o...

"Kimin shiru fa Malama..dan kwanciyar hankalinki

wallahi kibi abinda na ce kiyi,period..

Shiru tai tana kallonshi,karfin hali sai gun

Jafar,tabbas sai tayi da gasken gaske,dan

abinshi gaba yske,shima Garban k'allonshin

yake,abu dai kamar wasa yake gani yanzu zai

zama babba.

By

Feenat Ja'afar.

[8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

35_Drama sosai sukai kan ta wuce gida rai 6ace

duk rai a dagule, dabarar ta ta kare kuma a akan

Ja'afar, duk hanyar da zai zuciya ya daina kulata

tabi ba nasara,tamkar ma zigi take mishi.

"Mtsww... Taja t'saki,Tabbas so so ne,amma na

Ja'afar son kai ne,dan shi yaja komai..

"Ke kuma ke da wa kike t'saki haka?..

Ba tare da ta dago ba tace "Ja'afar man.. Ya

hanani sakat a unguwar n...

Da sauri ta datse harshenta dan jin Mama fa ke

tambaya,

"Au har yau yana nan yana bibiyar taki koh?...

Kai ta girgiza da sauri, zarar bunu..

"A'a, ni nasan hanyar maganinshi,ki ban nan da

gobe.

Da sauri tace

"A'a Mama ba komai bane fa,kiyi hakuri zai

daina... Shiru tai ganin harar da take aiko mata.

Tun daga ranar Mama ta zama y'ar rakiyar

Salma hanya,sai ta tabbatar ta hau abin hawa

zuwa makaranta zata juyo tana aika mishi

harara,da tai na sati sai ya bar tare hanya kuma

ya dawo waya.

Ana haka shima admission nashi ya fito

shima,tuni ya shiga kunci,dan yasan ya kusa yin

nisa da Salma,hakan yana nufin komai zai iya

faruwa.

Ranar da yamma ana washegarin zai tafi yazo

mata sallama duk da sunyi fad'a.

Taimakonshi daya Mama bata nan ranar ma,dan

yana ga ita kad'ai zata iya tsaida shi a yima

Salma kashedi.

Shigarshi zauren kenan sukai kicibis zata

fito,harara ya sakar mata kan yaja ya t'saya.

Fita take shirin yi ya ruko gyalenta da sauri har

yana zamewa,don haka a fusace ta juyo da niyar

balbaleshi ya marairaice mata fuska.

"Saken g'yale toh.. Murmushi yake yaki saka, ''ka

saken gyale koh na fuce... Da sauri ya cika yana

tare kofar fitar.

"Maganar fahimta nake so muyi dake,dan Allah ki

t'saya..

Hannu ta hard'e a kirji ta k'alleshi,itama zata so

su fahimci juna.

"Ina wuni toh,tunda har gaisuwa kin soke dani.

Da kalar tausayi ya kara yana sukui da kai har

taso yin dariya kamin ta gaishe shi.

"Ina Miemie?.

"Da Mama suka fita,kayi kai maganarka kan su

dawo fa.

Tsayuwa ya gyara tukun ya kira sunanta, rai sake

ta amsa,fatan ta yasa zancen azziki zai mata ba

wai shirme ba.

"Salma".. A karo na biyu ya kara kiranta, bai jira

amsarta ba ya cigaba,

"Gobe zanje Zaria kan batun makaranta da zan

fara, kima Allah Salma ki yi kamar ina nan dan

Allah,banda kula tsagerun samarin nan wanda

har yau basu mallaki hankalin kansu ba dan

Allah.

"In ma aure naso kiyi ina ga ni ya dace na baki

mijin aura,bare a agendar mu bamuyi haka dake

ba...

T'sam tai tana kallonshi da halamun ya zare tana

murmushi, amma zata bishi a haka a wanye

lafiya.

"Toh naji,zan kuma kiyaye,happy?..

Kai ya kad'a da murmushi, "yauwa koh ke fa,dan

Allah Salma ki riken alkawari nan..

Kai ta kad'a tana taji ai.. Da haka suka rabu ya

bata kayan zakin Miemie, murna fal ranshi suka

rabu ranar.

K'warai ta samu sakewa sosai bayan tafiyar

shi,tuni ta kara bud'e shafin zawarci sabo,duk da

kasan ranta tausayinshi take ji sosai.

A wata daya tai samari biyu irin son Mama, barin

Alhaji Usman Dan chanji.

Kud'i sosai yake kar mata kamar ba gobe,

albarka kwa kullum samunta take gun

Mama,yace shi ba yaro bane,dan haka yana so ai

auren cikin k'ank'anin lokaci.

Ya sanar mata yana da mata daya da yara biyu

kachal,aurenshi uku,sun rabu da biyu sai Hajiya

ta k'arfen.

Tunda suka rabu tazo gida tana tuna abu uku,

tabbas a yanzu bata da ra'ayin auren mey

mata,dan taga aya akan Bintu.

Sannan bata son mutum mai irin kud'in Alhaji

Usman sam a rayuwarta.

Gwara ma Kamal dan shi matashi ne kamar su

Ja'afar, kuma yafi kwanta mata a rai,gashi da

saukin hali da saukin kud'i.

"Oh ni y'an nan,ashe arziki ke binki Salma a

rayuwa?..

K'allon Maman take yadda take daga abubuwan

da Alhaji ya bata,ita dey nata ido.

"Bana jin koh lokacin y'an matancinku kun ta6a

had'uwa da irin wannan, babbar harka ai tayi y'an

nan...

"Mama ni fa mutumin nan bai kwanta min ba

sam Allah,gashi har ya fara maganar aure tun

yanzu,ga yana da mata fa,ga ni sam irin kud'in

nan baya...

Baki sake Mama ke k'allonta,tuni ta tsayarta

cikin fad'a.

"Rufe baki ni sauraniyar y'an iya t'sari, ashe har

yau kina nan da halin nan Salma? Arziki na binki

kina zura da gudu?..

"Ina ruwanki da matarshi?.. Koh a kanta zaki

zauna?..

Kai ta girgiza zatai magana ta dakatar ta.

"Koh dai Salma hudubar yaron chan tai tasiri

akanki?..

Kai ta kad'a,

"Allah Mama ba haka bane,ni ina tsoron kishiya

ne,kinaji fa wai aurenshi uku suna rabuwa sai ita

ke zama...

"Sai mey toh?.. Kar ki bada mata mana Salma?..

Baki sake take k'allon Maman,kamar ba ita ke

fad'in ba mai zama da kishiya ba a yaranta tunda

itama bata zauna ba,wace daga ce ba'aci ba

lokacin auren Bintu da Ja'afar amma yanzu kud'i

ya warware Mama?... Kat'seta tai,

"Saboda haka komai yace ki ce toh, in ma ita ke

fidda su toh ke zama daram,dan wannan ba

gidan fita bane in an shiga...

Hawaye ke zubar mata yayin da tazo k'wanciya

tana tariyo zancen Mama, dole in dai tana son

faranta mata wai ta ba wa Alhaji dama.

Waya ta d'auka jin shigowar text message,tasan

na Ja'afar ne.

_"Salmatee,remember, a heart dat truly loves

never loses hope..but always believes in d

promise of love,no matter how long d time and

how far d distance,at d right time,love will fine a

way".._ ki rike alkawarin ki,love you..

*Ja'afar*

Kukanta ne ya karu sosai bayan ta gama

karantawa, tabbas in ta cigaba da sauraran

kalaman Ja'afar zasu sa ta karaya har ya ci

galaba akanta..

"Bani da kamar ka har kullum Ya Ja'afar, sonka

gareni ba mai misaltuwa bane,amma kai kaja

mana koma meye...

Fuska ta goge sakamakon jin tahowar Mama da

Miemie na kuka.

Washegari kanta t'saye ta bawa Alhaji damar ya

turo magabatanshi kawai koh ta huta da

dawainiya da son Ja'afar.

Sabon sim ta siya tasa a sabon wayar Alhaji da

ya bata,a haka suka raka wata kusan biyu, duk

da tai kewar text da kiran Ja'afar din.

Shikam yana chan hankali tashe na rashin samun

wayar Salma, ga Abba ya sanarshi kar ya sake

ya dawo sai an nemeshi a makaranta,

Duk da an sanarshi ana kawo Miemie gidansu ta

yini.

A jikinshi yaji abu na faruwa,duk sai yaji bai da

nut'suwa sai ya je gida dan tabbatar da

zarginshi.

***

Tunda daga d'anno kanshi layin su Salman ya ja

ya t'saya. T'saye take da dan murmushi a

fuskarta, sanye cikin favorite dinshi riga da skirt

na atamfa purple, tai kyau matuka gyalen nan a

kafada,daga inda yake zai iya gano bakin

gashinta a tufke ta chan kasan dankwalinta,

tasha ado tamkar zata party.

Wani abu ne yazo dai dai makogwaronshi ya

tsaya,kishi...

Bai san ya isa gun ba sai da yaji ana "lafiya?..

Kallo shi yayi, duk sai yaji yau baida ma k'warin

g'wiwar fad'a,Salman ya kalla,da sauri ta kawar

da fuskarta gefe ta had'e rai.

Sai ya dawo kan Alhajin,tsaf sai ya haifi

Salma,sai t'sabar kud'i da jindadi da suka 6oye

shekarunshi.

Kallonshi yake tun daga sama har zuwa kafa, so

yake ya gano ta inda ya fishi har Salma ke mishi

murmushi haka. A zuciya yace

"Babu... Sai dai kud'i kawai da sa kaya masu

t'sada.

"Kai fa,daga ina ba koh sallama?..

Cike da haushi ya kallota, "baki sanarshi ko ni

waye ba ne?.. Kan Alhaji ya dawo,ba shakku

yace "matata ce ita,zaifi mana k'yau in ka daina

zuwa gunta Alhaji.

Murmushi yayi Alhajin,kan ya kallo Salman, "sai

kinji ni kawai.. A takaice ya k'alli Ja'afar din,ba

sai an fada mishi waye ba,halamu ya nuna

tsohon mijinta ne,har zaga wa tai ta rufe mishi

tana daga mishi hannu d'auke da murmushi, har

ya kule tana daga mishi hannu kan ta d'au

kayanta koh ta kanshi bata tai hanyar gida,da

zafin nama.

"Wato abinda ki ke kenan tun bayan tafiya ta

shine yasa ki ka kashe waya? Salma mey yasa

kike son ki 6ata min rai wai?.. Jibi fa shigar ki,ji

gashi a waje,wace iriyar rayuwa ki ka za6a

mana?

Cike da fada tace

"Wace iriyar ka za6arwa kanka dai Ja'afar.. Ya

zaka zo kana fad'an wata iriyar magana mijin da

zan aura?.. Karan nan bazan dau abinnan naka

ba wallahi, aure zamuyi dashi nan da wata biyu...

Sai kayi abinda zaka yi.

By

Feenat Ja'afar.

[8/7, 11:07 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

36_Kan yai k'wak'waran mot'si ta shiga gida tare

taru kofa harda sa sakata.

Jiginna tai hawaye na neman zubo mata,daga

yar bular dake jikin kofar ta leka waje,kofar gidan

yake kallo jiki a sanyaye kamar yasa kuka,juyawa

tayi hawayen dake makale mata ya zubo,dak'yar

ta seta kanta ta shiga ciki rai cike da tausayin

Ja'afar.

Kusan kullum zai zo ba zuciya dan bata baki

akan Alhaji tana mishi wulakanci,shi kam Alhajin

har dariya yake bashi wani sa'in, dan baijin da

abinda zai iya rabashi da Salma a dai dai lokacin

nan,sai dai jin saki uku ne kawai sai ya bar jin

komai,iyaka ma yai ta tusa ma Ja'afar din bakin

ciki in ya gansu da kalamai ma Salman.

Biki ya karato ga makaranta,amma haka duk

week end daga Zaria zai zo kan batun Salma ta

janye zancen bikin nan.

Duk ya fita a hayyacinshi duk akan auren Salma.

Da halamu ya fara hankalin daina zuwa gun

Alhajin,sai dai in yazo ya tsaya chan gefe sai

tazo shiga ya tare ta da magiya.

Yau saura k'wana biyu biki, sai gashi shi da

Garba,dawowarsu daga gidan g'yaran jiki kenan

ita da Ummi.

Turus ta ja ta t'saya ganin Ummi ta wuce ita ya

tare mata hanya.

"Ka ga yau bani da lokacin jin wannan

mahaukatan zantukan naka,jibi iyanzu na d'aura

aure, ya kamata kasan inda dare ya maka,

sabuwar rayuwa zan fara,saboda haka kai yanzu

ya rage ma,danni yanzu baka gabana...

Kai ya kad'a mata,

"Karan nan bazan hanaki aure ba Salma,sai dai

ba da Alhaji ba.

Baki sake take kallonshi, Garba ya nuna,

"Garba zaki aura Salma,kimin wannan alfarmar.

Kai ta dauke daga kallonshi ta k'alli Garban

wanda shima ya cika da al'ajabin kan maganar

Ja'afar.

Sai ta girgiza kai da murmushin takaici.

"Tanan kuma ka bullo min?.. Auren kisan wuta

Ja'afar? Lalle kayi nisa ba zakaji kira ba.

Bayab hannunta tasa tana goge hawayen idonta.

"Wai ka zata ni din auren kisan wuta zanyi da

wanda zan aura?.. Kai ta kara kadawa,

"Kai kuskure toh,dan ni aure zanyi na tsakani da

Allah,ba wai nayi na fito ba Ja'afar..

"A'a Salma,ba haka ne nufi na ba.. Da muryar

kuka ta tareshi,

"Hakane man,haka kake nufi,wato ka kawo min

abokin ka na aura bayan wani lokaci ya sake ni

sai ka halartawa kanka ni koh?..

Baki sake duk suke k'allonta,ganin yadda hawaye

ke zubar mata.

"Jahilcina bai kai nan ba Ja'afar, a bazan ta6a

abinda ka ke so ba, a gareni yanzu k'allon Yaya

nake ma,da kuma uban yarinyar dana haifa,

bayan haka.. Kai ta girgiza, kan tace "you mean

nothing to me a yanzu kam..

Jin baice komai ba yasa taci gaba.

"Banzaci haka daga gare ka ba Garba,a ganina in

shi ya 6ata kai mey dawo dashi kan hanya ne,

wallahi auren t'sakani da Allah zanyi, ku sani

kuma auren so zanyi,wanda nake fatan mutu ka

raba ne,dan Allah,dan kaunar ka da Allah ka bar

bibiyata,dan Allah..

Shiru tai dan ganin shima idonshi ya taru da

hawaye,da sauri ta shige gida tana goge

hawaye..

Har ta shige yana binta da ido ba magana, sai

hawayen da ya zubo mishi shar, da sauri yasa

hannu ya share.

Kafad'arshi Garba ya dafa, "kaji zancenta, tai

mana fassara baibai,ya kamata kai hakuri ka bar

kulata in har kana wa Allahn data had'a ka dashi.

Kai ya daga, "InshaAllah..

~~~~

Taro ne iya taro,taron shedar auren Salma da

Alhaji Usman, daga inda yake t'saye a chan nesa

da kofar gidan yana k'allon komai har aka shafa.

Juyawa yai da jaka biyu hannunshi tare da sanya

bakin glass dan 6oye sirrin dake idonshi.

Yasan yanzu kam Salma ta mishi nisa.

"Mama taki ta bud'e dakin fa,daga ina jiyo sautin

kukanta Allah.

Ta window Ummi ta leka,gata k'wance ta tasa

tsohuwar wayarta a akan fuska tana razgar kuka,

So ba karya bane Salma.

By

Feenat Ja'afar.

[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

37_Har aka kai amarya gidanta bata bar kuka

ba,dayawa sun zata kukan na Mama ta cire

Miemie ne, dan basa ji koh auren farkonta tayi

haka.

Kowa ya wat'se sai ita kad'ai, ko'ina take kallo a

dirare, gida ne iya gida,tun bata fita ba ta

zaga,yau gata a gidan da ba Ja'afar, ba kuma

Miemie,tuni ido ya cika da kwallar tuna baya.

Anya tai ma Ja'afar adalci kuwa?.. Anya bata ci

amanar so ba kuwa?.. Ta sani da takai Ja'afar

bango,hakan yasa bai kara waiwayarta ba,ta

yuwu yai zuciya... Ido ta goge da sauri jin motsin

za'a bud'e d'akin.

Ango ne yasha babbar bunjima da rike da leda,

bakin nan har kusan kunne,jan mayafinta ta kara

yi ta rufe fuska.

"Amarya! Amarya!!.. Ba k'ya laifi wai koh kin

kashe dan maigida koh?..

Murmushi ta k'akalo mishi, zama yayi a gefenta

tare da ajiye ledar a gefen bedside, bata aune ba

taji ya yaye mata g'yale yana kallon fuskarta.

Alwala yace ta d'auro suyi nafila,dan wai

agareshi babbar kyauta ce ita daga Rabba.

Sun gabatar da duk wani al'ada,sai dai har ango

ya d'ane gado amarya tana t'saye a gaban

madubi

sai sininiki take,gabanta sai mugun fad'uwa yake

tamkar wacce tai auren fari.

Murmushi yayi da kanshi ya taso ya karaso har

gaban madubin tare da kamo hannunta.

"Muje ki kwanta haka dare nayi sosai..

Kamar yarinya ya kwantar ta gefen shi yana kallo

da murmushi.

Salon ya sauya,tuni ta fara digar da hawaye,shi

kadai yake kid'anshi yana rawarshi,sai dan sautin

kukanta dake fita kad'an-kadan,wanda a gareshi

tamkar zigi take mishi.

Kai ta juya ta kallo Alhajin dake bacci

hankalinshi k'wance,abu uku sun hanata bacci,na

farko kukan zamanta ta wani ba Ja'afar ba,na

biyu tunawa da Miemie, na uku minsharin Alhaji..

Har gari ya waye bacci sai jefi-jefi-jefi ke

dibanta,sam taki jinin minshari kusa da ita,tsaf

yake hanata bacci.

Shikam da farin ciki ya tashi irin na sabbin

ango,ita kam da ido kawai take binshi.

Tara sai ga yaron uwargida ya kawo abinci,da

fara'a ya gaida ta,kanshi ta shafo kan tace ya

sunan shi?

"Sunana Ja'afar".... Kallonshi take da mamakin

jin sunanshi, koh dai bataji dakyau bane?...

Kat'seta yai da fad'in

"K'anwata kuma Nabila,Umman mu tace sai

anjima zamu shigo kar mu tashe ki a bacci.

Murmushi tai mishi yace ya tafi.. "Ja'afar...

Ido ta rint'se jin maigidan ya kira sunan,ba shiri

ta d'au abincin tai kitchen.

Bayan sun gama komai yace suje bangaren uwar

gida zai magana dasu.

Batai zatan da kishiyoyi masu kaunar kishiyar su

ta ra6e su sama da matar Alhaji ba,sosai tai

mata bazata,tun tana d'ari-d'ari har ta saki jiki da

ita da yaranta, musamman Ja'afar..

Yau Miemie ce tazo mata,sai murna take taga

Auntyn ta.

Duk babyn ta rame,yaye bai amsheta ba.

''Miemie, ga nan Abdul yazo ku tafi gun Mama

koh?...

Kafad'a ta make halamar taki tana neman kuka,

"Yi hakuri gobe zanje gida mu taho koh?..

Kuka ta saka mata baji ba gani, sai mak'e

kafad'a take tana ita "um-um.

Sai ta sallami Abdullahi kan gobe yazo ya d'auke

ta, har ya jima da tafiya Miemie bata bar kuka

ba.

Sai um-um kawai take fad'i, suna haka Alhaji ya

shigo,duk yai kicin-kicin da fuska, cikin fad'a-

fad'a yace ta lallasheta man,shi baison hayaniya

bare ta yaro...

Baki sake take kallonshi,kaya ya ajiye ya juya ya

fice harda dan tsakinshi,toh mey yake nufi?...

Y'arta ta d'auka ta sa6a a baya sukai kitchen

tana fad'in tai shiru ba inda zata toh,kan aje

ko'ina sai ga nan Miemie harda dariya tana bata

labarin Mama cikin gwaranci.

Har dare ba Alhaji ba duriyarshi,abinci ma sai

Ja'afar ya turo ya d'auka.

Suna k'wance Miemie sai k'allonta take,gani take

kamar guduwa zata yi ta barta.

Kanta ta shafo tana mata murmushi,

"Yi baccinki my Miemie, ina nan fa tare da ke

kinji?.

Kai ta daga mata tana k'allonta.

"Antee...

Kai ta dago kan tace

"Na'am Miemie nah...

"Abba...

Tsam tai tana k'allon Miemien,Abba? Ta nanata a

ranta.

Murmushin dole ta k'akalo tana fad'in Abba yana

nan Miemie,bata aune ba taji ta kara fad'in

Abba...

Hawayen da take makalewa ne suka zubo

mata,da halama yanzu Miemie ce matsalar

ta,dan zata dawo mata da hannun agogo baya.

Da dabara ta d'auke hankalinta daga tunanin

Abban ta hau lalla6ata har tai bacci.

Photocopyn Ja'afar ce Miemie,barin yanzu data

kara girma, tunani take koh dai Ja'afar har yanzu

baya zuwa gida, laifinta ya shafi Miemie?

Dan tasan sai Miemie ta kwana biyu bata ganshi

ba take nemanshi haka.

Tana nan har maigidan ya shigo,sai wani k'allo

yake aikama Miemie wanda ta kasa fassara shi.

Tun daga ranar ya zamana in dai Miemie zata

zo,toh fa zata rasa gane kan maigidan, ta rasa

dalili, musamman in tai la'akari da hadithn

hausawa na Duk mai son uwa toh yaso d'iyanta.

Ranar har ta kasa d'aurewa tai mishi magana,

amsar da ya bata ta jima tana sata hawaye.

Ga Miemie da kulafuci bare tace kar a sake kawo

ta,asalima duk randa tazo fara'arta karuwa take.

Sa6anin in tazo mata,data gane sai take d'akko

ta duk randa bata da girki su k'wana, ranar da

maigidan yake da ita su wuni ai rabuwar kuka

har uwar.

Allah yaga Miemie kadai take gani taji sanyi a

ranta.

Ranar suna fira a bangaren uwar gida take mata

korafi kan halin maigidan akan Miemie.

Murmushi tayi kamin tace

"Sai kinyi hakuri da halin Alhaji Salma,ba tone-

tone ba,a'a kawai dai ya kamata ki sani, Alhaji

sam baya son yara,musamman hayaniyar

su,hakan yasa ya d'aurawa kansa kin haihuwar

k'arfi da yaji, nayi ta zaman takaicin halin nan na

Alhaji har t'sawan shekara bakwai,a lokacin aka

tada kayar baya kan sai ya kara aure tunda ni

sun zuba ido shiru.

"Hanna ta shigo itama ta shekara biyu shiru, ni

dai nasan kusan kullum yakan tasa ni da Hanna

dan shan maganin daukan ciki.

Ana nan ranar wata kawar Hanna tazo suna

jajanta ko dai matsalar gun mijin ce,toh a ranar

dai asirin Alhaji ya tonu,dan kawar Hanna taga

magani tace na hana d'aukar ciki ne.

"Ranar muka mishi tawaye har Hanna,in takaice

miki yace shi bai shirya haihuwa ba yanzun,anan

sukai baram-baram da Hanna ya bata takardar

ta.

"Haka sauran mata biyun kowa tazo zai fad'a

mata ra'ayinshi, da taga bazata iya ba zata fice,

duk kuwa da tarin arzikin shi,a lokacin muna da

shekara kusan sha uku da aure,koh mai zaiyi na

daina shan magani, hakurina ya kare,nan na kai

kara gun Hajiyarshi.

"Ya saduda muka haifi Ja'afar, yace daga nan ta

isa haka,wai incigaba shan magani,a gabanshi

zanyi kamar nasha, daya kauce zan zubar.

Koh shekara Ja'afar bai ba na samu cikin

Nabila,cikin da a kullum sai naga tasku gun

Alhaji,gar da gar zai nuna bai kaunar su,barin in

Ja'afar na kuka,haka nai ta hakuri har na haifi

Nabila.

"Yanzu kam magani sai dai shi yai tasha,amma

banda ni,kinga Nabila har ta shiga shekara ta

biyar.

Tsam tai tana tunani bayan kammala bata labarin

waye Alhaji, ita ba kullen ne yafi damunta ba

sama da rashin son haihuwa..

A kalla yanzu ta doshi wata na biyar a gidan nan

amma ba bayani,sam bata kawo wani abin

ba,ashe wannan ne dalili?..

Bazata iya tuna ranar fitarta ta karshe a gidan

nan ba,tun kwa bayan aure sau daya taje gida sai

dai aukin waya koh azo mata, lalle duniya labari.

"Zaman hakuri kawai zamuyi Salma,sai adu'ar

shirya in da rabon zai gane, amma shawarata

gareki ki rike y'arki, dan kar kiyi sakiyar da babu

ruwa tun kina yarinyar ki dake,shi ba ruwanshi.

Kai ta kad'a mata,Allah sarki Ja'afar, ta tuno

lokacin data fara period tana kukan samun ciki

yana murna.

Ta tuno da abinda yace mata

"Allah sa Miemie ta samu k'ani a kusan nan...

Ta tuna data hau bori ya hau lallashinta,

harda alkawarin shi zai mata reno in bata shirya

ba...

"Ba kuka zakiyi ba Salma,muyi ta adu'a.

Hannu takai fuskarta, ashe kuka take bata sani

ba.

By

Feenat Ja'afar.

[8/7, 11:08 AM] Feenat Ja'afar: *A BAKIN

AURANKI*

*漏 Feenat Ja'afar*.

38_Ranar sakwa-sakwa ta yini tana tuna halin

Alhaji, bai da mugun hali koh daya sai na bakin

kulle da kin yara,bayan nan baza tace ga mugun

halinshi ba.

Zataso sanin wane hali Ja'afar yake ciki a

yanzu,dan tabbas tasan ya zuciya da ita,tunda

gashi ance koh wajen Miemie baya zuwa sai

aike?..

"Mey nai kenan?.. Mey nayi ni Salma?.. Mey yasa

ban iya jure zama ba aure ba a rayuwa kamar

yadda yaso muyi..mey yasa?..

Juyi tayi tana hawaye,

Kila rabon Miemie kadai take dashi a

duniya,tasan kuma aure dai ana yinshi ne dan

abu biyu,samun zuri'a na daga ciki, gashi ita

anan ana son a haramta mata.

Tabbas d'aukar y'arta shine babban mafita a

game da yadda take jin son ta haihuwa a yanzi..

Wayarta ce tai ruri, a hankali ta goge hawayenta

ta tashi,

"Billy" taga a rubuce.

Da sauri ta saita kanta kamin ta daga.

"Sarauniyar kirki kina gida ne?...

Dariya ta danyi kan tace tana nan..

"Toh ina kofar gidan ki yanzu haka.

Da sauri ta tashi dan g'yara fuska tana fadin gata

nan zuwa.

Sai da ta tabbatar da ba mai gane tai kuka kamin

ta fita kofa shigo da Billy.

"Matar nan kinganki kuwa?.. Kin zama big

madam da gaske fa.

Murmushi tayi tana kar6an Ilham.

"Kai Billy banda fa sharri..

Dariya tai tana "ba wani sharri, koh dai mun

karu?.. Miemie tayi k'ani?

Shiru tayi tana murmushin iya le6e.

Bayan sun gaisa take ce mata ai daga wajen

Miemie suke,tai ta kukan zata zo tana jin tace

gun Auntyn ta zata.

Murmushi tai tai kasa da kai,Allah sarki Mimi.

"Yau Miemie aka kaima ziyara kenan?.. Murmushi

Billy tai kan tace "ai duk sati sau biyu Abban

Ahmad (Garba) ke zuwa dan dubo ma Abban

Miemie lafiyarta.

"Shine yau muka je tare,Miemie akwai

wayo,kusan wata shida amma bata manta

Abbanta ba,tana jin muryarshi a waya ta fara

murna..

Shiru tai tana nazari,ba dai ace tun tafiyar

Ja'afar ya zuciya ya bar garin nan ba?..

"Ja'afar kanar wasa,kinga wata shida muke nema

yaki waiwayo mu,sai kulafucin a dubo mishi

gudan jininshi... "Rayuwa kenan fa,kana naka

Allah na nashi,in kai hakuri sai ka ga na Allahn

ne dai dai a gare ka.

"Amma Abban Miemie namijin duniya ne,mai

ra'ayin kanshi,tunda ya jima haka nasan alhinin

aurenki ne bai sake shi ba.

Shiru tai tana jinta,a hankali ta fara jin nadamar

wulakancin data kartawa Ja'afar, Abban y'arta.

Yau Billy ta kawo fitina,dan har ta tafi bata da

sukuni,har sai da ta tiki kuka son ranta taji

dad'i,yanzu burinta Miemien ta dawo gare ta.

Koh da maigidan yazo yaga yanayinta yasan

tasha kuka,da ya tambaye ta sai tace Miemie

take son gani ta d'akko ta.

Anan ya tada mata bori,har sai da tai da na sanin

maganar Miemie.

Ba abinda yafi kona mata rai sama da yadda

tanaji tana gani yai mata haramiyar

makaranta,sannan Mama ta goya mishi baya,abu

goma da ashirin sun had'e mata.

Adaddafe akai shekara, lokacin tuni ta jima da

d'akko y'arta,dan bazata iya da rashinta ba a irin

yanayin da take na son yaran nan.

Sai sai wani abu,fur Miemie taki jinin Alhaji, ko

abu take in zai kwan dubu yana ta bari bazata

koh k'alleshi ba,asalima har wani kumbura baki

take in ta ganshi,Salma tai magana tasa mata

kuka,ga bala'in Alhaji na wai yarinya tun kan ta

girma ta rainashi shi da gidanshi, har harara wai

take mishi...

A tunaninta kamar Miemie wane harara ta sani

bare wai kumbura mishi baki?.. Amma dan a

zauna lafiya yasa kullum take kwa6ar ta.

A gaban kowa har su Nabila zatai wasa harda

k'yak'yatawa, amma fa koh a nan bangaren taci

ka'ro da Alhaji zata d'unkume,tamkar ba ita

ba,shima kwa da harara zai bita, wani sa'in harda

t'saki..

By

Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:33 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

39_"Aunty A'i na rasa yadda zanyi ne,yadda yake

nuna t'sanar Miemie karara yafi damuna,abu

kadan tayi sai ya hantara,t'sawa, ga kullum yai

ta surutun wai tana hararar shi,koh fa wai turo

mishi baki,nawa take fisabilillahi?... "Allah bansan

haka agolanci yake sai gun Miemie. Murmushi

tayi "bari muga,ke dai sa ido... ta kallo Miemie

dake chan gefe tana mota da motar wasa. Da

k'arfi Aunty A'in tace "ke Miemie... Rai had'e,

itama ta dago tare da 6ata rai tana kumbura ma

Aunty A'in baki. Sai Aunty A'in tai mata

murmushi tare da mika mata hannu, "zo Miemie

naga kitso, waya miki?.. Kafad'a ta make

halamar bazata zo ba kenan. Cikin wasa Aunty

A'in tace "haba Miemie ta,zo zan baki sweet fa..

Da sauri ta taso har tana dariya ta d'are ta tana

kiran sweet. Baki sake Salma take k'allonta,Allah

yaga banda yau ta gani da idonta bazata yarda

Miemie zatai haka ba. Gira ta daga ma Salman

halamar ta gani ai. Miemien na fita tace "Ikon

Allah Aunty A'i, ashe dai gaske ne Miemie na

mishi hakan. Kai ta kad'a, ''amma in ya mata irin

yadda na mata,kila koh wasa take yana mata

ne,yaro kamar Miemie dan lallabi ne,shi yasa tun

farko banso kin karbi yarinyar nan ba

Salma,gudun irin matsalar nan.. Ba magiyar da

Abbanta bai min ba shima a waya kan baison

ya'rshi ta zama agola, Gashi in bakiyi wasa ba

shi kenan ta gama raina miki miji. Cike da

damuwa tace "Nikam ta rufan asiri karta kashen

aure Allah.. Dariya Aunty A'i tayi,lalle ma

Salma,wai karta kashe mata aure? "Haba dai ke

kuma,sai kace wata babba,kawai dai ita tata

salon fad'an ne haka,amma zata daina. Ajiyar

zuciya ta sau,kan tace "Bazaki gane ba Aunty

A'i,wallahi in Abban su Nabila zai kwana yana

cewa Miemie bari koh kallonshi bata yi,wannan

nasan tana dashi,shi kuma sai ya kule,baya duba

yarintarta,sai ma ki ga ya hauni da sababi. "Toh

ki dinga sata misali kai mishi abu haka,kina kuma

kula d yanayinta in yana mata magana,sai kina

sata a hanya. Har magriba suna abu

daya,matsalar gida Alhaji har ta tafi. Washegari a

ita ke da shi,tun wuri ta shirya Miemie ta d'auke

duk kayan 6arna duk dan a zauna lafiya.

Chankula chankoto take mata tana dariya,ta

sunkuya tana mata "aci ladan gabe" tana dan

mata duka yai sallama. Kallo daya ya musu ya

d'auke kai, dagowa Miemie tayi,in ba idonta ke

mata gezau ba kamar harara ma ta mishi,tuni ta

gintse fuska ta daina dariya. Ya salam, Miemie

tai nisa a tsanar Abban su Nabila. Yake tai kan

ta tashi dan binshi d'aki, "Miemie tashi muje gun

Abba koh?... Kafad'a ta mak'e tana turo baki, sai

tai kamar bata gani ba ta kinkime ta,a ranta tana

fad'in "sai nayi da gaske a kanki Miemie. Ihu ta

fara tana zazzamewa,a dole ita bazata je ba,jin

suna iyowa dakin yasa da sauri yace "Kar ki

shigo min kina min wannan kukan dama.. Chak

ta tsaya tare sauke ta,kafadar ta kara makewa

tana kallon Salman,sai ma ta fita tayi bangaren

su Ja'afar. Kai ta dafe tana mai mamaki ita

kam,Miemie,toh mey take so da ita?. *DAN

KUKA...* ************************** Dube yake

zai k'alli news amma baiga d'ayan remote ba, ga

Salman ta shiga wanka, Kamar ance diba hannun

Miemie dake chan gefen corridor tana wasa sai

ga shi kuwa,yau shine motar ta ma. Da zafin

nama ya tashi ya nufi gunta.. "Jiyinnnn" take

dashi cikin tsawa yace "Wannan ne abin yin

motar?.. Dagowa tai tana t'sareshi da ido cikin

had'e rai, "Bani nan ni labarai zai wuce ni

sarauniyar 6arna. Kafad'a ta mak'e mishi tare da

yi da remote din bayanta tana zunguro mishi da

baki. Cikin zafin nama ya dagota, dai-dai fitowar

Salma dan jin fad'anshi, binta yake daga zaunen

tana matsawa taki bashi,kawai sai ya fizgota da

niyar kwata ta tun karfi, kai cikin fushi ta kwada

remote din a kasa tana kuma mishi ihun kukan ya

hanata wasa.. Dagashi har Salman suka bi

remote din da kallo wanda kowanne part yai

nashi gun battery ya cire. Da sauri Salman ta

karaso ta kwada mata mari,sauke ta yai kasa

yana sababin ai wai ita tasa ta raina mutane yai

waje,k'allon da baiyi ba kenan ya fice. Harara ta

kwada mata kan ta kamo kunnenta ta murde

tana kuka, "Baki isa ki chazan matsala ba ja'irar

nan,wato bakin hali ki ke son kowa koh?. Kashen

aure zakiyi ne?.. Kullum baza'a aji kanmu da

mijina ba sai akanki?.. Cikata tai tare da dan

rangwashenta, "Toh baki isa ba,dole kizo ki koma

gurin Mama koh dangin Abbanki da zama... Bata

karasa ba Miemie ta fad'i tana burburwar fad'in

taki,ita bazata ba. Ido kawai ta sa mata,kan tai

kwafa tai d'aki,da gudu itama ta bita tana kukan

bazata ba Salman ta rufe kofarta ta batta da

bugun "Antee,Antee bata cho. Anan tai ta

mitarta tanaji daga dakin tana "Ai sai kinje...

Tuni ta kara jiniya, kuka harda shudewa amma

tai burus da ita tana kwalliyarta. Zuwa chan taji

shiru,sai tai murmushi, Miemie matsala. Fito wa

tai dan ganin koh fita tayi,sai ta ganta kwance

bakin kofa sai sauke ajiyar zuciya take tai bacci.

Sunkuyawa tai ta leka,ido har ya kumbura, duk

sai ta bata tausayi,batasan lokacin da ta d'akko

abarta ba,batajin tunda Miemie take ta ta6a

dukanta haka tai kuka. Kwantar ta tai a gado

tana goge mata fuska da tissue,baki ta kai

fuskarta, "am sorry kinji... kamar ta sa kukan

itama,Miemie taurin kai toh,Alhaji hancini,ya

suke so tayi da ranta ne? By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:34 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

40_Washegari bayan la'asar tace mishi zata

maida Miemie gidan Mama dan Allah ya batta

taje daga nan sai tai barkar Ummi data haihu

cikin dare. Da har zai hana,ganin kayan Miemie a

akwati yasa bai gardama ba ya batta,kwarai

tasha mamaki,dan rabonta da fita har ta

manta,amma dake wacce bai kauna za'a mayar

ya batta. "Ga driver in kin gama ya kaiku,kar

kuma ki dad'e.. Kai ta daga tace ta gode.

Rayuwa kenan,da ya batta ma taji dad'i,koh ba

komai zata leka gida yau. Gidan Ummi suka fara

zuwa,sai ta6e baki take tana korafin yadda ta

zama matar k'ulle. "Aure sama da shekara

wannan ne zuwanki na biyu gidana,wannan wace

iriyar rayuwa ce,mutum sai shegen kullen t'siya..

Tana jinta tai shiru,tana tunanin hali irin na dan

Adam,mai wuyar gane hali,lokacin Ja'afar mai

barinta fita haka ta gurza,yanzu kuma ta had'u

da dai dai kowa,ga kud'i ga cima, amma ba fita

ba haihuwa.. Zaman lafiya wai yafi zama Dan

Sarki. Ita kanta Miemie murna take sun fita

yau,sai dai suna zuwa gidan Mama taji Salman

na maganar zamanta ta d'ane cinyarta ta riketa

tam. Ban6are ta Mama take ajikinta tana ihun

kiran Aunty,ita kuka Salma kuka, ga magriba ta

sawo kai. Suna haka Abba ya shigo, duk ta rike

gyalen Salma kam tana ihu. Dak'yar ta fizge tai

hanyar fita da gudu tana kuka. "Subhanallah... Ta

shid'e fa wannan... Chak ta tsaya jin daina kuka

Miemien,da sauri ta juyo taga Abba na jijjiga ta.

Ba shiri tai gun dai dai Miemien ta kawo wuta ta

kar6e ta. Kuka na fitar hankali take tana bata

hakuri, ''Ni bansan mey yarinyar nan zata tsare

miki ba in ta zauna achan gunki ba,kullum sai da

kuka koh jinya za'a rabu?.. Ki bar y'arki a kusa

dake man tunda ita mai kulafuci ce... Kai ta

daga tana share ma Miemien hawaye tana tai

shiru toh.. Dole tana ji tana gani ta koma da

Miemie, dan yau fir taki yadda tunda ta d'andana

zama da ita. Kanta take shafawa,ita kam ta

tasata gaba tana ta kallo ba koh kiftawa. A

hankali tace "Miemie.. Idonta a kan Salman tace

"Uhmm. Kwanto wa tai a gefenta tana g'yara

mata kwanciya, kamar wata babba ta fara mata

fad'an ta zama mai ji dan Allah. "Ban san

matsala Miemie, ki rufan asiri ki daina halin nan

naki na kumbura ma mijina baki,kinji?.. Kai ta

daga mata kamar gaske. Sai tai murmushi tai

kan tace ta taso suje suyi girki a kitchen. Shikam

Alhaji da murnar yau Miemie ta tafi ya shigo

gida,shi kanshi ya rasa mey yarinyar ta tsare

mishi a gidan,duba ga su Ja'afar na gidan. Sai

dai tun daga bud'e kofar parlourn farin cikin ya

kau. Dariyar Miemie ya fara cin karo yana

shigowa ta kitchen,dan haka da sababi ya isa.

"Mey ya zaunarki har bayan magriba baki dawo

ba?... Mey kuma ya dawo da wannan? Duk ido

suka zuba mishi,mai hali kuwa Miemie tuni ta

chunno baki gaba tana mishi wani irin kallo jin ya

fara sababin nashi. "Wallahi har kusan suma tayi

dan kuka yau,tausayi ta bani shine na dawo da

ita,kai hakuri duk ita tasa muka kai magriba.

K'allon Miemien yayi da kamar harara kamin ya

kad'a kai dan takaici ya fice. Ajiyar zuciya ta

saka,ta tsalake rijiya da baya da k'yar,kan ta

dawo kan Miemie ita tuni har ta cigaba da

sabgarta. Sai dai ana zuwa kwanciya yace daga

yau Miemie zata bar kwana dakin su,koh ta koma

kasa. Ya ta iya,dan a zauna lafiya ta sauke

Miemie kasan,dan ba yadda za ai ta luluka

yarinya chan wani waje ita tana wata jahar,a

ganintq Miemie nawa take. ******* Fur yanzu ta

daina ganin fuska gun Alhaji, in ya shigo ba

wanda ya isheshi kallo,asalima ya daina zama

bangarenta sai cin abinci koh bacci. Yau dai ta

d'au damarar fara koyawa Miemie sabo da Alhaji.

"Abba ki ne kinji Miemie nah?.. Ki dinga mishi

oyoyo kina mishi dariya kinji?, banda

harara,banda turo baki,kina ji na? Shiru tai tana

binta da kallo kawai,chan sai ta yak'e mata

hakori. Cikin farin ciki Salman tace "yauwa,koh

ke fa,be a good girl ba? kai ta daga mata tana

dariya. Alhaji yai wanka ya shirya yaje parlour

yana duba abu a system nashi su kuma suna

daki gun shirya Miemie. Daga parlourn ya kwada

ma Salma kira wai ta fito mishi da agogon shi na

kan mirrior. Murmushi tai ta k'alli Miemie,tasha

parking da ribbon sanye da gown ja da baka iya

g'wiwa, dake fara ce sai tai mata k'yau sosai.

Agogon ta d'akko ta kamo hannun Miemie, "Kai

ma Abba a maza yana parlour,ki nutsu dan Allah

kinji Miemie nah.. Kai ta daga tana dariya ta

karbi agogo tai parlour. Bayanta ta biyo dan

ganin ya zata kaya, daga yau ne zata fara koya

musu kusanci da juna shi da Miemie. A dunkume

ta isa gunshi yana duba abu a laptop, mika mishi

tayi ba koh magana, sai ya dago ganin itace,tai

mishi kyau sosai,ga sai kamshi take,ba abinda ta

bari na babanta a ganin shi har dacin ran,in baxai

manta ba yanzu ne zata shiga shekara uku,amma

duk ta tara dacin rai wai da fitsara. Kai ya

d'auke ya cigaba da abinda yake, Salma har ta

fara murna ganin bai mata dan halin ba yau. Ita

kwa Miemie sai ta ajiye agogo kan hannun kujera

ta juya tsautsayi agogo ya fad'o kasan tiles sai

glass din ya fashe. Da azama ya juya,ganin

agogon akasa a fashe Miemie ta juya ta mike ya

fara sababi. "Duk wani mugun hali irin na ubanta

yarinyar nan ta iya,agogon nawa zaki saka da

gangan ki fasa min?.. Waje Salma ta fito ganin

ya yo kan Miemien a sukwane, duk tana k'allon

abinda ya faru. Kumatun Miemien ya ja tare da

kai mata rangwashi akai yana sababi,tuni ta hau

kuka jin zafin abin,da sauri Salman ta karaso dan

bashi hakuri. "Shegiyar yarinya kawai,kin san

kud'in agogon da kika fasa kuwa?.. Ja Salman tai

ta tsaya tare da rintse ido. Ga ihun Miemie tana

kiran Aunty,ga sai zagin y'arta yake harda

sheganta mata ita? "Alhaji.. Cikin fusata ta kira

shi tare da bud'e, Rai 6ace shima ya dago da

niyar huce haushin shi kanta ta rigashi. "A

gaskiya ka daina sheganta min yarinya, dan da

ubanta gaskiya,haka kawai, ina fa kallo tana mika

maka ka d'auke kai,ta ajiye ya fad'o kasa,toh

meye lefinta aciki har irin wannan zagi?.. A'a toh

gaskiya... Kai ta kawar ranta 6ace. Cika Miemien

yayi yana kallonta, wannan ne karo na farko da

ya fara ganin fitsarar Salma,shi zatai wa tsawa

akan Miemie? By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:37 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 41_Da

gudu ta karasa tana kama hannun

Salman,d'aukarta tayi a ta sa6a a baya, "Yi shiru

kinji.. Muje daki... "Kar ki kuskura ki shigar min

d'aki da wannan yarinyar.. Chak taja ta tsaya

tare da juyowa tana kallonshi. "Kema kar ki

shigar min d'aki,ni zakiyi wa rashin mutunci kan

y'arki?.. Toh baki isa ba,dan ba ayi macen da ta

isa daga min murya ba ki sani. Cikin karfin hali

tace "Toh mey ka ke nufi da hakan?.. Daga fad'in

gaskiya?.. Haba Alhaji,Kullum ina fuskantar

yadda ka ke tsagwamar yarinyar nan,shi yasa

sam bata shiri da kai ai... "Ba wani nan,bakin

halin yarki dai irin na tsohon mijinki dai,da kuma

shegen taurin kanta irin nashi,koh kin zata na

manta da waye shi zamanin neman aurenki? Da

sauri ta tare mai numfashi harda sauke Miemie

kasa da sauri, "Ba ruwan Ja'afar cikin maganar

nan tamu,zai fi kyau in ka daina sakoshi

ciki..kuma na fad'a maka y'ata bata da wani

mugun hali,sai dai naka mugun halin rashin son

yara, da kuma.. Shiru tai tare da ja da baya ganin

ya zaburo kanta, "wallahi kar ma ka soma,dan ba

yadda za ai in zuba ido kullum kana aibanta min

yarinya wallahi, nawa Miemie take? Amma k'arfi

da yaji so ake ta iya dan hali.. "Salma ni nake

fad'a kina fad'a?.. Ashe baki da mutunci?.. Kai

ta kad'a tare da juyar da kai, "Nikwa nake da

mutunci tunda a cikin gidan ubana ka auro ni

kuma... "Subhanallah,haba ku k'wa.. Juyawa tayi

taga Maman su Nabila na shigowa dakin. "Tun

ina shanya nake jiyo ihun Miemie da naku,bai

dace ba Allah,kuna abu a gaban yarinya.. "Ba

ruwanki cikin zancen nan,in ba so ki ke ya taso

da kwantaccen naki ba ke ma.. Shiru taja

bakinta tayi tuni idonta ya fara zubar da kwalla,

ya cigaba "Yara nawa ma basa gabana bare ta

wani, saboda haka akan yaro ba mai sani ciwan

hawan jini,dole yau ki mayarta gun ubanta,koh ki

san nayi da ita. Cikin kuka tace "Bazan iya

rabuwa da y'ata ba,kai hakuri raina ne ya 6aci..

Malalacin murmushi yayi,kan yace "Daga baya

kenan,amma dole ki za6a zaman dani koh da

yarinyar ki... Maman Ja'afar ta kallo da itama ke

hawaye tana kallonta,sai ta cije le6e da takaici.

Juyawa tayi ta d'au Miemie, kan ta kalloshi ido

na fidda kwalla. "Ni kam na kasance daga masu

taya annabinmu kishin Al'ummar shi,dan haka ina

son haihuwa,bi ma'ana zan iya rayuwa da Miemie

kad'ai mud'in Annabin mu zai alfahari dani...

Cikin zafin rai yace "Kimin hausar da zan gane

Malama ni.. "Annabinmu yace kuyi aure dan ku

hayaiyafa,domin go6e kiyama nai alfahari daku..

Kayi aure,amma baka fatan tara zuri'a, hakan

yana nufin kana tarjiya a bisa umarnin manzon

Allah.. A tunzure yai yo kanta, "Kimin shiru

fitsararriyar kawai,koh yayarki bata isa ja ina ja

ba wallahi, dole ne yau ki za6i d'aya.. Cigaba tai

da batun ta ido rufe, "Nai ma biyayya ta t'sawan

shekara guda ina bin yadda kaso,toh ka sani ni

Sunnah na dauki aurena,kuma zan cikashi ne ta

hanyar tara zuri'a, dan zanyi alfarhari idan na

kasance a daya daga wanda Annabi zai alfari da

ita... Mari ya de6eta dashi jiki na 6ari,da sauri ta

dafe gun tare da bud'e ido,kuka Miemie tasa

ganin an daki Auntyn ta, "Mutuniyar banza

kawai,ni zaki mayar jahili?.. Murmushi tayi kan ta

kad'a kai. "A'a,dan kuwa kafi jahili,danshi dama

bai sani ba bare take,kai kuwa ka sani amma

kana taya shedan rawa,dan baka kaunar.. Shiru

tayi ganin zai kara mata wani,da sauri ta rintse

ido tana hawaye,jin shiru bataji saukar mari ba

yasa ta bud'e ido. Hannunshi rike a hannun

Maman su Ja'afar, "Lalle lokaci yayi da ya

kamata in tanka maka Alhaji,lokaci yayi da zan

daina bin umarnin ka ina 6ata.. Ashe har alfahari

ka ke cewar yaranka ma basa gabanka?.. Jiran

amsa take tana kallonshi, da borin kunya yace

"Cika min hannu... Ba musu ta cika, Salma ya

nuno "Ke kuma ki tafi gidan ku,na sake ki saki

daya,na koyan hankali,in kin koyo kofa a bud'e

take ki dawo.. Ido ta rintse gabanta na fad'uwa,

wai ya saketa?.. Daga fad'in gaskiya. Kan

Maman su Ja'afar ya dawo, "Wato zuwan

fitsararriyar yarinyar nan ta sa kin fara sauya hali

Halima koh.. Kai ta daga da sauri.. "Kwarai

kwa,dan yanzu na gane kuskuren dana tafka a

zaman baya da nayi da kai, nima ina son zuri'a,

ina son su Ja'afar sama da komai yanzu,kuma

zanso wanda duk yake son su,zan kuma yi fad'a

da duk mai kinsu, aciki kuwa harda kai usman...

Baki ya saka yana mata k'allon mamaki

"Usman?.. Babbar magana.. Halima yau ke kike

kama sunana ba ma Abban Ja'afar bare Alhaji?..

Shiru tayi tana kallonshi,sai sababi yake daga

karshe itama yace taje sai ya nemeta. T'saki

sukai mai lokaci daya ita da Salma,duk da kallo

ya bisu Salma tai d'aki. "Ai nima ka sallame ni

kawai,dan bazan zauna da mutumin dake

kyankyamin zuri'a ba,dole yau na barka,Allah ya

yafen baya,amma yanzu kam ta kau,ka sake ni

nima kawai... "Bazan saki ba,amma dole ki fuce

min a gida,dan ba mai sa min hawan jini... Kuka

Salman take tana jiyo sababin da Alhajin ke yi..

Hannu Miemie ta kai tana girgiza mata kai itama

tana kukan,gaba daya ta rungumo y'arta tana

kuka mai cin rai,ita kuma haka Allah yayi ta

marar sa'a a zaman aure,gashi yau a dalilinta

auren shekara sama da ashirin na neman

tsinkewa bayan ta t'sinke nata. By Feenat

Ja'afar.

9/29/16, 9:39 AM - Queen Safiyyert馃憫: *A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

42_Jugum Abba yai bayan jin bayanin Aunty

A'i,ita dai Salma sai kuka take,dan tasan yau

kam sai ta Allah,fad'a kam sai dai ta toshe

kunnenta. Amma da mamakinta sai ji tai ya

sauke ajiyar zuciya tare da fadin "Allah ya

kyauta toh,dama tun farko ni mutumin nan ba

wai ya mun ba ne. "Yadda naga kowa na yinshi a

gidan musamman Babar taku yasa nabi yarima

nasha kid'a, sai fatan Allah yasa haka shi yafi

alkairi.. Mama ce ta riga kowa saurin fad'in

"Amin,ni nasan naso shi,amma daga baya sam

mutumin ya fice min akai,dan daga gani ba wai

zaiyi wani mutunci bane,ga dankaran kulle,yanzu

kuma an kara da rashin son haihuwa.. Dame

yarinya zata ji?.. Kallon mamaki suke ma Maman

musamman Salma, yau mama ke fad'in aibun

Alhaji da bakinta?... Lalle abu ya 6aci. Da dare

suna kwance ta tasa Miemie a gaba tana

kallo,itama ido ta sa mata, tunaninta zancenta ya

tabbata. A dalilin Miemie aure ya 6alle..

Murmushi tai kan ta gyara kwanciya. "Miemie..

Kai ta daga tare da fad'in "Uhmm.. Sai ta

mirgino kusanta tai rub da ciki "Kina murna

kuwa?.. Baki ta yage mata ba dan ta fahimci

nufin Auntyn ba. Sai ta kad'a kai,ta rasa wane

irin nishad'i ke shigarta da yamman nan zuwa

daren yanzu.. "A k'ya kam yi murna,wato kin

rabu da alakakai koh? Kai ta daga mata tana

dariya.. Itama tana dariya ta fara mata chakulkuli

su na k'yak'yata dariya har su Abba dake waje

suna jiyo su. Mama ya kallo,itama shi take kallo,

"kina jin mutananki koh?.. Kamar yau take

Sallah.. Murmushi tai tana sadda kai kasa, sai ya

girgiza kai yana tuna wani abu. ****** Tun daga

wannan lokacin hankalinta ya koma kan

makaranta, babban bakin cikinta bai wuce yadda

Alhaji yai burus da maganarta ba,a ganinta in har

da mutunci koh Abbanta ya samu da zancen..

Gashi a kalla yanzu ta kusa cinye kwanakin iddar

ta. Duk suna waya da Maman su Nabila tace

yana zuwar musu,sai dai ita baya samun ganinta.

"Aunty!.. Aunty!!.. Da dan gudunta ta shigo gidan

tana k'wada mata kira rike da leda tana ja,bakin

nan har kusan kunnen Miemie. Kamar a mafarki

taji kira ana ta6ata,a hankali ta bud'e ido dan

bata jima ba da bacci ya debeta sakamakon

ciwan period da take. "Uhmm Miemie.. Ya akai?..

Ledar hannunta ta hau bud'e mata tana mata

magana duk a hard'e dan murna. Riguna ne y'an

kanti masu kyau da tsada da takalma, sai teddy

guda biyu da y'ar tsana mai feeder a baki. A

zabure ta mike tana duben Miemien,tasan ba mai

irin ma wa y'arta tsarabar nan sai Abbanta,yawu

ta had'iye kamin tace "Miemie,ina kika samo

kaya haka?.. Dagowa tayi kamin tace "Abba ne...

Tsam tai tana kallon irin farin cikin da Miemien

take,wato in zai shekara bata ganshi ba tasan

Abbanta. K'allota tayi tana mata yake ganin

yadda take cire feedern a bakin y'ar t'sanar tana

fad'in Inya.. Inya. Da sauri ta tashi tare da zarar

gyale tai waje. A kalla zataso ganinshi koh dan

ganin yadda yake a t'sawan shekara guda da

d'auri. Sai dai har ta gama leke bata koh hango

mai kamar Ja'afar fa sai sawun mota. Zaure ta

koma tana lumshe ido tare da dafe kirjinta. Babu

makawa Ja'afar ya shigo zauren nan.. Dan ga

nan kamshin turarenshi ciki tana iya shakarshi.

Jiki a sanyaye ta juya ta koma cikin gida, a chan

d'akin Mama ta jiyo karad'in Miemie na ba ma

maman labari tana dariya. Da murmushi ta samu

ta dan dosana tana kallonsu kamar ta sa kuka.

"Na fuskanci yarinyar nan in dai tai arangma da

Abbanta tana kwanan murna, haka kwanaki

dak'yar na ban6areta jikinshi ashe bata manta shi

ba tana kuka,shima harda y'ar kwalarshi yana

daga mata hannu... Ido ta kurawa Maman ba koh

kiftawa.. Ba dai Mama na nufin Ja'afar yana

zuwa garin nan ba kuma har gidan nan?... Mama

ce ta kat'se mata tunani da fad'in "Ban tunanin

yaron nan koh a hanya ya ganni zai gaidani ba

sam bayan aurenki, duba ga yadda na rika mishi

fatattakar arziki.. Zuwan shi biyu gidan nan ashe

makaranta ya koma kinji.. Murmushi tai Maman

da iyakar shi le6e tare da daga kai. Tuni ta

zurfafa tunani,har bata jin mey Mama da Miemie

ke fad'a,kan ta farga har idonta ya cika da

kwalla,da sauri ta juyar da kai tare da goge wa

kamin su gani. Sakkowa tai tana taya Miemie

rad'awa teddy suna suna dariya. Kallonsu kawai

Mama take tana wani tunani, kai ta kad'a kamin

ta tashi ta basu gu dan tasan Abba yana gaf da

zuwa. Washegari da yamma tana kokarin shiga

wanka akai mata sallama. Hijab ta zira harda

shafa powder da zumudin Ja'afar ne ma,kila ya

samu labarin tana gida. Turus tayi tare da

chunno baki kamar Miemie ganin Alhaji da

abokinshi. Baki ya washe mata yana fad'in ta

karaso man kusa... Murmushin mugunta tai kan

ta kalloshi "Dan bani minti biyar na fito a gida...

Kai ya daga yana mata murmushi, ashe bazai yi

wahalar shawo kan Salma ba kamar Halima.

Ruwan da ta zuba na wanka ta d'auka da wani a

buta dan tsarkake kai in tai wankan t'sarki. Tana

yi tana murmushi har ta gama. D'aki ta shiga ta

tsane kanta da towel kan ta dan shirya a

gaggauce ta fita. Yadda take murmushi ne yasa

Mama tambayar waye yazo, a tunaninta koh

Ja'afar ne,tana cewa Alhaji ne ta 6ata rai. "Ki dai

kama kanki ki saiwa kanki mutunci,dan sam

mutumin ba nagari bane,kinjini ai? Kai ta kad'a

tana murmushi, lalle Mama, yau Alhajin guda?..

Sai ta kad'a kai, "adu'a bata fad'uwa kasa banza.

Bayan sun gaisa yake zungurar abokin nashi

sarkin iya t'sari, duk tana jinsu tana murmushi

dan feleke harda tambayar Miemie,sai da suka

gama tass tana jinsu tana kad'a kai. "Ai yanzu na

fita sahun matarka Alhaji,sai dai kabi sahun

zawarawa na..dan nayi iddah ni... Fuska ya

g'imtse yana kallonta, "haba kar muyi haka dake

man,ina fa lissafi,yau watanki biyu da kwana uku

rabonki da gida na, kinga ai bakiyi wata uku bare

ace kinyi iddah koh ba haka ba abokina? Kai ya

jijjiga yana fad'in "kwarai kuwa,dan haka muka

sani a al'adan ce. Kai ta kad'a tana murmushin

takaici, wato ga babyn roba,a hular a lokacin da

akaso a d'auka a randa aka ga dama.. 6aro-6aro

tai mishi dalla-dalla kan ita ai duk bayan sati uku

take period, kuma ya sani sai dai ya take. A fafur

yace shi baisan zance ba,kawai ya maida ta

dakinta. Juyawa tai ta koma gida,tana ji sai

kwad'a mata kira yake tai mishi banza. Da farin

ciki ta shiga har baya misaltuwa, dan da yanzu

dabarar yin wanka ba tazo mata ba da tuni

ansha da ita an gama. "Ba dai ya maidaki ba

naga kina murna tun yanzu Salma?.. Yanzu ke

bazakiyi kishin kanki ba har kin bada kai daga

fita bori ya hau?.. Ina laifin ya samo Abbanki da

maganar in dai da mutunci aciki... "Au dariya ma

na baki koh Salma?.. Ga shash.. "Mama ni fa ba

aure a t'sakanin mu da Alhaji yanzu,dan tau nai

iddah ta.... Baki sake take kallonta,dariya tasa ta

bata labari,sai ga Mama na tikar dariya. "Lalle

yarinyar nan da wayo ki ke,kwarai kinyi dabara,

dan sam mutumin ya sane min, dan ban fad'a

miki bane,ba'a fi sati da dawowarki gida ba muka

had'u da dan talikinnan,d'auke kai yai kamar bai

ganni ba fa,bayan sarai mun had'a ido.. "Shi yasa

yaron nan Ja'afar nake ganin kimarshi har

kullum,dan koh bayan rabuwarku yana daraja

mu,musamman zai sa azo har gida abokinshi yai

mana goma ta arziki in sun d'au Miemie... Shiru

tayi tana sauraran maganar Mama, wai Ja'afar

take ma ya6o haka da kirari?.. Farin cikinta a yau

bai misaltuwa,ina Miemie na nan ta rad'a mata

itama suyi tare,tasan dai duk inda take yanzu

tana neman gida,dan tun dazu tai mata kwalliya

da kayan Abbanta kaninshi yazo ya d'auke ta.

Murmushi tai tana jijjiga kai. Lalle ne *Duniya

Labari ce* By Feenat Ja'afar. feenat-jafar.my

wapblog.com

Feenat Jaafar's Mobile Blog

feenat-jafar.mywapblog.com

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 9

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

43_Waya yake d'annawa a nitse yana duba sakon

waya kamar bayaso,kamili ne,da hasken

shi,sajenshi a yanzu shine sirrin 6oye kyanshi na

ainashi, sanye cikin kananan kaya da glass

manne a idonshi,da gani yana ji da ajinshi a dai-

dai lokacin nan,dan miskili ne yanzu na karfi da

yaji. A yanzu ne yake tsone idon y'an mata

musamman na jami'a, dan ya iya t'sare kai da

tsare gida. Rayuwarshi ta sauya,dan ya dawo

ainashin halaiyar shi ta da,koma yafi da din,

Ja'afar kenan,namijin duniya. Dago kai yayi yana

duba yanayin garin da yadda kowanne shago

suke hadahadarsu,sai ya sauke kai kan Abdull

mai tahowa dauke da baby a kafad'a tana ta

washe baki tun kan ta karaso. Tuni fara'a ta

maye g'urbin rashin walwalar shi,kashe wayar

yayi tare da ajiye ta gefe dan tarar gudan

jininshi,duk Abba dake gefe kad'an yana kallo.

"Abbaaa... Miemien ta fad'a lokacin da yake

k'ar6ar ta,murmushi yayi mata tare da shafo

fuskarta "Na'am Miemien Abba.. Sai ta washe

baki. Ciro changi ya mika ma Abdull, "Kan

magriba kazo ka maidata kaji?... Kai ya kad'a

tare da amsa yayi godiya. Zama yayi tare da

d'aura ta cinyarshi, Tasha kwalliya da rigar da ya

yo mata tsaraba cotton ja da pink,kan nan kamar

an mata shampoo sai kyalli yake yasha ribbons..

Hannu yakai kan dan beauty point nata ya latsa

sai ta sa mishi dariya. A hankali shima yayi har

hakorinshi suka baiyana. Tashi yayi zuwa gun

Abba dan mishi sallama,kai ya kad'a Miemie na

mishi bye-bye tana dariya. Kamar kullum nai yai

ta yawo da ita suka sai ice cream suka nufi

gidan Garba nan suka yada zangon su. Miemien

Garban ya kallo yadda take tsalle kan Abban nata

shikam sai murmushi yake mata. "Abokina ina so

yau dai daya ka saurare batu na,sama da wata

hud'u dana fara ma magana zaka ce a'a kai baka

so.. Kallonshi yake jin inda yake neman dosa,tuni

ya fara sauya kama. Ba tare da yabi ta kanshi ba

Garban yaci gaba "Salma fa au... Cikin t'sananin

fushi ya rufe ido tare da daga mishi hannu. "Dan

Allah ka d'aina dawo min da hannun agogo

baya,ina a cikin farina yanzu,banson jin sunan

wata Salma chan.. Gefe yayi da kai yana

chunkune fuska,kai Garban ya kad'a kan yai y'ar

dariya, "Karyar banza kenan,yanzu da zance

Salma tana gida an sakota da nasan ba wanda

zai farin ciki a yau,kaine fa.. Baki sake yake

kallonshi, "kana sanin abinda zaka fad'a man

malam.. Matar mutanace fa yanzun. Murmushi

yayi yana mishi k'allon bakasan komai. "Toh

auren Salma ya rabu tun wata hud'u da ya

wuce,sai ka kurbi ruwan sanyi ka huce.. Baki

sake yake kallonshi ba koh kiftawa. Baya Garban

yayi da kai yana shafa ha6a tare da daga mishi

gira,ya dan jima a kame kamin ya d'auke tare da

wayance wa. "Wannan bazai sauya komai ba

kama ji da wai,dan ban manta abinda ta dirka

min ba a baya.. Kama d'aina wata dariya..

Kafad'a Garban ya make,kan yace "Daga baya

kenan kuma,chan ta matse ma,dan nasan yau sai

kafi kowa farin ciki a garin nan,karyar kawai.

Tashi yayi yana daukan Miemie tare da hararar

shi, "Kanka ake ji,ni nayi kaga tafiya ta.. Dariya

yai kan ya mike dan sauke su, "Kaima an kusa

jin naka soon. Harara ya sakar mishi kan suka

fice yana ta mishi t'siya. ***** "Mama zan tafi,a

min adu'a Allah yasa kar na samu mat'sala

kamar yadda principal yace.. "Amin kam, in Allah

ya taimaka zasu karbi uzirin.. Kai ta kad'a, ''Amin

toh, na tafi kan wannan ta farka. Da sauri ta fice

ganin zatai latti. Allah yasota tana zuwa wata

Napep zata tashi ta d'au wani da dan sauri ta

t'sayar ta shiga ba tare da ta dubi na ciki ba.

"Dan Allah ka taimaka school of... Shiru tai jin

wani kamshi da ya bigeta,turaren da koh ajikin

wani taji,toh mutum daya ke zuwa ranta. A

hankali ta waiwaya dan ganin waye masanyin

turaren. K'yam tayi tana kallonshi da murmushi

ba koh kiftawa, shima hakan take,kan da sauri ya

d'auke kai kamar ma bai ganeta ba yake nufi..

Dad'i ne..koh farin ciki a ranta a safiyar yau..

*Ja'afar* Wannan shine yaushe gamo. Kokarin

mishi magana take yace da mai Napep ya t'saya.

Ba musu yaja ya t'saya, da mamakinta taga yana

kokarin sauka a Napep d'in, da sauri mai napep

yace "Kazo gaba toh. Ba tare da ya kalle yace

"Kai hakuri,bana shiga keke da mata... Gaba yai

ya batta baki sake.. Kuturu,wa ya ga turnuku...

Ji tai tamkar ta d'aura hannu a ka ta kurma

ihu,wai ita Ja'afar zai haka?. By Feenat Ja'afar.

9/29/16, 9:44 AM - Queen Safiyyert馃憫: Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*.

45_Washegari kowa da farin ciki ya tashi kamar

ma ance an shirya. Yau tana son ta koma

Salmanta ta da ne. Yau shima yana son komawa

Ja'afar d'inshi na Salmateen shi,dan haka tun

wuri yaje yai g'yaran fuska,ya rage sumar kai,tuni

ya hasko kamar zamanin angoncinshi da Salma.

Gun Garba yaje yasha kwalliya kamar wani sabon

ango. "Ya mutumina nayi kyau kuwa?鈥� banda

shakiyanci pls. Daga sama har kasa yake

kallonshi,yai kokakarin 6oye dariyar shi. "Kayi

man,ina zuwa haka da sanyin yammacin nan

haka?.. Da zumudi yace "gun Salmatee hayatee

man. Da rashin fahimta yace mishi "wace haka?..

Harara ya sau mishi tare da fad'in "Ban sani ba,

kaima ramawa zaka yin?.. Dan Allah ni taso

muje.. Kai Garban ya juyar yana fad'in "ba inda

zani bansan mace ba, haka kawai, Da zumudi

yace "Salma ta fa,kar kace baka gane ba mana

mun dinke.. Kunu yasha yace "ban gane

ba,yaushe aka dinke?.. Koh ka manta

kalamanka?.. Lallami ya fara yana kasa da

kai,tuni Garban ya ware yana dillika mishi dariyar

mugunta. Shi dai yau bata tashi yake ba,burinshi

kawai su isa ga Salman shi. Yau d'aya ta zauna

zaman kwalliya duk da bata da tabbas din

ganinshi,har Mama na mata t'siyar ina zuwa?.

Murmushi kawai tayi ta ciro wani arnan purple

swiss tana kallo, shafashi tai tana tunano colorn

da Ja'afar yafi kauna ya gani ajikinta. Riga da

zani ne single, dinkin yai mata kyau tsam ya

kama jikinta, da gaske yau ta fito a Salmanta.

Tana daga d'aki ta jiyo yaro yazo wai Salma

tazo,tana jin Mama na fad'in inji wa?.. Bataji

amsar yaron ba taji Mama tace kace tana zuwa.

G'yale ta rufa fari da ratsin flower purple tana

k'allon kanta a mudubi,ina ma Ya Ja'afar ne

man... "Ki fito ana kiranki a waje Ja'afar yanzu...

6ata rai tayi tana gunguni, "Ja'afar kuma

Mama?.. Ni fa ba danshi zan fita ba fa.. Harara

ta sakar mata,kan ta juya tana fad'in

"magulmaciyar kawai,ni zakiyiwa alaye?.. Da gani

shigar Ja'afar daban take gunki ai... Dariya ta

kunshe kan ta kara k'allon kanta a madubi ta

fita. Suna tsaye sun rike hannun Miemie da suka

dakko chan gidan su jaafar suna mata y'ar dage

tana dariya. Murmushi ta tsaya yi musu da

sallamarta. Ido ya zira mata,yayinda itama take

kallon sauyawarshi a yau kadai kamar sabon

ango. Murmushi ya sakar mata yana daga mata

hannu halamun tayi k'yau, da sauri ta d'auke kai

a kallonshi tana cinkune fuska. Kai ya kad'a yana

murmushi, karya kuma ai ta kare, tunda har

shigarshi an mishi. Ha6a Garba yake shafawa

yana kallon wani fulakon karya gun Salma da

Ja'afar. "Kaganta ni dai ya kamata nayi fushi

bisa abinda ta dibga min,amma kaga an dakeni

an hanani kuka... Harara ta sau mishi,kan ta kau

da kai, "lefinka ai dayawa,bar tunatune kawai.

Kai Garba ya kad'a,kan ya kallo Salman. "Salma..

Kalloshi tai,bata tunani ta ta6a ganin Garba ya

zama serious haka, hakan yasa ta bashi

hankalinta gaba daya. "Nasan nima har yanzu

kina ganin baki na sakamakon zuwanmu na

karshe gunki. Rantsuwa ya mata,kan yace

"Ja'afar baizo ranar gunki da neman auren kisa

wuta ba sam,asalima yazo ne danya sadaukar

miki da farin cikinshi gare ki sakamakon sanin

waye Alhaji Usman.. Kai ta dago tana kallonshi.

Sai ya kad'a mata kai, Ja'afar din ta kalla,shima

itan yake kallo. Yacigaba, "yana son ki samu

farin ciki ne Salma,wanda yasan a gidan Alhaji

dak'yar ki sameshi,dan kaf halin Alhaji ba wanda

ba'a karanto mana ba,hakan yasa ya gwammaci

ya baki ni,duk nai imani sai ya fi mishi ciwo

sama da auranki a waje.. Ya kallo Ja'afar da

murmushi, "nasan abuna. Murmushi sukai ma

juna,tabbas hakane,dan da Garba ya auri

Salma,da yana gani bashi ba sake ganinshi bare

hulda da gidanshi. "Dan haka banajin da wanda

ya kai Ja'afar son farin cikin ki,ki d'aure ki bawa

abokina second chance a zamanku kamar yadda

bukaci haka. Nan yai ta musu fad'an rayuwa sai

y'ar hakuri ce,da sanya tsoron Allah a

lamari,gashi sunji dad'in tawakallin tunda suna

fatan in Allah yaso su maida aurensu. Kan Garba

ya tafi sai da ya tabbatar kowa ya yafe. Zaure

suka koma ta sa musu taburma. Kallonta yake

suna ma juna murmishin so cikin kauna. Sai wani

dan sinke kai take halamar kunya. Hatta Miemie

ta gane iyayen sun dinke, sai kallonsu take tana

murmushi. "Assalam Alaikum.. Kai suka

dago,Ja'afar ya amsa. "Aunty Salma wai ana

kiranki a waje.. Kallon Ja'afar d'in tayi, Shima ita

yake kallo,sai yai mata murmushi. "Tashi muje

naga wane tsageren ne wannan... Miemie ya

d'auka itama ta tashi tana murmushi suka fita.

Alhaji ne yasha gayu da babar riga da wata

katuwar mota yana murmushin ganinta. Fuska ya

tsuke ganin fitowar Miemie da Abbanta suna

wasan su. Tana ganin Alhaji Miemie ta g'imtse

fuska,murmushi Ja'afar ya mata tare da shafo

fuskarta suka karasa. Hannu ya bashi dan su

gaisa Alhaji ya juyar da fuska gefe. "Gunki nazo

fa. Kallonshi tayi tana murmushi, "toh

Alhaji,gamu ai.. Da halamar tambaya ya k'alleta.

"Ban gane ga ku ba?.. Kina nufin dashi zan

ganki?.. Ja'afar d'in ta kallo tare da Miemie dake

kallon Alhajin duk rai had'e daga shi har y'ar.

Murmushi tayi tare da matsawa kusansu suka

jeru mishi a gaba. "Alhaji, kai hakuri, kai

hakuri,ka daina zuwa,InshaAllah aurenmu zamu

mayar da Abban Miemie.. Ka d'auka zaman mu

yazo karsh.. ka d'auka rabuwar aure na da kai da

auran duk had'i ne na Allah... Ja'afar ta kalla tai

mai murmushi tare da shafo fuskar Miemie. "Kai

hakuri na na zauna da iyalina, ka yarda sune

farin cikina, ni ce tasu,kai hakuri pls... Kai ya

kad'a,tare da kallonsu,duk daga gani suna a farin

ciki.. Tabbas yasan yai sake,gashi ya tashi a

tutar babu,ba Halima ba Salma,ba su Nabila ba

Miemie... Wa zai gane a jiya yayi nadama?.. Ya

zasu gane yasan dad'in jin motsin D'a kusanshi a

yanzu?.. Wa zai gane ya hakura yanzu kam yana

son zuri'a?.. Murmushi yayi yana d'auke kai,kila

haduwarshi da Salma sanadin shiryuwarshi

ne,koh yanzu ya gode Allah. Kai ya kad'a tare da

masu fatan alkairi, k'warai tai mamakin jin harda

mata godiya a bisa gaskiya da take tsage mata.

Hannu ya mikawa Miemie fuska d'auke da

murmushi. Kafad'a ta mak'e tare da lafewa a

kafad'ar Abbanta. Mota ya shiga tare da fitowa

da leda cike da shopping na chocolate da ice

cream.. Alawa daya ya fito dashi tare da fad'in

"Zan baki sweet fa,zo mu gaisa mana Miemie..

Salma ta kalla kamar mai jiran umarninta.

Murmushi tai mata tare da daga mata kai,abin

kai sai taje ba musu,yau sai ga Miemie harda ma

Alhaji dariya. Da zai tafi hannu ta daga mishi

tana mishi bye-bye tana dariya. Duk sai Alhajin

ya bata tausayi Alhajin,har Ja'afar na daga mata

gira halamar tambaya. Marairaicewa tayi tare da

shagwa6e fuska. "Y'arka ta rabani da Alhajina

shikenan kunji dad'i.. Harara ya sakar mata

kamin yace "toh bishi, Allah yai ma y'ata albarka

yarinya mai kishin Abbanta koh? Kai ta daga

mishi tana dariya,da murna ya shillata sama ya

chafe suna dariya. Gwalo yai ma Salman,sai

Miemie ma ta hau mata,tuni ta fara chunno

musu baki suna cikin shagwa6a. By Feenat

Ja'afar.

Like 路 2 路 Reply 路 Report 路 Aug 11

Feenat Ja'afar Novel's

*A BAKIN AURANKI* *漏 Feenat Ja'afar*. 46_Ba

sauran jira,dan karara suke nuna ma fitsara a

gidan Mama, su Ja'afar abin nema ya samu,ba

guntun fulako,ba shiri ta bama Abba shawarar ayi

a mayar da auren nan. Wata daya aka sa suka

sha biki kamar ba gobe.. Nan take jin labarin

auren Bintu a gidan mai mata uku,tana chan ta

zama bora. Su Maman Abba duk sun halarci bikin

nata,nan take tsurkuta mata labarin Maman

Ummi kan ranar ta fita gantali miji ya

dawo,bayan ta dawo yace ta nemi inda dare ya

mata,karshe dai akai saki. Murmushi tayi,tasan

Allah ba azzalumin sarki bane,dole yadda taga

tasku Maman Ummi tagani itama. Jingina yayi a

jikin bango yana kare mata kallo,fuska rufe ruf da

g'yale,murmushi yayi dan tunawa da daren

farkonsu a wanchan gidan. Karasawa yayi tare

da g'yaran murya kad'an yana leka fuskarta.

Zama yayi tare da sauke ajiyar zuciya. A hankali

ya kai hannunshi tare da daga mayafin da ta rufe

fuskar. Tsam yayi yana kallonta ido cikin ido,tuni

ya marairaice mata fuska,kuka fa?.. Hannu yasa

yana share mata wani na zubowa,duka ya hayo

gadon tare da janyota yana shafo bayanta

halamun tai shiru. Sai da tai shiru kan ya dago

kanta. Ido suka zuba ma juna ba koh kiftawa.

Chan ya nisa cikin murya kamar mai jin bacci

yace "Kin tuna kalaman da na ta6a turo miki na

karshe cikin text message dina kuwa?.. Tunowa

ta fara,sai yai murmushi tare da zamewa kan

katifa da ita a kafad'arshi. Ajiyar zuciya suka

sauke tare da kamo y'atsunta. "Na ce miki _" a

heart dat truly loves never loses hope..but

always believes in d promise of love,no matter

how long d time and how far d distance,at d right

time,love will fine a way".._ "Hope kin yarda da

maganar ba wai soki burutsu Masoyinki bane?.

Kai ta daga mishi halamar ta yadda,tunda ga nan

K'ADDARAR wani zama ya kara had'a su waje

daya. Yau kam ya gama gasa mata jiki da

d'anyun kalaman da ya tanadesu kawai da

Salmanshi,fatanshi Allah ya kare sa6ani a

tsakani. Washegari da t'sant'sar farin ciki suka

tashi,suna kitchen had'a break fast sai nannan

yake da ita. Tashin Miemie suka ji tana kiran

Aunty cikin kuka taga sabon waje. Ganin iyayen

waje daya ita kanta sai binsu take da kallo,

mot'si kad'an ta kallesu,kamar wacce bata so su

rabu da juna suyi rayuwarsu tare. ********** Yau

ziyara aka fito ta sallah ita dasu Ummi, Sun zaga

duk inda ta tambaya saura gida 1 taga sun

karkata zasu shiga gidan kawunsu wanda jiya

sunje. Ja tai ta tsaya tare da ce musu su shiga

su fito dan yau bata tambayi nan ba. Murmushi

Aunty A'i tai tare da kad'a kai,a lalle kullum

Salma hankali na kara zuwar mata. Tuni Ummi

kam tai gaba tana t'saki. Tana nan tsaye

kawunsu ya fito a gidan,bayan sun gaisa yace

mata ya bata shiga ba ga y'an uwanta suna ciki?

Kai a kasa tace "Abba ban tambayi nan ba

ne,dan jiya munzo yini. Murmushi yayi na jin

dad'i, "hakane kinyi tunani mai kyau,Allah ya miki

albarka. Kai ta kara kasa kamin ta amsa. Kud'i

ya ciro daga aljihu ya kirga dubu ya bata,dan

sosai Salma tana wa mutane bazata,yana

matukar son mutum mai gyara kuranshi. "Sannu

da jira uwar y'an ka'ida... Juyawa tayi daga

kallon wani a mota sun tsaya da Kawunsu da ya

wuce yanzu,sai dai kan ta tantance su Ummi sun

fito. Murmushi ta mata tare da basar da zancen

suna tafiya. "Wannan ai wahala ce,ace duk inda

zan shiga sai miji ya ban izinin shiga?.. Kai ta

girgiza, "gaskiya da sake.. Hararar da Aunty A'i

ta mata ne yasa tai shiru. Kallo Ummin tayi da

murmushi, a irin hudubar nan a baya suka

dilmiyarta,ita kwa yanzu a shirye take da yima

Ja'afar biyayya matukar bazata sa6a Allah ba.

Har akaje gida nan ma Ummin ta hau zaiyyanawa

Mama halin da Salma ta tsiro, tuni Mama tai

mata kacha-kacha,Ummi harda kukan takaici

ranar. Da dare yazo ya dauke su,sai taga a motar

Garba da kamar ta ganshi dazun. Taga anje gida

yana kokarin rufe mota da abin rufa sai ta kasa

d'aurewa ta tambayi nan zata kwana? Murmushi

ya mata tare da bud'e gida. Sai da akazo

kwanciya yake sanarta ai shine albishir din dazun

da yace sai sun zo gida. "Ya sai sabuwa ne,sai

mukai cinikin wannan dashi tawan, munyi abin

hawa. Murna tai ba kadan ba tana k'allon

mukullin motar. Ido ya zuba mata yana kallo ba

koh kiftawa. Baki ta kai kan idon tare da hurewa.

"Salma.. Hankalinta ta bashi tana murza

yatsunshi cikin nata. "Daga yau na yard'e miki

koh ba idona ki taka ko'ina u r free... "Dazun

naga komai Salma,ina horn bakiji bane,kin sani

farin ciki dazun kinsa naji ni din na isa gun

matata.. Duk inda ta tambaya nan zata jefa

kafarta. "Sai ganan kuma kawu shima ya labarta

min yadda kuka yi sai murnar wai kin san ya

kamata yake.. "Nagode sosai,yau har kawu

yasan ni mai fad'a aji ne a gidanshi.. Murmushi

tayi tana kara ruk'unk'umo shi. Ta gode Allah da

yasa ta gyara dabi'ar ta maras kyau ta maye mai

kyau. Fatanta duk wata mace mai irin halinta ta

daina,dan ita taga misali akanta. Dan a yanzu

rayuwarta ta fi mata dad'i da kwanciyar hankali,

ta gane yanzu kulle ma wasu matan ke ja ma

kansu, tana fatan kowacce mace ta guji fita a

bisa sharad'in *A BAKIN AURENKI* da suke

yi,dan gudun haifar da saki irin nata mai

gabadaya. Alhamdulillah.. Nan na kawo karshen

littafin A BAKIN AURENKI.. Ina rokon Allah

kuskuren da nayi ya gafarta min. Da fatan

darasin ciki ya isar masu halin Salma za kuma su

gyara,Allahu ya datarmu aikin kwarai a

gidajenmu. Gareku dubin masoyan Feenat

Novel's, na gode kwarai da kaunar ku

gareni,Feenat na son duk mai sonta, dama wanda

bai yinta.. Luv you all. Sai kun sake jina a sabon

littafi mai sunan... *RABO IN YA RAT'SE*...

Nafisa Bashir Tanko, (Feenat Ja'afar) ke muku

fatan saduwa da alkairi.

0 Response to "Abakin Aurenki HausHausa Novel"

Post a Comment