-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

'YAR KWALLIYA Hausa Novel

'YAR KWALLIYA Hausa Novel

 WRITING BY HIS ECCELLENCIY NOVELS GROUP.. 


'YAR KWALLIYA Hausa Novel

Page 1-5

March 07, 2018

'YAR KWALLIYA ..



Bismillahirrahmanir

Rahim

.

Wannan kirki raren labarine

nayi shi dan fada karwa da

nisha dan tarwa ban yishi dan

wani ko wata ba Written by Jabeer.. 

.

Wata yarin yace 'yar shekara

15 kafa fururu komai babu

fuska kuma tasha Jan baki da

hoda harda gazal ta fallo da

gudu kanta daukeda tulo

tadebo ruwa a guje ta fada

gida Tana shiga ta saki tulun

yafadi ya fashe Nidai gaskiya

bazan yar daba hikenan ni

banda kata bus hine fa ya bini

har inda zan debo ruwafa

inna yana cemin *YAR*

*KWALLIYA* kafa ba mai

fuska tasha ado hine

nakamahi da danbe na fasa

mihi baki hine dan bahida

kunya ya biyoni gida Yasin

bazan yarda ba inna kalli

yanda bakina yake zubar jini

inna Abu muguwace wlh Kayi

hakuri kaji kaima da naka ina

ruwanka da tsokanar ta kuma

kasani sarai bazata barkaba

Au abinda zaki ce kenan to

shi kenan zan turo me rama

min Kayi hakuri mana kai

baka jin hakurine Ina

kotsayawa beyiba yatafi Inna

ki barhi ki barhi nace kaje ka

kawo bindiga karhe kenan

Yanzu Abu Wannan rayuwar

kika zaba to shikenan

zandena tsare miki wlh tinda

ke bakida hakuri yanzu

Wannan gabjejen kato kika

kama da fada Inna hinefa ya

nemi tso kanata fa Yanzu

ruwan da kika debo ma gashi

kin fasa tulon kaini inna ina

zansa kaina Inna Wannan fa

laifin tulun kine ina ruwanhi

dani nan naso na ajiye hi hine

ya fadi ya fahe sai hakuri

Kamarya sai hakuri Abu girkifa

zan Dora yanzu ya kikiso ayi

To ni kome ma za ayi ayi

tuludai yafahe nikuma na gaji

bazan iya komawaba

.

Kin isa komawa kamar kinyi

kin gama ga wani tulun can

jeki dauka kidebo wani

ruwan Kai inna kinemo wani

ya debo kinga janbaki da

hudana ya kare sonake na

zagaya baya na siyo I dan har

baki debo ruwan nan ba ba

inda zaki Abu kin jini da kyau

hikenan zan debo Abu ta

dauki tulun tatafi Rake

yauwa bari naga maya finda

ke daure a kugunta ta kwance

ta Ciro Hamsin ta mika wa me

rake Yabata rake da canji

tana tafe tana sha harta

karasa rafi Yauwa wana

kama wato jiya kika watsa

min kasa kika gudu ko yanzu

wana kama cewar Abu Ke

Abu kinga diban ruwa aka

turoni ba fada ba matsa na

wuce cewar binta Ke binta

me kike nufi ni wasa aka

turoni kenan bari kiga wasa

cewar Abu Hannu tasa ta

ture tulun dake kan binta

yafadi kasa yafashe Yauwa

kinga wasa nan nafasa banza

ko kinada abinyi ne Kaiiii ni

kika fasawa tulu wallahi kinyi

karya saina rama Abu kome

kike takama dashi kin tara kin

samu ni binta saina gyara

miki zama Binta na gama

fada tasa kafa ta daki tulun

Abu yafashe Nanfa Abu ta

daka tsalle ta dire ta kamo

wuyan Binta suka kama fada

da kyar aka rabasu Aina fada

miki Abu ni Binta nice dai dai

ke saina gyara miki zama

Tohi kenan idan baki gyara

min zamaba nizan gyara miki

kuma saikin biyani tuluna

kona daka ki a gurin nan

wlh Allah ko Abu bazan biya

ba kiyi abinda kika gadama

koda me kika zo ni Binta na

fiki haka kikace ko to

hikenan Kallon ta Abu take

tana gyada kai da buga kafa

Banga wanda ze fi karfinaba

ni Abu wai saiwata banza

bazara iskar damuna binta

wlh kintarowa kanki aradu da

ka Hannun ta Abu ta kama

ta sakar mata cizo dagudu

tabar wajan Binta tabi

bayanta da gudu haka suka

yanka cikin unguwa dagudu

harzuwa gidansu Abu Abu ta

boye a bayan inna Inna ki

matsa Wannan fadan ba naki

bane kimiko min Abu na nuna

mata abinda binta zata iya ni

kika ciza dai ko cewar Binta

Yar gidan marasa tsoro

mekikeyi a bayana aina fada

miki ni nadena bada hakuri

kinga Binta gata nan zoki

mata abinda kike so cewar

inna Gadan gadan Binta

tataho Kinga Binta tsaya Abu

ina ruwan dana aikeki kidebo

cewar inna Inna asara kika

aika dankuwa ni Binta nice

nan na fasa tulun *'YAR

KWALLIYA* tafasa min nawa

shine nima na rama wata

tsiyarce cewar Binta Ahh

babu bakomai kinyi daidai

yanzudai kiyi hakuri Binta

kibari idan tafito kuyita takare

mutuwama tana tsoron idon

ma haifi cewar inna Inna

kenan kince haka ko to ina

waje ba inda zanje kekuma

Abu zaki fito kisameni hoda

bawanka kidinga Wanka idan

zakiyi kwalliya Binta tajuya ta

fita Inna ki matsa kibar ni da

ita kina jin metake cemin

Karya tayi Abu gaskiya tafada

yau kwananki nawa rabonki da

kwanka Inna batun wankan

nan kibarhi aikyan kwalliya

kayihi batateda wankaba

gawani kamhin turare na

musamman dayake tahi a

jikina gahi turaren babu a

kasuwa me yafi raina shine

zan tsaya inta batawa kaina

lokaci wajan yin kwanka Dalla

rufemin baki kazamar banza

kazamar hufi ina kyau Anan

*HODA BA WANKA* Baki

tabude ta gir_giza kai ta

dunkule hannu inna harda ke

yasin duk wanda yasake ce

min hoda ba wanka na dena

raga mihi yasin cewar Abu

Yanzu da kika dunkule hannu

damben zakiyi dani nima

cewar inna Jifa tayi da

takalmin kafarta ta debo

kayan Kwalliya ta zube a

gabanta tadauki Wannan

tashafa ta ajiye takalli kanta a

madubi tayi dariya

.

Inna jiya da naje dan dali aka

dinga tambaya waye yafesa

turare nayi shiru tsabar kanhin

turaren jikina hanci suka

toshe Niko kayan nan ma

bacanzasu zanyi ba Wanka

kuwa nadena Kaza kankida

motsi afakaice suka zageki

baki saniba ba abinda kikeyi

sai bugawa kitemaka ki ajiye

kayan kwalliya kiyi Wanka

kekanki zakiji dadi Tab tab

aaah waii saidai wata Abun

badai niba wanka nida hi

munyi hannun Riga inna kifara

sabon lissafi daga nan

harranar sallah nida Wanka

Haka kikace to Allah

yashigoda yayanki da malam

su insun isa dake Sa saki kiyi

tinda ni kin rainani dan Allah ji

yanda kika cika mana gida da

tsami cewar inna Kinji ko

inna kinji irin kamhin turarena

ko hakama wani saurayi yajiyo

kamhin yace yana sona nace

bana son hi ni fako inna har

bana son fita dik inda nabi

ansan nice saboda turturarena

cewar Abu Waiyoo waiyoo

tasa kafa tayi koli da kayan

kwalliya inna ban fada

mikiba yau ake cin kasuwar

gangare natafi Tayi fice

warta Badan Allah yasa akwai

sauran ruwa agidan nan ba da

Abu ta gama dani cewar Inna

Tafiya take a hankali tana

tafiya tana yanga acewarta tafi

kowa haduwa ga turaren

jikinta yafi na kowa kanshi

tana tafe tana cin gyada

hannun takuma rikeda sandar

rake ga wuwar danmara tasha

a kugunta binda na labe tana

kallon ta Abu nakara sowa

inda Binta take Binta tariketa

Wana kama yasin saina

dagargaza bakinki zan kyaleki

yanzu ina inna take balle

kibuye a bayanta cewar Binta

Yasin Binta kanki baya aiki

kalli yanda kika rike min Riga

a gaban mutane gasamari a

gefe kalan ki zubarmin da

mutunci a idonsu haba kidena

abinda kuda zebiki Karsan

kuda nice mangoro kobakijiba

cewar Binta Janyota tayi

zata daka bashiri ta saketa

tatoshe hanci Abu

dagaskene abinda ake fada

kenan Wannan warin daga ina

lallai kinci sunan ki huda ba

Wanka sammin raken mana

Abu taraba shi2 ta bata

Yauwa nagode gyadar fa

Tadiba tace Gahi kibarni zaki

rakani cewar Abu Eh ni yanzu

kawarkice gaskiya kinada

hankali Abu Dariya tayi tace

ko nasani suna tafe suna

shirme harsuka siyo suka

dawo

.

Atare suka shiga gidan Inna

na ganinsu ta fara salati Abu

mekika kuma yiwa Binta

cewar inna Inna ai yanzu

Binta tazama kawata cewar

Abu Ina baze yiyuba ban

yardaba wlh dama ya kike

bare ankaraki da binta waye

besan bintaba cewar inna

Kinga Binta jeki gida zanzo na

same ki cewar Abu To inna

sai anjima cewar Binta

Sallama Alaikum inna ina

wuni Lpy kalau Nura sannu

dazuwa kaga Abu tayi

sabuwar kawa mara aji irinta

Ke Abu yatoshe hanci inna

meya yake bugawa haka

cewar Nura Wacce inbanda

*'YAR KWALLIYA* Fari Abu

tayi da ido tareda

juyawa New writer's

Taku husba'ahfama

.

Yaya Nura a hekaima kaji

kanhin tiraren nawa Dalla

kanshi ko wari kazama kawai

dubi yanda gidan nan yadauki

warin jikin ki Wari karyama

kenan Yasin kanhi kaji cewar

Abu Yau sai kinyi Wanka

bazan iya zama dake kina

wariba wlh inna bani ruwan

nan na kusa dake cewar

Nura Banga abinda zesa nayi

wanka ba Yasin kalan kanhin

turarena ya tafi Nura ya

dauki ruwan yasa a bandaki

yakai mata soso da sabulo ya

karyo bulala yarike Shiga kiyi

wanka Yaya Nura ina ganin

gir manka fa cewar Abu

Yadaga bulala bashiri ta fada

bandaki tayi zamanta Kayi ka

gaji yaya ba wankan da zanyi

cewar Abu Tana tawasa da

ruwan kamar tana wanka

tawanke fuska da kafa da

hannu Kate makeni ina

fitowa zan cika fukata da

KWALLIYA na raka Binta tallar

gurjiya hahhh Tabude ta fito

ta harareshi tashige daki tayi

KWALLIYA ta tafi gidansu

Binta taje tasamu Binta ta fito

tallar gurjiya A hanyarsu na

tafiya Abu tayi ido4 dawata

taci ado da KWALLIYA tayi

kyau sosai harta bace Abu na

kallon ta Ke mekike kallo

cewar Binta Kinga yanda tayi

kyau tafi yanta kayanta komai

yayi Nanfa Abu tashiga yin

irin tafiyar Kibar Wannan abin

Abu kinsan daga ina take

cewar Binta A'a cewar Abu

Daga birni take haka suke

tasu KWALLIYAR dasa kaya ba

irin nakiba HODA BA WANKA

.

Yasin yanzun nan bakinki

zeyi jini Binta nizaki cewa

haka nifazanyi fada da duk

wanda ya kirani da Wannan

sunan kowaye hi cewar Abu

Maida wukar nataba zuwa

birni sau1 yanada kyau ginin

su ba irin namuba kinga baze

yu nabaki lbr ba saikin gani da

idon ki cewar Binta Kai nima

inaso naje zaki kaini dan Allah

cewar Abu Inna inna ce

matsala Abu damunje yasin

cewar Binta Kinga bawata

matsala ki kaini kawai inzaki

kaini ya kika ganni zanyi kyau

a birni ko cewar Abu Ehhh to

ban saniba saikinje tukunna

saboda gaskiya tsoro zaki

basu kalle kifa tab cewar

Binta Waike hikenan bakida

magana sai kice na kalli kaina

me zan gani kodai ciki baki

kike min ne cewar Abu Ko

daya KWALLIYAR takice abin

tsoro ga kafarki Fari fat

gaskiya bazan kaikiba saikin

waye cewar Binta Abinda

Binta tafada yabatawa Abu rai

yasa tayi gaba ta barta a

baya

.

Wani yarone yazo siyan

gurjiya gun binta Binta zuba

min gurjiya Karki zuba mai

cewar Abu Tinda na ganka

nadawo mekace min jiyama

Meka ce mata Eh cewar

Binta Shiru yayi yakasa cewa

komai saida ya gano

yayanshi yace ' *YAR

KWALLIYA* nace Ohh me

dadtin dankwali itace *'YAR

KWALLIYA* cewar Binta

Barshi dani yanzu nanuna

masa kalata Yasin harni zaka

tsokana ka gudu anhi kudin

nahi Binta cewar Abu Binta ta

ansa tace kuma bazan siyar

maka da gurjiyan ba na

karfine Gaya mihi binta waihi

Wannan dame yake dakama

ne naga saiwani jijjidakai

yakeyi cewar Abu Kasa ta

diba ta watsamai a ido Binta

tasamai kafa ya fadi suka

rufeshida duka abin mamaki

kato a kasa mata na duka

abinda mutane ke cewa

kenan Yayan shina kara sowa

ya daka musu tsawa Suka

bar dukanshi suna Harar shi

Lpy kaikuma meya kawo ka

kasan muko suwaye cewar

Abu Suwaye Ku inbanda

kucakai marasa hankali dalla

dubeki kafa furu furu komai

be ganiba dubi kayan jikinki

fuska saikace Aljana waike

kinyi KWALLIYA Ap abanza

yafi na tsohuwa kaga ka

gaggauta barin gurin nan inba

hakaba kuma hmmm cewar

Binta Karkusake suce zaku

yimin haukan da kuka saba

danni bazan daukaba wlh Ko

Binta mu gwadamai aiki dan

nakula saimun koya mishi

hankali cewar Abu Waige

Binta tafara can ta gano dutsa

tace haryanzu bakinka be

mutuba ko tsaya ka gani

Dutsen ta dauko da buga

mishi a kai Banza a banza

cewar Abu Jini ya fara zuba

a kanshi Abu da Binta suka

zuba a guje suka wuce

gidansu Binta Umma ga

gurjiyar ki yau an hana talla

inji me gari cewar Binta Ke

Binta waya fada miki cewar

umma Umma Nifa ganauce

ba jiyauba Gashi can ya baza

yan *DOKA* A gari cewar

Abu Kunga bana son shegan

taka waca tsiyar kuma kukayi

na sanku da kyau cewar

umma Wani ne ya nemi tso

kanar mu hine muka fasa mai

kai cewar Binta Eh banjiba

naji kamar kince fasa kai

Allah na gode maka daka bani

Binta nidai shikenan bakina

baze zauna shiru ba saboda

inada Binta cewar umma

Kofar gidan su Binta aka siga

duka da karfi Kufito mana

dasu ko mushigo yara sun

gagari kowa wlh yau zamu

sharewa kowa hawaye kufito

dasu cewar mutanan da suka

zo Kuna jiko yara kunzama

dan kuka mejawa uwarsa jifa

Umma kinga jeki kiji dame

suka zo idan da sulhune

kusulhunta idan kuma akasin

hakane kikira womu katkenan

cewar Abu Kushiga ciki bari

naji dasu

.

Wai baza a fito dasu bane Eh

mumafa yan zama nine kofar

suka bude suna kokarin

shiga Haba dan samari gidan

matan aure ne fa Nasani ina

'ya'yan Allah banin nan suke

Binta da Abu Basa nan sun

fita Karyama kenan ina ganin

su suka shiga gidan nan dan

haka ki fito dasu kawai mu

baza mu hakuraba dan

uwanmu suka fasawa kai

gashinan sai zubar jini yakeyi

yanzu haka yana Asibiti Allah

yabaku hakuri kuje idan sun

dawo nida kaina zan kawo

muku su cewar umma Eh to

na yarda dake saidai be

kamata mu tafi haka ba bari

mu bar miki sheda idan sunzo

ki nuna musu Yadaga gora

ze sauke mata dagudu tabar

gurin ta shige gida tarufo

kofa Yauni umma naga ikon

Allah ina kuke Umma sun

bar miki sheda banzaye

sokaye sun yarda ba ma nan

gamunan muna jinsu kuma

cewar Binta da Abu Au kujin

dadin kune a bar min sheda

saboda kun amsa sunan Ku

Binta da Abu ko Allah yate

makeku suna nan suna jiranku

kuna fita sai abinda hali ya

yiwu cewar mama Basu isaba

yanzuma ba barinsu zamuyiba

narike muryar su zan ne mesu

1 bayan 1 cewar Abu Umma

kawo mu kai miki dan dali

cewar Binta Gashi nan kutafi

amma dan Allah karku nemi

tso kanar kowa kuma Ku

canza hanya karsu ganku

cewar umma To sai mun

dawo suka fada gaba dayansu

suka fita

.

Suna fita umma taji wani

hadeden wari Umma taja

dogon nun fashi Wannan

wani sabon yayi ne kuma Abu

irin Wannan bugawa haka

nida Allah yasa kar Binta

tadau Wannan halin na rashin

Wanka Suna tafiya suna

waka suna ciye ciye suna

neman tso kana Abu ta gano

bishiya tace Binta ajiye

gorjiyar nan muhau bishiya

kinga yanzu basu fara zuwaba

zuwa anjima sai muje dan

dali To muje suka tarar da

yara a jikin bishiya suna

wasa Kubar gurin nan Abu

da Binta sunzo ko sokuke jiki

yayi tsami cewar Binta Tinkan

Binta ta karasa magana yaran

suka bar gurin dan sunsan

halin Abu da Binta Suka cire

takalmi suka haye bishiya

suna wasa kamar yara Wasu

yan mata suka zo wucewa

suka gano Binta da Abu suka

kwashe da dariya Abu na

ganin su ta sauko Binta ma

sauko wa tayi Wakuke wa

dariya Eh daku nake magana

Abu ta fada tana dungure

musu kai Karki sake dun

guremin kai kinsan kowaye

babana kuwa A garin nan

.

koma waye hi beda meniba

abinda yasa kika kallemu

shine yanzu ze Ja miki dukan

tsiyama kuwa cewar Binta

Jiki ko kayama baki iya

sawaba ji hodar fukarki

janbakin ma tsohon yayi ne

amatse ciki asai sabo cewar

Abu Kaji wai harkurace zata

ce da kare maye jiki kalli

kafarki kalli fuskarki ji wani

wari mara dadi da kikeyi

gaskiya kinci sunan ki HODA

BA WANKA Nanfa Abu tayi

kukan kura ta rufesu da duka

Binta nadukan daya Abu ma

na dukan 1

.

Duka sukai musu bana wasa

ba harda yaga riga Cikin

muryar kuka yarinyar tace

saina nuna miki bakida wayo

Saikin ga gatana Abu tace

Jeki turo duk wanda kika

gadama ni Abu ina jiran hi

banza qazama Eh nice

qazama idan ni kazamace ke

kuma fa fada min cewar yarin

yar Bakinki be mutuba ko

Abu saimun zubar mata da

hakwara tukun na cewar

Binta Kuyi duk abinda kuke

so lokacin kune yanzu nima

lokacina nanan zuwa cewar

yarin yar

.

Tana gama fada ta mike ta

debi takal manta a hannu ta

kalli kawarta da suke tafe

tare Tace 'YAR KWALLIYA

suka zuba da gudu

Matsoratan banza kawai harni

zakibawa tsoro da baban ki

Wannan kalmarta zakiga me

rama min yazama tamkar

tatsoniya a gurina ni Abu naci

dubu sai ceto Sukayi dariya

Kinga dauki tallar mu karasa

dandali yanzu kowa yazo

zamusha kallo kai ni harnaji

ma bana son zuwa cewar

Abu Binta tace meyasa

Tiraren jikina Akoda yaushe

shine matsala ta dana je

dandali daga kallo sai tohe

hanci a gurin sama ri cewar

Abu Binta tace dagaske kike

Abu warin najan hankalin

samari Abu tace bana son

wula kanci binta wayace miki

warine kanhidai nibama nason

irin kallon da sama rin suke

min nasani nafi matan dandali

kyau da kanhin tirare sosai ma

nice kadai nasan sirrin

Nanfa Binta ta tafi tuna ni Ke

tina ninme kikeyi Abu gaskiya

nima zan fara fashin Wanka

konima turaren jikina zefito

kwana nawa zanyi banyi

wankaba Abu tace yauwa yar

gari kinga bake ba Wanka

indai kinaso tiraren yazauna

tareda ke duk inda kika higa

ansan kin higo Binta tace To

hi kenan nagode kawata

Tadauko farantin gurjiya tace

debi kici iya San ranki aikin

bani sirri babba Abu tace

Bakomai yiwa Kaine Binta

amma ya zakiyi da umman ki

idan tagane kin dena kwanka

Kibari kawai nikaina bansan

abinyi ba mutafiko kinga

yamma tayi kar a fara

bugawasa bama nan Abu

tace ga aiki zan saki indan

mun higa dan dali ki ki zuba

ido kiga abin mama ki gurin

sama rida yan mata To

hikenan muje Abu

Suka je dandali hakan kuwa

akayi Abu nazuwa masu toshe

hanci nayi masu dariya nayi

Abu harda sake tafiya

Kawata Abu gaskiya nima na

rike sirrin nan hannu 2

Sukayi dariya suka tafa

Suka sha kallo sukayi tsokana

iya son ransu suka koma

gida Daga ina kike Waye

Wannan Abu tace tana daga

kai taga Nura Daga dandali

nake Yariko hannunta

yawuce da ita ciki ya watsar

da ita kamar kayan wanki

Nura ya fara shin shine shin

shine Yace Inna bana

tunaninda Abu ta shigawanka

tayi Inna tace Ko hmm zata

aikata nasani Wannan nan

gaba kadan nizan fara yimata

Wanka da kaina

.

Abu tace Waaa niii tab

bawanda ya isa dan bakin ciki

turaren nawama rabani dahi

za a yi Nura ya Wanka mata

mari tafashe da kuka Inna

abinda ya dace kenan kifara yi

mata da kanki tinda ita bata

yi Nifa bawanda zemin wanka

Nifa yaya anyi walkiya na

ganka bakin ciki kawai ka keyi

dani dakaji kanhin tirarena

saika dinga yamutse fuska

saboda bakin ciki Tirare ko

wari kinga kidena shiga cikin

mutane kina kiran waikin fesa

tirare dariya zasu miki

Wannan warine warinma mara

dadi qazama cewar Nura hi

kenan Inna kina jinhi ko ni ya

kira qazama tafara timami

akasa Nura yace Inna kice

mata ta tashi kokuma yanzu

jikinta ya fada mata Bashiri

ta mike tana gunguni harya

fito fili tace nagaba yayi gaba

kanshi kuma nayi bawanda ya

isa yakwace Ehhhe Waye ze

kwace inbanda Wanka Inna

duk sanda kika tashi wankar

*'YAR KWALLIYA* kitanaji

kwalin sabulu saboda tsoro

Inna saida safe Yana fada

yayi fice warsa Allah

yakaimu Inna kinji shi ko

Yasin yaya kajawa budur

warka Allah ya hadani da ita

Kinga Abu bana son neman

tsokana karki sake kitaba

musu 'ya kisamu wanda

yamiki badai itaba ki kwanta

saida safe To Inna Allah ya

kaimu WASHE GARI DA

SAFE Abu ta fito tana

hamma

.

Inna Allah dai yasa kin gama

abinci dan yau yunwa

nakwaso abaccin Bagai

suwa ba komai sai Neman

abinci baza kiciba saikin goge

baki kinyi sallah tukunna

cewar Nura Tamatso kusa

dashi tace yaya a gidan nan

kaine kwai matsalata yanda

sauran suka tafi suka barini

kaima zaka tafi ko ince kagaji

kabarni Yatoshe hanci tinda

tafara magana harta gama

Nura yace Wai Wannan bakin

naki Abu ai sai ya kashe me

rai yaushe rabonki da goge

baki AF anzo wajan nikaina

na manta gawayin da gihirin

na ban wuya Yasin hiyasa na

dena wankewa yawan goge

baki na kahe hakori Nura

Yana nesa da ita yanda bazeji

warin bakin ba Injiwa Yau

saikin goge baki yaushe

rabonki da sallah dan Inna

tace rabonda taga kin kalli

gabas harta manta cewar

Nura Eh hakane yaya hadasu

nakeyi hiyasa bata ganina

Hadasu kamarya Abu Nasati1

nakeyi a rana1 sauran

ranakun kuma ina hutu tafada

tana dariya Nura yace Abin

ma dariya yabaki ko Abu

amma kin dena zuwa isilamiya

ko Tab tsohon zance tin

yauhe nadena zuwa bari kaji

laifi nayi yace ze dakeni

nikuma nace be isaba shine

yasa yara suyimin waka

waini *HODA BA WANKA*

hine na sace mai tayar keke

hine fa yake ne mana ruwa a

jallo

.

Tana fada tana Sosa kai da

jikin ta Inna haka lamarin Abu

ya kara lala cewa cewar Nura

Inna tace kaji da kunnan ka

kakuma gani da idonka yazu

kuma abin zekara finnada

tinda ta hadu da Binta Ido

yazare yace Binta gagare Ita

dai yanzu kawartace sosai

duk inda Abu take zakaga

binta Cewar inna Dole nakara

samiki ido Abu jeki kwanke

baki kiyi Alwala kizo kiyi sallah

a gabana kuma ma inbanda

rashin hankali irin na Abu a i

na akace miki hada sallah a

keyi kowacce ana yinta akan

lokacin ta kina jiko cewar

nura Abu tace Yashiga tanan

ya fita tanan bayan kai ba

malami bane me zaka fada

min nayarda bayan sanin ma

nafika Na yarda jekiyi alwalar

kizo Taje tayi ta zo

gabanshi tace yaya na hutar

dakai dama yau nake hadesu

guri guda barima nayi ka gani

Nura yace Ke bana son hauka

fa sallar Asuba raka'a

nawane Lallaima yayan nan

nawane inbanda 2 Sallama

Alaikum Nura yajiyo sallama

daga kofar gida girgiza kai

kwai yayi yatashi yatafi Nura

ya Inna taku Lpy kalau cewar

nura To Alhamdulillah

megarine yace kuzo dakai da

inna dakuma Abu Allah

daiyasa lpy cewar nura

Ehhhhhto lpy ba lpy ba saidai

koma meye idan kazo fada

kaji To gamu nan zuwa yace

yakoma ciki Inna yarinyadai

tasake ballo ruwa megarine

yake Neman mu To Bakomai

bari ta idar da sallah saimu

tafi cewar Inna Abu tace Inna

Nifa ba inda zani idan banci

abinci ba Ehhhhe Waiba

sallah kike yiba Abu cewar

Inna Abu tace Inna kwantarda

hankalinki na idar bani na

bawa cikina tukunna Inna ta

bata ta ansa tana hannu baka

hannu kwarya harta gama

Tasha ruwa Tace Inna saura

kwalliya idan banyiba bazan

iya sa kafata wajeba Nura

yace kin isa waye ze zauna

jiranki Inna tace kai kanka

kasan hakan baze yiyuba

kabarta tayi mutafi Abuta

baje kayan KWALLIYA tayi

kamar yanda ta saba fukarnan

kamar Aljana Inna mutafi

naga ma Warin bakinta yadoki

hancin Nura Kaiiiiiii Abu baki

wanke bakiba ko Eh ban

wankeba bakina ko naka

.

Tayi gaba abinta sukuma suna

binta a baya harsuka karasa

fada kowa na gaida megari

amma banda Abu Megari

yace Ke Abu me yarin yata tai

miki kika daketa jiya tareda

bakuwar gidana Tawatsawa

yarin yar harara tace kuma na

dake ta nadaki banza ba uwar

dayasa tace min HODA ba

Wanka Ke Abu baban nawa

kike fadawa haka cewar yar

megari Anfada mihi ubanki

ubanane cewar Abu Kaji

yarinya mara kunya me garin

kike fadawa haka Ayi hakuri

yarin yace cewar Inna Abu

tace Inna saboda ni karki fara

karya niba yarinya bace

hekarata goma shabiyar Inna

nayimata alama tarufe baki

amma ina zance kwai Abu

take saki..

Writing By Jabeer Rabiu Idris.. 

Whatsap Number.. 

07034488635...


'YAR KWALLIYA Page 6-10

.

Can saiga Binta ga gare

sarkin kwadayi da umman ta

suna ta howa Yauwa Allah

na gode maka ga binta cewar

Abu Dan rainin wayo da

sassafen nan a aiko gidan

mutane ace suzo ko uwar me

za a mana cewar Binta Abu

tace Kema dai kya fada

gamunan ana surfo mana

zancan banza Eh waye yake

zancan banza ke kuma Binta

ba a koya miki gaisu waba

bakya ganin manyane a gurin

nan cewar liman dake zaune

a gefen me gari Binta da

umma suka samu guri suka

zauna Abu tace Wanda

yatsargu dahi nake Babba

bangan shiba saidai naga me

gari tinda ba a barni naci

abinci ba nazo nan to kowa

yayi hakuri da abinda zeji koya

gani cewar binta Liman yace

kaji yara da rashin kunya

Barsu dani liman cewar

megari Umma ta gaida me

gari binta kuwa aikin gun guni

kawai takeyi Sauran mutanen

gurin hanci a to she sun kasa

cewa komai daga liman sai

megarine kawai suke magana

Binta kinji wai dan mun daki

wa yancan 'yaran hine aka

kawo mu nan gasu 'ya'yan kuli

da mai cewar Abu Binta tace

Kan uba Yasin bazan zauna

ba akan su aka hanani cin

abinci tafiya zanyi Yasin

karki yarda binta kanki tafi

kizo ki daki rabon ki zan taya

ki cewar Abu Sukayi kansu

zasu daka liman da megari

mutuwar zaune sukayi wato

kanhin jikin Abu dana binta da

itama tafara hawa layi sukaji

sukayi lup kamar basa gurin

Megari yace Karku sake Ku

tabasu kuna jiko wai warin me

nake ji haka ina kuke kusa

baki mana meye aikin ku

liman Caraf Abu tayi da

cewa nice nan kanhin tirarena

babu inda baya zuwa megari

ka gode Allah tinda kaji

kanhin tirarena Megari yace

Tirare kuma tab Wannan uban

warin shine tirare

.

liman ba lbr yakasa cewa

komai sai kallo da ido sauran

ma sunyi shiru Megari cikin

bacin rai yace waime nake

gani haka kun dena magana

ne kuma banson sha shanci

kunwani zuba min ido me

kuke nufi Me gari sai hakuri

binta Abu kuzauna cewar inna

da umma Binta hannu a dun

kule tana shirin kai naushi

take cewa Inna kubar mu

dasu yanzu mu koya musu

hankali Nura cikin muryar

tsawa yake cewa kuzauna

karku bari na kara magana

Ganin fuskarshi ba alamar

wasa yasa suka zauna

Megari yace gaskiya yaran

nan abin naku azimun ne

kuma da laifinku wajan bata

yaran nan kuduba fa Ku gani

baruwansu da babba koyaro

duk wanda ya musu yi mishi

zasuyi Me gari ayi hakuri

zamu gyara insha Allah cewar

umma Me gari yace To shi

kenan gaskiya kudau mataki

inba haka ba ni da kaina

zandau mataki Wani yaro ya

fito daga gidan me gari

hannun shi rikeda samira

Tinkafin ya karaso Binta

sarkin kwadayi tafara hadiyar

yawu wayanda suke kusa da

ita saida sukaji karar Yaron

ya gaidasu ya ajiye kwanon a

gaban liman Binta idonta na

kan kwanon ko kiftawa bata yi

ta janyo kwanon kusada ita

Kanshin abinci yadawo da

liman daga dogon suman da

yayi Liman yace Ke me kike

nufi yajanyo kwanon gaban

shi Binta ko magana ta kasa

hankalinta nakan kwanon

Liman Allah ya yanka maka

binta taga abinci ranta ya biya

dan haka ka bata taci cewar

Abu Liman yace In naki fa

dawani bakinki dayake zuba

wari anya kina wanke shi

kuwa Abu tace Yasin wanke

baki kahe hakori yake hiyasa

bana yi liman kaida kanka

kace hi bakin me azumi

kanhin Almuski yakeyi hiyasa

nima na dena wanke baki

saboda Almiskin yazauna a

bakina nafita daban daku

nawa basai ina azumiba ta

fada tana Dariya Liman baki

yasaki yana kallon Abu

Megari yace ke Abu anya kina

da kai kuwa Abu tamika

mishi kanta tace shafa kaji

Inna ta rufe bakinta tana

kallon Abu Megari ina fada

maka saika dauki babban

mataki akan Abu da binta

cewar liman Bakomai kubani

lokaci zansan abinyi kuna iya

tafiya amma kubar binta da

Abu liman ze musu fada

cewar megari Waaaanii

gaskiya babu abinda zan iya

fadawa wayan nan yaran

banshirya takun saka da suba

sunyi nisa basa jinkira cewar

liman Yi shiru liman nagama

magana cewar megari

Inna,umma da Nura suka tafi

Binta batama San tafiyar suba

itadai burinta taji abinda ke

cikin kwanon a cikinta Liman

kabata abincin nan taci yasin

tanada cutar duka idan aka

hanata abinda takeso hine

suke tahi cewar Abu Liman

Ya kalli binta dake zaune

hannu a dunkule ido akan

kwano tana sude baki Liman

yace Me gari Abuya tabbata

duka zatayi kalli kaga

.

Liman karka zama soko mana

kayi musu fada sutashi su tafi

ita kuma binta ka bata taci

cewar megari Kwanon ya

miki mata ta ansa tabude tana

ci kamar kura yaga nama

Binta ta gama ci tasa kafa ta

ture kwanon ta kalli 'yar me

gari tace jeki kawo min ruwa

Niii kalle ni sama da kasa nayi

kama da 'yar aikin gidan Ku

cewar yar me gari Zancen

banza meye dan kin debo min

ruwa yan matan garin nan kaf

yan aikina ne saboda na fisu

haduwa cewar Abu Ya isa

kunutsu kuyiwa kanku fada

kungirma aure zakuyi gidan

wani zaku kuyiwa Allah

kudena abinda kukeyi Dariya

suka yi suka tafa kinji wai

aure cewar Abu Binta tace

kaika sanshi nidai tinda ba a

bani ruwaba bangode ba taso

mu tafi To tace suka tashi

zasu tafi Binta tarike ciki

tace washiii cikina ya

motsa Binta tayi nishi

saiga tusa ya biyo baya

Megari yatoshe hanci yace

liman Sa a kamo min yarin

yarnan Binta da Abu najin

haka suka sa gudu

****

*WACECE BINTA DA ABU*

ABU 'yace ga munzali

malam munzali fatauci ne

sana arsa shikadai yake tafiya

inya tafi saiya jima kafin ya

dawo sai matarsa Suwaiba

yaranta na kiranta da Inna

yaransu 4 Ramatu itace ta

farko tana aure a garin da

suke me suna *DARAUDAU*

sai zulai itama tayi aure sai

Nura da Zainabu Abu itace

auta

ABU yarin yace mara tsoro

duk girman mutum inya mata

saita mai farace tas amma

qazanta ya maida ta baka dan

qazanta kokitso intayi saiya

dankare layin ya bace kafin

inna tai mata ta karfi ta tsefe

Binta 'yace ga murtala

Malam murtala mahaucine

Allah ya masa rasuwa tin

Binta tana karama a hannun

ma hai fiyarta ta tashi sunan

ta Baraka binta kadai ta

haifa BINTA yarin yace

mara nutsuwa ga kwadayin

tsiya idan taga abinci jikinta

har rawa yakeyi itama bata

barin ta kwana dan haka tasu

tazo 1da Abu gasuda

taurinkai

*****

Binta da Abu na cikin gudu

wata yarinya kanta dauke da

buhu ta tsaya a gaban su ta

shaki wuyan Abu Ke meye

haka a ina nasanki cewar

Abu Tace idan maye ya

manta uwar diya bazata

mantaba nice wadda kika

daka kika cimin gyada kika

kuma zubarda sauran Abu

tace Kinsan abin da yawa

yanzu me kike nufi da kika

shaki wuyana Dukanki zanyi

na kwashi saura nakai

gidanku cewar yarin yar

Banga Alamaba ance da

kuturu a gama lpy ni Abu

banga wanda ya isa yamin

abinda kika fada ba ba a hai

fehiba Binta tace ke ware

inba haka ba hmm jiki zeyi

tsami Ke waya sa dake ni din

nan da kike jida gani ban

tinkare kuba saida na samo

makarin ki ke binta dan

nakula kema matsalace ta

daban cewar yarin yar

Makarina kuma ni binta

banganshiba anan gurin yau

banga abinda zesa na bar

kiba batareda na sosakida

bulala ba Ko to shikenan nida

ke za a ga me gaskiya yarin

yar ta Bude buhun taciro

goriba,kurna,magarya da

gyada Tinda ta Ciro Binta ta

hadiyi yawu kamar yanda ta

saba tabi hannun yarin yar da

kallo Abu tace Ke karki sake

ta rudeki da abin hannunta

Binta nizan siya miki fiye

dahi Ko jinta binta bata yiba

Tamika hannu alamar ta bata

harya rinyar ta miko mata

saita janye Binta tace meye

haka kuma bana son irin

Wannan Kina zaton kai tsaye

zan baki batareda na kafa miki

doka ba Meye dokar cewar

Binta Yarin yar tace zakiyi

Alkawarin cewa bazaki sa

hannu a fadana da Abu ba

inkikasa hannu zan kwace

abina Binta ta kalli Abu ta

kuma kalli ledar hannu

yarinyar da irin abinda ke ciki

Nan tashiga raba

idanu

.

Jikin Binta sai rawa yake

Na amince bani Yarin yar

tace in na baki ki tafi ko

juyowa karkiyi Binta tace to

bani dai Tana ba binta

tawuce ta tafi Yarinyar tace

yanzu daga ni seke Abu

tace hakane kuma zam miki

dukan tsiya kamar mu2 muka

miki Yarin yar ta kama Abu

da duka Abu na ramawa Abu

ta Bude baki ta sakar mata

cizo a hannu Waiyoo kika

cizeni Yasin bazan yarda ba

koni koke a gurin nan cewar

yarin yar Saukar duka yarin

yar taji bazata koda ta juyo

Binta ta gani zatai magana

binta ta dauketa da mari binta

da Abu sukayi mata taron

dangi saiga yarin yar a kasa

wanwar tana kuka Abu ta

bude buhu ta leka taga garin

tuwo tayi dariya Binta ta daga

ta juyewa yarin yar a jiki

Inkinje gida saikiyiwa tsohuwa

bayani yanda Akai da garin

tuwo cewar Abu Suka tsalla

keta suka wuce Binta tace

Abu kina jin abinda liman yayi

mana dan yaga me gari

waimun girma aure zamuyi

Rabu dashi nasan abinda za

muyi mihi damu yake magana

ba a taba mubama munyi fada

bare ka ta bamu zomuje

cewar Abu Ina zamu cewar

binta Zaki gani cewar Abu

Koda suka tafi basu tsaya ko

ina ba sai gidan liman Abu

tace Sallama Alaikum goggo

me tuwo Goggo me tuwo ta

amsa da Wa'alaikumus salam

Abu Binta yaukune agin

namu Eh wlh cewar Binta

Goggo me tuwo tace Gashi

kuma ban gama tuwonba

yanzuma na dora Bakomai

mu abindaya kawo muma

daban ne bansan ta yanda

zanfara fada mikiba goggo

cewar Abu Kar kuji komai

kufada min idan baku fada

minba wazaku fadawa bayan

nasan Ku tin kuna yara nan

kuke zuwa cintuwo cewar

goggo Binta tace Hakane

munsan da wannan goggo

hine dalilin da yasa mukejin

nauyin abinda zamu fada

miki Binta Abu kufada min

bakomai komai girmanshi

zansan abinyi Abu tafashe da

kukan karya taceTo hikenan

goggo kiyi hakuri da abinda

zakiji sai Abu takara sautin

kun da takeyi Binta ma kukan

karya takeyi tace yi hakuri

Abu bakomai sakai yar daze

mata kenan Nanfa hankalin

goggo ya tashi tace kunga

kufada min duk kunbi kun

daga min hankali Abu tace

goggo dagir manki da komai

liman ze miki kishiya Gogo ta

mike tsaye tarike kirji tana

huci

.

Ni liman zewa haka zezo ya

sameni bemin kishayaba tin

ina yarinyata saiyanzu dana

tsufa Goggo abinda ze kara

daga miki hankali hine irin

kalaman da yake mata idan

yaje zance cewar binta tafada

tana kuka Dan rahin mutunci

hine ta aiko mu da kala man

soyayya muzo mu fada mihi

Takuma ce karya manta yau

yazo zance ita kadai tasan

abinda ta tana dar mihi cewar

Abu Kafar goggo ya haurawa

taji juwa na ibanta tajin gina

da bango ta ciji lebe a nan

gidan ze kwana daiko

badamuwa ina jiranka cewar

goggo Binta takara sautin

kuka tace babban abin hine

mahaifin yarin yar yace liman

yaturo anbahi ita Suna fada

goggo ta zube kasa ba

nunfashi Munhiga 3 Abu

munyi kisa cewar binta Abu

tace ke bata mutuba tsabar

kihine kawo ruwa kigani

Binta takawo ruwa Abuta

watsa mata taja dogon

nunfashi tabude ido tana

Cewa ina yake kumiko min

shi Abu tace goggo aibaya

nan bari zahigo saiku yita

takare Goggo tace bakomai

zaka dawo kasa meni liman

nida kaine yau agidan

Goggo mu zamu tafi Nagode

muku binta da Abu Allah ya

muku Albarka Goggo me

tuwo macace me kishi akan

kishi zata iya yin komai sanin

hakane yasa Abu da binta

sukazo gurinta sunsan ita zata

hukun ta musu liman yanda

suke so Ameeen goggo

aiyiwa kaine suka ce suka

nufi hanyar fita harsun sa

kafa zasu fita Abu ta gano

liman yana ta howa da alama

gidan zezo da sauri ta riko

binta suka boye cikin wani

duhuwa dake zauren gidan

liman Liman yayi sallama ya

fada gida kai tsaye ya nufi

bandaki Goggo na jinshi

binta da Abu Suka dauke

sawun takalmi suka matso

tayanda zasuji kuma suga

Abinda ke faruwa Liman

yafito yashiga daki yasa

sababbin kaya yafesa tirare

Nanfa kishi ya turnike goggo

me tuwo tashiga waigen

Abinda zata samu tarike ta

hukun tashi dashi Me gari ya

fito yana gyara hula yace in

na kike na fito zan tafi Goggo

tafito tana huci tace nasani

kagai sheta wato danka raina

min hankali nika ajiyeni a gida

kaikuma ka fita kana neman

aureko har ance katuro Yace

ni liman a ina kikaji zan cen

nan wlh bana ne man aure a

ko ina ni liman ke kadai kin

ishe ni Tace karyar banza ba

abinda zaka fada min na

yarda bayan nasan komai

yanzu kayan nan dakasa

kafesa tirare ina zaka Abuda

binta na labe suna ji kuma

suna ganinsu suna dariya

Yace daliban malam rabi'u ne

zasuyi sauka yau shine aka

gai yace ni na shirya yanzu

zan tafi Bata gamsu da

abinda yace ba yasa tafara

buga kafa tana tsaki

.

Tace malam malam ni goggo

ni zakai wa kishiya Tana

juyawa taga murhuna cida

wuta ta Ciro icen dayafi ci

tasa mai ababban Riga wuta

yafara ci liman na ihon

temako yana kokarin cire

baban riga dakyai ya samu ya

cire abin beyiwa gogoba ta

dauko tukunyarda ta gama

hada kayan hadin miya ta

kwaramai a fara ren kayan

shi Binta da Abu dariya

harda faduwa Ta rarimo

bokiti tana jifan shi dashi

ganin abin nata bana Kare

bane yasa liman ya mike ya

zuba da gudu Binta da Abu

suka Tsaya a gaban shi

Abu tace liman mun girma

aure zamuyi ko toga auren

mun gwada maka tafada tana

dariya Binta tace waiyoo

cikina liman mezan gani haka

yazaka gudu kaida yadace kai

mata fada kamar yanda kayi

mana dazu Amma dai yaran

nan kwai shedanu kune kuka

hadani da matata bakomai

dani kuke magana Abu tace

gogo me tuwo gashinan

Liman yasa gudu binta da Abu

na dariya Raina fesa cewar

binta Duk wanda yace ze

higa harkarmu to yadebowa

kanhi kwarkwasa cewar Abu

Sukayi dariya suka tafa Suka

nufi gidan su Abu Liman be

tsaya ko inaba sai fada gurin

me gari wayanda suke tareda

megari ganin liman yashigo

da gudu suma suka mike

zasu gudu Megari yace

kudawo Ku zauna liman

mezan gani haka da girmanka

da komai Allah yabaka

yawan rai ai duk abinda ya

sameni kaine sila saida nace

ba fadan da zanwa Binta da

Abu kace kaisam saina

musu gashi abin daya jamin

dagir mana da komai na yanko

ta cikin unguwa da gudu kowa

na kallona Yanzu binta da

Abune sukai maka haka a

garin nan cewar me gari

Liman yace hmmm ni nasan

su sarai shiyasa tin farko naki

kadage kace sainayi yanzu

gurin saukarma ba halin

zuwa ta kona babban rigar

sukuma wayan nan kaga dai

yanda tai musu harda manja a

jiki kamar za a Kada miya

gashi badamar na koma gida

yanda ranta yake a bace Kai

kutashi kuje Ku ne mo min

su A'a kudawo Ku zauna

Allah ya baka yawan rai

nayafe Abarsu kawai nidai

goggo me tuwo itace kadai

damuwata ita taimin hakafa

.

Nan yakwashe duk abinda

ya faru yafada wa megari

Shine zakace a barsu gwara

mu koya musu hankali cewar

megari Eh Bakomai a barsu

cewar liman To shi kenan

zansa a kiramin gogo me

tuwo zan mata bayani karka

samu damuwa To shikenan

godiya nake Allah ya baka

yawan rai Kai tsaye suka

shiga gidan ba sallama

Yaushe zaku girma abin naku

kara lala cewa yakeyi ko Abu

da Binta cewar Inna Saida

suka samu guri suka zauna

sannan sukace salama

Alaikum Inna tace Allah

nagode maka binta da Abu

Nura yatafi maka rantar boko

Yinme inna cewar Binta Inna

tace Yaje saku a maka rantar

boko daga nan yamai daku

isilamiya dan harda rashin

ilimi a abinda kukeyi Abu

tace Boko tab ba inda zani

Inna bokoko awuta kike nunfin

zamu toko su yan bokokon

Awuta tsoron bokon sukeyi ba

inda zani saidai ko binta gata

nan Waaaaniii tab namutu

Allah yasani awuta ba bokon

da zani cewar Binta

.

Wlh baku isaba haka kuke so

mu zauna daku a jahirce

cewar Inna Yasin bazani ba

wuta tsilim cikin sauki bokoko

Awuta bada niba cewar Abu

Binta ta tashi daga inda take

ta koma kusa da Inna Tace

Inna kisa baki akahe maganar

nan dan baze taba yiyuba

Yasin haka kawai ze Kaimu

lahira da kanhi Kanshi kanshi

inna taji yana tashi A jikin

Binta Tato she hanci tace

Binta warin me nake ji haka

kardai kema kinhau layin

rashin yinwanka Dariya Abu

tayi tace Inna nice nan

nadorata alayi tam bayeta kiji

ita kanta tafijin dadin jikinta

yanzu fiye da da Rufemin

baki sakarai qazama nayi

dake *'YAR KWALLIYA* Binta

kiyiwa Allah karki bari Abu ta

koya miki rashin Wanka da

Wannan maya taccen

KWALLIYAR nata Inna saidai

kar a kuma dankuwa karatu

yamin qanhi yabi jiki bakiga

irin kallon da megari yake

minba nikadai nagane meyake

nufi cewar Binta Abu tace

Nagani rabu dahi binta ze

fado hannu banda hima ya

tema kawa kanhi besa bakiba

aida tuni munkoya mihi

hankali kamar yanda muka

koyawa liman Oohni Inna ina

zansa kaina nan nasamu lbr

anga liman yana zuba gudu a

gari har ana zaton ya Hauka

ce ashe ba Hauka cewa

yayiba gamo yayi da 'ya'yan

Aljanu binta da Abu babban

gamo yai cewar Inna Abu

kwaso kayan KWALLIYAR

muyi muje gidan Amaryar da

aka kawo nan bayan layin ku

cewar Binta Abu tace Hakane

fa banjeba kuwa Tashiga ta

dauko ta ajiya a gaban binta

Inna tace shiyasa tin farko

banso qawan cen kuba wlh

nasani sarai cewa abinda kuke

da NA yanzu saiya fishi kuma

gashi na gani Suka kafe inna

da idanu Inna tace bance

komai ba ni badaku nakeba

Allah yabaku hakuri Suka juya

suka cigaba da KWALLIYA

Salama Alaikum inna nadawo

Wa'alaikumus salam gonda da

Allah ya kawo ka Yi shiru

Inna nasamu lbr komai inaji

nasan sune zasu aika tawa

liman haka komai yazo karshe

na sasu amaka rantar boko

hakama isilamiya ga kayan

maka rantar nasu

Alhamdulillah shikenan

kurinkus kandan bera boko

Saikun je kokuna so ko ba

kwaso cewar Inna Abu tace

Boko Boko dai hikenan naji

duk abinda ake fada akan

boko ance yan wutane hine

mu za a kaimu saboda ba a

sonmu Ba a San naku gobe

zaku fara zuwa daga nan idan

kuntaso saiku wuce isilamiyar

malam rabi'u Binta ta tashi

ta daka tsalle tace rabi'u

Yasin ba inda zani Wannan

bakin mugun baki da Wannan

kan nahi dayake kyalli kamar

an cirohi A tandun mai

Malamin naku kinga binta

nasan irin takun sakar da

kukeyi da malam rabi'u idan

kika bari yakawo min karar ki

kikuka da kanki irin dokan

dazan miki baze faduba harda

ke Abu cewar Nura Abu tace

hikenan dai zamu leka wutar

bakomai amma idan mukaji da

zafi bazamu sake koma

waba Tsaki Nura yayi yatafi

ya basu guri Sukaci uwar

KWALLIYA suka fice basu

cewa Inna komai ba

.

WASHE GARI Abu tana tashi

tasa kayan maka ranta ta

janyo kayan KWALLIYA zata

yi Nura yace karki sake kiyi

KWALLIYA makaranta zaki ba

dandaliba Abu tace Tab yaya

Nura gaskiya bazan iya fita

banyi KWALLIYA ba ga kanhin

tirare i nayi Amma ba

KWALLIYA a fuska ta Nura

yace Eh ba a KWALLIYA idan

za aje makaranta Abu dole

kidena wasu abubuwan yanzu

tinda kinfara zuwa

makaranta Binta ta shigo ba

sallama agaban kayan

KWALLIYA ta zauna zatayi

KWALLIYA Nura yace ke

Binta ba sallama Bakomai

kiwani zo gaban kayan

KWALLIYA Binta tace yaya

Nura tinda nafito banyi

magana da kowaba Gahi

yanzu kasa nayi magana

Almiskin bakina yafita Hanci

yatoshe yace naji Almiskin

kice kema kinbi layin qazantar

Abu ko makaranta zaku zakuje

kuga yanda Ake safta Binta

tace *'YAR KWALLIYA* mezan

gani haka meyasa bakiyi

KWALLIYA ba Abu tace Binta

kibarni kibarni kwai ni Abu

*'YAR KWALLIYA* ni za a

hana yin KWALLIYA badole

kiga haka ba Binta tace

shine kike daga hanka linki

ina Inna Abu tace tana ciki

Binta tace yaya I na bayanka

gwanda daka hanata bani

kayan KWALLIYAR NA shiga

dasu au baza kibaniba bari na

dauka da kaina Binta na

shiga ta juye kayan

KWALLIYAR a Jakarta tafito

Binta tace bata cikifa Abu

tace hakane yanzu ta fita

zomuci Abinci bayan sun

gama cin Abinci Nura ya

kaisu maka ranta Duk wanda

yaga fuskar Abu ba KWALLIYA

sai yayi mamaki dan bata taba

fita ba KWALLIYA ba Suka

shiga Aji Binta tace Abu

Albishirin ki Abu rai a hade

tace goro Binta ta bude

Jakarta tace kalli Abu cikin

mamaki tafasa kara ta

rungume binta ta tsalle a

aji Hankalin daliban ya

koma Kansu Abu tace muna

fukai me kuke kallo da sannu

duk zanyi maga ninku

.

Daliban Suka dena kallon su

Suka baje kayan KWALLIYA

sunayi malami ya shigo aji

akatashi ana gaisuwa banda

Abu da Binta KWALLIYA kawai

suke yi Malamin ya karaso

gurin su yace Ku meye haka

kwalliya a cikin aji me kukeyi

a nan aji bantaba ganin kuba

Abu tana shafa Jan baki tace

baza kasan muba hime maka

rantar be sanar dakai komu

suwaye bako hege wato ya

cinye kudin ko to hikenan

Yace bagane me kuke nufiba

fa Binta tace kaga waimu sa

babbin dali baine kuma nanne

ajin mu kana jiko jeka to

Yace kee Nifa malamin kune

kibani girma bakowana

magana zaki dinga fada

minba Abu tace inji kaba

girma idan karike girmanka

mutayaka rikewa idankuma

kaki rikewa mubi takai mu

wuce Malamin yayi

murmushin keta yace kugoge

fuskarku sannan kubani kayan

KWALLIYAN Abu tace tab ba

abinda zamu baka kuma ni

Abu bazan goge KWALLIYA ta

ba Binta tace nimadai bazan

gege ba malam kabar daliban

naka a tsaye fa Yace kuzauna

yayi murmushin yaje gaban

Allo yafara koyar dasu kamar

yanda ya saba Abu tace

gaskiya nagaji baza a yi wani

abin bane bayan Wannan kazo

ka I hemu da surutu Binta

tace a he kekina jin hi tinda

yafara har I yanzu banji

komai ba ni yunwa ma nakeji

Yace Anya karatu kuka zoyi

kuwa Abu tace waya sani

Abu a duhu Nifa karatun higa

wutan nan beda meniba dahi

da bahi duk1ne bokoko

Awuta Binta tace gaya mihi

kadai koyarda su dan naga

kamar suna gane wa Yace

anya Ku muta Nene kuwa ke

dawani fuskarki kamar aljana

waya gaya miki karatun shiga

wuta nake koyawa Binta tace

baka jiba bokoko a wuta hine

zakace bakaratun higa wuta

bane Yace kutashi Ku fita

daga ajin nan kufita kuyi shir

menku a waje Abu tace

seme danka koremu kahiga

wutar kaika dai kacike gurin

karkabari asa wani Yace keni

zaki fadawa haka Tamurguda

baki Yadauko bulala ya zuba

mata Tasaki kara

.

Binta tace meyasa ka daketa

kai ko a qauyen mu mune

muke yiwa maza duka

hmmm Yace me kike nufi

nima dukana zakuyi kenan

Abu tace meze hana tinda ka

dakeni saina rama Yace waya

gaya miki idan malami yadaki

daliba tana ramawa Binta taja

hannun abu Tace Abu rabu

dahi zomu fita ze fito ya same

mu damu yake maga mekoya

karatun higawuta dole mukoya

mihi hankali Suka fita

Abu kinga ya aika a siyomai

abinci Abu tace waye

ya aika asiyo mihi abinci

mekoya karatun higa wuta

Binta tace Eh hine zomuje

Yaron ya siyo abincin zekai

wa malam binta da Abu suka

tsare shi Abu tace Kai bamu

abinci kaje kadebo min ruwa

zansha kagani ba quwace

Yace malam ya aikeni bari

nakai mishi nadawo saina

debo miki Binta tace harna

hadiyi yawu banga abin dake

cikiba amma nasan zeyi dadi

tafada tana dariya.....


0 Response to "'YAR KWALLIYA Hausa Novel"

Post a Comment