-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

YAA SHEIK Hausa Novels

YAA SHEIK Hausa Novels

 [21/04, 9:59 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



            *_YAA SHEK_*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ  





๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*๐Ÿค๐Ÿป


*_BY : U.K.Y for real_*


*_Dedicated to Mmn khaery_*





 ```Assalamu Alaikum yan uwa musulmi wannan littafin nawa nayishine ba Don wata ko waniba ko Don cin zarafin wani ba aa kawai sai Don nishadi ,fadakarwa da kuma wa'azin tarwa ina fatan yadda na fara lafiya na gama lafiya```




              1⃣to5⃣



Tashin kira'ar Yaa shek ne ke tashi tun kafin ka karyo kwanar islamiyar mai suna Sahsib kasancewar Allah y hore mai murya gaza'ki ga balaga, kowanna harafi yana fitarwa bisa ka ida


 d'alibai ne a zaune cikin wani aji, matasa ne maza d mata jikin su sanye da uniform maroon color suna zazzaune kowa d al'quran a hannun sa sun nutsu suna sauraran karatun



 shikuwa malamin nasu wato Yaa  shek yana kan wani benci yana ta rero karatun cikin kwanciyar hankali da nutsuwa idon shi alumshe saboda shauki, da ka yake karatun kasan cewar shi hafizin al qur'ani,


sanye yake da wani  hadaddan yadi milk color yasha guga, da wata hula brawn,kasan cewar aykin dake jikin kayan ma brown ne, kannan yasha gyara sumar nan baka kirin tayi luf luf da ita takalmin ma brown ne yasha mai sai kyalli yake wandon nan a d'age kai daka gani kasan sunna ta ratsashi ga wani gemu mai ban sha'awa yazauna das dashi sai 'kamshi yake kanagani kasan cikakken mai tsaftane,



Yana kaiwa karshe wata aya yace sadakallahul aziim kafin ya 'Dan nisa yadago kyawawan manyan idanun shi yana kallon yan ajin d'aya bayan d'aya yai gyaran  murya yace lokacin fitasalla yayi karfe hud'u da minti biyar duk Wanda bai shigoba to kuwa bazai shigoba yana kaiwa nan ya mike yafita 


Ayko yana fita mazan da matan suka hau shewa suna cewa yaaaa sheeek d'aya daka cikin yan matan ce tai magana tana cewa kunga kutashi muyi sauri mu dawo Don ni wlhy dana rasa lecture din yaa shek gara nai zazzabin wuni Don nasan idan na rasa dolene sai nayi 


Caraf wata tace ayke zazzabi ma kikace da sauki wata tace nidai wlhy idan namakara zama zanyi naita kuka har sai yace nashigo, ayko kinsan yaa shek ba cewa zai yi kishigoba Don haka kunga tafiya ta ayko  gaba daya yan ajin suka rufa mata baya,



 suna zuwa wajen sallah wasu yan mata biyar sukawo Kansu d'aya daga cikin yan matan nan tace wayyo kunji dadin Ku yau yaa  shek a ajin Ku yake wata takuma cewa kai kugayama na yau wani kalar wanka yayi d'aya tasake cewa nima abinda nakeson ji kenan d'aya daga cikin wayanda yaa shek yafito daga ajinsu tace wai saurin mekuke? nagadai zaku ganshi sai kujira yafito daga office naga kuma Idan a ajin Ku yake bakwa gaya mana Don haka kujira suna cikin haka kuwa saiga yaa shek yafito daga office,

yana takawa cike da kasaita d gayu  yana goge fiskandhi da wani Brown hankacif da alama alwala yayi ayko suka bishi da ido  






Afilin makarantar d'aluban sukeyin sallah Don haka tako ina dalubai ne suna jira atayar da sallah   




Yaa shek matashi ne mai shekaru ashirin da bakwai 'Dan gayu ga tsafta uwa uba ilimin addini da na boko masanin hadisai da littafan addinin islama ya gama degree dinshi a usman dan fodiyo university sokoto ya karanci 'bankaran hadisai da zamantakewar aura tayya hakan ne yasa hukumar makarantar suka bukaci yadinga yima d'aluban da zasuyi sauka lecture duba da yadda aure yake mutuwa da wuri a wannan zamani Don haka d'aluban keson ya shiga ajinsu saboda yadda Yaa shek yake warware musu zare da abawa ga daukar wanka, 

wasu daga cikin daluban sonshi suke wasu kuma burgesu yake ajin yan sauka guda biyu ne  Don haka yau idan yashiga daya gobe sai ya shiga daya cikakken sunan sa kuwa Abdallah Gaddafi a makaranta ne d'alubai ke ce mai Yaa shek batun aykin gwamnati kuwa yana nema saidai har yanzu shiru,





Sauri sauri suke saboda su koma bayan kowa ya hallara saiga Yaa shek yashiko yana shikowa duk suka nutsu sabada sun san bayason hayaniya kuma yana iya korar mutun  


Bayan yadai daita zaman shi ne a kan bench din ne yace kundai San dokokina ko?kuma kunsan hukuncin Wanda yasaba min Don haka ba bukatar na mai mai ta suka hada baki wazen fadi na'am yaa shek 



ya nisa ya cigaba da bayani daga inda ya tsaya jiya. 


Baki iya hiraba baki iya kwalliya ba baki iya shagwa'ba ba baki iya komai ba kuma kina korafi wai lado baya dawowa gida da wuri to taya zai dawo d wuri bayan in ya dawo d'in ma yasan kayan haushi zai gani, 

kuna kallo a tb an nuno wani dan wasan kince wai ke wannan gayan yana burgeki duk a gaban lado yo ba lado ba ko ni ne sai na shanbe ki ina mijinki kice wani yana burgeki agabana ta yaya kuke tunanin aure bazai mutuba?  



duk yana maganane yana kallon gurin d 'yan matan ke zaune Don dasu yake, kafin ya dawo da kallonsa gurin mazan yana mai cewa 



"kai kuma lado baka iya siyan brush ba baka iya shiyan acuci maza ba baka iya siyan kayan kwalliyaba inzaka shigo gida kazo rannan abace, kana tsamin daud'a kashige gansan gansan ba fara'a,tayi tayi da kai kayi wanka kace kai baza kaiba sannan kuma kazo kana mata Yar murya idan dare ya tsala" 




ayko duk d'aluban dariya suka sa kasa kasa Don kar yajisu,

  haka tsarinsa yake yayin lecture idan zai bada misali akan namiji sai yace lado idan mace ce sai yace kande ,


shikuwa ko ajikin sa da irin wannan Jan hankali da nasihohi lokacin tashi yayi yayi musu addu'a ya fita sannan d'aluban kowa ya watse,

 saida yashiga office y dauki littattafan sa sannan ya kama hanya yayi gida.

[21/04, 9:59 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ            

                   

                 *_YAA SHEK!!_*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



*BY:U.K.Y.       for real*๐Ÿ˜˜




๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*๐Ÿค๐Ÿป


*_dedicated TO mmn khaery_*๐Ÿค๐Ÿป









                     5⃣to1⃣0⃣




Z,aune suke a tsakar gidan nasu, ummee da abdulmalik da abdul majid suna kan tabarma,



Shi kuwa yaa shek yana gefen  su akan wata katuwar sallaya,  waya ce a hannun shi  yanajin wa'azin Dr Zakir Naik, 


Ummee ce ta kalleshi tace Abdallah wai baza kaci abincin bane? 


Nace a kawo ma abinci kayi shiru,


 ummee nah zanci mana, 


 ay nazata baza kaci bane da naji kayi shiru, abdulmalik  jeka ka dauko mai abincin shi ya nanan a flas sai ka dauko cokali d flet, 



Kawo masa abincin yai gaban sa ya ajiye ya koma ya  zauna,  


dago kai yayi ya  kalli k'annan nasa wato su abdulmajid,sannan yace "wai kuwa ma kunyi hadda ne kukazo kuka zauna kuna wa muta ne surutu?"



Nidai nayi  inji Abdulmalik, shi kuwa abdulmajid cewa yayi ni saida asuba zanyi yaya Abdallah wlhy idan nayi yanzu ba zai zauna ba, 



umme ce tace bazai zaunaba?!  dama bakaso yazauna ba ne.   sai asuban tayi Ay  ta tashinka kaki tashi makaryaci,   wai saida asuba kamar da gaske,


Shidai Abdul majid bai sake cewa komai ba don bayaso a ja zancen da yawa ga ya Abdallah agurin, yasan Zane mai jiki zaiyi don ya Dade da fuskantar ya abdallah 'kyaleshi kawai yakeyi amma yasan sarai ba kararun yakeba.



Acikin su ukun Abdul majid ne yake da wasa ba shida maida kai a karatu, amma alamu sun nuna Abdul malik zai biyo hali irin na yayan nashi wato Yaa shek.


Shima Abdallah shiruyayi da kudurin zai gyarawa yaron nan  zama a zuciyar shi,



Suna zau nan ne kowa yayi shiru suka jiyo kuka a ma'ko tansu,   da suke Katanga d'aya da su, wato gidan kanin babansu baffa usman mai rasuwa




ihu take tana kiran yayyo ummee nah wayyo yaya Abdallah nah kuzo kutai makeni nidai wlhy bazan ci ba,



Ummee ce ta ce ikon Allah waye kuma yake dukan min yarinya a cikin daran nan?



Abdul majid ne yana dariya. yace wlhy ba wani duka in kin bibiya ma'kiyin ta  akace taci   wato   tuwo  shine  take  wannan ihun

 kamar ana yankata, sai kace  bakusan halin  *Jidda* ntaku ba,


Wlhy kuwa  inji Abdul malik  yana 'kyal,kyala dariya shima



To ay sai a 'kyalemin yarinya ko a dafa mata indomie din nata data keso ko? Yariyar nan da gaske take batason tuwon nan tunda idan tacima sai tayi aman sa don haka sai a kyale ta,   kai Abdul malik  jeka ka gani mene ne idan tuwan ne baza taci ba ka kawo min ita ga abincin yayan kunan tunda bai ciba sai a d'iba mata,



Yaa shek da tunda yajiyo ihun Jidda ya kasa kunne yanaso ya gane me take cewa don yasan dalilin kukan nata don in akan cin tuwo ne bazai sa baki ba ace yarin ya wai baza taci tuwo ba sai kace ba mace ba ay halin rayuwa ake gudu idan babu halin a dafa mata abinda ranta  yakeso to ayi yaya kenan?



amma duk da haka bazai iya jure jin kukan nata ba saboda bai son kuka balle ma kuma kukan Jidda Yar rigima,




Kai abdulmalik zo kazauna bari na dubo ummee,    yawwa Abdallah zeka kaji.





Yana fita ya fad'a gidan yayi sallama sai da aka amsa akai mai izini sannan ya shiga, (abunka da masu koyi da koyar war annabi Muhammad wato sunnah)




Kafin ya gama shigowa Jidda tayi maza tayi gunsa tana shashshe'kar   kuka    tana ajiyar zuciya kamar wadda akaiwa dukan kawo wu'ka,




A'a baba na Kaine kunjiyo kukan wannan ja'irar ko? 


Samu guri kazauna tana nunamai tabarma, zama yayi sannan ya gaishe ta, 


Kaga baba nah wlhy ko yatsa ban d'ora    a kantaba kawai tuwo na bata nace ta ci shine take wannan ihun tafiso idan na dafa tuwan na dinga   bi makota ina asanmin abincin na bawa Jidda ko kuma  in nemo mata wani abun, duk da ita yarinya ce amma ay kullum girma take kuma koba dad'e ko ba jima.    gidan wani zata.





Hakane mamy kiyi hakuri sai a hankali zata ci ne, yadaga kai ya kalli Jidda da ta make kafad'a ta cuno baki Dan bakin nan mitsil dashi alamun ba 

ranar da zata ci tuwan ,  


       yace ke,    to sami guri kizau na, ayko ta   bare   mai   baki   zata Dora a inda ta tsaya, 


Mamy     tace baba nah baci za tai ba kyaleta kawai kar ta Tara mana jama'a ,   haka take  cemai baban ta saboda su nan baban ta abdullahi.






To shikenan mamy bari naje dama  ummee ce  ta ce azo aduba ko lfa, 

yamike   zai tafi,



 ayko Jidda tace  batasan    zancen ba ita sai ta bishi  don  idan   yatafi   mamy   Zane  ta   za  tai,




Itadai mamy    da kallo  tabi ta don  halin  Jidda sai   addu'a.




Harta rigashi kaiwa zaure tana gaba yana ba ya yaiwa mamy sallama ya fice.



Ta  riga shi  shiga gidan don haka ya hango ta akan cinyar   ummee  tana   ta  zuba  ta'barar  ta dama  halin Jidda ne, 




Ummee nah nidai agidan nan zan kwana yau mamy  tace   saita   Zane    ni  saboda  banci   tuwo  ba, 


  kai jiddo   banda sharrifa inji Abdumajid, 


Ayko tahau shure shure ummee nah kinji wannan yaya abdulmajid din yana cemin jiddo ko? Ta karashe    maganar tana   nuna Abdulmajid da  yatsa  cike  da  shagwa'ba  da  ta'bara,



Abdulmajid banason tsokana  wlhy zan sa'ba maka akan  tsokanar yata da  kake  yi,


To nima sai na rama wool bai iya hadda ba tana nai gwalo ,



Ayko takashe bakin abdulmajid yai shiru an ta'bo maganar hadda,



Abdallah bai sa musu bakiba donshi ta'baran jiddan ma mamaki yake bashi , yafara cin abincin shi da tun dazu da aka ajiye mai,  


tsilum saiga Jidda agabanshi ,  yaya Abdallah nah  abinci  zakaci? Nima zanci, amma nidai a baki zaka bani takarasa maganan kice sa shagwa'ba 


Kallon ta kawai ya tsaya yanayi yacigaba da cin abincin sa 



Ummee kinga yace wai bazai bani ba 


Kafin ummee tai magana ya zuba mata wani razanan nan kallo mai ma'anar ki shiga taitainki fa, 


Ayko tsiiit tayi tana kallon sa kuri da ido, candai dataga ba bata zaiyi ba tace don Allah na ci?




"Jeki wanko hannun ki "


Ba musu raje ta wanko hannun ta tadawo




Yabita da kallo azuciyar  shi  yana tunanin  kai yarinta kenan wai mutun yanajin yinwa amma wai yace bazaici tuwoba  wai   sai  abinda   ya  taza'ba,  ummee ce ta katshe mai tunani tana tambayar shi Abdallah kunyi waya da abii kuwa?



Eh ummee munyi ay goben zai dawo ko ko yasake shawara ne?  



   A'a goben zai dawo dama natambaye Kane ko bai gaya maba,


"Ok ya gayamin ummee Allah y dawo da shi lfa"




"Dukansu suka amsa da amin"


Itako zuwa tai ta zauna jikinta har rawa yake tasa hannu ta fara ci,


Saida suka cinye na fleet dinne yake tambayarta ko ta koshi ,   tace,  a'a  yakara mata shikuma ya tashi yaiwa   ummee     sai da safe  ummee   tace   Allah   ya tashe  mu lfa.           


Yanufi dakinshi dake  zaure ,



Ikon Allah kai bakace  dakin matashin   saurayi  bane  kamar haka ba ,



Dakin bawani babba bane amma  tako ina carpet ne ashinfide da 'Yar durowa ajikin bango mai biyu,     sai    d'an  mirror da turarurruka  kala kala amma dai  bawasu  masu  tsada  ba , sai katifa  dai dai kwanciyar mutun biyu ya lailaye ta da bed shit  da wata anger ta  rataye kaya,   d'akin  fes fes dashi  sai 'kamshi yake kamar dakin budurwa budurwar ma mai tsafta,lol




Kayansa ya rage ya sa jallabiya  sannan ya kuma nufar cikin gida don watsa ruwa da d'auro alwala don  haka tsarinsa yake baya konciya sai da alwala ,     



koda yashiga  har su abdulmalik sun shiga dakinsu ummee ma tadauki Yar rigimarta sunshige, don anan ta bingire bayan tagama tsokanar abdulmajid tai bacci,




Bayan ya gama ne yakoma d'akinshi  ya cire jallabitar ya fesa body spree  yasa wayanshi a chage yai addu'a yakwanta   hadida  addu'ar Allah y sa kar yayi  mafar kin  nasa na  jaraba,


      shi yana mamakin wannan Abu  ace rana d'aid'ai ne ba zaiyi mafarkin yana Tarawa da   mace ba  shidai yasan  bawai yasa son mata  aransa  bane  kuma  yana  azumi litinin da alhamis  kuma  yana kokarin kauda  idon  sa ga duk abinda  zai  sashi jin  shaawa don kare  addimin sa da imanin sa don gudun sabawa mahaliccin sa  




Eh  bazaice baya son kasan cewar mace a kusa  da  shiba saboda yasan shi lafiyayyan namiji ne,



 amma yasan  ba  abu ne   mai yiwuwa ba kasancewar  bashida  ayki  kuma albashin sa na Sahsib islamiyya bawani mai yawa bane,



         kuma abii ma ba wani karfe ne dashi ba sai dai rufin ashiri duk da yasan abii mutum ne mai kokarin   yaga  yarufawa  iyalin asiri,

             


ga iyalan 'kanin shi baffa usman wato     mamy   da jadda duk shi yake dawainiya dasu duk   da  dai tasu dawainiyar ba mai yawa bace saboda mamy tana Yar   sana'arta   don    itama   taga tarufawa kanta   asiri  amma duk da haka bazai iya bijiro da zancen aure   ba   shiyasa  yake kai   zuciyar shi  nesa.





Da ire iren wannan tunani bacci yayi gaba dashi....

[21/04, 9:59 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ

                  *YAA SHEK!!*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



*BY:U.K.Y.          for real*๐Ÿ˜˜



        ๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*๐Ÿค๐Ÿป



*dedicated to mmn khaery*๐Ÿค๐Ÿป




            1⃣0⃣to1⃣5⃣


Koda ya farka karfe hud'u dai dai duk da cewa ya makara tashi sallan dare, amma fa aykin gama yariga ya gama, abun dai da bayaso shi yagani,



Ya Allah wannan wace irin jaraba ce abinda ya furta kenan,


Nifa bansan ma nayi mafarkin ba amma dai gashi alamu sun nuna,    duk shi kadai yake wannan zancen  kamar wani zautacce,


Goge jikinsa yayi yana nai addu'ar kar Allah y sa ummee ta ganshi idan zai shiga wanka don kusan kullum sai ta ganshi kuma ba karamar kunya ce take kamashi ba,   don  yasan  duk  Wanda yaganshi  yayi  wanka da asuba to kuwa yasan me  ya faru d shi,don ma dai   Abii   ba mazauni bane da kunyar sai tafi haka , 


Futowa yayi yana sand'a kamar 'barawo bakin shi d'auke da addu'a,


 ya samu yai wuf yafada toilet sannan yasauke nannauyar ajiyan zuciya saboda ummee bata ganshi ba,



Saidai baisan shine bai gantaba amma ita ta ganshi, don tazo d'akinsu Abdul Malik taga ko sun tashi, tana fitowa ne ta ganshi yana sand'a,


ta koma d'aki zuciyar ta cike da tunanin wai meke damun abdallah,



 kusan kullum sai yayi wanka,to komadai meke damun shi saidai yasama ranshi hakuri don aure ba yanzu ba, shida bashi da ayki.



Bayan yafito agurguje ya shirya yanufi masallaci, 




"Abdul Malik wai bazaku fito Ku karya bane lokaci yana kurewa? Inji umme 


" ummee gamu nan zuwa"



To Ke kuma Jidda aydai yanzu kin bushe ko saikizo nashafa miki mai, 


Turo baki tai tana ma'ke kafad'a "nidai nizan shafa da kaina, wankan mafa na iya kika ce saikin yi  min"


Naji to jeki shafa kifito ki karya inji ummee, 



Suna karyawa ya shigo sai lokacin yadawo saga masallaci, ya  nemi guri kusa da ummee ya zauna yana gaishe ta,


Fuskan ta dauke d fara'a tace lafiya klau abdalah,


 kana azumin kuwa yau alhamis?


A kunyace yace 

"Eh ummee inayi"


 To da kyau madalla Allah ya muku al barka, 

"Suka amsa da amin"


Su Abdul Mali suka gaishe shi shima ya amsa yana mai cewa kuyi Sauri kun kusa makara fa, 



Kafin suyi magana sukaji sallama, mamy ce tashigo hannun ta dauke da uniform din Jidda,



 suka amsa mata, tazauna suna gaisawa da ummee ,     suma duk suka gaisheta ta amsa cikin fara'a  ta Dora da cewa amma dai waccan Yar rigimar ita tashafa wannan man?  tai maganar tana kallon inda jidda ke  zaune da daurin kirji Wanda tayi da 'Dan kwalin ummee,



Ayko su  Abdul Malik suka kyalkyale da dariya, ganin yadda fuskan jiddan take maiko




Sukuwa manyan yara wato Jidda Yar aji daya a primary an sha Vasilin a fuska sai maiko take , kuma ko ahikin ta,



 ta dago ta kalle yaa shek Wanda tunda ya gaishe da  mamy yamai da hankalin shi kan wayarshi,  tace



"  yaya abdallah batajira amsar shiba tadora da cewa gaskiya nidai  yau Kaine zaka kaini makaran ta, idan muka tafi dasu yaya Abdul malik dukana sukeyi suce wai bana sauri,kuma basa Shiga dani makaranta a bakin layi suke barina, ta'karasa maganar har da 'Yar kwallar ta.



'Dago kai yayi yana kallon su rannan abace   yace mai yasa kuke dukan ta?



Wlhy 'karya takeyi yaya idan muka tafi da ita bata sauri , taita bata mana lokaci,yaya don Allah kawai tunda makaran tarsu banisa tadinga tafiya ita kadai, tunda idan yawanta yatashi har gaba da makarantar tasuma tana zuwa,  




Many tace aykuwa dai ingun gama kuringa tafiyar ku, zanje ay gurin auntyn taku nace taringa zaneki idan kin makara,

Karbi uniform dinki ni kisaka, 


ta karba tana bubbuga 'kafa, 


Ummee tace 'karfa Ku takurawa auta ta,  zonan na sakamiki kinji,



Takarba tasaka mata tace abdallah zo kakai ta tunda tace kai zaka kaita ,


Bamusu yatashi ya rike mata hannu suka fita, suma su Abdul majid suka kama hanya, 



Ahanya ne tasa mai kuka wai itasaiya d'auketa, bayadda ya iya haka ya d'auketa,



 saboda shi fa duk 'kan 'kartar Jidda idan tana wannan shagwa'bar ta ta sai yaji wani iri kuma hankalinsa yana tashi matuka.



                 Asalin su Jidda da Yaa shek!...

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


           *YAA SHEIKH!!*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


*BY:U.K.Y.         for real*๐Ÿ˜˜


     ๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป


*dedicated to mmn khaery*๐Ÿค๐Ÿป


_Note: masoyana ina mai   ba Ku  ha'kuri don zakuga spelling d'in rubuta sunan littafin nan ya sauya daga Yaa Shek zuwa Yaa Sheikh,amma hakan ne ya kamata ya zama ,ina godiya gaduk kan masoyana, nima  aylobiyu Lodi lodi_.๐Ÿคฃ


*Special tanx to*:


Ummy Abduol,Ummu farheen and Aunty Fauziyya.


         1⃣5⃣to2⃣0⃣


Malam Gaddafi da wato Abii mahaifin Yaa sheikh, da kuma malam Usman mahaifin Jadda, 'yan uwan juna ne uwa d'aya uba d'aya suke.


Mahaifiyar su Hajiya Laila  Shuwa ce ita 'Yar garin Borno, shi kuwa mahaifinsu Alhaji Mahi d'an 'kasar Sudan ne.


Kasancewar ba inda aure baya kai mutum ne yasa ya kai Hajiya Laila kasar Sudan ,bayan auran ne Allah ya azurta su da yara biyu wato Gaddafi da Usman, Gaddafi shine babba sannan Usman.


Usman yana da shekara d'aya Allah yayiwa mahaifin su wato Alhaji Mahi rasuwa, k'warai rasuwar ta jijjaga Hajiya Laila da 'yan uwan Mahi.




Bayan ta gama takaba ne ta shaidawa 'yan uwan Mahi  Zata koma kasar su Borno,basuji dad'i ba matu'ka,  amma ba yadda suka iya dole ne ta tafi tunda dama ba 'Yar 'kasar Sudan ba ce.


Haka ta koma Borno ita da yaran ta, da al'kawarin duk sanda ta samu lokaci zata Ke kawo musu ziyara, tana kuka haka suka rabu tana kewar mijin ta,tana mai addu'ar Allah ya ji'kan mijin ta.


Bayan tadawo Borno ne ta koma family house d'in  su kasan cewar ita din ma marainiya ce haka dai take zaune gidan, yau da dad'i gobe babu,mutun d'aya ne take gani taji dad'i  wato 'kanin ta Abdallah shine ya ke 'kwantar mata da hankali.




gidan daga daga 'kannan baban ta Sai matan su hakadai take zaune,  saboda babban burinta bai wuce taga yaranta sun sami ilimin addini da na boko ba.




Alhamdulillahi burin hajiya laila yana cika,  ta tsaya tsayin daka wajan ganin yaranta sun samu ilimi, don kuwa sun sauke al kur'ani,kasan cewar su yara masu haza'ka, inda Gaddafi yake aji shida a primary shi kuma Usman yana aji biyar, yanzu kuma abunda yake damunta bai wuce rashin auren 'kanin na taba wato Abdallah.


To kana taka Allah na tashi 'kwatsam Sai ciwan ajali ya riski Hajiya Laila,tace ga garin Ku Abdalla 'kaninta yayi kuka  haka su Gaddafi shida Usman.



Dan haka Abdallah ba shiri ya fara Neman aure saboda yasan wahala su Gaddafi zasu sha idan ya barsu a family house d'in nasu, ammafa ranshi ba dad'i yaso yayar tashi taga auran nashi.



Ba'a d'au lokaci ba yasamu yarinya Yar manyan mutane,mai tarbiyya itama shuwa ce , mai suna khadija ,bayan sun dai daita ne aka yi aure.




Bayan auran da wata biyu ya d'auko Gaddafi da Usman suka dawo gabansa inda yaci gaba da d'aukar d'awainiyar su na makaranta da kuma tarbiyyar su, kuma itama  Khadija bata da matsala tana kula dasu tsakani da Allah. 



Bayan wani lokaci itama Khadija wadda ayanzu su Gaddafi suke kira da hajiya kamar yadda suke kiran Hajiyarsu kafin ta rasu, ta haihu ta samu 'yarta mace kyakkyawa da ita,inda taci sunan Hajiya wato Laila.



Haka suka cigaba da zama cikin so da 'kaunar juna, su Gaddafi suna son   Laila shiyasa ma itama Khadija keson su.





Kwance tashi ba wuya don Gaddafi da Usman sun gama karatun su,itama Laila ta girma tana secondary.



Gaddafi da Usman sun fara kasuwanci suna saro kaya a kano suna kawowa Borno kuma ba laifi Suna samun alheri, da hakane har suka sami uban gida.


Kasuwanci su ya bunk'asa inda suka daina kawo kaya Borno Sai dai su siyar a kano, idan suka zo kano basa komawa Baron Sai 'karshen sati.


A hakane har Allah ya ha'da Gaddafi da Aysha wato  ummee, Gaddafi yazo ya sami baffan sa Abdallah da batun aure, baffa Abdallah yaji dad'i yakuma bashi shawaran ya Gina gida a can kano saboda yawo a moton yayi yawa gara su zauna guri d'aya.



Haka kuwa akayi, gadan gadan suka fara gini a kano a unguwar gandun albasa, gida biyu suka gina, d'aya na Gaddafi d'aya na Usman duk da dai shi ba auran ne a gabansa ba.



Aka daura auran Gaddafi da Aysha duk lokacin da suka samu dama kuma suna zuwa Borno. 




haka har Aysha ta haihu ta sami namiji aykuwa Gaddafi yasa ma yaro sunan baffan sa Abdallah, yaro kyakkyawa dashi ga shiga rai, Sai yafito sak kyawawan Sudan d'innan hanci har baka, baffah Abdallah yaji dad'i matu'ka,awannan lokacine kuma baffa ya takurawa Usman sai ya fito da mata, da Usman yaji baffan nashi ya matsa masa ne yafito ya fad'a mai gaskiya shifa Laila yakeso, ay kuwa wannan abu ya yiwa baffa dad'i' haka hajiya ma don tasan Usman zai ri'ke mata tilon  'Yarta ta don daga kan Lailan bata kuma haihuwa ba.





Ba 'bata lokaci akayi aure aka kawo wa Usman amaryarsa Laila.




Aysha taji dad'i sosai saboda acewarta ta samu 'Yar uwa, ayko tasamu d'in don  Laila bata da matsala kullum Abdallah yana hannunta saboda mai sunan baban tane kuma gashi kyakkyawa.



Bayan Abdallah yayi shekara Tara ne aka yi mai 'kani Abdul majid,  Abdallah yanazuwa makaranta kuma yana da ko kari, yana da shekara Taran ne ya haddace alkur'ani .





Itadai lailah shuru Allah bai kawo haihuwaba amma itada Usman sunata addu'a  suma Allah ya basu.


A haka rayuwa ta cigaba da tafiya inda Aysha wato  Ummee ta kuma haihuwa shima na miji aka samai suna Abdul malik.



Bayan wasu 'yan lokaci Allah ya amshi addu'ar Usman da Laila inda su ma Allah ya basu 'yarsu mace Inda taci suna Jidda yarinya kyakkywa son kowa 'kin Wanda ya rasa fara tas da ita kana ganinta kaga jinin Shuwa ga kyau ga gashi.





Jidda tana da shekara uku  Allah ya yiwa Usman rasuwa, kai wannan rasuwa ta gigita su musamnan Laila wato mamy da kuma Abii,haka shima baffa da hajiya ,Abdallah shima yaji mutuwarnan sosai ita kuwa Jidda bata da wayo don haka bata San ma me a keyi bama. 



 Bayan Mamy ta gama takaba baffa yace "ta koma gida" amma Sam Abii yaki Yar da a cewarsa ay ko ba matar Usman bace ita ba ay  ita k'anwar  sa ce shi mai iya rike tane kuma Dama tana 'Yar sana'ar ta gashi sun saba kawai ta zauna idan Allah ya fito mata da miji tai auran ta, haka baffa ya ha'kura ya kyale ta.



         *Cigaban Labari*

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


             *YAA SHEIKH*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


*BY:U.K.Y.       for real*๐Ÿ˜˜


       

      ๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป


*Dedicated to mmn khaery*๐Ÿค๐Ÿป


            2⃣0⃣to2⃣5⃣


Haka suka 'karasa makaranta Yana d'auke da ita a kafa'da, ya kai ta har cikin makarantar tasu sannan yace,



"Saura kuma idan antashi ki tsaya a hanya kina wasa"


"Nima bazan tsaya wasa ba ay yau Abii zai dawo zai kawo mana kayan dadi ko?"


Yace mata "eh kiyi karatu da yawa"


Ya juya ya fice daka makarantar.


Bai tsaya ko inaba sai gidansu Bilal.


Bilal abokin Yaa Sheikh ne tun suna yara haka kuma tare suke karatu saida su kazo university ne Yaa Sheikh ya tafi sokoto shi kuma Bilal Yana kano, shima Bilal yanzu haka bai samu ayki ba kuma shima malami ne a Sahsib islamiyya.



Yaa sheikh Yana zuwa ya tarar da Bilal a 'kofar gida Yana duba wani littafi, ya 'karasa shima ya zauna sannan suka yi musabaha fuskar Bilal dauke da murmushi, amma fa ta Yaa Sheikh cike take da damuwa kuma Bilal ya fahinci hakan sai dai baiyi magana ba, don yasan ko yayi ma ba lallai ne ya gaya mai abin da yake damun shi ba saboda Yaa Sheikh mutum ne mai zurfin ciki.


Zama Yaa Sheikh yayi suka cigaba da duba littafin suna muhawara irin ta masu imilin addini a tsakanin su,daga bisani suka koma hirar su ta abokai, anan ne  Bilal ya takura akan lallai sai Yaa Sheikh ya fad'a masa abun da yake damun sa.



Yaa  Sheikh ya d'ago fuskan shi d'auke da damuwa yace,


"Bilal"



Sai da Bilal ya d'ago ya kalle shi zuwa lokacin fuskan shi har ya sauya kala, kana iya karanta damuwar da Ke d'auke a fuskar tashi.


Yace "Jiddah itace damuwa ta Bilal, bani da wata damuwa da ya wuce Jidda"


Bilal ya sake kallon abokin nashi kuma Yana mamakin abin da yake cewa, taya zai ce wai Jidda ce damuwar shi, Jidda karamar yarinya? to kodai wani Abune ya sami Jiddan ?



Duk Bilal ne ya kewa kanshi wannan tambayar sai dai yasan Yaa Sheikh ne zai iya bashi amsa, don haka yace,


"Abdallah me yasami Jiddan kodai ba Jiddan Ku kake nufi ba?" 



"Ita nake nufi Bilal, Jidda yarinya CE karama sai dai ina jin wani babban al amari game da ita, kuma nima na kasa tantance mai hakan yake nufi,idan naga Jidda nakan rasa hankali na, ina shiga wani yanayi aduk lokacin da nake tare da ita, ni mutum ne mai son shagwab'a ita kuma Jidda ba abun da ya zame mata jiki kamar shagwab'a,Bilal akwai abubuwa da dama da nake ji game da Jidda, kuma banaso Ummee ta fuskanci halin da nake ciki".



Ya d'ora da cewa " nidai nasan ba wata mace da nake  jin hakan game da ita, hasali ma ni mata basa gaba na, why sai Jidda? Why?" 


"Allah kaga zuciya ta, Allah kayi al'kawarin baza ka jarabci bawan ka da abin da yafi 'karfin shi ba ya Allah ina rokon ka da ka dubeni da idon rahma"


Bilal da yai kasa'ke yana kallon abokin nasa da tausayin sa da ya cika mai zuciya kuma yana mai mamakin wannan lamari, saboda yasan abokin nasa ba mai damuwa da mata bane hasalima ko mace ce tace tana sonsa to daga ranar tsana ta shiga tsakanin sa da wadda tace tana son nasa.


Bilal ya nisa yace "Abdallah kar kasa damuwa a ranka kacigaba da addu'a nima zan tayaka,sai dai ina tunanin kawai fa son Jidda kake" 


"Nima ina zargin hakan, amma ay Jidda ba tsara ta bace taya zan fara son ta? Yarinyar da ko kanta bata sani ba, ya Allah gani gare ka"



"Kardai kasa damuwa a ran ka komai zai zo dasau'ki da yardar Allah kai dai kayi addu'a, kuma da kake cewa baka son Ummee  tasan halin da kake ciki idan bata sani ba waye kake dashi da zai tayaka addu'a? kadai San addu'ar iyaye akan 'ya'yansu daurewa zakai ka fad'mata"



"Hakane amma gaskiya Bilal ko zan gayawa Ummee ba yanzu ba zan dai cigaba da  daddu'ar"


Bilal yace "to shikenan nima zan tayaka "


Yaa Sheikh ya mika wa Bilal hannu suka yi musabaha yace "to bari na k'arasa gida yau Abii zai dawo sai mun had'u a islamiyya"


"OK to shikenan nima zan shigo nayiwa Abii sannun da zuwa"


Haka suka rabu Bilal yana tausayawa abokin sa, shima Yaa Sheikh yana tausayawa kan sa.



Yana shiga gida ya tarar da Ummee ta gyara gida ko ina fes fes itama tayi wankan ta tana jiran shigowar mai gidan ta.


Ya shiga yana murmushi yana yaba yadda Ummeen shi keda kokari tana da tsafta ga son ado, ya k'arasa kusa da ita yana mata sannun da gida tace, 

"Yawwa sannu Abdallah, kakai min yarinyar tawa ko, amma dai ka tsaya wani gun don ka dad'e?"



Ta jera mishi tambayar. 


"Eh Ummena natsaya a gurinbBilal ne" 




Ta sake cewa " 'Yar tawa kuma fa?"


"Na kai ta"


Ya bata amsa a ta'kaice don baya so Ummee ta gano wani Abu, saboda shi ko maganan jiddan tana sa shi tuna nin ta.



Tsayu war mota a 'kofar gidan sune ya dawo dashi daga duniyar tunanin da ya tafi, Umme tace


"Abdallah wannan kamar Abii ko?"


"Bari na duba "



Ay kuwa shi ne, Abdallah ya 'karasa wajen baban nashi yana cewa,

"Abii sannun da zuwa ka sha hanya"


"Wallahi kuma babana shiga da wannan sauran kuma ka barsu a but din idan su Abdul majid sun dawo saisu shigarwa Mamy"



 (Shima Mamyn yake CE mata tunda dai sunan  mahaifiyar sa gare ta.)


Abdallah yace "toh Abii"   yana mai daukan kayan da Abii din ya nuna masa.



Ummee da murna ta tari mijin ta,Abdallah ya kuma gaushe da Abii, ya tashi yana cewa   "Umme bari na Dan watsa ruwa na kwanta kafin azahar"



"To Abdallah"

Itama ta fad'a tana kokarin tashiga d'akin Abii ta ha'da mai ruwan wanka "


Karfe 12:15 Jidda tashigo tana murna don taga Motan Abii a kofar gida tana cewa,


 "yeee Abii ya dawo"


 tai hanyar dakin Abii da gudu ta fad'a dakin, aiko tana ganin sa ta fad'a jikin sa, shima da murna yace


" 'Yar gidan Abii kin dawo, ya makaranta kina dai karatun ko, ko kina nan kina kukan ki na banza?"



Ya jera mata tambaya saboda ya San mai hali baya fasa halinsa.



"Abii banayi kuma ina karatu,Abii ka kawo min tsaraba"?


" na kawo miki Jidda na idan bankawo miki ba Wa zan kawowa?"


Aiko ta washe baki tace "yawwa Abii na, na gode, sai anjima zaka bani?"


"Eh zan bawa Umme ta ajiye miki yanzu kije ki gaishe da Mamy kuma kice nima Ina gaishe ta,


" Abii to ina Umme?"


Yace"tana d'akin ta"


"To idan ta zo kace na dawo kuma kabata tsaraba ta' ta ajeye min"


Tana gama fad'a tafice da niyyar zuwa wajan Mamyn ta, sai dai tana zuwa wajen 'kofar d'akin Yaa sheikh ta shige d'akin, tana shiga ta ganshi yana bacci, yayi d'ai'dai ya kunna fankar 'kasa tana ta hurashi.

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




              *YAA SHEIKH*




๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




*BY:U. K. Y.      For real*๐Ÿ˜˜





   ๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป 




*Dedicated to Mmn kheiry*






_masoya na bansan irin godiyar da zan muku ba wlh nima Ina sonku na gode da kula warku kuma wadanda sukai min adduar samun nasara a exam dina to alhamdulillahi nasamu nagode sosai da sosai_






*my ANFA  ilobiyu Lodi Lodi wooo*๐Ÿ˜…๐Ÿ˜˜




             *25 to30*



Jiddah Tana shiga d'akin tai wajen madubi turarukan shi ta fara feshe jikin ta dasu 


"Ay wallahi sai na fesa kowanne nima naita kamshi kamar Ya Abdallah na"


Nan dai taita fasawa sannan ta koma yimai bincike ta hargitsa komai  zuwa wannan lokacin ta gaji tulus dama ta gamo rashin jinta a makaran,  gefen shi ta kwanta itama sai bacci, 




Wani abu yaji ajikin shi kamar ruwa ruwa sannan yaji  kamar wani yazo ya kwanta abayan shi, 




 ay kuwa da sauri yafarka juyawar da zaiyi yaga Jiddah kwance cikin fitsari sharkaf tai musu don shima ajiken yake kawai kallon ta yake yama rasa mezai ce, 



 ita kuwa sharar baccin ta take ko ajikin ta, tsaki yayi kawai ya yunkura zai tashi kenan      ay kuwa baiyi aune ba kawai yaji Jiddah ta cafko shi tana magagin bacci,  




wata galabai tacciyar 'Kara ya saki yana kiran 




"ya ilahi" 






Ya jima kafin ya tattaro karfinsa, 




janye hannun ta yayi daga jikin nashi yana tunanin wai yaushe ma ta shigo d'akin nashi har ta kwanta kusa dashi? 






 sai alokacin yaga iri ayka aykan da taimasa gaba d'aya ta hargitsa d'akin, juyawa yayi yasake kallon ta tananan tana sharar baccin ta wani 'kaya taccen murmushi ne ya kubucemai ya furta


 *"inda rai da rabo"* 



ko me ya tuna oho, 



sannan ya tashi ya sake wasu kayan ya fita daga dakin, 



Yana  fita ya tarar da Ummyn su tana alwala  



"Yanzu nake cewa Abdul malik yazo ya tasoka kafin karasa jam'i"




"Wlh na tashi Ummy wannan yarinyar taki ce  wai ta rasa inda zata kwanta sai d'aki na kawai sai farkawa nayi nagan ta,  gashi tamin fitsarin kwance"


 

Dagowa Ummy tai tana tambayar sa "fitsari dai,  akan katifar kuma? "




"A wlh Ummy" yafada fiskan shi cike da takaici shi sai yanzu ma abin yake batamai rai, 

 "To ay shikenan Kayi alwala kar ashiga sallan"




"To Ummy na,  Abii fa ko ya tafi masalkacin?" 




"Eh " Ummy ta fada tana shiga   dakin ta shima ya sheikh alwala yayi ya tafi masallaci ko takan Jiddah bai biba, 





Ita kuwa Jiddah ya sheikh yana fita ta farka ganin abin da taine kunya ta hanata fita saboda tasan indai su Abdul majid sunji abinda tai tashiga uku, 







 tanajin fitarsu masallaci tai maza ta sulale tai gidan mamyn ta,  tana shiga ta tarar mamy ta tada sallah,  tasamu guri tarakube tana jiran mamyn ta idar, 




Mamy tana idarwa Bayan tayi addua ta kalli Jiddah dasai muzurai take tace "meya jika miki kaya? "





"Fitsarin kwance nayi"

Tabata amsa tana dukar da kai,  



"Fitsarin kwance Jiddah a Ina kikai? " 



"A dakin ya Abdallah "




Mamy ta sake jefa mata tambaya "a kasa ko a Ina? " 




"A katifa"




Tafada tana turo baki na borin kunya. 


*5 years*




Kuyi hakuri da wannan fans ba yawa๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ

  

               *YAA SHEIKH*



๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



*U. K. Y.    For real*๐Ÿ˜˜



๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป




*Dedicated to mmn kheiry*





             *30to35*






 

*5 years*




Shekaru biyar da suka shud'e abubuwa da dama sun faru, ansamu nasarori da dama.


A halin yanzu Jiddah ta gama primary school sannan ana cuku-cukun sama mata secondary.




Jiddah idan kagan ta a wannan lokacin bazakace yarinya Yar shekara goma sha biyu bace, Jiddah doguwa ce fara siririya Mai cikakken diri da kyawun zati,       wani abun burgewa game da Jiddah shine Jiddah irin yarannan ne masu shegen iyayi ga tsafta ga son iyawa a 'bangaren karatu Jiddah nada kaifin 'kwa'kwalwa afannin Arabic da kuma boko idan Jiddah Tana magana Sai kayi mamaki  saboda tsabar iyayi kai a ta'kaice Jiddah tana da d'aukar hankali. 




A 'bangaran Yaa Sheikh kuwa a halin yanzu Yaa Sheikh  cikakken mutum ne kyakkyawa,  to dama abinka da jinin sudanawa  dole Ya Sheikh ya kasance Mai jan Hankali, 



Ya Sheikh yanada sura Mai d'aukar hankali ga nutsuwa abinka da malaman sunna ba hayaniya.



Shekaru biyar da suka wakana Ya Sheikh ya samu scholarship na zuwa 'kasar  Madina, sakamakon musaba'ka da akayi ta 'kasa ba'ki d'aya inda ya samu nasarar lashe gasar kowa yayi farin ciki da hakan, 



Ya tafi k'asar Madina inda ya cigaba da karatun masters d'in shi ahalin yanzu ya kammala. 





Sai dai sun nuna buk'atar su akan Ya Sheikh da ya zauna don yayi musu Ayki a kasar tasu wato Madina koda ba 

na din din din ba kuma Yaa Sheikh ya amince da bukatar su, Sai dai ya basu nashi uzirin cewa yanason zuwa gida nawani d'an lokaci sannan yadawo ya kar'bi aikin,  suma kuma sun amin ce.




Babban burin Ya Sheikh yanzu bai wuce yaje yaga abin k'aunar saba kuma sanyin idaniyar sa wato Jiddah,  don ba abinda ya sauya game da abin da Ya Sheikh ya keji akan Jiddah, don daga Ummy har Mamy sun gane Ya Sheikh yana tsananin 'kaunar Jiddah, Sai dai ita Jiddah bata sani ba. 





Ummy tasha yiwa Ya Sheikh magana akan ya nemar wa kanshi mafita ya samu wata cikakkiyar budurwa ya aura don ya yiwa Jiddah girma, Jiddah baza ta iya dashi ba amma kullum tazo Mai da zancen Sai ya hau yi mata magiya don Allah Ummy na kibar wannan maganar kafin Jiddah taji itama tace nayi mata girman.




Ummy dai jinshi kawai take kuma tana mamakin yadda Abdallan  nata yake mugun son Jiddah wanda ta lura ko gurin da yake Jiddah tazo Sai yanayin sa ya canja, to inaga an kaimai ita gidan sa a matsayin mata.




Mamy har yanzu Allah bai kawo mata miji ba tana zaune dai tana 'yan sana'oin ta kuma rashin auran bai dame ta ba saboda ba abunda tarasa  yadda Ya Sheikh zai yima Ummyn shi ayke haka yake yiwa Mamy ma sannan Abii ma duk abunda ya kawo Sai an kai mata, tana zaune cikin kwanciyar hankali,            

Sannan koda ta gane ala'kar Ya Sheikh da Jiddah abun ya mata dadi sosai, sai dai Tana tunanin Anya Jiddah tana son Abdallah kuwa? 






Abdul Malik da Abdul Majid suna Sokoto suna karatunsu na degree wanda shima Ya Sheikh ne ya dauki nauyin Kara tun nasu. 



Kai Sai dai muce Alhamdulilah amma dai kam an samu ci gaba.





"Nidai Mamy Allah boding nakeso kinga Nana ma can za a kaita ba Sai akaimu tare ba? "






"Oh wato ita Nanan ce ta cemiki boding za a kaita shine zakizo ki sani a gaba ko? To ni kifita a idona na rufe kina jina ko tun wuri ki cire zancen boding d'innan ma a ranki Jiddah  kinsan Abii ba yarda zaiyi ba."


Jiddah bata sake cewa komai ba saboda tasan Ya Sheikh ya kusa dawowa kuma tasan zai yarda kuma yana yarda shi kenan,



"To shikenan Mamy bari naje na gaishe da Ummy Da Abii kafin ya fita."



Mamy tace "toh ki ce ina gaishe da Abii kuma kicewa Ummyn taku nima Zan shigo anjima."



Tana fita tafad'a gidan Ummyn bayan ta gaishe su tai sauri tafita tana cewa "Ummy na tafi.....         na baro Mamy tana Ayki "


"To Jiddah na kice mata Sai ta shigo din"




Jiddah tana fita tai gidan su Nana aminiyar ta, 

Nana tana ganin ta ta hau murna don a tunanin ta Jiddah tazo gaya mata  an yarda itama za akaita boding d'in.


"Ke Mamyn ta yarda ko? "

Nana ta tambaye ta 



"Wlh bata yarda ba Nana amma dai kinga Ya Sheikh ya kusa dawowa idan ya yarda shikenan."




"Ya Sheikh ubanki ne shi da zakice Sai ya yarda? "



Wani mugun kallo Jiddah  watsawa Nana kana tace "idan shi ba ubana bane ai yaya nane shi ko kuma idan bai yarda ba uban wane zai biya kud'in makarantar?  Ko babanku zai biya min?" ta k'arasa maganar tanawa Nana kallon up and down 





"Kefa baki da M wlh yanzu me ne nasako Baban mu a ciki? "





Jiddah tace "ke kika fara ai, ni tashi muje ki rakani  kar Mamy taga na dade."



"Tom naji, shine ko ki tambaye ni mutumin naki ko? "



Jiddah tace" wafa? "



Wani kallon kinma raina ni Nana taiwa Jiddah  "oh kina nufin kice baki san wa nake nufi ba? To *FIGO* nake nufi jiya ya bani letter na baki."






"Uhmmm kanki ake ji" inji Jiddah 




"Kema anajin Naki kan.....  Yaro 'Dan gayu Kamar figo kiringa jamai aji " 





Jiddah tace" nidai ba ruwa na ina yarinya ta bazan kula namiji ba don idan Mamy tasani Sai ta zaneni"




"Nidai bari na dauko miki letter in kin gadama ki yaga"






*birnin MADINA*




Ina Sau raron comment din ku๐Ÿ˜ƒ09032749200 what's app only.........

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


             *Yaa Sheikh*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



*BY:U. K. Y.   For real*๐Ÿ˜˜ 





    ๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป



 



*Dedicated to mmn kheiry*





Wannan page din nakine my *zanna* I love ❤️ ๐Ÿ˜ Ana tare๐Ÿค๐Ÿป




                  *35to40*






*MADINAH*



Yaa Sheikh ne ya fito daga wani hall yana ta sauri hannun shi dauke da takardu. 





Yana cikin tafiyar ne yaga wata mota ta faka  kusa da shi koda yajuya Sai yaga Nuaym ne. 



(Nuaym shine abokin da Yaa Sheikh Yayi a garin madina kuma makocin shine don haka sun saba, Nuaym balaraben misrane shima karatu ne ya kawo shi madina) 





Cikin harshen larabci suka fara magana Nuaym yake cewa Yaa Sheikh 


"Abdallah yau da safe ina jiran ka kazo mu taho makaranta ashe kai kayi tafiyar ka" 



Nuaym ya 'karasa maganar yana mai jin haushin jiran Yaa Sheikh da yayi. 





Yaa Sheikh Yayi murmushi ya na mai bud'e murfin motar Sai da ya dai-dai ta zaman shi sannan ya kalli Nuaym da ya 'bata fuskanshi wai shi Yayi fushi, sannan ya ce 




"haba abokina tun jiya na fad'ama ina so na gama komai yau a cikin makarantar nan tun 6:00 na taho nasan lokacin baka tashi ba,  amma yanzu dai kayi ha'kuri mukarasa gida "




             "  Ok " 


kawai Nuaym yace ya tayar da motor suka nufi gida. 





Koda suka isa gida Yaa Sheikh gidan sa ya shige akan  cewar da yamma zasu had'u. 





******




Su Jiddah suna fitowa Nana tace"ke ni ungo letter ki, ana so Ana kaiwa kasuwa " 




  Ita dai Jiddah  bata ce komai ba ta kar'bi letter suka cigaba da tafiya. 





"Kinga Jiddah don Allah kizo mubi ta hanyar shagon askin su Figo dama jiya da ya bani letter Sai da ya cemin ya naso ya ganki"





"Gaskiya nidai bazani ba so kike ace mana Yan iska ko? "



"Kaiii!!...... Gaskiya  ke Jiddah wlhy banza ce  ina ruwanmu da mutane? Ay wlhy dama Figo ni face yana so"




"Mtswww to Sai me?  Don Figo yace yana sonki mutumin da yake sa sar'ka yasa wando duk Bayan shi a bu'de, to ke Figo ya dama amma ni bai dameni ba"





Nana tace"to naji Kiyi hakuri Tunda bazaki ba ki tsaya naje na kirawo shi"


"Kinga Nana tunda bazaki rakani ba shikenan , nidai bazan tsaya ba"





"Kai don Allah ki tsaya haba kawata Zan rakaki har gida fa "




Da haka dai Nana ta ja ra' ayin Jiddah har ta tsaya ita kuma ta tafi kiran Fito. 




"Kaganta can Figo muyi sauri in ba haka ba wlhy zata iya tafiya" 




Bayan sun karasone Figo Yabi Jiddah da wani mayataccen kallo yana ayyana abubuwa da dama a zuciyar sa sannan yace




    "yaaa! Baby Tunda ke bazaki zoba to ni gani nazo , baby kina kofsawa da yawa fa mene a ciki don kinzo gurina"




Jiddah da ta sunkuyar da kanta 'kasa ta Dan saci kallan sa sannan ta kuma kau da kanta gefe tace. 





"Ke Nana tun da yazo to ki taho mu tafi "ta karasa maganar tana tafiya. 





"To naji muje, Figo Sai anjima bari na rakata" 

Figo da Yayi sa'kare yana shafa gefen fuskar sa yana sakin wani lalataccen murmushi gaba d'aya hankalinsa ya tafi kugin kallon Jiddah baima san me Nana ke cewa ba. 





Nana ta sake mai mai tawa da karfi



 "kai Figo mun tafi"


 sannan ya dawo hayya cinsa



 "ok tom see u leter " 




 Wane *FIGO*


Figo sunan shi na gaskiya musa matashi ne Wanda a'kalla zaiyi shekara ashirin da uku. 



Musa (Figo) yoroba ne 'Dan garin Ibadon, yazo karatu ne kano to kunsan yoroba da neman kud'i wannan dalilin ne yasa ya bud'e shagon aski a Latin su Nana Figo abokin Ali ne shi kuma Ali yayan Nana ne shi yasa suka saba da Nana, don wani lokacin ma Figo a d'akin Ali yake kwana. 




Iyayen Nana irin iyayen nan ne da basa 'kwa'bar 'ya'yan su. 




Don haka daga Ali har Nana suke abinda ransu yakeso, wai don ma Maman su Nanan tana Dan 'kwa'bar ta sabo da ita mace ce. 




Tunda Figo yaga Jiddah ya kwallafa  ran shi akan ta shine yabiyo ta wajen Nana don yasan zata taima kama sa. 





Ay kuwa hakan akayi don tun Jiddah bata kula shi har tazo ta fara duk da tai makon Nana. 



Saboda Jiddah bata da wata 'kawa Sai Nana ajinsu daya a primary. 




๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜๐Ÿ˜ bari nace muku see u๐Ÿ˜‰๐Ÿ‘‹๐Ÿป

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


              *Yaa Sheikh*



๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




*BY:U. K. Y.    For real*๐Ÿ˜˜





๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso* ✍๐Ÿป





*dedicated to mmn kheiry*๐Ÿค๐Ÿป




               *40to45*





Tana shiga gida ta- tarar da Mamy tana sallah, itama alwala tayi ta shige d'aki. 





Bayan ta idar da sallah tafito ta sami Mamy itama ta idar, 


"Mamy wai Ummyn tana amsawa "



Mamy  ta kalleta tana zargin ba a gidan Ummyn ta zauna ba har tsawon wannan lokacin ba amma Sai ta kyale ta bata ce mata komai ba. 



"Ok nima ay yanzu Zan shiga ki tashi ki gyara min kayan miya Sai kizo gidan Ummyn ki same ni"



"Toh Mamy,....  wai goben Ya Abdallahn zai dawo ne? "




Mamy ta washa mata harara tace"kin bashi sak'o ne da kike tanbayar yaushe zai dawo? To idan ma so kike ya dawo ki mai maganar boding garama ki sake tunani don ko ya biye miki ni ba barinki zanyi ba"


Mamy tana kaiwa nan ta d'au mayafin ta-tafita. 



Aykuwa Mamy na fita Jiddah ta ciro lettern Figo ta karanta, ba komai bane illa dai abinda ya saba rubutawa wato yaushe zata fito su ha'du, ... Ta'be baki tai tace,  



"kaji da shi"


Sannan ta 'boye lettern a inda ta saba b'oyewa, sannan ta fara gyara kayan miyar. 




Bayan ta gama ne itama ta kulle musu gidan ta shige gidan Ummy da niyyar idan ta shiga zata kar'bi wayan Ummy ta kira Ya Abdallahn ta,  taji yaushe zai dawo. 



A sa'a kuwa tana shiga ta iske ya kira suna ta hira da Mamy. 



"Yawwa Ummy ya Abdallah ne ko? " 



"Jiddah na shine yanzu shima yake tambayar ki "



Ta cuno baki cike da sgagwab'a sannan tace"Hmmm ke dai Ummy kina kare shine amma nasan bai tambaye ni ba"



Dariya Ummy tayi sannan tace "Auu hakama zaki ce to ay gashi nan ya kira saiki bari idan ki kaga ya kashe wayan bai neme ki ba Sai kice haka"


Ita dai Jiddah bata kuma cewa komai ba ta cigaba da cuno baki tana jira taga ko Ya Sheikh zai kashe wayan bai neme ta ba. 



Ita dai Ummy abunma dariya ya bata kasan cewar wataran Ya Sheikh zai kira musammam don Ita amma  'kiri-'kiri zata ce baza ta karb'a ba,  haka Ya Sheikh zai hakura,... Don haka yau abun yayiwa Ummy dad'i tana adduar Allah yasa Jiddah da fara son Abdallahn tane. 




Mamy kuwa Sai hira suke ita da Ya Sheikh amma fa shi burin shi yaji tace ga Jiddahn amma shiru, hakane yasa yace "



"Mamy Ummy bata kusa ne inason na gaya mata me zata dafa min goben"



"Toh babana bari na bata"



'Kin kar'ba Ummy tai don tasan sarai so yake ta ha'da shi da Jiddah don haka tace  Ayki take don haka  Mamy kawai ta bawa Jiddah  inyaso ko anjima ne za suyi magana. 




Mamy mi'kawa Jiddah wayar tayi,  tana cewa Ummy zata koma gida. 





Koda Jiddah ta kar'bi wayar bata tsaya a tsakar gida ba d'akin Ummy ta shige, 




"Hello Ya Abdallah nah"



Wani sanyi yaji yana ratsa shi gami da wata cikakkiyar nutsuwa kice da zumud'i ya amsa mata "na'am Jiddo nah ya kike? "




Kamar yana kallon ta-ta wani cuno baki cike da tab'ara tahau bubbuga 'kafa tana cewa "shine da ka kira waya ko ka tambaya ina nake ko? To Allah nayi fushi idan ka dawo bazan kula kaba "



Ay  kuwa karkuso kuga yanda Ya Sheikh ya ru'de kamar wani wawa ko ince k'aramin yaro. 




 magiya ya shiga yi mata kamar zaiyi kuka



"please my Jiddo don't  be angry  with me,...  Jiddo wallahi na tambayi  Mamy tace ta barki a gida kina mata Ayki ki tambayi Ummy ma idan baki Yarda ba"




"Ok Toh na yarda"




"To kin hak'ura? "



"Eh na hak'ura"


Wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yana jin da'di har cikin ran sa sannan yana mamakin yadda Allah ya jarabce shi da son 'yar 'karamar yarin kamar Jiddah. 





 amma ko ba komai yasan Jiddah tana da duk wani Abu da yake so a tattare da mace. 



 Jiddahn ce ta katse mai tunanin da yake da shagwa'bar ta ta fara cewa





"Toh Ya Abdallah nah yau she zaka dawo 'din wai? "



     Ya Sheikh da ya shagala da sauraron shagwa'bar ta mai sashi a wani hali a kasalan ce yace mata"Jiddah yau Zan hawo jirgi 'karfe Tara insha Allah  Kinga zuwa gobe iwar haka muna tare " 



"Kai amma naji dad'i Ya Abdallah dama Inaso in gaya maka wata magana ne sai ka dawo Zan fa'da ma"




(Har yanzu dai tananan da k'udirin ta na zuwa boring saboda Nana ta gama yima ta hud'uba) 




"Ok tom shikenan Jiddahn Abdallah,  bari na gama shiryawa Kinga lokaci yana tafiya amma kafin nan sai kin cemin kina so na"



Dariya tayi, ko ajikin ta tace ina sonka Ya Abdallah nah Kaima kana so na? "



"Kai Jiddah ina sonki mana"



Ya sake lumshe ido yanajin cigar jikin shi ha tashi saboda shauk'i (kamar wami mai magana da cikakkiyar budurwa lol) 




Sannan Ya cigaba da cewa



" ay kaf duniya bacin Mamy ba Wanda ya fini son ki "



"Yeeeee naji da'di Ya Abdallah" 



"Toh Jiddah bari na 'karasa shiryawa ko?.....  sai anjima Zan sake kira Kafin mu tashi"



Da haka sukai sallama.





9:00pm jirgin su Ya Sheikh ya 'daga sai Nigeria ๐Ÿ‡ณ๐Ÿ‡ฌ 



I love ❤️ u all my fans๐Ÿค๐Ÿป




Khairaty ๐Ÿ˜๐Ÿ˜˜

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ


              *Yaa Sheikh*


๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



*BY:U. K. Y.    For  real*๐Ÿ˜˜





๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป




*Dedicated to Mmn kheiry*๐Ÿค๐Ÿป



*Note*: *naji sa'kon ku masoya na cewar bakwa so Jiddah taje boding school to amma Idan kunyi ha'kuri na d'an lokaci ne kucigaba da bina kudai kawai*๐Ÿค๐Ÿป๐Ÿ˜




               *45to50*



 _Wannan page din nakune abokan arzik'i   ๐Ÿ˜ *Yaa Sheikh fans* ๐Ÿ˜_




'Tun safe Jiddah take zaman jiran Yaa Sheikh amma shuru kakeji, harkusan magarib bashi ba labarin sa. 





Kallon ta Mamy tai tace "tashi ki shiga gidan Ummy ki tambaye ta kiji ko baban nawa ya kira ta?nasan dai yanzu kam sun iso".




Jiddah kamar mai jiran hakan,  ta mi'ki da sauri ta sa hijab ta fita sai gidan Ummy, 



Tana shiga ta tarar da Ummy itama tana zaune ta cab'a ado na tarbar d'an ta. 





Bayan ta gaishe da Ummynne take tambayar ta

"Wai Ummy Ya Abdallahn bazai dawo bane kodai dama bai taho Ba? "



Ta k'arasa maganar kamar zatai kuka Don har idon ta ya kawo kwalla. 





"Au kuka zakiyi saboda bakya raina abin kuka? To Abii ya tafi d'akko shi yanzunnan zaki gansu,  Dan Tun d'azu Abii ya tafi d'aukan shi "





Sai a sannan taji dad'i ta saki ranta ta hau yiwa Ummy hira. 






Suna cikin hirar ne su kaji tsayuwar motar Abii, Jiddah kawai k'urawa k'ofa ido tai tana jiran taga shigowar Ya Abdallahn ta. 




Da sallama suka shigo,....... Ido hud'u sukai da junan su ay kuwa Jiddah ta wani zabura tai kan Ya Sheikh, bai Ankara sai ji yayi Jiddah ta rungume she, 




" *YA SALAM*" 


Shine abin da ya iya furtawa saboda yadda yaji tsigar jikin shi ya tashi ga wani jiri da ya d'ebe shi, taga-taga ya fara kamar zai fad'i, Ummy da ta Ankara da halin da Ya Sheikh ya shiga tai saurin cewa "kai Jiddah bakisan kin girma Ba yanzu ay saiki kada yayan naki",



Da Wannan damar Ya Sheikh yai k'ok'arin tattaro nutsuwar shi sannan ya zame jikin shi daga na Jiddah. 




Abii ne yace" to ay sai ku samu guri ku zauna ko? "



Dukan su zama sukai sannan Ya Sheikh ya gaishe da Ummy zuciyar shi cike da murnar ganin shi a gida. 


"Lafiya kalau Abdallah ya hanya ya karatu to Allah ya sa angama a sa'".



"Amin ya Allah,  Ummy na"


haka dai sukaita gashe-gaishen su da hirar yaushe gamo,  Abii yana ta tambayar shi game da aykin da madina suka bashi, kafin daga bisani Abii ya tashi ya shiga d'akin shi. 




Ya Sheikh sai satar kallon Jiddah yake yana mamakin girman da ta k'arayi, ga wani iyayi da take kamar wata cikakkiyar budurwa, Ummy ce takatse mai tunanin da yake tace,"Abdallah  akawo ma abinci KO? "


"A'a Ummy bari dai na fara wanka"



Bayan yayi wankane ya fito cikin shirin sa, sanye yake da wata black jallabiya, kannan a gyare sai zuba k'amshi yake Idan kagan shi kamar balarabe duk dade hasken shi Ba irin na larabawa bane irin na yan sudanne ne amma Ba k'aramin kyau yayi ba. 




Zama yayi sannan yace"yawwa to yanzu Kinga sai naci abincin ko Ummy na? "




Murmushi Ummy tayi sannan face"to Abdallah bari na d'auko ma"



Tana fad'in  haka ta nufi kitchen . 



Jiddah itama mik'ewa tayi da niyyar taje ta taya Ummy d'auko abincin, da sauri Ya Sheikh ya ruk'o hannuta ya maida ta ta zauna suna kallon juna sannan yace


"Jiddah na baki ce nayi kyau ba kodai banyi ba ne? Don kefa nai wannan wankan"


Ya k'arashe maganar yana kurawa k'wayar idonta kallo, kamar mai jin bacci. 


Kallon shi itama tai sannan tace


"kayi kyau mana ka ganka kuwa kamar balarabe"


"Toh Jiddah nah nagode, yanzu to kice kina sona"


Ta kyalkyale da dariya tace"kai Ya Abdallah nace fa Ina sonka kuma kaima kace kana sona ba shikenan ba"





Zuwan Ummy ne ya hanashi sake cewa komai, Don haka kawai ya fara cin abincin da ta kawo mai. 


Bayan ya gama yace



"Ummy bari na shiga na gaishe da Mamy naga dare yana yi"




Haka kuwa akai suka tashi shi da Jiddah, Jiddah mata yiwa Ummy saida safe. 





Mamy tayi Farin ciki sosai da ganin Ya Sheikh, sun d'an tab'a hira Karin Ya Sheikh yayi mata saida safe, Jiddah tanajin haka tabi Bayan sa, a zaure suka tsaya Jiddah tayi k'asa-k'asa da murya tace" Ya Abdallah karfa ka manta nace maka zan gaya maka wata magana amma sai da safe"


"Toh Jiddah Allah ya kaimu"



Sallama sukai ya nifi gida,....  yana shiga -yayi wa Ummy da Abii saida safe, yashige d'aki yayi shinrin kwanciya Bayan ya gama duk abubuwan da ya sabayi. 




Yana kwanciya tunani yace salamualaikum, haka yaita tunani,................ Tab wai Jiddah ce ta k'aragirma haka, amma daga nayi magana Ummy tace wai nayiwa Jiddah girma baza ta iya dani ba, to ay in ita bazata iya Dani Ba ni zan iya da ita. 


Da irin wad'annan tunanin bacci yayi awangaba da shi. 





Khairaty๐Ÿ˜˜๐Ÿค๐Ÿป

[21/04, 10:00 a.m.] Shooly: ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ



            *Yaa Sheikh*



๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ๐ŸŒธ

๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ๐ŸŒผ




*BY:U. K. Y. For real*๐Ÿ˜˜





๐ŸŒˆ *kainuwa writers asso*✍๐Ÿป





*Dedicated to Mmn khairy*๐Ÿค๐Ÿป ๐Ÿ˜˜




Surah Al-Araf, Verse 27:

ูŠَุง ุจَู†ِูŠ ุขุฏَู…َ ู„َุง ูŠَูْุชِู†َู†َّูƒُู…ُ ุงู„ุดَّูŠْุทَุงู†ُ ูƒَู…َุง ุฃَุฎْุฑَุฌَ ุฃَุจَูˆَูŠْูƒُู… ู…ِّู†َ ุงู„ْุฌَู†َّุฉِ ูŠَู†ุฒِุนُ ุนَู†ْู‡ُู…َุง ู„ِุจَุงุณَู‡ُู…َุง ู„ِูŠُุฑِูŠَู‡ُู…َุง ุณَูˆْุขุชِู‡ِู…َุง ุฅِู†َّู‡ُ ูŠَุฑَุงูƒُู…ْ ู‡ُูˆَ ูˆَู‚َุจِูŠู„ُู‡ُ ู…ِู†ْ ุญَูŠْุซُ ู„َุง ุชَุฑَูˆْู†َู‡ُู…ْ ุฅِู†َّุง ุฌَุนَู„ْู†َุง ุงู„ุดَّูŠَุงุทِูŠู†َ ุฃَูˆْู„ِูŠَุงุกَ ู„ِู„َّุฐِูŠู†َ ู„َุง ูŠُุคْู…ِู†ُูˆู†َ


O children of Adam! let not the Shaitan cause you to fall into affliction as he expelled your parents from the garden, pulling off from them both their clothing that he might show them their evil inclinations, he surely sees you, he as well as his host, from whence you cannot see them; surely We have made the Shaitans to be the guardians of those who do not believe.

(English - Shakir)  


via iQuran  juma a Mubarak




*masoyana ina godiya da kulawar da kuke bani, wad'anda suka kirani da Wanda suka bini pc duk ina godiya kuma ina k'ara baku hak'uri abu buwa ne sukai min yawa*




                 

                *50to55*





'Dumin abinda ya fitar daga jikin sane ya farkar dashi daga mafarkin da yake, gaba d'aya ya had'a gumi afili ya furta "hasbunallahu wa ni'emal wa kil, why!?  Me yasa haka ne?"



Duk shi kad'ai yake surutan sa kafin daga bisani ya kalli agogon dake mak'ale a jikin bangon d'akin nasa, k'arfe 3:00 dai-dai don haka ya tashi ya nufi toilet. 







Bayan ya tsarkake jikin sane ya fara gabatar da nafilfilu yana adduar Allah ya kawo masa mafita don shi kansa wani lokacin Yana gasgata maganar Umme cewar Jiddah ta mai k'ank'anta ya nemi wata, 


To amma fa shi bashi da wani interest Akan wata mace Bayan Jiddah da ya kwallafa ranshi a kanta,  don haka dole ne ya rok'i Allah mafita, ahaka har lokaci shiga sallar asuba yayi, don haka ya feshe jikin shi da turare   ya nufi masallaci ba tare da ya shiga cikin gidan nasu ba. 






Da misalin karfe 8:00 na safe Jiddah har ansha wanka za'aje rok'ar al farman tafiya boarding school gurin Yaa Sheikh sai addua take Allah yasa ya yarda, fitowa Tayi ta iske Mamy a falo, kame kame ta fara kafin ta nemo abun fad'a. 





"Umm Mamy zanje gun Umme na gaishe ta"



Mamy tace "hmmm Jiddah kenan zadai kije gurin babana ay ba hanaki zanyi ba sai kin dawo".      



Aykuwa sim-sim ta fice ta nufi gidan Umme, 

Tana shiga bata tsaya ko ina ba sai d'akin Yaa Sheikh a cewar ta koma ina yake ai zai shigo d'akin sa, tai zamanta, Aikuwa tana cikin tunanin nan Yaa Sheikh din ya shigo, dawowar sa kenan daga masallaci don Tun fitar sa sallan asuba bai dawo ba sai yanzu. 






Tashi tai da gudu zata rungume shi Aikuwa k'irjjn shi har dukan uku-uku yake Saboda shi yasan wani  irin yanayi ya shiga jiya da ta rungume shi gashi yau yana azumi don haka yayi sauri durk'usawa ya dafe cikin sa Yana cewa"Asssshhhhh" 

 


A tsorace ta dago tana kallon sa "yaya mene? "Ta tambaye shi. 




 


      "Cikina "yabata amsa






    "To sannu yaya muje ka kwanta"





Haka ta tusa shi gaba kamar k'aramin yaro, saida taga ya zau na Sannan ta sake yimai sannu. 



Shidai a cikin ran sa Allah yake wa godiya da bata tabashi ba sannan yana tunanin ya rayuwar sa zata kasance a gaba,  ba zaiyiwu ace kullum zai dinga k'arya Saboda Jiddah kar ta tab'a shi ba, kuma ya fuskanci kamar bata da ranar daina rungumar sa, " tab akwai aiki"ya fad'a a zuciyar sa. 





"Sannu yaya kasha magani ko zai daina "



"Toh Jiddah zan sha sai anjima, yanzu dai ki fadamin abinda kika ce zaki fad'a min"

Ya k'arasa maganar yana kallon ta. 





Ita kuma ta sunkuyar da kai tana jin tsoron abinda zai biyo baya idan ta fad'a mai ko zai yarda ko bazai yarda ba. 


Cikin k'ink'ina ta fara magana"umm emm... Dama yaya so nake a kaini boarding ni banason day Saboda a boarding anfi karatu kuma inason boarding school nidai yaya "ta k'are maganar tana zuba mai shagwa'ba. 



A rud'e ya d'ago yana kallon ta duk Yabi ya susuce" kiyi shiru mana, badai kince kina so ba,  kuma zaki iya? "




"Eh yaya inaso"




"To shike nan ki bari Zanyi shawara "



"To yaya amma kar kayi shawaran da Mamy kaji"



"To naji tashi kije "


Ba musu ta fita ranta fari k'al,  don ga dukkan alamu zatai nasara. 



Shi kuwa Yaa Sheikh wata ajiyar zuciya ya sauka had'i da furzar da wata zazzafar iska. 



 "banida wani zab'i da ya wuce na bar Jiddah ta dafi school nima zan samu sauk'in abinda nake ji idan bana ganin ta, indan yaso in Zan koma madina sai nai mata transfer don har ga Allah banason makarantar kwana ko don karatun islamiyyar ta" shi kad'ai yake maganarsa kamar zau tacce. 




**************



Three weeks ago 



Komai ya kammala Mame ta amince da maganar zuwan Jiddah makaranta, haka, Abii da Umme duk sun yarda kasan cewar sunga yadda Jiddah ke so taje makarantar kwanan. 





A b'an garan  Nana har tafi Jiddah Farin ciki da jin wannan labarin sai dai  ita Nana acikin satin nan za a kaita Saboda angama mata komai, Nana bata so haka ba amma Jiddah ta kwantar mata da hankali cewar ai itama ba dad'ewa za taiba an kusa gama mata nata shirin.   




Figo baiji dad'in Nisan da masoyiyarsa Jiddah zatai ba amma acewar sa ba wani abun damuwa bane Tunda tana tare da Nana mai yi masa ban ruwa a soyayyar tasa.  lol๐Ÿ˜‚





Haka akayi kuwa Nana ta tafi a satin,  inda kuma Yaa Sheikh yaketa yima Jiddah nata shirin don yace bayason ta buk'aci wani abu.






A kwana goma da Nana Tayi a makaranta ba Wanda bai santaba Saboda bak'in rashin ji da rashin kunya, hatta malamai sun gane ta. 


A yanzu Nana bata da wani buri da ya wuce taga k'awarta ta a makarantar Saboda kowa yak'i   k'awance da ita gudun kar a Shafa mai bak'in fenti. 





Yau ta Kama ranar Monday kuma yau ne Yaa Sheikh ya d'au niyyar kai Jiddah makaranta.





Keep flowing 

Khairaty๐Ÿ˜˜✍๐Ÿป

2 Responses to "YAA SHEIK Hausa Novels"