-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Mijinki A Tafin Hannunki

Mijinki A Tafin Hannunki

MIJIN 'KWAILA



sabon salo daga labarin *zahra adam ishaq*


"-chapter one-"

Ahankali yake tafiya da motar sakamakon yanda ya iske saitin bakin makarantar yaran yacika yakuma batse da dandazon yaran da'aka riga aka taso daga makaranta,ya d'anja gajeren tsoki lokaci guda yana kallon tsadadden agogon dake hannunshi ya taka burki kamar yanda sauran masu ababen hawa y'an uwanshi sukaja nasu burkin sakamakon dakatar dasu da yellow piper yayi.
Ranshi 'kwarai yana a dagulene koda yake ba abin mamaki bane ganin fuskar tashi babu walwala kusan dukkan na tare dashi sunsan dahakan duk da yake mutum mayen barkwanci lokaci kankane yakoma kamar wani horror abin tsoro ga kowa saboda yanda yakecin magani kullum idanunshi suna manne da farin gilashi saboda yanda ya matsama idanun nashi da kuka wanda har yazuwa yau d'innan yakasa dena kukan,
Baya zato ko tunanin zaidena kukan rasa jigon rayuwarshi dayayi a cikin watanni shidda dasuka gabata.
Yazuwa wannan lokacin yazama abin tausayi ga kowa to ai dolene dukkan mai imani ya tausayama d'an sangirin saurayin maicike fal da 'kuruciya akan fuskarshi da dukkan sassa na jikinshi,
Rashi yayi babba rashin dayake ganin bazai ta'ba samun tamka ko madadin taba.ZAHRA ADAM ISHAQ cikakkiyar budurwar dasuka sha'ku tun yarinta shine yaci kashinta da fitsarinta ya goyata a gadon bayanshi yamata soyayya dabai ta'ba yima wani mahalu'ki a duniya irintaba rana guda ciwon mara yayi fatali da rayuwar zahara yazuwa barzahu,
Adai dai lokacin da yarage saura kwana uku rak!
Daurin aurensu,
Yashiga rud'u mara misaltuwa dayawa yawa anzata ya haukace,amma dayake allah gafurune kuma rahimu saiya tashi kafad'unshi yakuma saka mashi dangana duk da ikirarinshi na dena kallon kowacce y'a mace da gashi tunda yarasa zahra.
Y'amma dayawa sunsha kawo kansu gareshi wasu iyayensu zasu kawo talla wasu text zasumai amma haryau baiga mai maye gurbin zahra ba,
Yashafi gefen fuskarshi daya tuna aneesa wacce tanace mashi kamar chewing gum saboda so,
D'iyar 'kawar mummy ce,
Ya girgiza kai batare daya ankare ba.
Kamar ance dashi ya kalli gefen damarshi ya hangota cikin dandazon yara sa'anninta kamar sauran yara akwai uniform bulu da farin hijabi jikinta sai y'ar jakar makaranta saqale a hammatarta,
Wata mummunar fad'uwar gaba ta riskeshi lokaci guda ya cire gilashin fuskarshi yasake murza idanu gabanshi na bugun goma goma,
Dai dai lokacin data tsallako gefen dayake yara sun ragu sosai,
Tana tafe tana tsokanr yaran dake gefe da ita.
Caraf idanunta suka sar'ke cikin na ishaq wanda tuni anbasu hannu amma tsabar kallonta baimasan anbasu hannunba.
Tarin ababen hawa dasuke bayanshi suka addabeshi da horn hakan yasakashi waigawa da sauri, lokacin wani har yayi mashi overtaken yana fad'in "amma kai wawane,idan kallon mata kazoyi toka bamu hanya mu wucewa zamuyi "
Ishaq bai tankaba yagyara parking mota zuciyarshi kamar zata tsage saboda tashin hankali.
Ganin ita yaketa kallo yasata cewa da 'kawayenta"ummilolo kukalli d'an 'kauye yanata kallona kutsaya kuga yanda zanmashi gobe bazai sake kallonaba,ummana tace mai kallon mutane mayene."
Saita lalla'ba kamar zata wuceshi sai dai tana zuwa saitinshi inda ya sauke glassa d'in motar ta tofa yawu, cikin sa'a kuwa ya sauka akan fuskarshi.
Sauran students y'an uwanta suka saki baki suna kallonta duk sun kasa tafiya,
Yayinda su ummilolo suka hau tsalke suna kyalkyala dariya.
Itama dariyar take don asukwane tabar wajen da gudu,
Tana zuwa tami'kama su ummilolo hannu suka tafa, kafin tacigaba dayima ishaq gwalo tanasaka hannayenta saitin kunnuwanta almar eho...ya numshe idanu yana tunano zahranshi a irin wannan lokacin tayi makamancin hakan gareshi, lallai batada maraba da zahra, hannu yasaka ya lakace miyon,ya sumbata zahra daban take, komai nata so yakeyi.
Bai ankareba ya hango zahra can kusa dawani matashi irin masu tallar agwaluma d'innan,
Ta mararaice fuska tace dame agwaluma "kai don Allah bani d'aya?
Me agwaluma cikin mamaki ya kalleta yace"kibada kud'i sai abaki agwaluma yammata."
Sudai su ummilolo sun 'kunshe baki sunason dariya suna tsoron bala'in zahra don sunsan akwai daru.
Ta murgud'a wa mai agwaluma baki,"nace kabani d'aya kawai."
Me agwaluma ya fusata yace"tunda ubanki yabani jari meze hana inbaki d'aya."
Tazaro idanu"la la la..kazagi ubana?
Me agwaluma yayi tsaki,
Aikafin ya ankare tuni ta duma wawa uku ta sura ta fece aguje da fad'in "pdp!!!"
Sauran yara dasuke tsaye sukace "wawaaaa!!!"
Tuni sun duma hannaye suna dumbuzar agwaluma,
Ganin yara sun kwashe agwaluma yasaka me agwaluma binta aguje bayan ya jefar da tiren dayazama empty.
Shegen gudu gareta ko barewa ta shafa mata lafiya,
Sauran yara sukad'au ihu "sai zahra !!sai zahra!!!!
Gaban ishaq dake kallon duk abinda yafaru yabuga da karfi.
Ya maimaita sunan ZAHRA???


��������

Aunty y'ar charas��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA* ����‍♀


chapter 2.
 




Gudu take kamar wacce zata tashi sama,
Ahaka tasha kwanar layinsu da yawa y'an unguwar sunsan halinta don haka suna ganinta suka fara dariya,
Wasu nafad'in "mai hali baya fasa halinsa zahra."
Saida ta kutsa d'an sirdad'en lungunsu kana ta dakata da gudun tana luliya agwalumar abango dafad'in"luliya-luliya danya awakin baba da dad'i."
Sai dai batayi auneba ta hango mai agwaluma a three thirty ya kutso lungun,
Hakan yasakata idasa fad'awa gidan kamar wacce aka cilla da kibiya .
Umma dake tsaye bakin band'aki da buta a hannu, zahra batamasan ta angije ummanba,ta danna d'akinta gami da gar'kama sakata.
Umma tabita da idanu,
Yayinda anty hafsat dake tsaye gefe tabita da tambayar lafiya zah....
Bata 'karasaba sukaga me agwaluma ya fad'o gidan,
Baikobi takansuba yarufama zahra baya zuwa d'akin datake ciki.
Anty hafsa cikin mamaki ta tareshi dafad'in"lafiya malam bakada hankali zaka fad'o cikin gidan matan aure bako sallama.?"
Yayimata kallon banza ranshi yana zafi kafin yace"aiba sallama ta kawoniba,wlh sai anbiyani kud'ina kokuma in karya yarinyarcen,
Yanuna d'akin da zahra take ciki.
Yayinda take lekowa ta window tana mashi gwalo,
Yakuma 'kufula,
Anty hafsat itama hararshi takeyi tana nuna mashi kofa"get out"
Ya kalleta da jan idanunshi"bansan wannan yaren ba."
Anty hafsa itama akwai masifa don haka tamike dafad'a,
"nizakama rashin kunya,wato kashigo gari ka waye haryanzu jahilcin kauye bai sakekaba,idan laifi akamaka kai ataka basirar da wannan cin maganin dakakeyi zaka kwatarma kanka y'ancine,?
Tajuya a fusace ganin yanda yake harararta,yana mata qunquni.
"bari inkira police idan yaso idan kaje bayan kanta zakayi bayanin abinda yashigo dakai gidan matan aure."
Umma tariketa tana fad'in"me yayi zafi hafsat,bansanki da hakaba,
Kifara tambayar abinda zahra tayimashi don bana raba d'aya biyu itace ta tsokanoshi.."
Umma tasake kwantar da murya tana tambayar me agwaluma abinda yafaru,
Idanunshi taf da hawaye, yake bama umma ba'asin yanda komai ya farun.
Umma tagyad'a kai tana fad'in"nasan za'a rina ai,
Nidai zahra bazan maki bakiba sai dai ince allah ya shiryeki,abinda kikeyi amma nagaji nagaji da halinki bari babanki yadawo a tattara amaidake can kauye inyaso kici gaba da halinki a can am.a nikam nagaji."
Tajuya afusace tanufi d'akin da zahra tuni ta danna mashi sakata.
Anty hafsa tazuge jakarta tafiddo da dubu d'aya tamikama mai agwalumar tana hararashi dafad'in"next time kasan yanda zakayi magana da nasama dakai ".
Shima hararta yayi,
Sai dai bai tankaba.
Anty hafsa tadafa kafad'ar umma wadda tazauna zugwui da damuwar da zahra ke sakata akoda yaushe,
Tace"umma pls banason ganin damuwarnan taki,kina sane da lalular dakike fama da ita,
Umma kamata yayi kinama zahra addu'a bawai yawan damuwaba."
Umma tasauke numfashi"toyaya zanyi kinasaje da halin yarinyar nan,khatta da sunan da yaran unguwa suke kiranta dashi wai *zahra'u mala'ikar yara inkin mutu ba ruwan Allah walakiri ya jibgi kayanshi*."
Umma taci gaba"sam idan kinga nasamu naji sa'ida to kuwa zahra tatafi makaranta toyanzu hatta da makarantar abin yaci tura iya shege kullum sabon salo take fiddowa,jiya Monday tafara zuwa makaranta js 1,take amma wai baifi wata biyu da shigartaba yara bakwai ta fasama kai da dutse,dacirema wata yarinya ha'kori,
Principal ta bugeta shine tatara yara bayan antashi makaranta sukayima motar principal ature,da 'kasa har suka fasamata glass din mota.shine fa akazo hargida dakorarta sukayi dakyar babanku yasamu ya mayar da ita suka amsheta ,amna saida yabiya kudin duka asarar dasukayimata kinga ayau har ta dakko wata maganar.
[9/20, 1:16 PM] mum meenat: Anty hafsa ta sauke ajiyar zuciya,
"nidai umma sainake ganin kamar lamarin zahra fa akwai sa hannu wannan abin datakeyi bafa normal abu bane,gaskiya is abnormal ne umma yakamata mutashi tsaye,yarinya saikace ana kad'ata da ruwan hanji sam zahra bata d'auko halayyarmuba."
Umma tace "kema kya fad'a ai,nida ace ba'a gida na haifi zahraba tozan iya rantsewa da Allah anyiman musayar tane batawa bace ba.gata sam bata d'auko kamanni dakuba,hakanan bata dauko halayyarkuba.
Ku shidda na gaifa allah ya dauki ran maza biyun dasuke cikinku sai kumata guda hud'u da allah yabarmun,duk na aurar daku ku ukku akan matakin karatun zamani dana addini dai dai gwargwado bamu tauyekuba,gakunan duka cikin rufin asiri amma zahra sam tazamo zakka acikinku,itabaga karatuba baga natsuwar ba,itakenan kamar tunkiya duk inda ta gifta sai ance kayya."
Umma ta'kare maganarta kamar zata fashe da kuka.
Da'kyar anty hafsa ta shawo kan umma,ta lalla'bi zahra ta bud'e dakin tanufi kitchen tadauko abincinta wanda tuni ya sandare saboda hucewa,
Tazauna kamar wata saliha tanacin abincin anty hafsa namata fad'a akan rashin jinta.
Itadai bata tankaba,
Har lokacin sallar la'asar yayi tatashi tayi wanka akaja wata kwasheshiyar jagira wadda tasamu matsugunni a gefen kunne,
Tad'auko janbaki jajawur ta dafsa bayan ta zagaye bakin nata da tarin ba'kin kwalli.
Tajuya da fuska tanama madubi murmushi tana tsuke d'an matsakaicin bakinta aganinta ba nabiyunta wajen kyau.
Duk da tana cikin 'kunci baihanata ganin kyawon nata ba
Sai dai aranta kullum tanajin haushin meyasa anty hafsa da anty salma kai harma da anty lubna duka suke farare tas,
Amma ita saitayo duhun fata,
Taja tsoki ita d'aya dafad'in"nadaisan dama ummanmu ba sona takeyiba shiyasa ta haifoni ba'ka.
Tasaka uniform na islamiyya check blue dasuka d'au guga sukayi luf dasu,
Tafito har lokacin umma bata dena fushi da itaba,
Takalli umman cikin kukawa tace"umma natafi,"
Umma tace"adawo lafiya sauran yauma akawomun 'kararki kinyi fad'a dawani mutum zaki bani labari."
Ta turo baki gaba,batare da tatankaba,
Umma tayi tsaki dafadin"shashasha kawai shekaru shabiyu amma fitinarki tafi ta masu shekaru ashirin."
Itadai gaba tayi abinta kamar yanda tasaba,
Tafito lungunsu tana gunaguni,charaf idanunta suka sauka akan na ishaq wanda ya sar'ke hannayenshi a kan kirjinshi yakafe kofar lungun nasu da idanu,
Duk da rashin tsoro irinna zahra saida gabanta yafad'i,amma dayake tsiwa gareta saita murgud'a mashi baki dafad'in''kurwa
ta kur namana d'aci,me d'a yaci d'anshi mara d'a yaci 'ko'kon tsuliyarshi."
Ishaq duk da baya jiyo abinda take fad'i shidai komai takecewa ahakan burgeshi tayi,
Yanason d'an murgudennan nata,
Ya numshe idanu daya tuno da zahra gaf da bikinsu yakafeta da idanu tayimashi murgud'e dafad'in "kallonfa,
Alokacin murmushi yasaki yanace da ita"nanda wata biyu saina tsotse bakin murgud'enanna naki."
Alokacin dariya tasaki dacewa"kai yaya ishaq,bakajin kunyata nifa kanwarkace".
Ya runtse idanu,kamar zai fashe da kuka afili yafurta "i really luv yhu zahra,inason koda mace mai sunankine bare kuma mai kammani dake."
Post everyday nsha Allah
September 20, 2017 at 7:31pm ·

         ��������

      by
Anty yar charas ����
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*����‍♀

*to you maman Aliyu this page is for you*��



Chapter 3.


'karfe hudu na yamma dai dai lokacin da matashin ya cinna hancin motar tashi yazuwa cikin tanqamemen get d'in gidan,tare da matsa horn wanda yasaka megadin tashi da sassarfa yaxuwa bud'e katon get din.
Kamar almara ko mafarki haka baba yusha'u yake kallon fuskar ubangidan nashi dake cike da zallah nishad'i,
Yasake murza idanuwa aranshi yana ayyana'shin anma oga kyautar d'an mutum ne da kayanshi kome,?
Ganin yakasa aiwatar da aikinshi yasaka ishaq sake matsa horn da 'karfin gaske wanda yasaka baba yusha'u tale get din yana washe hakora dafad'in"barka ubangidana barka dazuwa isyaku na zahra baban zahra kaga angon zahra'u...
Isha'q ya numshe sexy idanunshi lokaci guda yanajin wani yanayi yana tsalga ainahin 'kasan zuciyarshi,
Ya'isada shigoda hancin motar lokacin daya saka hannu a aljihun jeans dinshi ya dumbuzo kud'in da bazai tantance adadinsuba ya dam'kasu ga baba yusha'u wanda tuni ya warcesu yana sake jinjinama isha'q d'in.
Yafito daga motar bayan ajiyeta a mahalinta,yana cilla key's din motarshi sama yana cafewa a tattare dashi akwai zallah nishad'in daya kwashe watanni shidda gam batare dayayi makamancin hakan ba.
Yakutsa kai acikin 'katon falon dayakai ma'kura wajen tsaruwa,dagani babu tambaya yasamu tagomashin dukiyarda tsayawa 'kididdigeta 'bata likacine.
Da sallama yashiga cikin falon idanunshi suka sauka akan 'katon kyakyawan hoton zahra wanda tayishi alokacin datake saukowa daga cikin jirgi,ajikinta akwai ba'kar suit saitayi roling white gyale akan wuyanta harzuwa kanta.
Fuskarta akwai full make'up don ita gwanar kwalliyace abinda yake karama isha'q kaunarta don yanason mace y'ar gayu.
Tasaki silent smile dake 'kayata fuskarta mai matsakaicin kyau.
Duk da ganin doctor ruqayya (wato mahaifiyarshi)
Baihanashi 'karasawa ga hotonba yasaka yatsanshi guda ya xagaye gefen kumatunta dake murmushin,lokaci guda idanunshi suka canja kala,
Yajuya kamar zaifashe da kuka,muddin zaidinga kallon hoton zahra bazai ta'ba kallon wata d'iya mace da gashiba,
Face zahra mai kamanni da zahransa.
Yadad'e tsaye jikin hoton yanason tabbatarma kanshi banbancin dake tsakanin waccen zahra 'karamar dakuma real zahramshi,amma yakasa gane koda abu d'aya dazai iya tabbatar mashi cewa bafa zahranshi ce takoma 'kan'kanuwaba.
Doctor ruqayya tatako a hankali zuwa kusa da d'an nata tadafa bayanshi cikin sanyin jiki da'alamar tausayawa kamar yanda tasaba.
Sa'banin da ayau fuskarshi fayau take babu tarin damuwarnan dake 'boye kyawon fuskar tashi.
Kama hannayenta yayi duka guda biyun idanunshi cikinnata duk da nata idanun suna manne da siririn farin glass din (medical).
Saida ya 'kawata fuskarshi da murmushi sannan yace"mummyna nasamu zahra..zahra tadawo gareni mummy awannan karon bazatayi nesa daniba,d'iyarki tadawo gareki mum....!
da hannu ta dakatar dashi"isha'q wai sai yaushene zakasan wanda yamutu baya dawowane,ayaushene zakasan cewar allah daya d'auki zahra yafimu 'kaunarta.saiyaushene zaka dena takura tunaninka da lafiyarka akan wadda babu ita a doron duniyane?
Zahra ta mutu, a gaban idanuna aka wanke gawar zahra.zahra d'iyar 'kanwatace nice na reneta tundaga ranar da mahaifiyarta ta haifeta batakoga fuskartaba takwanta tamutu,naso zahra na tausayama zahra nasani bayagani kaine mutum na biyu dayasha d'awainiya da zahra amma kasani zahra ba rayayya baceba.
Mutayata da addu'ar gafara dabeman dacewa don zahra mutumce guda harda 'kari
Ama yamuka iya'allah yafimu 'kaunar zahra ya amsheta a daidai lokacin damukafi bu'katarta,saimu bita da add'ua kaikuma kasaka dangana wa ranka ka rungumi 'kaddara matsayinka na musulmi nagari."
Bai katsetaba har saida ya tabbatar da takai aya,sannan yaaja hannayenta yaxuwa d'aya daga cikin kujerun falon yazauna yana fuskantarta,bayan yagama saita dukkan natsuwarshi gareta don ta yarda dashi takuma gane baizo da wasaba a wannan karon."mum wlh kiyarda dazancena mum,naga zahra ganin idanuna,zahra dai mum tana cikin students mum, a tattare da ita akwai yarinta nasani bawai ainahin zahrata baceba.amma inada tabbacin wannan itace zahran da zahrana take gayamun akoda yaushe,itace wacce zahra kefad'amun cewar _isha'q zaka samu zahra madadina koda bayan raina,zakasamu xahran da zata d'auke maka kewata.naro'keka da kobayan babu raina kajirayi xahra,kasota kamar yanda kake sona koma fiye da hakan._ _inamai tabbatarmaka itace alkairi a gareka._
Yaci gaba dafad'in"mum dani dake daduk wani ahali na gidannan yasan dahakan,mum kinatsu kituna maganganun zahra don allah kada kice wai bana cikin hayyacina."
Doctor ru'kayya tami'ke cike da tsantsar tashin hankali,tana zagaye katon falon hannunta goye a bayanta akan fuskarta akwai zallah damuwa dakuma rud'ani.
Sai dai kuma batasan tayaya zata'iya 'karyata isha'q a 'irina wannan lokacin dayazo mata da magana sahihiyaba.
A dukkan nazarinta dakuma hasashe irinnata tanada tabbacin isha'q yana cikin natsuwarshi ne.
Tasauke numfashi,itakam a dukkan tarihi ko'a mafarki kai a film's ko fili bata ta'ba ganin soyayya zahirinta irinta isha'q da zahraba,
Idan zahra tayi ciwo isha'q ko baya 'kasar shima saiyace bayada lafiya,
Kuma dsame inda zahra tafad'a yana mata ciwo.
Kai tasha jaraba soyayyar tasu tana ganin ko plane ne suka had'a mata amma inaaa,saitaga zahirin 'kaunane kawai dakuma had'uwar jini.
Sam bazata iya wancakali da bu'katar isha'q a wannan lokacin dayake neman taimako daga garetaba.
Tataka a sannu ta'isa gareshi tadafa kafad'arshi"bazan kiraka da wanda baya cikin hayyacinshi ba isha'q,nasani soyayya ba 'karya bace ba.
Koma dai menene kaci gaba da bibiyar yarinyar,nikuma zansamu lokaci kakaini har gidansu inganta da idanuwa don tabbatar da gaskiyar zancenka,kafinnan kasamama zuciyarka salama.zahra adam ta isha'q ce."
Yawani d'ane bayanta yana fad'in"tnx so much my luvly mother."
Ta murmusa kawai,gami da kama hannayenshi yazuwa dining don bin abinci.
**************
Zugar su zahra da'aka taso makaranta,kai dagani babu tambaya kasan yau akwai masifa,itada 'kawayenta duka zasu tseremata a shekaru amma tafisu yanayin girma,saboda jikinta irin ga'ba-ga'ba dinnan yake.
Su shidda reras duka suna fadanci wa zahra wadda keta ruwan bala'i ta d'aura kallabi saman hijabi taci d'ammara da dardumar dasuke xaunawa kanta a makaranta.
Bakinta har kumfa yake tana bamasu ummilolo labarin yanda zasuci uwar dije ali,wacce tasaka malam yayimata bulala biyu d'azu a aji.
Taraba yaran gida uku tace"ke ummilolo kune da hinda zaku shiga gidan saikuce a sammaku ruwa zakusha,daganan saikuce ina dije 'kawarmu tazo ta rakamu tana zuwa mukuma zamu la'be zaure mu'kunshe mata baki,mujawota aje lungun bata kashi.
Wlh saita gane batada wayo."
Sauran yaran sukace"eeeefaa haka za'ayi kuwa."
Sukatafi d'uuuu kamar garken tumakai,
Kafin sukai gidansu dije yamma tayi sosai,
Can wani kango suka hango almajiri yana kashi,
Zahrace tafara hangoshi taja dabaya da sauri,tace da sauran 'kawayennata"kutsaya kai ga al'majiri yana kashi,asamu d'an dutse a jefe takashin kashin."
Suka la'be suna lekenshi,can ummilolo ta dau dutse sauko a qeyyar almajiri,suna fad'in amma ka'iya kanannad'a maciji."
Kowando baigama sakawaba yabiyosu a guje,dayake ko barewa nan tagansu ta barsu almajiri ko 'kurarsu baiganiba.
Basuyi burkiba saizauren su dije,
Saida suka huta sannan suka gyara kamar natsattsu,ummilolo ce tashiga da sallama,innar dije na alwalar mangarib ta'amsa da kallon rashin sani akan fuskarta.
Ummilolo ta gaisheta ta amsa,sanna tace"don allah a sammun ruwa zansha".
Matar mai fara'a ta debomata ruwa a randa mai sanyi,ummilolo baki kawai ta d'ofana, ta mikamata kwanan dafadin "angode"
Matar tace"yauwa".
Tana juya baya ummilolo tayimata gwalo,
Sannan tace"ina dije yau banganta a makarantaba."
Matar tajuyo da fara'a tace"aiko na aiketa siyen manja aitadad'e da dawowa.kema naga kinmakara ko aikenki mamanki tayine.?"
Ummilolo tayimata gatsine dafad'in "uhm".
Matar tace "to ayimaza akai lada gida ko.?"
Ummilolo tajuya dasauri,tafita donyima ogarsu zahra albishir amma saita hango zahra ta nad'e 'kafar wando tacire hijab ta'ajiye gefe guda.
Tana turza 'kafafu a'kasa
Sauran yaran sunja masu layi 'atsakaninta da dije,
Dagudu ummilolo ta 'karaso ta bugi 'kirjin dije,sannan ta bugi na zahra tace"wanda yaji zafi ya rama."
Aikafin kace miye,zahra ta kaima dije duka"ninaji zafi."
Dije da tuni jikinta yad'au rawa tace"nidai bafad'a nazoyiba uwata ta aikeni,kuma inajin maganar uwata."
Zahra ta fidda manyan idanunta dafad'in"lalalala towaye bejin maganar tasa uwar?"
Dije da ido yacika da hawaye tace"kigane".
Zahra takaimata duka,
Nanfa fad'a yasar'ke,zahra 'karfi kamar doki nan danan tadunga sunkuta dije da 'kasa,
Yara sunamasu wa'kar "bamu rabawa sai dai mu'kara zugawa bugi cikin."
Zahra ko harwani 'kara za'kewa takeyi tana nusar ruwan cikin dije.
Isha'q daya dawo daga gidan abokinshi sadiq suna takowa a'kafa saboda hanyar batada kyau yayi parking motarshi acan farkon unguwar.
Yaci gaba dabama sadi'q labarin "abokina kai idan kaganta sam batada maraba da zahrata,"
Sadi'q yace"gaskiya abokina kakamu sosai wlh."
Isha'q yasaki dariyar 'kasaita dacewa"kawai kamanninta da zahrane yasaka naji wani mayen sonta,kai bayaga zahra banta'ba 'kaunar wata d'iya mace kanartaba."
Sadiq ya kwashe da dariya"gaskiya abokina koda banga girl dinnanba nasan mai zafice,don nasan bakayi da 'kwaila."
Isha'q ya murmusa...
Maganarshi ta ma'kale cik,
Sakamakon hango zahra dayayi da bataliyar yara suna dambe,zahra har 'kara over acting takeyi.
Sadi'q dake duban yaran yace"kai yarinyarcan badai masifa ba,allah tsine ranar da zata fito takoma ga allah batare da anrabata fad'a da yaraba.
Yarinya saikace shed'aniya,
Wannan zanga wandanzai kwasheta yakwashi bala'i.
Isha'q yaji 'kirjinshi yabuga dam.
muje zuwa guy's
September 21, 2017 at 12:05pm ·





     ������������
   *Anty 'yar charas*��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA* ����‍♀





Chapter 4.


Isha'q yaji 'kirjinshi yabada dam,
Amma dayake jarumine saiya fuske gami da janye hannun sadi'q dafad'in "kayi abinda yadameka malam",
Sadi'q yasake kyal'kyalewa da dariya yana fad'in"allah yarinyar ce so funny"
Isha'q yaja tsoki bai tankashi ba,
Sai gab da isha'i zahra tanufo gida,'kirjinta yana bugun uku-uku aranta tana addu'ar "Allah yasaka umma bata tsakar gida,
Talala'bo tana sand'a lokacin datashigo gidan takalma a hannu bayan tafara zuro kanta taga gidan babu kowa.
Tafara tafiya sad'af-sad'af danufin fad'awa d'akinta sai dai batayi auneba taji umma tacafketa caraf ,
Ta waigo fuskarta da alamun tsoro,
Kafin tayi wata magana umma takifa mata mari.
Da tambayar "daga gidan ubanwa kike?"
Zahra idanu suka raina fata,
Tafara ro'kon umma"wayyo ummana kiyi ha'kuri bazan sakeba."
Umma tace"rufemun baki shashashar banza,bazan 'kara d'inkiba datana tasiri dayanzu namance dawata aba wai ita damuwa.meyasa kikeson sakamun hawan jinine zahra,abinda duka y'an uwanki basuyiba."
Umma ta'kare maganar kamar zatayi hawaye.
Zahra dai kuka take tana"allah umma nadena."
Umma bata bartaba saida tayimata ligi-ligi tasaketa,tafara haramar alwalar isha'i.
Zahra ta 'kyalla idanu taga umma tashige d'aki,
Hakan yabata damar sake ficewa gidan da saurin gaske,
Bazata mance kirarin dasukeyima kansuba wai *abuga asaki bata maganin d'an iska sai dai ta'kara taurin fata*.
Azauren su ummilolo tala'be,tana 'kwalama ummilolon kiran,
Hajara kishiyar innar ummilolo tafito tana masifa don tasan zahrace"kewai wacce irin ballagazar yarinyace,halan kekam uwarki bata kwa'ba maki.duka yaushe kuka shigo gidan amma dayake bakida tarbiyya harkin sake fitowa,to oya maza fice anan ummi babu inda zataje."
Shegiyar yarinyar yarinya mai kama da d'inya,ke ba'ka halinki ba'ki.
Zahra ta murgud'a baki dacewa "badai niba."
Inna hajara tace"sai ubanwa"
Zahra cikin rashin tsoro tace "ubanki"
Aiko inna hajara tayo kanta zahra tajuya da niyyar rugawa amma tuni inna hajara ta cafketa.
Mari biyu 'kwarara tayi mata, taci gaba dafad'in"duka iskancin dakikeyi 'kyaleki akayi.wlh kinshigo gonata ubanki zakici."
Zahra dayake ruwa ruwace tuni ta 'barke da kuka tayi waje aguje,
Takuwa koma 'kofar gida ta tara duwatsu tadinga yima gidansu ummilolo ruwan duwatsu,
Duk da haka bakinta bai sassauta da zagin datake d'urama hajaraba.
A tsotsayi d'an hajara yafito zashi kicin d'aukar abinci dutsen ya sauka akanshi jini sosai ya tsinke ganin hakan yasaka hajara kama hannunshi suka nufi gidansu zahra tanata masifa. 
 Zahra daganan zugar yaranta sukaja,suka la'be lungu ilai kuwa saiga inna hajara tadawo da abbalo ansaka mashi bandage,
Zahra da sauran 'kawayenta sukayi masu ature da 'kasa har cikin bakin hajara da idanuwanta.
Zahra data du'ka tana 'kyalkyala dariya tace"kuma wlh kisake dukana saina kama wannan d'an naki a islamiyya saina fasamai baki."
Inna hajara tace"tsinanniya kije zaki samu dai daike."
Zahra dake wani gantsarewa tace"tsinanniya tana bayan uwarta tanashan nono,"
Sauran yaran suka kwashe da dariya.
'karshe dai inna hajara ganin zasu kunyatata gaban mutane yasakata sulalewa tayi gida,acan tad'ora sabon bala'i tana sauke kwandon zagi akan zahra da iyayenta.
A filin gad'a ma zahra saida suka dambace da yara kusan uku,
Daganan tace ayi zuga atafi jan fad'a.
Suna tafe duk wanda suka gani saisun tsokana,wani ya 'kyalesu wani yabisu a guje amma baya iya kamosu.
Dai dai wani lungu suka hango saurayi da budurwa na tad'i,
Zahra tace "yauwa alhmdlh dama waccen habibar dake fira prefect d'in makarantar muce gata muguwa tayita dukanmu,
Kuzo muje"
Yara suka bita d'uuuu,tana gaba.
Dayake garin akwai hasken nepa dakuma na farin wata,
Habiba na tsaye gefen saurayin nata can gefe wasu samarine data gama yima wula'kanci taga mai mota yazo.
Bata saka hijabiba sai d'an gyale daya tsaya iyakar kafad'unta.
Gefe dasu teburin masu shayine damasu tsire antara majalisa ana cafta.
Zahra tana isa kusa da habiba batayi wata wataba tasaka iyakar 'karfinta ta fincike zanin habiba,
Habiba gashi sam bata saka undey ba.
Saiga 'kafafun habiba tsaye zalo .
Zahra kuwa tace 'kafa menaci ban bakiba.
Takwasa aguje,yayinda saurayin habiban ya rufa masu baya
Tsabar kunya habiba saita du'ke inda take.
Sauran samarin data yan'kwana kuwa har fad'uwa sukeyi suna burgima saboda dariya .
Majalisar masu tea ma dariya suke suna 'karawa.
'karshe habiba d'an gyalen dake kafad'arta ta yafa a kafafunta.
Da rarrafe ta shige gida .
Su zahra sunyi gudun da yakai nisan inaa.sannan suka yarda zanen saurayin ya tsintoshi bayan ya du'ka yanata hakin wahala
Dafad'in "shegun yara saigudu kamar zomaye."
Daga tonon wannan fad'an kowa ya ware gida,
Kanshi tsaye banda zahra dake faman ra'be ra'be.
Tamakure a lungu,
Abba yadawo daga nemanta har yagaji yanufo gida yaci karo da mutum...
Matsalar nepa.
Ayi ha'kuri da wannan
September 22, 2017 at 7:44pm ·


          ��������

   by yar charas��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*����‍♀



Chapter 5.


Da touch light ya haske mata fuska ta d'ago fuskarta da alamar tsorata don sarai tasan abba bayada wasa.
Da 'karfi yakira sunanta"zahra,mekikeyi anan daga ina kije.?"
Kanta tsaye tace"wasa naje yi",
Abba ya gyad'a kai,"dakyau".
Kawai yafad'a yayi cikin gida abinshi,yayinda zahra ta rufa mashi baya.
Umma tana tsakar gida hankali a tashe abba yashigo zahra nabin bayanshi,
Umma tana ganin sundawo tawuce d'aki abinta ranta a dagule yake.
Bai tanka zahranba ya kutsa dakin da umma take,tahad'a kai da gwuiwa idanunta daf da hawaye.
Abba yadafa kafad'arta dakiran sunanta"amina,kiyi hakuri kifidda damuwar zahra acikin ranki,kisani kowacce rayuwa akwai jarabta mu tamu jarabtar kenan,don haka kima dena zancen wai kiyita dukanta.kitattara kici gaba da addu'a amma ni sam lamarin zahra yadena bani mamaki yakoma bani tsoro."
Umma tasauke numfashi,"to yaya zan'iya cire damuwa abban zahra,damuwa ai ita keyin kanta.ace babu rana ta ubangiji dazata fito takoma ga allah ba'azo ancedani zahra ta'aikata wani abuba.saikace tafi sauran y'ay'ane."
Abba yace"kul dakiyima yarinyar nan baki,mudaici gaba da addu'a,jiyama liman yazo hargida yanamun kashedi wai tajefashi kwata zashi sallar isha'i."
Umma tazaro idanu dafad'in "liman d'in dakanshi,,?
Abba ya gyad'akai"'kwarai kuwa,waisuna wasa anrufe idanunta toyazo 'ketare kwata tazata yarinyace shinefa ta cakumeshi,shikuma wai yana addu'ar zuwa masallaci bazaiyi maganaba.
Nana kokuwa ta sar'ke tajefashi kwata."
Umma duk da 'bacin ran datake ciki saida ta dara,
Data tuna yanda liman yake saka malummalum idan zashi masallaci.
Ta girgiza kai,"Allah ya shirya,"
Abba yace "ameen."
Zahra kam tuni ta kwanta abinta, bata tsaya neman abincin dareba don dama ba ma'abociyar cin abinci dayawa bace.
Barta dai ga 'kwalama wannan fa ogace.
**********
Bayan kwana biyu....
Zaune yake a tsakiyar grass carpet d'in daya gewaye tsakiyar 'katon falon,
Gabanshi laptop ce yana 'kara nazarin banbancin dake tsakanin zahransi da little zahra kamar yanda yasaka mata suna,
Gefe guda 'kanwarshice hanan wacce bazata shige tsaran zahraba,
Doctor ru'kayya ta tako ahankali daga stairs cikin dakakken leshinta mai tsadar gaske,jikinta akoda yaushe yana fitar da siririn kamshin turarenta mai tsada.
'yar kyakyawar fuskarta dabata tsufa tana manne da glass din daje kuma kayatata.
Isha'q da hanan atare suka mi'ke dukansu suna sakarmata murmushi
Tazare wayar dake kunnenta tana sakarma kyawawan yayan nata murmushi,
Ta kalli isha'q dafad'in"yayankane muke maganar yarinyar dakake bani labari,yace kamata yayi mushirya muje muganta ayi komai da lissafi,sannan yakira wayarka tana a kashe."
Isha'q yasaki dariya yace"nakashetane nasaka charge mum".
Yami'ke da sauri yana fad'in"mum kice kawai inshirya yau saigidansu pretty,yawani dun'kule hannuwa da naushin iska,wlh mum saikin ganta she's very beautiful nd younger."
Mum tace "kome kakeso isha'q aibaka ganin muninshi,haka kake tun kana yaro.sa'banin yayanka dayakeda a'kida dakuma ra'ayinshi na santseni."
Ya shafi gefen fuskarshi yana murmushi,"Allah mum tanada kyau,iluv zahra very much mum."
Zaunawa tayi tana canja channel''idan kagama surutunka inajiranka,haka zakaje kana rawar jiki ai yarinyar saita raina class dinka,ya murmusa yana tafiyarshi ta 'kasaita yace"haba mum kada kisa wannan ta'kwalar ta rainani mana."
[9/23, 10:00 PM] mum meenat: Yanuna hanan wadda ta zubama yayan nata idanu tana kallonshi,
Dasauri ta tashi ta la'be bayan mum dafad'in "mum zakije dani".
Doctor ru'kayya tamurmusa tace"kibari dai watarana saikije lokacin kinsamu hutun makaranta,yanzu kam ai zaki takuratane."
(tazata zahra babbace )
Isha'q kam fakaitarta yayi yasaki dariya dafad'in"sai mumcy",
Tana zaune tana kallon wani series yafito cikin hadadd'en yadinshi filtex mai yal'ki ruwan madara,
Kanshi yasha hular zanna bukar baqa,
Kafarshi cikin bakin takalmin daya matu'kar dacewa da shigar tashi.
Handsome and giant,
(abinda na raya kenan.)
Hadadd'en 'kamshin turaren American crew yakasa barin jikinshi,
Still akwai farin glass a idanunshi,
Ita kanta doctor ru'kayya tana alfahari da isha'q matsayin d'anta very handsome guy.
Yanada dukan qualities daya kamata mace taso a tattare dashi,
Dogone irin tsayin hadaddun maza d'innan,yanada fasalin 'karfi da jarumta a tattare dashi don 'kwarae mayen exercise ne.
Yana rud'a makwad'aitan mata da kamfacecen 'kirjinshi dakuma murdadden jikinshi.
Wankan tarwad'ane wato ya d'auko kalar doctor ru'kayya ne,
Sa'banin yayanshi aliyu dayake fari tar yad'auko kalar mahaifinsu.
Isha'q gogaggen matashine wayayye daya samu shedar kammala karatunshi na degree mataki na biyu akan mass communication ma'aikacine da gidan talabijin ta 'kasa wato NTA sosai yake samun sa'konnin yammatan dasuke mutuwar 'kaunarshi musamman don fara'arshi,
Dakuma iya zama da mutane don isha'q bdai iya kyautatawa ba.
'karasowa yayi jikinta ya tallafi fuskarta da hannayenta"am readay my mum"
Yafad'a da shagwa'barshi,memasa kyau.
Tace "i see"
Tami'ke tana gyara zama mayafinta dasaka glass d'inta,
Isha'q ya tsuramata idanu"am proud of you be my mother mumma."
Tashafi fuskarshi itama da murmushi,aranta tana jin zallah farin ciki saboda dawowar walwalar d'anta daya rasa tsawon lokaci.
Tare suka jera gwanin sha'awa suka shige cikin d'aya daga cikin motocin gidan,
Tazauna a mazaunin kusa da driver yayinda isha'q yake driving suka lula gidansu zahra.
Umma tagama gyara d'an matsakaicin gidansu,tana saka turaren wuta tajiyo sallamar doctor ru'kayya,
Taleko da fara'arta tana fad'in "lale marhaba da ba'kin yamma."
Doctor ru'kayya ta murmusa aranta tana yaba wayewar umma.
Ruwan randa mai sanyi umma ta'ajiye gaban doctor ru'kayya,bayan ta shimfid'a mata tabarma.
Dr.rukayya tazauna tana cire gilashin idanunta,likaci guda tana kai ruwan da umma ta'ajiye mata a baki.
Takur'ba kana tace da umma"nasan baki sanniba ko?."
Umma ta gyad'a kai"kwarai kuwa."
Dr. Ru'kayya tasake murmusawa tace a ta'kaice"sunana ru'kayya anas kado malumfashi,ni haifaffiyar malumfashi ce,iyaye da dangi mahaifina y'an canne,sai dai dangin mamana sune mutanen funtu'a, nayi karatun likitana anan Nigeria sai dai nasamu sakamakon zama babbar medical doctor ne a India,inda acanne na'karasa karatun nawa.
Nayi aure anan kaduna da mijina babban d'an kasuwane anan abubakar gumi,awancen lokacin ayanzu yanada manyan kamfanoni a ciki da wajen 'kasar nan.
Inada y'ay'a uku maza biyu sai autata hanan,
Babban sunanshi aliyu yayinda mai binsa shine isha'q,
Daganan haihuwa ta d'aukemun sai daga baya Allah yabani hanan,Aliyu yanzu haka yana 'kasar turkey yana kula da kamfanin mahaifinshi dake jigilar rid'i."
Muje zuwa
September 23, 2017at 10:27pm ·



*by anty y'ar charas*����‍♀
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀


NEW WORLD NOVELS


BY MAMAN MEENAT

EDITED :AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR)

Wannan shafin naku ne yn (Madarasatul Tahafeezul Qur' an Funtua, Allah ka qaramana fahimta a
 iliminmu)


Chapter 6.


Doctor ru'kayya tad'an tsagaita jin ana kwad'a sallama,duka itada umma sukakai dubansu ga hanyar shigowar,abbane yashigo da ledar yalo a hannunshi,umma tami'ke da sauri tana mashi sannu dazuwa ta'amshi ledar dake hannunshi tawuce d'aki da'ita.
Abba yadubi hajiya ru'kayya kallon rashin sani,
Itakuwa 'kasa tayi dakai tace"malam ina wuni ya hidindimu."
Abba ya'amsa da "Alhmdlh"yawuce ciki bakinshi fal da tambayoyi.
Daki yasamu umma tsaye da alama zaman jiranshi takeyi,yamata kallon tsaf kafin yace"wace hajiyace nagani anan tsakar gida,kuma hada wani d'an saurayi nagani a 'kofar gida dawata kwatsetsiyar mota,wasuke nema kuma?."
Umma tad'anyi jim kafin tace"to malam nikam bazan iyacewa komai ba,nadaiga tazo batace ga abinda yakawota ba,amma naji tad'auko tarihin yaruwarta tana bani,bansan da wacce tazo ba."
Abba yace "shige muje,aiyanzu zamani ya canja bana barki ked'ayaba.ina zahra ne,ko bata dawo daga islamiyyar ba.?
Umma tace"kaima kasan nanda isha'i yayima zahra kad'an kaganta anan gidan,watakil sai takwas na dare idan tagama yawon tsokanar jama'a.
Abba yayi 'kwafa yace"gab nake da kawo 'karshen iskancin yarinyar nan ai.
Umma tafito har tsakar gidan tana mitar"ai indai zahra ce,bazance bazaka iyaba amma abune mai wahalar gaske."
Dr.ru'kayya ta kafe umma da idanu tanason nazarin maganar datake jiyowa tana tashi daga bakin umman.
Gefe baba yazauna bisa kujerar roba,yayinda umma tazauna akan y'ar tsugunno.
Abba yasake gyaran murya yace da dr.rukayya"baiwar Allah lafiya dai,bamusanki ba,maid'akina tace kinzo kinata bata tarihinki kodai kinyi 'batan kaine.?"
Dr.ru'kayya murmushi tasaki dacewa "ko d'aya malam.kamar yanda nabawa matar ka labarina hakane,inada yaro isha'q wata'kila kaganshi anan waje,hakane?"
Tayi tambayar gami da tsatsare abba da fararen idanunta masu cike da zallah wayewa.
Haka kawai abba yaji tayi mashi kwarjini idanu,tanada tarin baiwar cika ido.
Ya'amsa dacewa"kwarai kuwa."
Tace "gud"
"Yarona isha'q yarone nagari,yanada kyakyawan hali abin ayaba,bawai don yana d'anaba a'a,halin isha'q yasha banban dana sauran maza donshi mutum ne dayasan hakkin wanda yake tare dashi,bayada girman kai bayada miskilanci,yataso tun yana yaro tare da zahra,d'iyar kanwatace wadda Allah yayima rasuwa tun ranar data haifeta batako kalli fuskarta ba.zahra tatashi cikin maraicin uwa hakan yasaka nad'auke duk da mahaifinta baiso hakanba, nareni zahra cikin 'kauna da aminci.
Zahra tasha'ku da isha'q saboda idan bani ko isha'q ba zahra bata yarda dakowa acikin gidanmu.
Lokacin da isha'q yashiga secondary zahra anyayeta,komai nata isha'q ne yakemata shine ya canja mata sunanta daga zahra adam yamayar mata *zahra adam isha'q*,tunda nake a rayuwa banta'ba ganin soyayya da sha'kuwa irinta zahra da isha'q ba.
Kai intakaice maku labari,lokacin da isha'q zaitafi Germany karatu gaba d'aya dashi da zahra saida suka kwanta asibiti.
Alokacin munzata sha'kuwace,sai dai abin mamaki sam zahra bata kula samari duk da takammala karatunta na secondry ko saurayi zuwa yayi wajenta saitace yaje yatambayi isha'q idan yayimashi to itama yamata.
Isha'q kam kullum cikin kushe samarin zahra yake,kullum cewarshi hadadd'en gaye zahranshi zata aura."
Doctor ru'kayya ta numfasa tacigaba,
"zahra yarinyace mai tarbiyya da tsoron Allah,tanada matukar natsuwa da kamala,mahaddaciyar Alqur'ani ce.zahra wankan tarwad'ace tanada yanayin girman jiki,don duka sa'anninta zaka zata tagirme masu saboda jikinta mai saurin tofone,
Sam magana bata dami zahra ba,gwanar kwalliya da tsafta,gwanar iya kalailaye mutane da tattausan lafazi ce.
Lokacin dana lura cewar zahra da isha'q sunkamu dason junansu sainafi kowa murna,don inaganin isha'q yayi matarvda har duniya tanad'e bazaiyi kaico da itaba.
Sa'banin yayanshi dabai dace damacen kirkiba.
Isha'q baitafi karatuba saida baikonshi da zahra,
Koda yaushe suna manne a waya suna firar soyayya,
Alokacin itama takoma makaranta tana karantar likita cewarta zata gajenine.
Isha'q yagama karatunshi da sakamako mai kyau yadawo gida,alokacin aka tsaida maganar aurenshi da zahra dangi kowa yayi murna."
Tashare hawaye taci gaba,
"sai dai kash ana saura kwana uku bikinshi zahra tatashi da matsanancin ciwon mara cikin dare wanda yayi sanadiyyar d'aukewar numfashinta duk da kokarin ceton ranta damukayi Allah ya amshi abarshi.
Alokacin isha'q haukane kawai baiyiba saboda zautuwa saida yakwashe sati guda baisan inda kanshi yakeba,daga baya zama tamkar wanda yarasa memory nashi.dataimakon Allah da addu'u a isha'q yazama normal sai dai duk barkwancin isha'q yatafi yazama tsakaninshi damu gaisuwa kawai,yaci alwashin bazai taba aureba.har yakoma ga mahaliccin shi muddin baisamu kwatankwacin zahra ba,
Tad'ora dafad'in "babu tallar yammatan daba ayiwa isha'q ba amma yace ina.shifa angon xahra ne,tausayinshi yasaka naxura mashi idanuwa,har tsawon watanni shidda.
Dayake Allah gafurune kuma rahimu saiya maido mana abinda muka rasa tsawon lokaci muke kwana muke tashi da kukan rashinta."
Tadakata tana nazarin fuskokin dattijan biyu,
Sai dai cikinsu babu wanda yasan inda zancenta yadosa,hasalima anasu ganin wannan matsalace data dace tasanarma wad'anda suka santa bawai basuba.
Indai ba'itama tarasa nata hankalinba,su menene nasu illah iyaka suce Allah yajikan rai.
(anasu ganin ba.)
Abba yad'an numfasa yace"to dafarko muna maki ta'aziyya dakuma bakin cikin rasa y'a tamkar zahra.saimuce Allah yajikan rai,abu nabiyu daya tsayamun araina shine mudai bamusan menene ainahin dalilinki na za'barmu a matsayin wadanda zaki sanarma damuwarki ba.
Idan har kina son sanarda wani damuwarkine babu mafi cancanta kamar yan'uwanki da danginki bawai muba,da bamuda maganin dazamu iya baki domin warkewar damuwarku.
Ummata jinjina kai"wannan gaskiyane."
Murmushi doctor ru'kayya tayi tace"malam aikune maganin matsalata,nazone da 'kokon barata dakuma nan arziki akan ku taimakeni,kamar yanda Allah ya taimakeku idan baku za'bama d'iyarku zahra mijiba kubama d'ana isha'q aurenta."
Daga umma har abba had'a idanu sukayi,lokaci guda suka sakarma juna murmushi,abba yace"toga dai dukkan alamu acikin abu biyi dole asamu d'aya,imma dai makuwa kikayi kokuma kema bakida hankalin.idan bayaga haka yaushe zakice inbama d'anki auren zahra.? Tukunnama haka kawai siyaa bagatatan sai ind'auki y'a inbaki saikace banida hankali."
Dr. Rukayya taji zafin maganar abba,amma dayake ance mai nema baya fushi,saita sake numfasawa tace"kayi ha'kuri abban zahra nafahimci baka gane zancena ba sabo......"
Sauran maganar ta ma'kale a fatar bakinta lokacin da zahra ta kunno kai gidan, tana fad'in"Allah ya isa banyafe ba,muguwa azzaluma kinbugi wuta balbal har kabarinki na balbala da wuta,kuma wlh yaro ya'kara cemun zahra'u mala'ikar yara sainaci kutmar babbar saibitin babakeren buuuuu........."
Bata 'karasaba umma takaima bakin naushi,tace "to jarababbiya ko'ina saikin nuna halin naki."
Zahra cikin hawaye tace"to umma sai takamani tayita dukana wai don nabugi d'anta aishi yafara jana."
Umma ta zuba mata harara"gara dayajaki aike karyace ko.dakowa zaidinga tsokana,kinzama sakarya a layi kowanne datti badole a sauke a kankiba."
Zahra tace "wlh anjima sainayima gidansu ruwan duwatsu."
Umma tayi tsoki"aikin da kika iya kenan fitinanniya."
Dr.ru'kayya datayi mutuwar zaune,tasaki baki aranta tana tasbihi ga Allah wanda ya'kagi kamanni yakuma banbanta halayya."
Nima sai naga comments xan cigaba don naga kamar buk din beyi muku dadi ba

Kuna tare da maman meenat, Aisha t. Fulani Insha Allah
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀


By maman meenat

EDITED BY AISHA ABDULLAHI(UMMUN FAROUQ)

CHAPTER 7.


Umma taja tsoki takoma tazauna abinta,
Yayinda zahra ta cillar da jakar islamiyyar dakuma hijabi tafad'a band'aki.
Dr.ru'kayya tasauke numfashi tana kallon su umma kafin tace"wannan kuma 'kanuwar Zahran ce kokuwa.?
Umma ta kalleta da mamaki tace"a'a itace zahran ai."
Wani shegen gumine ya karyoma dr.ru'kayya lokaci guda tafara tsane zufa da handkerchief dake hannunta aranta tana addu'ar tafarka daga rud'adden mafarkin dayayi hajijiya da tunaninta dama kwakwalwarta.
Tad'an saita kanta kad'an kafin tad'ora dafad'in"to agaskiya dolene ku kalleni a matsayin wacce kanta ya zautu,kokuma 'batan kai inba hakaba babu mahaluki mai hankalin dazai dubi karancin shekaru irinna zahra a gari ba 'kauyeba yace ayimata zancen aure."
Tad'an tsagaita tana sauke numfashi kafin tad'ora dafad'in."adukkan zatona dakuma tunanina nayi zaton zahran babbar budurwa ce,amma don kamanni da tawa zahran tabbas suna kamanni nagasken gaske,sai dai kash wannan zahran tayi kankantar dabe kamata ace anyimata aure yanzuba."
Sai lokacin su abba suka fahimci inda tasa gaba,
Abba yami'ke yana cewa"inace dai yaron dakeson zahran shine awaje tsaye ko.?"
Doctor ru'kayya ta'amsa dacewar"shine malam",
Abba yafita kofar gidan,isha'q har lokacin yakafe kofar gidannasu zahra da manyan idanunshi yanason ganin ta'inda kyakyawar fuskar zahra mai kama data black Americans zata 'bullo,sai dai sa'banin zahra saiyaga abba yafito yana sa'ba babbar riga.
Isha'q yayi saurin du'kawa yana gaida abba,
Abba ya'amsa kanshi tsaye yace"kaine isiyaku."?
Isha'q yawaro idanuwansa masu kwarjini da haiba,yace"abba isha'q nake."
Abba yace "afto ai duka dai d'ayane,to inason magana dakai ga mahaifiyarka can cikin gida don haka kashigo ayita a gabanka ta 'kare."
Gaban isha'q yabuga da 'karfi,idanunshi tuni sun canja launi daga farare zuwa green tsigar jikinshi tabada yarrrr,aranshi yana addu'ar kada Allah yasaka yasake rasa zahra akaro na biyu bayan tadawo gareshi.
Kai yama rantse komai rintsi bazaifa rabu da sanyin idaniyarshi ba,aidukkan mai imanin dayasan tarayyarshi da zahra abaya bazaiga laifinshi don lokaci guda ya mayincema little zahra ba.
Abune mafi tsanani agareshi yakice soyayyar da'aka dasa tun zamanin 'kuruciya yanason zahra yana 'kaunarta yanamata *so d'aya tak*son daya rantse babu mi'ki ko algussu acikinshi.
Jikinshi babu 'karfi yabi bayan abba wanda tuni yakai zaure,
Inbayanga addu'ar samun nasara babu abinda isha'q yakeyi acikin zuciyarshi.
Da sallama ya kunna kai cikin gidan,lokacin yayi dai-dai da fitowar zahra daga band'aki,
Idanunta suka sar'ke dana juna lokaci guda duk rashin kunya da fitsarar zahra taji isha'q yamata wani kwarjini wanda ita atata haukar jitayi ya burgeta don zahra akwaita dason y'an gayu,uwa uba tanadason kwalliya duk da cewarta ita ba'kace amma saitafi su anty hafsa zama y'ar gaye.
Tasauke idanunta cikin na isha'q wanda yamace atsaye yana kallon baiwar gashin dake kan zahra,yatunano tashi zahran batada irin wannan gashin,
Ya runtse idanuwa,yana tasbihi ga Allah wanda ya'kagi kamanni tsakanin zahra dakuma little zahra.
Itama dr.ru'kayya mamakin irin gashin zahra takeyi,lokaci guda taji yarinyar tazaunan daram acikin zuciyarta tabbas soyayyar datake yima marigayiya zahra ce zata koma akan wannan zahran,
Kai itama tana ganin kobada aureba yakamata zahra tazama wani 'bangare daga jikinta,she luv xahra moree.
Isha'q yatako kamar wanda kwai ya fashemawa aciki yazauna kusa da mahaifiyarshi yana gaida umma wadda takafe kyakyawan saurayin da idanu tana dad'a tasbihi ga Allah daya tsara halitta mai tattare da baiwar natsuwa irinta isha'q.
Zahra kam bata saurare suba taja jakarta da hijab tajefa d'aki,
Tadawo kitchen tana neman abincinta hankalinta kwance dukkuwa da sarai tagane isha'q,shine mayen kallonta d'innan idanunshi basamata kyan kallo,saitaji gabanta yana fad'uwa idan tana kallonshi.
Dr, ru'kayya ta kalleta a tausashe tace"zonan d'iyata zahra,
Kamar baki,saiga zahra tataka sif-sif zataje inda dr.rukayya take,
Idanunta suka sar'ke dana isha'q akaro na biyu,
Ta murgud'a mashi baki had'i da jefa mashi harara.
Yasakar mata murmushi,
Abinda ya 'kufulata yasaka tacije baki had'i da girgiza kai.
Saida taje kamar zata wuceshi taje wajen doctor ru'kayya tasaka 'kafarta ta take hannun isha'q wanda yadafa 'kasa dashi.
Yajanye hannun da sauri,yana yarfawa.
Ta kwashe da dariya lokacin data ra'ba jikinta dana dr.ru'kayya tace"yaro kaci gaba da kallona kamanta ranar dana 'kala maka sheri sojoji suka kamaka ko.?"
Tafad'a tana cije le'be da fiddo sexy eyes dinta waje.
Isha'q ya girgiza mata kai alamar kada ta fad'a,
Amma saicewa tayi"tomiye kuma naga kanata girgiza kai,hhhh katuna marin da wannan mai 'katon cikin yayi maka ne.?"
Abba ya daka mata tsawa yace "rufe mana baki,waya tambayeki."
Umma ai kunya bata barta zama wajenba,saita tsiri fura wutar dole.
Dr. Ru'kayya tayi tsam tanason tunano ranar da isha'q yadawo yacemata bashida lafiya dataga fuskarshi da kumburi ta tambayeshi yace mata yafad'ine wajen training.
Ta girgiza kai kawai.
Abba yafara magana"to masha allah isha'q kaine ka aiko mahaifiyarka akan kanason inbaka auren zahra."?
Isha'q ya gyad'a kai kanshi yana 'kasa yana wasa da yatsun hannunshi.
Abba yasaki murmushi nasu na manya yace"to isha'q bazan 'boyemaka ba,bakuma don kunada arzi'ki yasaka zan fad'i ra'ayina akanka ba,wlh kallo d'aya namaka naji nasamu natsuwa dakai.sannan akwai alamar kwarjini da wata baiwa da Allah yamaka wadda dukkan mahalukin daya mallaki hankalin kanshi ya kalleka zaigane kai kamilin mutim ne,"
"Hakane"?
Yajuya yana tambayar umma,wadda ta tsugunna bakin adarkin kitchen,
Umma tace"hakane malam".
Dr. Ru'kayya sai murmushi take anyaba mata d'an lelenta.
Abba yad'orabdafad'in"kaikuwa wacce 'jarabta ce takaika za'kulo zahra amatsayin matar dakakeson aure,nafarko zahra dai yarinya ce 'karama nabiyu zahra bawani kwayon da zaya rud'i mutum gareta ba,illa tulin sumar kai wadda harmun gaji da askewa mun barta taji da abarta.sannan bazan 'boyemaku gaskiya ba,zahra batada kunya ka ganta nan,"
Ya nunata da yatsanshi,
Takuwa zumbure baki tana 'kunkuni.
Dr. Rukayya tace"a'ah zahra d'iyata meyasa kike hakane,abban kikema gunaguni."
Zahra tace"nifa badashi nake ba,"
Umma ta 'amshe to anan ciki waye tsarar wasanki dawa kike"
Ta nuna isha'q da yatsa,tana sake turo baki"bashine yaketa kallonaba,kuma wai har yana runtse idonshi d'aya,(kashe ido)
Kunya kamar ta kashe isha'q haka yaji.
Dr.ru'kayya maka mashi mafecin dake hannunta tayi dacewa"tashi maza kabar nan,mara ta idanu kawai."
Yakoyi 'kememe abinshi baiko motsaba.
Abba yad'ora dafad'in"to agaskiyar zance nikam bantashi yima zahra aureba,donkuwa dukkanin yayunta babu wacce na aurar batare da ta samu sakamakon takardar n.c.e ba,don haka idan nace zanyima zahra aure awannan lokacin na zalunceta nakuma shiga hakkinta duk da bawai musuluncine ya hana aurar da yarinya tana shekaru sha biyu ba,hasalima shekara tara musulunci ya yarda ka aurar da yarinyarka,amma yanzu zamani ya canja akwai cutuka da dama da ada bamudasu sai yanzu,sannan zahra bawai wayone ya iaheta ba,bayaga rashin ha'kurinta tanada mugun surutu dakuma su'butar baki.
Amma nayi maka al'kawarin muddin zahra ta girma tace tana sonka zan aura maka ita,wannan shine kawai maganata."
Dr. Rukayya ta kalli isha'q wanda idanunshi suka kad'a sulayi jajur,
Tace "tokaji da kunnuwanka abinda abba yace,saikayi hakurin zahra ta girma kusan shelaru goma nan gaba 'kila."
Hawayen dayake 'kokarin ri'kewa tuni sun 'balle,babu kunya ya ri'ke kafafun abba yana ro'konshi"abba don girman Allah kada ka nisantani da zahra abba,ka tausayamun soyayyata da zahra *had'in Allah*ne,bana nufin cutar da rayuwarta har abada pls abba."
Duk da taurin zuciyar abba saida yaji tausayin isha'q amma kuma donme ze tauye rayuwar zahra.
Umma jitayi bazata iya kallon hawayen isha'q ba,saita shige d'aki abinta.dama ita nata biyayya duk abinda abba yatsara awajenta yagama tsaruwa.
Dr.ru'kayya ta kalli isha'q daya kasa dena fitar da hawaye tace"kajiramu awaje inazuwa."
Yatashi ya fita,yana sake waigen zahra wadda dukkan jikinta yayi sanyi 'kalau tana kallon isha'q badai tagane akan me suke tattaunawa ba.
Dr. Rukayya tasake rusunama abba tace"nagode da kyautar dakayima d'ana amma na ro'keka daka taimaki rayuwarshi,don Allah kada kayi fancakali da lafiyar damuke tarairaya tashi,natabbata isha'q zai rike zahra amana,
Wlh namaka rantsuwa babu wani abu na ga me da auratayya dazai shiga tsakanin isha'q da zahra harsai takai munzalin hakan,
Sannan karatu konan da inane zan tsayama zahra tayishi,inada yarinya bazata shige tsarar zahranba atare zan renesu don dukansu y'ay'a nane."
Ta tsagaita tanason jin amsar da abba zai bata.
Nima natafi break
September 26, 2016 at 10:43pm · Public
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀

BY MAMAN MEENAT


EDITED BY AISHA ABDULLAHI (UMMUN FAROUQ)


Chapter 8.


Tad'anyi jim tanason jin amsar da abba zai Bataan .

Abba yasake gyaran murya gami da tofar da wayu gefe,yana sakace ha'kori da asuwaki yace"nifa hajiya kindai gaza fahimtata ne,amma tayaya zan baku auren yarinya haka kawai nifa bansanku ba,nadai ganku ne kawai gaskiya abune mai wahalar gaske hakan."

Dr. Ru'kayya taja numfashi"malam mu bawasu 'boyayyu bane a garinnan,mijina sunanshi alhaji saifullahi mai rid'i yana sana'ar kai rid'i turkey yanada shagon gold anan abubakar gumi."

Abba ya kafeta da idanuwa kafin yasaki dariya dace"Allahu akbar azzawa jallah gwanin hikima,dama ku iyalan alh saifullahine,mutuminane kai mutum na gari.bazan ta'ba manta alkairinshi gareni ba."

Yanuna umma data le'ko daga d'aki tana murmushi yace"gata kinganta nan haihuwarta ta farko kamar bazatayi ba,banida sisi a aljihuna banida kadarar sayarwa aka tsawwala mana kudin yimata tiyata dubu tamanin nad'aga gidan danake ciki zan sayar bawan Allah yaganni a asibiti ina kuka yake tambayar meya faru,na sanar mashi wlh hajiya atake ya shiga ofis din likita yarubuta mashi kudin a takaddar banki,yace ayi gaugawar ceto rayuwar saudatu.kuma yace nabishi ofis dinshi,bayan yabani takarda ta address naje shine yabani dubu d'ari nafara sarin bulawus ina kaiwa kasuwa da wannan sana'ar Allah ya d'aukakeni gashi ina cikin rufin asiri har yanzu."

Dr. Ru'kayya tasaki
 lallausan murmushi tasan mijinta yafi dahaka kaf halinshi isha'q ya d'auko.

Abba yadinga mamaki itama umma saida tasake yima Dr Rukayya godiya,
Abba ya 'kwalama zahra kira yace maza kice 'bakonnan na waje yazo yanzu yashigo ciki.

Tafita kai bako d'an kwali tahangoshi yajingina bayanshi a mota yayi lamo Allah kadai yasan abinda yake tunawa.

Ta dage iyakar 'karfinta tace"kai mai motar nan,kai mayen kallon mutane kazo ana kira."

Isha'q yaji gabanshi yasake bugawa yace "ina zuwa,tajuya zata shige gida,
Yace"jirani mana."
Tawaigo tana 'kare mashi kallo saikuma tabuga zani da murgud'a d'uwawu"sumbuqa sagwaigwai takashin mage da barima hada sarqa a gabanta",
Isha'q yadafe kai "oh Allah zahra kam anya tanada cikakkiyar lafiya kuwa?"
Ita komai nata sai tasaka wauta da shirme.
Ya ta'be baki dacewa "aini nace naji nagani."
Yashigo da sallama yasamu waje ya zauna,
Abba yasaki murmushi dacewa"taso kadawo kusa dani d'ana isha'q. "
Isha'q yakoma jikin abba yana du'kar dakai.

Abba yace"isha'q kadaiga wacece zahra,amma ahakan kace kaji kuma ka gani ko.?"
Isha'q yace "hakane abba agaba duka wannan zata dena aikowa da tashi 'kuruciyar."
Abba ya gyad'a kai yace"kuzama sheda ni malam adamu jafar nabama isha'q saifullahi auren d'iyata zahra ko bayan babu raina."
Wata zabura isha'q yayi dacewar "Allah abba gaskene kabani zahra,bakuma mafarkin dana saba yi bane.?"
Abba yace"ba mafarki kakeyiba isha'q idan mahaifinka yadawo daga tafiyar dayayi za'a tsaida lokacin biki,kafinnan zakaji sharad'ina daga bakin mahaifiyarka."
Dr. Ru'kayya baki har kunne take zuba godiya gasu abba da umma.
Takamo zahra wacce takoma gefe tana y'ar 'kwado tace"zo d'iyata zahra kina sona,zaki zauna wajena?".
Zahra tayi jimm kafin tace"indai kinsan gidanku akwai bene tozan zauna indinga shan dad'in bene."
Dr. Ru'kayya tasaki dariya dacewa "kema d'akinko akan bene yake ma."
Zahra dad'i yac tace"indai da gaske kike tokice kwarakwatsi",
Umma tace "au zaki fara shirmen naki kenan,"
Dr. Ru'kayya dari take sosai dacewar "zahra koban rantseba bazan maki 'karya ai."
Tazuge jakarta tafiddo rafar y'an hamsin-hamsin tami'kama zahra"karbi kisaya sweet kinji d'iyata zahra,aibanzata 'karama bace dana siyo maki ice-cream."
Zahra ta kalli kud'in gami da zaro idanu tace"nidai banaso,ki'aje kud'inki bene kawai nakeso kihau dani,indingayin sululu."
Mamaki yacika dr.ru'kayya aranta tana riyawa ashe duk wautar zahra tanada tarbiyya?
Lallai zasuji dad'in zama da'ita lokacin da 'kuruciya ta barta.
Babu yanda batayi da zahraba,amma 'kememe ta'ki karbar kud'in dole ta mayar a jaka.
Tanamasu umma godiya dacewar zata aikoma zahra da sweet tunda ta'ki karbar kudin.
Har zaure umma tarakata itakuwa tari'ke hannun zahra tace taje taraka mota.
Sunfito bakin lungun isha'q yana bud'e mota,idanun zahra yasauka akan jabiru wanda jiya ya 'kalamata sheri wai taje kwad'ai gidansu ummilolo,
Bata tsaya tabi takan dr.ru'kayya ba,tafincike taruga da gudu tayi wajen jabiru wanda ya d'auko ni'kan gari akai.
Tana zuwa ta hankad'ashi garin ya zube a kwata,sannan ta cukumi rigar jabiru tafara 'kuli-'kulin kubura dashi Dr.ru'kayya tana daga nesa ta hango yara harsun fara zagayesu suna wa'kar"bamu rabawa sai dai mu'kara zigawa bugi cikin."
Subhanallah cewar dr.rukayya wadda tuni tanufi inda zahra take dambacewa,
Dasauri tarike hannu zahra wadda take yayyafa ruwan bala'i,
Jin anri'ke hannunta yasaka batare data waigo ba tace "wlh kowaye yasakeni inba hakaba najuyo saina yima mutum wanka da ruwan kwatar nan,
Dr. Ru'kayya tace"oh oh zahra haka kike ashe.
Zahra tawaigo suka had'a idanu da Dr Rukayya,
Tace"shinefa jiya wai yace naje gidansu ummilolo naci garin kwaki,alhalin karya yakeyi ni aigidanmu anmafi cin dad'i abbanmu kullum da dare yanama siyomana kifi itakuma umma saitayi wanka taje can d'akin abban mu har....."
Dr. Ru'kayya tace "ya'isa zahra nasan kunacin dad'i ai,amma kiyi hakuri bakiga kin sakashi kukaba."?
Tace"aima wlh danban shillirashi nayi mashi fad'an y'an chanis ba,dasaikinga nafasa mashi baki.
Rannan ma damukayi fad'a da hinde saida nakusa 'kwa'kulo mata kunne,itakuma irin fad'an sharuhkan nayi mata."
Dr. Ru'kayya ta jinjina kai tana kallon isha'q wanda yayi tsuru,baiso mummy tagane halin zahra yanzu ba.
Yasanta dasakama ranta damuwa dayawa,
Tajuya ga zahra dake cema yaron"yaro zan kamaka,zamuje lungun bata kashi saina gurje maka baki da kashin kaji ha'koranka sun zube,banza latas karas kabeji masu kwana abakin titi d'an kabewa mai..."enough pls."
Dr. Ru'kayya tafad'a ranta a'bace"kewai waccce irin yarinyace,ahaka kikeson inje dake gidan bene kina dakarmun d'iyan ma'kota.tonikam ba'a haka dani,idan bazaki sake haliba lallai zan 'bata dake sam banason masifa kin ganni nan."
Zahra tayi tsit,sannan tace"nadena ai."
Dr. Ru'kayya tayi murmushi dacewa "gud girl"
Tashafi gashin kanta,
Tayima yara y'an kallo tsawa kowa ya kama gabanshi.
Itama mota tashige tana d'agama zahra hannu,lokacin gaf da magrib.
Motarsu na 'bacewa zahra ta hango su ummilolo da sauran 'kawayenta,taje suka kashe "tace yara albishirinku?"
Duka suka kasa kunne dacewa"goro fari 'kal"
Tarage murya sosai"amanatun amana wa'azabatun azaba,idan kuka tona taciku,kun yarda?"
Duk sukayi tsuru,
Tace "inbaku yardaba shikenan."
Sukace "munyarda zahra,"
Zahra ta tafa hannaye dacewa"yara kuka gayama wani saina dirji baki ehe."
"amanatun lauratun 'kwan kiyashi,yara ankusa yimun aure.
Duk suka zaro idanu waje suna kallonta sun sandai 'karya ba halin zahra bace,don sam tsage gaskiya take komai d'acinta.
Ummilolo tayi karfin halin cewa"mai 'karya"
Zahra ta'amsa da "d'an wuta abishi da duka har wuta lantarkin babalo da an kyasta sai wuta."
Duk suka ce"yeeeee dagaskene.
Nanfa aka zauna ana labarin aure,ummilolo tace "tab ashe zahra ke zaki dinga dafa abinci kiyita ci dayawa cikinko yayi 'kullumeme saimuga zahra ta haihu."
Sauran yara suka kwashe da dariya,
Zahra ido ya raina fata tace"ai sai in'ki cin abincin,inyita shan ruwa kawai."
Uwande tad'an fisu wayewa tace"kai wlh ance bacin abinci kesa mutum ya haihu ba."
Duk suka zaro idanu sukace "to menene"?
Tace inkun yarda amana,
Sukace sun yarda.
Tace"wlh yara idan kuka yarda namiji ya ri'ke maku hannu ya luliya tafin hannunku saikuga ciki yafito 'katoto,"
Zahra data gama tsorata tace"lalalala aikuwa Allah yasoni ban wasa da maza."
Daga nan aka rufe cafta,akace atafi satar kifi,wajen y'an kifi.
Haka kuwa akayi xahrace gaba sungama tsara plane na yanda zasu saci kifi,
Suna zuwa saitin wani mai kifi yakasa a faranti yana tsaye gaban kifinshi,
Zahra nazuwa wajen saitin kifin ta yanke jiki tafad'a akan farantin kifi,
Sauran yaran duk sukayi fuskar tausayi"wayyo zahra sannu,"
Mai kifi ma fad'i yake subhanallahi sannu yarinya.
Zahra ta bala riga akan kifi ta dumbuji uku,
Sannan tari'ke ciki"wayyo cikina ummilolo zoki tadani.
Ummilolo itace mai hijabi,dan haka tana zuwa zahra ta 'kunsa mata kifin a hannu,
Tasaka ariga,
Suka mi'ke suna kakka'be jiki zahra na d'angyashi.
Kamar ance maikifi ya kalli kashin kifinshi yaga anyimashi rani,
Yabisu aguje yana 'kwala masu kira,
Sukuwa 'kafa menaci ban bakiba,
Tuni sun sata.
Maikifi saida yayi Allah ya'isa saboda balagaggun kifayen suka d'auke,gashi ranar ba ciniki.
Awani lungu suka ma'kale zahra ta'amshe kifin ta finfincinar masu,tana la'kume sauran.
Uwande ta kalli d'an nata,taga na ummilolo yaninka nata biyu,tace"gaskiya anyi son kai,na ummilolo dayawa namu kad'an".
Zahra takaima bakin duka tana harararta"sannu mara gode Allah,da kud'in babanku aka saya kifinne,"?
Uwande tayi gum tana mamular kifin da aka bata kai da bindi.
Nan sukayi gaba,
Dai-dai kwalbatin y'an ganda suka hango wata budurwa da saurayi ana tafe ana rangaji suna gogar kafad'un juna,
Ummilolo ce tafara gani ta lakaci zahra,duk suka ware idanuwa suna mamaki.
Zahra tace"aje ajanye gyalen tsinanniya,"
Nanfa kowa tacire takalmi suka ma'kala a jijiyar hannayensu,suka d'age zani sama.
Saida budurwanan tazo saitin majalisar masu ganda,zahra tayi wuf ta fizge gyalen dake kafad'ar budurwar,
Suka auna aguje,budurwar tarasa yazatayi,ta waiga dacewa"honey dallah kabisu ka'amso man gyalena,kaga kayan jikin rabin 'kirjina duk awaje yake."
Saurayin yace"tabd'i,sarai nagane yarannan masu gudu kamar barewa,nida rannan gaban idanuwana suka janyema wata budurwa zani,yaseen da rarrafe tashige gida,camon ki kare wajen kawai mutafi asfa gayu d'innan kingane ai "
Ran budurwar ya 'baci kawai saita tsugunna ta fashe da kuka,
Me mutane zasuyi banda dariya da ihu...
*Nima nadara,nabi bayan zahra balbali zahra bala'i ta'ba d'aya kaga goma*

KUNA TARE DA MAMAN MEENAT, INSHA ALLAH
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀

BY MAMAN MEENAT

EDITED :AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN FAROUQ, HYDR)

Muna miqa saqon ta' axiyan Hamma umar Allah ya jiqan shi yayi mishi rahma yasa mutuwa ta xama hutu a garesh, muma in tamu taxo Allah kasa muyi mutuwar shahada)




Chapter9.


Daga wajen tonon fad'a su zahra basic zame ko'inaba sai gida,saboda lokacin tuni angama sallar magirb,
Da sand'a tale'ka cikin gidan tace "inshigo'"
Umma dake ninke kayan da abba yacire dazu ta harareta dacewar "dawwama anan,har mahadi ya bayya,"
zahra taahigo kanta tsaye,tad'auki buta tafara alwalar magrib umma bata tankataba.
****************
Hadadd'en saurayin dake sanye cikin 'kananun kayan riga shirt dakuma wandon jeans kirar kamfanin Gucci,akwai kwatsetsen takalmin kafarshi mai shegiyar tsada gordon rush,
Face dinshi manne da space na Prada,watch na hannunshi dolce jikinshi manne da mayen turaren American crew.
Sumar kannan nashi ka rantse na macene saboda gyara da kula kai infarct isha'q 'karshene akan tafin hannayenshi kawai yakan kashen kud'i masu yawa,ha'koranshi kuwa akoda yaushe suna walwali da daukar idanu saboda time daya ware musamman domin su yakan je wajen wankin hakora lokaci zuwa lokaci.
Hatta da tafin kafar isha'q baya barinta face ya tsaftaceta da mayukan dake tsaftace 'kafa dasakata taushi.
Yanda yake wana steering kadai abin kallone,duk inda ya gifta mutane kan bishi da idanu musamman motar dayake tu'kawa new modern ce kirar mazda mx-miat abin saiya bada wani styles na daban.
Adai-dai kofar gidan sadiq ya matsa horn mai. gadin yale'ko dakai lokaci guda ya wangale get din yanama isha'q barka da zuwa,
Yafaka mota inda aka tanada don hakan,lokaci guda yazaro wallet d'in dake manne abayan aljihun jeans dinshi,yafiddo 2thousand yamikawa mai gadin,baijira sauraren godiyar damai gadin keyiba yayi gaba abinshi yana wana keys na motarshi.
Dai dai shiga harabar gidan yahad'u da hindu matar sadi'q da tsohon cikinta tana ganinshi tasaki murmushi"yau makuwa kayine isha'q yau agidan,"
Yasaki simple smile nashi kafin yace"yakike ya jiki kuma."
Tayi gaba tashige falo tana fad'in"banacin mi'ke,"
Bayanta yabi ya nitse cikin manyan kujerun dasuka zagaye falon yadauki remote yana canja channel daga Bollywood zuwa dstv yana searching 'kwallo,
Hindu tuni tacika gabanshi da kayan sanyi tasani yafi shan hollandia ko malt sune best drinks nashi.
Ya fincine hancin malt na gongoni yana zubawa a glass cup yana tambayar"ina mutumina ne."?
"yana jinka yanzu zaka ganshi yafito wankane yana shiryawa."
Isha'q yad'an dara,dacewa kice nazo asa'a dama tad'i zai rakani."
Idanu hindu ta fiddo waje"to gaskiya bari yafita ba,haka kawai wata budurwar ta kwaceman shi."
Tafad'a tana turo baki da alamar fushi.
Isha'q dariya sosai yakeyi yanacewa"aigara kishirya don mutumina hudu zaiyi,"
Maganar sadiq ta katseshi"a'a banganeba,wato kai ka'ki aure shine zakazo ka 'killen dannawa auren ko,"
Yafad'a yana dariya lokaci guda yana zaunawa kan hannun kujerar da isha'q yake kai.
Yami'kama isha'q hannu suka tafa duk suna dariya
Isha'q yace albishir fa nazo inyi maka,
Duk suka bishi da idanu sunason jin abinda zai fada masu,
Yasake kora maltina yana kallon sadiq wanda ya tsareshi da idanu,
"anbani zahra abokina,daga yau nakoma angon zahra "
Wata zabura hindu tayi"nice to hear isha'q seriously pls dagaske kasamu zahra?"
Isha'q ya saki dariya lokacin da sadiq yakai mashi duka yana fad'in abokina bakada mutunci wlh,wato saida ka rikita masu yarinya da salon wankanka ko?"
Amma duka sati biyu da had'uwa ace har anbaka saikace kaza,koda yake nasanka gwanin iya sarrafa soyayya but natayaka murna sosai abokina aikawai daga wannan wankan muwuce inga amaryar nan."
Hinduma fad'i take "nayi murna isha'q kaga nasamu 'kawa,"
Isha'q ya sauke numfashi.
Headache wlh typin din bayamun dad'i kuyi hakuri pls,
Tun d'azu nakeson typing amma kaina yana matsamun dafatan zaku gafarceni.

Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha Allah
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀

BY MAMAN MEENAT


EDITED:AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR, FAROUQ)


Wannan shafin naku ne masoyan mijin kwaila, sai daku xamuji dadin cigaba da rubutawa in baku bamu hadin kai rubutun baxamu ji dadin yiba. Maman meenat nayi muku fatan alkhairi, t. Fulani ma baa barta abaya ba��


Chapter 10.



Isha'q yad'an murmusa yana shafar sumar kanshi,
Sadiq yace "Allah am serious abokina,yakamata inga wannan zahran tauraruwar mata.
Isha'q dake mi'kewa tsaye yana tafiya abinshi yana bashi amsar"zaka ganta very soon but not today,"
Hindatu tasakeyin dariya"isha'q bani phone number nata my be mu saba kafin tazo gida,idan dai tanada son jama'a."
Gaba yayi abinshi yana bata amsar"kidaice zaki koyamata gulma da kitififi kawa,"
Duk sukayi waje da sadi'q suna mata dariya.
Ajikin motar isha'q suka tsaya,sadi'q yana tambayar"abokina kamata yayi ashirya komai harkar girma kasan y'ammatannan yanzu suncika saka bidi'a a al'amarin aurensu."
"Banda zahra itakam batada wannan halin,"
Cewar isha'q wanda yabude motar yana kokarin tayarwa,
Sadi'q yabishi da kallon mamaki sam isha'q yawani canja kamar bashi ba,yatuna lokacin wancen auren yanda yaketa rawar jiki kusan koda yause maganar kenan yakeyi,koda yake watakila hakan nada alaka da rasa zahra dayayi akaro na farko yana tsoron rasa wannan zahran akaro na biyu.
Da sallama yashiga falon mummy tana zaune da hisnul muslim a hannunta,ta ajiye littafin bayan ta tsura mashi idanu fuskarta babu walwala,
Kusa da ita yazauna,lokaci guda yana matsa kafafunta"barka da yammaci mummy yau kindawo aaibiti da wuri hope lafiya dai".
Yatambaya dukkan hankalinshi gareta.
Tayi kokarin kauda damuwar dake kan fuskarta dacewa"banmaje asibitin ba yau banajin dadin jikina,nayi handling komai wa dr.aysha nasan zataji da komai "
Isha'q ya gyad'a kai yana kallon zalla damuwar dake fuskarta,
Yajuya ga hanan wacce take buga game hankalinta kwance yace"jeki d'akinki kiyi wasanki inason kadaicewa da mum".
Tamike abinta duka kanta yanaga game,
Yasake duban dr.rukayya akaro nabiyu yace"mum akwai zalla damuwa akan ni'imtacciyar fuskarki mai kwarjini pls mum sanar dani matsalarki i will save it insha Allah."
Kai ta girgiza mashi''banida wata damuwa isha'q kawai ina nazarin yanda zakaji dad'in rayuwar aure da yarinyar da kwata-kwata batasan me kalmar aure take nufiba,ina tunanin yanda zakaci gaba da rayuwar tazuranci alhalin kanada mata,ina nazarin yanda zaka zama *mijin kwaila*kuma mijin dazaiyi zaino,ina hango maka matsalar kada zahra tagirma ta gujeka bayan ta fahimta who you are.isha'q inajiye maka ka rainar ma wani mata".Kalamanta sun d'aga hankalin isha'q wanda idanunshi suka kad'a jajawur yana kallonta cikin idanu yawani koma kalar tausayi,musamman idan katuna duk soyayyar dayakema zahra saboda wata zahrance ba wannan fake zahran ba,
Ya sauke numfashi murya a raunane yace"pls mum don't say that,bana tunanin zahra zata gujeni bana fatan insake rasa zahra bayan tadawo gareni,kamata yayi kiyi courage d'ina akan zahra but kema nasan u feel loved her,nasani zahra tayi kankanta amma wata rana zata girma mum. Bajikin zahrane yake 'kayatar daniba da Zahra ko babu zahra zan iya kame kaina bazanyi abinda nasan addinina da al'adata bazasu soba."
Dr. Ru'kayya ta danyi dumm kafin tami'ke tadawo da littafin addu'o i tace"kaje kayi isthakara isha'q,nakuma saka malam babba yatayamu da rokon Allah akan zabin damuke so.amma nikaina inajin son zahra har cikin zuciyata sai dai halinta nake gudu wanda kowa yake kuka dashi"
Isha'q dake duba littafin yace"komai mai wucewane mum,kada ki kalli wannan ki hango alkairan dake tare da ita ba sharrintaba."
Mum tace hakane Allah yayimaka albarka,
Ameen yace gami da mi'kewa yahaye upstairs abinshi.
***************
Lala..la.la..lah.. ubanka ta tsinke mata azo asai nama sauran 'kashi da y'ar tsoka....muryar zahra data karad'e kaffatanin unguwar ce ke rera wa'kar zagi bayan d'an sabo ya kwasheta da mari,lokacin data jima 'kaninshi wankan gawayi.
Abinda yafaru kuwa shine hamid 'kanin d'an sabo,dayake gidansu dukansu fararene,shine yake tsokanar zahra dacemata wankan baqi asarar ruwa ko yayima kamar baiyiba,zahra dai tasan ko giyar wake tasha hamid yafi 'karfinta don garjejene zahra tarasa hanyar dazatabi tayi ramuwar gayya,hakan yasakata kama 'kanin su d'ansabo mesuna dady taje dashi gidan anty bilki wata makwafciyarsu datake shiri da zahra kamar me,don ita zahra dariya ma take bata.
To shinefa anty bilki tana bacci batasan shigar zahraba,tasamu gawayin da anty bilki take girki dashi tadaka a turmi lu'kwui ta yima dady wanka dashi tas duka jikinshi,bayan anmashi wanka da fararen kaya,
Yaron yafito waje yana kuka karantse aljanine.
Koda d'an sabo ya tambayi ba'asi yaro yace zahra ce,
Hargida d'an sabo yaje yakai kashedi wa umma,umma takama zahra tayimata dukan tsiya.
Dalilin dayasaka tatara duwatsu sunkai cikin fanteka ta tattaro basawanta wato su ummilolo suka dinga yima gidan ruwan duwatsu,zahra itake bada common datace "ajefaa"zakaji duwatsu nasauka bisa kwano kamar aradu.
Ashe d'an sabo yana bayansu shine ya lalla'bo ya cafke zahra ogar tasu,sauram suna ganin haka suka ranta ana kare,sukabar zahra wadda d'an sabo yake kwashewa da lafiyayyun mari har biyu.
Agabanshi tadinga ro'konshi yayi ha'kuri bazata 'karaba,mutane suna bashi hakuri yana sake d'uramata ruwan ashariya.
Aiko yana sakinta tafara antaya mashi style d'in zagi sunfi kala d"ari tun yana girgiza kai saida takai yakasa jurewa,babu irin kiran da umma batayima zahraba amma inaa zaginta dayafi bama d'an sabo haushi shine da'akace bananar
babanshi ta tsinke mata suzo susai nama .
Sai da hawaye suka zubo mashi,musamman dayaga abokananshi sunata kwasar dariya hada masu ri'ke ciki.
'kwafa yayi duk randa yakama zahra kashetane kawai bazaiyiba. .
Zahrama tahad'a mashi plane cewarta aitasan gidan budurwarshi saitaje ta kunyatashi...

Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha Allah
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN KWAILA*����‍♀




by maman meenat

editing (maman faruq)

Chapter 11.




Saida ta tabbatar d'an sabo yashige gida sannan tayi 'kwafa dafadin"yaro tunda kataboni kata'bo bala'i kuma marin dakayimun ban yafeba har kabarinka na balbala da wuta."
Tajuyo danufin tafiya d'aga d'aya tahango motar anty lubnah tana fakawa da gudu tabi motar tana ihun"ga antin mu ga antinmu,anty lubnah tafaka mota tafito sa'be da ammar da yusra dake tafiya zahra tana zuwa tacafe anwar tana juyashi sama sosai,anty lubnah tace"a'a bani abina kada ki kayar mun dashi,zahra ta batashi bayan ta dungure kan yusra data tsaya tana kallonta dacewa"miye kike kallo dawani 'kwalakwalan idanu kamar na mage",
Yusra tasaka kuka anty lubnah ta harareta "zaki fara ko,jarababbiya uban me ta maki"?
Zahra bata tankaba ta aunkuce jakar anty lubnah tana tsalle"Allah yasaka kinzomun da alewar kano mai dad'innan."
Anty lubnah datayi gaba tana cewa"ahakan zanbaki alewa kina makarmun yara,"
Suka shiga gidan da sallama,umma tagama jefa dan wake tamike"lale marhaba da ba'kin kano."
Anty lubnah tashige kafad'ar umma dafadin"nayi kewarki mamana,
Umma sai murmushi takeyi y'ar farice shiyasa bata cika janta ajiki ba.
Ta amshi ammar tana mashi wasa, yayinda anty lubnah tashige daki tafara bude kwanoni"ummanmu mekika ajiyemun",
Umma tace"oh oh nida bansan da zuwanki ba, ai babanki kadai kika sanarwa shima baidade dakirana awaya ba yake sanarmun."
Dariya antyn tayi"kedai kawai umma donba hafsa ko mirja bane aida kinyi masu dambun nama",
Umma tace"ah to kema basai babanki yasayo makiba."
Anty lubnah dake rage kayan jikinta don zafi tace"ai umma naki nakeso ina missing girkinki mai rikitan tunani,gaskiya umma keta daban ce".
Umma tayi dariya "kyaji dashi ai."
Zahra kam tuni atsakar gida tagama yakicema jakar anty lubnah albarka wai tana neman alewar kano,
Umma taganta tana kiciniyar bud'e zif din baya tace "mezakiyi?"
[9/30, 1:50 PM] mum meenat: Bata dena 'kokarin bud'e jakar ba take bama umma amsa "alewar kano zan dauko,ai tace zata zo man dashi,"
Umma tace "shikenan kuma don tace zata zo maki dashi saiki kama binciken mata sirrin jaka wacce irin yarinya ce kene zahra.meke yawo cikin kanki haka wai",
Zahra ta turo baki gaba saiga hawaye,umma tayi tsaki"kyaji dashi shagwa'babbiyar banza magana ba magana ba kin iya hawaye amma idan masifarki ta tashi zakice sam bakisan wani lamari waishi kuka ba."
Zahra dai tayi gum,bata tankaba.
Anty murja ta kwad'a sallama suna tare da anty hafsat, umma tace "lale marhaban kamar kun had'a baki ga 'bakin kano can ma sunxo,anty hafsa tace ai umma tunjiya mukasan dazuwan ta baba yayimana waya cewar yanason magana damu musameshi gida da yamma".
Umma tari'ke baki"halin malam sai shi,nadaisan bazata wuce akan auren zahra bane,"
Duka suka kalli umma darashin fahimta dai dai lokacin da anty lubnah tafito daki ta rungume kannen nata"oyoyo my sisters yakuke."
Sukam yaranta suka amshe suna cirawa sama,anty murja nacewa"gaskiya anty lubnah yarannan kara kyau kawai sukeyi kinga yara kamar wasu jinsin larabawa."
Anty lubnah dariya take sosai"kedai murja bakya rabo da shirme "
Duk suka saka dariya,
Anty lubnah amsar hinan tayi daga wajen hafsat tana mata wasa duk suka shimfid'a tabarma waje saboda zafin garin.
Sai lokacin anty hafsa takula da zahrah wacce tayi kicin kicin darai kamar bata gansu ba.
Kamota tayi"oh my sister waya ta'bamun ke,halan umman muce ta bugeki?
Zahra ta idasa saka kuka hada turza kafafu akasa"ba anty lubnah bace taki sayoman alawar kano,kuma umma batayimata fad'a ba"
Anty lubnah dake zuge hand bag ta jefeta da alewar dake cikin ledar "amshi fitinanniya kada ki taramun makwabta."
Zahra tasoma tsalle tana godiya,don duk abinta tasan ka kyautatamata tayi maka godiya.
Tashi sukayi suka kamama umma aikin gidan tas aka gama,lokaci guda umma tana d'an tsegun tamasu yanda zancen aurar da zahran yataso.
Duk sukayi shiru kowacce da abinda take sakawa acikin ranta,can dai hafsat tagaza ha'kuri tace anya umma kunyi tunani wajen yanke wannan d'anyen hukuncin?
Zahra haryanzu yarinya ce karama koma baga hakaba halinta yasha banban dana sauran yara sa'anninta gaskiya batada natsuwar daza'ayimata aure yanzu,sannan shi isha'q meyake nema jikin zahra dayake rawar jikin auren ta umma."
Anty lubnah ta amshe"ato tunda sunyi alkawarin bazai kusanceta ba harsai takai munxalin hakan gud and fine,nadai san zaiyi *auren reno*ne,kuma atleast umma taji saukin bari-bari,nasan dr.ru'kayya inada labarinta asibitinta 'kanwar abban ammar take aiki gaskiya matar so simple umma batada matsala sannan zansaka asake bincike akanta dama family dinta gaba daya,tunda akwai wadda tasanta."
Umma ta gyad'a kai cike da gamsuwa"hakan yayi allah yamaku albarka".
Duk suka amsabda amin,
Itadai anty murja bata tsinka ba,
[9/30, 2:08 PM] mum meenat: Tunaninta yafi karkata akan yanda zaiyiyu ace zahra za'ayima aure tab bazata mance abinda zahra ta'aikatama jamil d'inta ba,lokacin yana zuwa zance wajenta.
Tasauke numfashi dacewa"umma na tabbata isha'q dakanshi zai maido zahra gida batare da ansakashi ba,cox zahra tawuce dukkan tunanin mai tunani yarinyar nan bataji umma,saita sakama isha'q hawan jini watakila."
Umma ta harareta"bakinki dai ya tsaya can,kidena mana wannan fatan cewa akayi zahran bazata kimtsu bane ta tabbata a mai wauta da masifa? Haba ku sakarma autata mara tayi fitsari mana."
Anty lubnah takwashe da dariya tace "uhm..uhm..umma
,zahrafa karshe ce,gashi kiri kiri zahra ta hana abban ammar zuwa kaduna idan ba kwakwaran daliliba,"
Umma sai alokacin ta kwashe da dariya tana girgiza kai,"abar tada maganar data riga tawuce dai."
Wuf anty hafsa tayi tace pls sister halan me zahran ta aikatama abban ammar ne,umma kam mikewa tayi tana murmushi"badani za'a maimaita wannan abun kunyar ba."
Cikin dariya anty lubnah take basu labari"ina lokacin da'akayima ammar shayi(kaciya)duka suka ce eh" taci gaba,kunsan nan kaduna na dawo saboda shine d'an farina bansan yaya'akeyi ba,
Duk sun za'ku sukace munsani mana haba,
Anty lubnah taci gaba da kwasar dariya tana cewa"abban ammar yazo dubashi,ranar wata weekend,ga abbanmu zaune akan kujerar umma,itakuma umma tana bakin gado zaune nikuma ina kusa da abban ammar gefenshi yayinda zahra take zaune tajingina jikinta da nashi .
Shikenan sai bayan angama gaisawa sai abbanmu yakada baki yace"ammar an girma allah ya raya,
Abban ammar yana jin kunya ya'amsa da amin.
Nakira ammar na d'age mashi riga abbanshi yaga kaciyar,yace aikuwa ta warke Allah yakaro lafiya duka muka amsa da amin.
Zahra dake gefe saitayi caraf tace"aikuwa abban ammar baka ganiba kaciyarshi ta warke kuma tadena jini,
Yace mata nagani mana.
Saita sake kada baki tace dashi"abban ammar kaima anyima kaciya?,
Anty hafsat da murja suka kwashe da dariya sukace kai zahra batayi ba.
Anty lubnah tace,aimu dake zaune saimuka daskare awajen saboda kunya,
Shikuwa abban ammar kasa d'aga kanshi yayi saboda kunya,
Umma tanama zahra tsawa amma ina sake tambayarshi takeyi "kaji anmaka kaciya?
Cike da jin kunya yace mata"anyimun zahra."
Zahra ta gyad'a kai cike da rashin yarda saikuma tace"me 'karya"?
Abban ammar yabata amsa "d'an wuta,
Kanshi yana 'kasa.
Abba dake zaune baisan sanda yakaima zahra dukaba,
Amma dayake batada wayo saitace "abbanmu naga kanata dukana menayi maka.?"
[9/30, 2:25 PM] mum meenat: Taci gaba da tambayar abban ammar"to kaciyar taka ta warke?"
Yad'aure fuska kamar zaiyi kuka yacemata "eh ta warke,"
Amma zahra bata 'kyaleshi ba, saida tace "to indai da gaske kake ta warke bud'e ingani .....
Abban ammar tuni zufa tagama rufeshi,yari'ke hannayen zahra dake 'kokarin kwance mashi zariyar wando,wai zataga kaciyarshi idan tawarke ,
Gaba d'aya dariya suke she'kawa,cikin dariya anty hafsa tace"thanks god,lokacin dana kawo nawa habibin zahra tana islamiyya thanks Allah".
Anty lubnah tace kinsan Allah saida umma tazaneta sannan ta 'kyaleshi amma duk da haka,saida tala'be abakin kofa tana cewa dama ashe ba'ayimashi kaciya ba yace anmashi .
Ke ranar baiyima su umma sallamaba,yasa kai baisake zuwa kaduna ba har yau.
Suma su umma ranar kamar zasu nutse don kunya.
Anty murja tace to itadai zahra watakila aljanunta nason ganin meke cikin jiki gareta,hakafa tayima jamil yazo wajena fira allah yasaka ba'agaban su umma bane,
Shida abokinshi na shimfid'a masu tabarma azaure tazo har zata wuce jamil yakirata irin ga 'kanwar budurwa d'innan yace wai tazauna suyi fira.
Zahra tazauna kusa dashi tanata wasa da duwatsun hannayenta shikuma yana tsokanarta.
Can idanunta suka sauka akan abokin jamil wanda yasaka dogayen kaya,gashi riga ta tattare sai gaba d'aya halitar jikinshi ana ganinta.
Zahra ta lura don haka ta kalleshi lokaci guda takai hannunta idanunta waje alamar mamaki tace"yaya menene acikin wandon abokinka, ,
Gaba daya su anty lubnah suka saka salati,anty hafsa tace dama kince 'kaniyarkice aciki ,
Murja tace "anty ina nake da bakin magana,wlh gida nashige nabarsu zaure suma suka sa'be babu shiri.
Har yau abokin baya iya hada idanu dani
**************
Bayan sati guda aka saka ranar auren zahra da isha'q watanni biyu masu zuwa...
Zahra itace mai raba minti,duk inda taje akace na menene saitace nice za'ayima aure,ummana tace kuzo mata biki......
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀



BY MAMAN MEENAT

EDITED :AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR, FAROUQ) ��


ALHAMDULILLAHI ALA KULI HALIN

Chapter 12.







Acikin kaf dangin umma dama na abba babu wanda baisan da maganar auren zahra ba,
Kowa mamaki yakeyi nayanda abba zai aurar da kankanuwar yarinya kamar zahra abun saikace a film kokuma a novels.
Maganganu kam umma da abba suna shansu amma dayake abba kaifi dayane saiya saka tsumma ya toshe kunneshi daga maganar mutane yariga ya'amsa cewar yabada zahra tokuwa bazai mayarda hannun agogo baya ba.
Wannan kenan..
Zaune take cikin office dinta,gabanta akwai tulin files na patient wanda take dubawa sai dai azahiri kallo daya zakama kawayar idanuwanta kagano tsintsar damuwar dake makale cikin dattijuwar fuskar tata.
Fara tattara files din gaban nata takeyi bayan tamanna dan glass din idanuwan nata,
Gafe guda tana makala hand bag dinta a hannu,
Jin kwankwasa kofa yasata dakatawa lokaci guda tazubama kofar idanuwa bayan umarnin shigowa data bayar.
Kyakyarwar macen tashigo itama kamar dr.ru'kayya sam babu uniform na asibiti jikinta,farace tas da ita,doguwa sosai tanada manyan idanuwa dakuma yalwar gashin kai.
"dr.aysheh ",
Dr.ru'kayya takira sunanta idanunta fes akan fuskarta,
Matar ta karaso bayan tasamu matsugunni a kujerar dake fuskantar ta dr.rukayya,
Atare suka sakarma juna murmushi kafin dr.aysha tafara gaida dr. Ru'kayya,
Duka suka danyi jumm suna duban juna,
Dr.aysha ta kawar da shirun dake tsakaninsu tahanyar tambayar dr.ru'kayya damuwar datake yawan gani kwance a fuskarta cikin kwanakinnan.
Numfashi dr.ru'kayya tasauke kafin tace"abokin kuka shi'ake gayama mutuwa aysherh hakika ina cikin damuwa dangane da aurennan da isha'q ya jajibo,anawa ganin kamata yayi isha'q ya natsu,yasamu macen dazata kwantar mashi da hankali amma zahra kam tayi kankanuwa dayawa a matsayin matar isha'q wanda yakeda akalla shekarun dasuka tayarma talatin."
Saida tadan tsagaita dr. Aysherh tad'ora dafadin"nifa ru'kayya sainake ganin duka laifin abinnan yana akan wuyankine,bayag
a haka nisam banga dalili kokuma hujjar dazaki biyema isha'q akan aurennan ba,yaso zahra kuma yarasa zahra kamata yayi yahakura ga yammata dayawa dasuke kaunarshi kamar zasu mace akan soyayyarshi".
Tad'an tsagaita tana kallon yanayin karbuwar maganar tata awajen aminiyar ta din.
Saikuma tadora dafadin"ga aneesa nan haryau takafe akan bazatayi aureba matukar ba isha'q tasamu matsayin mijiba,ni anawa ganin kobayan auren zahra mezai hana ki aura mashi macen dazata kawar mashi da kewa da zaman zullumi don gaskiya duk da banga zahra ba nasan ayanda kike kwatantawa karamace ",
Dr.ru'kayya tasauke numfashi dayin kankanen murmushi don sarai tagane inda zancen kawar tata ya dosa,"kigane bawai nahana isha'q ya nemi auren aneesa vane don bana kaunarta a'a saidon bashi damar zabin ranshi wanda tun ayanzu nake ganin wautata dakuma gangancina,bawai nafara tsanar zahra ko kiyayyartaba, saidai ina hango yanda isha'q dina zaizama *mijin raino*saiya raini mace karshe tazo ta bijirema soyayyarshi abinda yaketa damuna kenan.
Murmushi aysherh tayi dacewa"bazakiyi gaugawa ba ai,kamata yayi kibama auren nasu lokaci nakuma tabbatar dacewar zaki iya renarma isha'q mata ayanda kike mashi soyayya ta gasken gaske kiyita addu'a allah yasa hakab shine yafi alkairi."
"Ameen"
Dr.ru'kayya ta amsa lokaci guda duka suka mi'ke suka fice daga office din suna sake maimaita matsalar dakuma hanyar maganceta.
: Farin ciki awajen isha'q tsayawa fasaltashi ma 'bata lokacine,dukkan abokanshi na gida Nigeria dama na kasashen masu jajayen kunnuwa babu wanda baisan da zancen auren isha'q ba,
Sau tari idan yazauna yana labarin zahra saika rantse wata babbar budurwa ce,sai daikuma haryau a cikin abokan nashi babu wanda zaice ga fasali ko kammanin zahra.abu daya dasuka sani zahra ta isha'q ce.
.......................................
Bayan sati biyu.........
Shirye shirye gadan gadan gidansu umma sukeyi akan auren yar auta zahra wacce haryau a halinta babu abunda yasauya illa iyaka ace yama 'karu don dai hali zanen dutsene,abba kwarai yayi rawar gani wajen bayarda tsabar kudi anty lubnah dasu anty hafsa suka gwangwaje amarya zahra da saitin furnitures y'an gaske masu kyau matuka,
Abba hatta da kayan kitchen da sauran tarkace saida yabayar asiya duk da umma tahana cewarta zahran aiba girki zatayiba,
Acikin wannan lokacinne dr.ru'kayya take sanarma umma cewar zasu kawo kayan lefen zahra,don haka umma tasanar ma abba dakuma yan uwa da abokan arzi'ki.
Mutanen unguwa kuwa da gayya sukayo runduna zuwa ganin lefen zahra don wasu suna zaton indai zahra ba mahaukaci zata auraba to lallai kauyene za'a aurar da ita,cewarsu wanne sakaran namijine zai auri zahra da sanin shi.
Dabara umma tayima zahra ranar daza'a kawo lefen tace da'ita taje gidan anty hafsa ta tayata aiki anty hafsa zataje unguwa.
Kamar abin arziki zahra ta shirya bayan tagama dafsa kwalliyarta taban mamaki,
Ahanya ta had'u da ummilolo tana d'ibar ruwan famfo.
Tun daga nesa ummilolo tafara wagema zahra baki dacewa "ahh amarya ansha kwalliya ina zakije?"
Zahra aka wani yi fari da idanuwa kafin tace"jekikai ruwan kizo ki rakani gidan anty hafsa".
Ummilolo jiki har tsuma yakeyi taji zuwa gidan anty hafsa don tanason zuwa gidan kullum sukaje sai anty tabasu nama.
Don haka dasauri tashige gida tanacema zahra "jirani yanzu zan fito,"
Mintuna kadan kuwa saigata tasha tsaka tsami fuskarnan har shining take saboda Vaseline data sha,
Jerawa sukayi da zahra suna tafe sun labarin boko.zahra nagayamata yanda taci uban wata prefect dinsu jiya sunata kyalkyala dariya,
Sanda suka isa gidan anty hafsa tagama gyara gidan tsaf,tashirya zaman jiransu zahra kawai takeyi.
Da sallama suka shiga,zahra tuni tafara bude-buden fridge wai zatasha exotic saida anty hafsat ta wona zahra sannan tabar gidan tana sake jadadda masu akan kada suyi mata 'barna.
Sundad'e zaune afalo suna kallo,kafin ummilolo tad'an yamutsa fuska dacewa"ni yunwama nakeji,dama banci abinci ba nataho",
Zahra tami'ke tana binciken kitchen din anty hafsa amma bata samu abinci ba,coz ta'boye duka abincinta saboda tasan halin zahra.
Ganin babu yasaka zahra cewa"kawai kizo mu girka da kanmu,"
Ummilolo tad'an zaro idanuwa,saikuma tace"to".
Fridge zahra tafara budewa dan'kare yake da nama dakuma kifi,hakan yasaka zahra kwaso uban nama tabama ummilolo wai ta soya masu ita bari ta d'ora shinkafa.
Haka kuwa akayi,
Zahra dake kokarin kunna gas tace da ummilolo"yarinya ki wanke namannan yafita tas naji ummana tanacewa nama 'karnine dashi."
Ba gardama ummilolo ta zuba uban ruwa acikin nama tasoma durza kamar tana wanke kayan sawa,saida ta tabbatar naman yacanja kala daga jaa zuwa fari 'kal sannan tanunama zahra wadda tazuba mai yakusa kwalba acikin tukunya tanata banka mashi wuta,
Saida zahra ta sunsuna naman kafin tace"yawanku amma kid'an kara durzashi naji yana 'karni ,
Ummilolo takuwa dage iyakar karfinta taci gaba da wankin nama.
Zahra bayan soyuwar man shinkafa ta dumbuzo batako wankeba ta afka cikin man...


Kuyi hqr nagaji yau


Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha Allah ��
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*����‍♀

*by maman meenat*

edited by Aisha T.fulani (umman faruq)

*wannan shafin cigiyane*
*inakuke my dada.aisha tasi'u yamel.kuna ina maman meenat na gaisheku.bilkisu gudaje ur page is here*��


Chapter 13.


Ummilolo takuwa dage taci gaba da wankin nama saida naman yafara zaganyewa tsabar azabar dayasha,
Tajuyo da robar da naman yake ciki tana tambayar zahra "yayi haka?"
Zahra tagyad'a kai"yauwa ummilolo shiyasa kike burgeni wayo gareki kinfi uwande wayo."
Ummilolo tahau washe baki zahra ta yabeta,
Tace"tome zanyi yanzu",
Zahra dake juya shinkafa cikin mai tabata amsa"kitsiyayi mai kawai kici gaba da soyawa".
Hakan ce kuwa takasance,ummilolo ta antaya uban mai a cikin kaskon tuya tawatsa naman ciki man baikoyi zafi ba,hakanan bata tafasa naman ba bare zancen su gishiri da magi da sauran tarkacen kamshi.
Zahra dake juya shinkafa saida ta tabbatar shinkafar tacanja kala daga light brown zuwa dark brown sannan tadebo tulin kayan miyan data jajjaga tawatsa ciki,taci gaba da soyawa tana bama ummilolo labarin "ina kallon yanda anty murja take soya shinkafa wai sunanshi ko frad race ne komenene oho mata,(fride rice)amma yanada dad'i irinshi zanmana. "
Ummilolo tagyd'a kai idanunta jajawur saboda yanda mai yake fantsalomata yana 'konata amma takasa sanarma zahra saboda tsoron masifar zahran.
Saida kayan miyan da zahra take soyawa yafara sarqesu sannan ta antaya ruwa yashanye kan shinkafar gaba d'aya,
Takuma dunbuzo maggi star da already anty hafsa tadakeshi ta ajiye a mazubi mai kyau,xahra tazuba yafi cokali biyar wai yanda zasu sha dad'i.
Takoma akan gishiri shima batayi zubawar wasaba,hakanan curry tace dole ta zuba mai yawa yanda abincin zaiyi dadi na hakika.
Saida ta kammala tajuyo wajen ummilolo tana bata labarin"yarinya idan yayi dad'i har ummanmu zan d'iba nakaimawa,ance babu kyau kaci abu mai dad'i baka kaima mamanka ba."
Ta tsaya cik da maganar sakamakon hango naman da ummilolo ke soyawa yakusa zama gawayi saboda tsabar baqin dayayi,
Wani wawan naushi ta sakarma ummilolo a baki,cikin rashin sa'a bakib ummilolo ya fashe sai jini.
Duk da haka zahra saida tarufeta da masifar"dalla can dubeki wawuya baki iya komaiba,kalli yanda kika qona naman,donkinga ba gidan y'an uwanku bane."
Idanun ummilolo suna fitar da hawaye tace"tokuma saiki kama dukana"?
Zahra dayake tana 'kaunar ummilolo saita rage murya"tokiyi hakuri nadena,mushirya."
Tami'kama ummilolo yatsa suka sar'ke cikin na juna,
Saida suka gama girki zahra tazuba masu a plate,
Sai daifa loma guda ummilolo takai bakinta lokacin zahra taje d'ebo masu ruwa.
Da'kyar ta iya had'iyeta tsabar mai acikin mai take tsamo shinkafar gawani minahikin gishiri da masifaffen yaji,
Naman kuwa aiko dutse ya shafa mashi lafiya.
Zahra ta 'karaso da sauri tana masifar"ummilolo kefa munafika ce,shine kika faraci tun kafin inzo ko?"
Ummilolo cewa tayi"Allah yabaki ha'kuri",
Zahra tazauna tana hararta,
Lokaci guda takai yankan nama bakinta saidai duk iyakar hikimarta da kokarinta nama yace baisan zancen taunuwa ba.
Hakan yasakata furzar dashi babu shiri,lokaci guda tarufe ummilolo da ruwan masifa wai itace bata iya soya nama ba,
Itadai ummilolo tundaga lomar farko tatsame hannayenta tace ta koshi.
Zahra takai cokalin shinkafa a baki,cikin abinda baifi daqiqa gudaba ta furzar dashi a'kasa lokaci guda tana guntsar ruwa abakinta don jitayi yaji yana neman daskare mata halshe,
Idanu tawatsama ummilolo wadda dariya ke kokarin kwacemata tace"hegiya kece zaki cinyeshi aike kika saka na girka."
Idanun ummilolo tuni sun kawo ruwa,tafara rokon zahra dakyar zahra tace "jeki samo almajirai kice suzo suda yawa."
Ummilolo baki har kunne ta falla waje tana kiran almajirai,saikuwa gasu sun tasarma goma har suna turereniya,
Cikinsu babu wanda robarshi bata cika da abincin ba ga tulin nama kamar hauka.
Amma koda kyalla idanu sukaga mugun man dake yawo cikin shinkafar saida jikinsu yayi sanyi,
'karshe a zaure suka zubar da abincin don tundaga lomar farko suka tabbatar masu girkin basuda lafiyar kwakwalwa.
Tiles din anty hafsa yasha mopping amma haka sukayi mata dama-dama dashi bacikin gidan ba hatta zauren saida suka la'anta karshe sukayita jifar su zahra.
.......................................
Ankawo lefen zahra abin yabama kowa mamaki,amma kuma ba'abun mamaki bane duba da irin dukiyar da mahaifan isha'q suka tara dama shi kanshi isha'q din.
Saitin akwati shidda ne,sha'kare da kaya na burgewa duka mfi yawan kayan English wears ne,hadaddun tops gasunan lesuna da atamfofi dayawa duk an dinkasu,
Kai hatta da takalma size dinta aka kwaso,musamman mummy taje dubai tayoma zahra siyayyar,
Mutanen unguwafa sai mamaki suke da kayan lefen zahra,ahaka taro ya watse dangin mummy suna ganin ankwaso zahra diyar talakawa kuma karama sosai,saidai sun yaba da irin tarbar mutuncin da akayimasu.
Yan unguwa kuwa zuga guda sukayita zuwa kallon lefen zahra balbali zahra bala'i.
Zahra kam koda suka dawo gida taga kayan kasa dena kallonsu tayi,babu abinda yafi bata mamaki da umma tace mata wai duk natane.........


real mum meenat.
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀


BY MAMAN MEENAT



EDITED:AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR, FAROUQ)

Muna tare daku masoyanmu, Allah yabar so sa qauna ��


Chapter 14.




Zahra ta gwada wasu daga cikin kayan yafi a 'kirga musamman takalman sunyi mata kyau a idanunta harwani canja salon tafiya takeyi wai yanda zata dinga yimasu uwande yanga take gwadawa,
Tun umma na korarta harta gaji ta zura mata idanu.
Mata kuwa har dare basu dena sintiri gidan umma kallon lefe ba.
Kwanci tashi bawuya gamai tsawancin kwana,cikin juyawar lokaci dare yakan wanzu yabada safiya safiya tazama maraice maraice yakoma dare,
Acikin wannan juyin na lokaci Allah yakawo mu ranar da take d'aurin auren zahra.
Abun kamar yaune akafara zancen amma dayake komai baida wuya awajen Allah saigashi lokaci yayi,shiyasa bahaushe yake cewa komai akasama rana tozaizo,hakanne kuwa tabbas!.
Ango isha'q cikin d'anyar shaddar githzener dinkin boda wanda ya masifar fito da tarin baiwar kyau da kwarjinin da Allah yabashi,gefe guda yakwafa hula kalar shaddar jikinshi mayen turarenshi yana aikin fitar da 'kamshin da'akoda yaushe yake manne jikinshi,
Akwai bakin takalmin Gucci akafarshi sai siririn glass dake kuma 'kayatar da kyakyawar fuskar tashi,
Lokacin daya fito cikin gidan ta'ke yake da mata y'an uwa da abokan arziki,gefe guda mummy da tarin 'kawayenta anata hada-hada da abincicika.
Ratsa mutanen yajeyi har yakai inda mummy take,yana zuwa ta bayanta ya rungumeta,turarenshi kadai ya shaidamata isha'q d'inta ne.
Juyo dashi tayi a hankali lokaci guda wasu siraran hawaye suka sauka akan fuskar isha'q dr.ru'kayya tasan me hakan yake nufi don haka tafara shafar sumar kanshi tana zuba mashi addu'ar fatan nasara dakuma dacewa akan auren nashi dayasa gaba.
Taron abokananshi duka suna waje suna jiran fitowar ango fuska kamar wanda akayima kyautar gonar auduga haka bakin isha'q yaki rufuwa,dayawa mutane suna mamakin yanda isha'q ya 'kallafa rai akan mace haka soyayya mai zaifi yakeyima zahra so bana wasaba.
Dady ma yana tare da manyan abokananshi wanda sune zasu amshi auren isha'q,sai dai ya aliyu dabai samu zuwa ba,saboda yanayin aiki dayasha karfinshi.
Gidansu zahra kam shina cike yake da mutane anata girke-girke,zahra kam musamman anty lubnah ta gyareta cikin wata atamfa super atamfar jace mai manyan fulawowi dinki doguwar riga bubu tamatukar daukar zahra, musamman jan abu ga ba'ki.
Basu saka mata relaxer aka ba,saidai sun gyare mata gashinta ya kwanta luf yasauka har akan gadon bayanta,duk yanda taso subarta tayi kwalliyarta sun hanata kwalliya maikyau suka tsara mata wanda tayi  matu'kar fito da kyan zahran.
Gidan anty hauwa nan kusa da gidan su zahran nan zahra ta tara 'kawayenta sunfi goma sha biyar..
Umma ce ta'aiko masu da abinci,zokaga yanda su ummilolo aka cakare da kayan sallah bikin babbar aminiya sukutum da guda.
Farko abun kamar abin arzi'ki zahra bata tokali kowa fad'a ba,
Saida lami tazo gidan ana cin abinci ana fira uwande ce tafara cewa"yauwa natuna ke lami bayan gulma da munafurci maiya kawoki gidanaanan bayan kince mun wai mamanku tace ko anyi auren zahra babu inda auren zaije tunda zahra batada hankali"?
Lami datakai lomar shinkafa abaki batasan sanda ta 'kware ba,ta fiddo idanu waje dacewa"kai uwande Allah yatsine uwar mai 'karya yaushe nace maki haka?"
Uwande wadda taci d'ammara tace"kada kimaida karuwa y'ar iska,ranar nan da aka aikeki shagon habu cheese zaki siyo maganin sauro da daddare konayi 'karya"?
Ta'tambayi lami tana fiddo idanuwanta waje,
Lami takasa motsi duka jikinta yad'au rawa.
Zahra kam aituni tacire d'an kwali tayi d'ammara tafara turza 'kafafu 'kasa dacewa"aidama nasan babbar munafukace lami,kuma saikin gayamun gidan ubanda nazama mahaukaciya".
Lami idanu suka kawo ruwa,amma dayake itama badaga bayaba wajen iya masifa tayi tamaza wajen cema zahra"gidan ubanki,kika zama mahaukaciyar kodan kinga nayi shiru,shiru shiru ba tsoro bane gudun maganane."
Aitun kafin takai aya su ummilolo sunfara zuga zahra da ri'ke baki"yanzu ke lami zahran kike zagi?wlh zahra kici ubanta rigima uban wata kashe?"
Aiko zahra jiki har tsuma yakeyi ta bugi 'kirjin lami,itama lamin takuwa dage iyakar karfinta ta mangaje zahra har saida kan zahra yabugi bango tafad'i 'kasa.
D'agowar da zahra zatayi idanunta yasauka akan jamila tana mata dariya,
Aiko koda zahra ta d'auki lami saita sunkuta da 'kasa,tahaye tana bugu iyakar karfinta.
Yara suna sake tura zahra,azabar duka yasaka lami cizon zahra a yatsa,aiko zahra kamar jira takeyi tafara naushin bakin lami iyakar karfinta cikin rashin sa'a hakorin lami ya fita baki yayita jini.
Koda zahra taga lami tari'kr baki tana 'buratin kuka,sapita d'aga lami tace dawa Allah ya had'ata bada jamila ba?.
Kama jamila tayi da kokawa,rigima kica-kica aka yaga rigar zahra,abinda ya'kara fusatata ta ri'ke kitson jamila d'aya iyakar karfinta su ummilolo suna jan jamilan amma saida zahra ta fincikeshi fitt kitson ya fita.
Hakan yasaka jamila fashewa da kuka,ta kwashi kitso tayi gida tana kuka itada lami,
Gidansu jamila gidan yawane gasu masifaffu hakan yasaka sukayo zangi guda saigasu sunyo gidan anty hauwa,zasu bugi zahra.
Ganin hakan yasaka zahra ware iyakar karfinta ta angije jamila wadda ke maida ba'asin yanda akayi,waje tayi aguje yayinda sauran yara suka rufa mata baya...
Dai-dai lokacin da motar su isha'q ta iso kofar gidan,tare da manyan abokananshi,
Gefe guda waliyyan isha'q ne cikin fara qal ta shadda.
Zahra nazuwa batare datasan waye gabanta ba,tasaka iyakar karfinta danufin angije kowaye ya tare mata hanyar shigewa gida.
Idanun isha'q ya sauka akan nata idanun,cik tatsaya takasa motsawa bayan hakin datake ajiyewa.
Sauran yaran harsun iso wajen,sadi'q ya kalli isha'q yana tambayar wacece wannan kuma?"
Baikai ga tankawa ba,zahra tasake kwasa aguje tajuya don ganin hanyar gidan nasu a cunkushe.
Gudu sosai takeyi yayun jamila suna biye da'ita dai-dai zata tsallake titin mandawari cikin tsautsayi da baya wuce ranarshi wata 'katuwar prado ce taxo wucewa sam idanun zahra a rufe suke,jikake 'kuuuuu karar buge mutum da motar tayi kasantuwar itama motar a guje take....
Yayun jamila na ganin haka suka juya aguhe waidon kada ace sune,
Zahra kam babu alamar rai a tattare da ita,
Sai jini dake kwaranya akanta harzuwa bakinta da hancinta,akid'imen matashin dake driving motar yafito cikin tsananin tashin hankali ya sunkucin zahra.....

Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha Allah
4 comments 09078902304
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀BY MAMAN MEENAT


EDITED :AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR, FAROUQ)

Wannan shafin naku ne yara manyan gobe Allah ya shirya mana ku baki daya meenat, saleem �� ismaeel, nasir, aliyu hydr zakin fama, my little haneef, umar farauq adon gari, fysal, little angel aisha



Chapter15.




Tsananin tashin hankalin ganin halin da zahran take ciki yasaka saurayin turata kujerar baya yabama motar wuta sosai yana gudu,addu'arshi d'aya kada yarinyar ta mace a hannunshi.
Wata tsadaddiyar private hospital yakaita,wanda anan suka yanki kati,nan likitansu yake muddin sukazo kasar shine yake kula dasu.
Dr.haisam siririn likita fari 'kal dashi yanada sanqo akanshi,
Shine yafito da sauri don already saurayin daya kad'e zahra yakirashi awaya.
Da nosing guda biyu suka taho suna turo gadon da zai d'au zahra,
Yanda jini ke zuba yafi sake d'aga hankalin matashin.
Kasa natsuwa yayi musamman lokacin dayaga anshige da zahra emergency room saiyake ganin kamar bazata tashi ba,
Zagaye asibitin kawai yakeyi yana naushin iska,gami da furzo da zazzafar iska daga bakinshi yatambayi kanshi fiye da sau d'ari how coms hakan ta faru shikam ko kaza baita'ba kadewa ba barantana dan mutum.
Kusan 2hours yakasa natsuwa,saiyake danasanin zuwanshi kasar Nigeria yazo a rashin sa'a lallai.
Ganin dr.haisam yafito da sauri yasaka saurayin nufarshi idanu jajur yake tambayar "doctor yajikinta bana fatan tamutu sanadiyya ta doctor pls"...
Likitan yayi gaba yana bashi amsa"biyoni muje office dina ko?"
Bamusu yabi bayan likitan jikinshi duka a sabule yake,
Akujera mai fuskantar ta likitan ya zauna yana matsar yatsun hannayenshi d'aya bayan d'aya.
Yan rubuce-rubuce likitan yayi kafin yakai dubanshi akan sauran yakira sunanshi a tausashe" Aliyu ahmad(A.A).
Aliyu ya kafeshi da jajayen idanunshi da babu d'igon walwala acikinsu yabama likitan amsa"sunana kenan,likita sanar dani halinda patient dinnan take ciki kasani sarai banason jan time inabama lokacina muhimmanci fiye da komai".
Gyad'a kai likitan yayi dacewa"hakane".
Yasake numfasawa akaro na biyu"A.A bazan 'boye maka halinda yarinyar nan take ciki ba,hakika tana cikin hali na tsaka mai wuya,babbar matsalar kantane yasamu matsala akwai yuwuwar kozata samu kanta lallai zatayi loosing memory nata."
Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,abinda A'A yake maimaitawa kenan,
Saikuma ya marairaice fuska kamar ba A'A da dr.haisam yasani ba,A'a da magana ma ta fatar baki wahala take bashi amma yau shine yake zuba surutu yaga wahala na tunkaro shi.
Cigaba da magana A'a yayi"doctor pls babu wata hanya da yarinyar nan zata zama normal,banason wani abu ya faru da ita ta sanadiyyata.
Natureta da mota kuma ace tayi losing memory what's wrong with me doctor"?
Dafashi dr.yayi dacewa"calm down my friend,wannan matsalar zamu iya solving nata ta hanya mafi sau'ki ammafa sai kabada hadin kai".
Cikin za'kuwa A'a yace"komenene doctor zanyi kokari nidai kada yarinyar mutane ta salwanta dalilina ".
Likitan ya gyad'a kai"d only thing shine a fitar da yarinyar nan waje shine kawai hanyar da nake ganin zamu iya controlin din matsalar tun kafin ta mamaye kwakwalwarta,jinin dake zuba a kanta shine bamaso ya ta'ba kwakwalwa da yawa hakan zai'iya zama sanadiyyarta korasa hankalinta gaba d'aya,
So kadaisan yanayin kasar tamu bawai bamuda kwararrun likitoci bane saidai likitocin dayawansu basuda lokacin patient dinsu."
Aliyu yasauke numfashi,lokaci guda yana cewa"matsalar bazata wuce yanda zan gano ainahin iyayen yarinyar ba,amma zanyi kokarin bada cigiya duk inda ya kamata inyaso sai ayi komai akan idanunsu."
Kallon mamaki dr.haisam yakema A'a kafin yace"abokina wannan matsalar fa bawai matsalace da zamu iya jan time akanta ba,matukar munason rayuqar yarinyar tofa dolene aga yau zuwa gobe ya kasance tana 'kasar cairo don ganawa da kwararruwuce wannan lokacin tamkar rasa yarinyar ne.so d only way inaga kafara processing yanda zakabar kasar da'ita nikuma zanmaka dukkan wani shige da fice daya dace don ganin kasamu manyan likitocin in time."
Mikewa A'a yayi jiki babu lakka,
Aranshi yana raya"kai tsautsayi baya wuce ranarshi,
Dakin da zahra take yashiga tana kwance tayi plat bazaka ta'ba gane kamaninta ba,matukar bakasan taba.
Kanta gaba d'aya ya kumbura fuskarta tayi suntum idanunta duka sunzama kananu saboda kumburin fuskarta impact dai kamaninta gaba daya bakace zahra bace.
A'a jiyayi wani mugun tausayin yarinyar yashigeshi,idan banda taimakon oxygen aibazaka taba yarda zahra tanada raiba,
To ba motsi ba motsawa gatananan kamar gawa haka take.
Dasauri yajuya yafice yabar dakin hankalinshi yakai kololuwar tashi,number mum dinshi yaketa try amma bata shiga sam.
....................................
Isha'q ango anata fama da jama'a amma sam hankalinshi baya tare dashi,saiyake ganin kamar akwai wani abu personal dazai faru.
Yanadai cijewa ne kawai bayason yanunama fans nashi cewar yarinyar data kwasa a guje itace amaryarshi amma a time din jiyake kamar ya bita ya rungume kayanshi yahana koda quda sauka ajikinta.
Duk jama'a sungama hallara liman yafara haramar d'aura aure,lokacin da su ummilolo suka 'karaso wajen a gujesuna kuka da majina sha'be-sha'be,isha'q yafara lura da hakan dasauri yayi wajensu yana tambayar abinda yake faruwa saboda yanda jikinshi yabashi akwai wani mummunan labari dazai riskeshi.
Cikin kuka ummilolo take sanar mashi"wani mai motane ya banke zahra kuma yatafi da i.."
Bata 'karasa ba,isha'q yajuya da saurin gaske ya fad'a motar dasukazo da abokanshi yajata aguje zuciyarshi tana wasiwasin anya zahranshi ce"?
Ganin yanda yafice cikin taron jama'a a kidime shine dalilin dayasaka mutane farga suka fara tambayar abinda ke faruwa.
Itakuwa ummilolo tana mayar da martani cewa zahra ce mai mota yabuge yakuma saceta,
Lokacin da ummilolo take maganar abba yafito daga cikin gida yana sa'ba babbar riga tsayawa yayi cik kamar wanda aka dasa.
Gaba d'aya ma'aikatun kwakwalwarshi sun dakata da aiki na wucin gadi...
Juyawa yayi cikin gida hankali tashe,yana sanarma liman adakata da d'aura aurennan tukunna...
Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha ��
4 comments, 09078902304
[12:03, 24/11/2017] hm: MIJIN 'KWAILA ����‍♀


BY MAMAN MEENAT

EDITED :AISHA ABDULLAHI T. FULANI (UMMUN HYDR, FAROUQ) ��




Kuna raina mmn Fysal, mmn Amna ina alfahari daku yn uwana




Chapter16.



Yanayin yanda mutane sukaga abba yashiga gidanne ya d'aga hankalin kowa,umma tana bakin gado a zaune abba ya aika kiranta.
Da sallama tashiga d'akin cikin abinda baishige minti gudaba tagano damuwar dake kan fuskar mijin nata,
Tambayarshi take cikin taushin murya:"abban zahra lafiya kuwa,meyake damunka"?
"bani ruwa tukun"
Cewar abba wanda yake kokarin tu'be malunmalun d'in dake jikinshi,
Ruwan randar abba umman ta mi'kamashi,ya kafa kai sosai yasha ruwan sida yafara karantama umma yarda daduk wata kaddara ta alkairi kota sharri kafin sanar da ita abinda ya faru da zahran.
Umma kam zuface tagama rufeta,tami'ke da sauri tana kai kawo atsakiyar d'akin sai alokacin ta'iya watsama abba tambayar"yanzu zahran tana inane"?
Shima mikewa yayi yana tafiya yana amsa mata"takamaimai banace ga inda take ba,amma zamu bincika asibitoci muga halin datake ciki."
Umma da ilahirin jikinta yagama yin sanyi ta'amsa da "Allah dai yasa abin yazo da sauki".
Ameen"
Abba yace yasakai yafice hankali tashe,
Tuni mutane suke tambayar umma ba'asin dake faruwa kowa yaji halin da'ake ciki saigaka jikinshi yayi sanyi.
Kai tsaye abba yafito waje yasamu kebewa da alhaji saifullahi yana sanar dashi abinda ke faruwa da zahra,abba yaci gaba dafad'in"anawa ganin kawai a dakata da d'aura aurennen harzuwa yanda hali yayi Allah yaga zuciyata banyi niyyar hana isha'q auren zahra ba.amma babu yanda na'iya da kaddara haka Allah ya nufa dole ce zata saka inhana isha'q auren zahra don bazan kaimashi wahala ba."
Ya tsagaita idanuwansa jajur,
Alhaji saifullahi kallon abba yakeyi da matu'kar mamaki akan fuskarshi yace da abban"amma malam adamu kabani mamaki kwarai da gaske,yanzu don *wata jarabta*tasamu zahra har kake tunanin zan'iya hana isha'q zama da ita?
Tokasani koda mungoyi da bayan hana isha'q auren zahra isha'q bazai lamunta ba,shine yaga zahra yaga tamashi a hakanta yake sonta na tabbata isha'q yanama zahra soyayya ta gaskiya yanama zahra *so d'aya tak*son da babu kiyayya koda yaya zahra takoma,zahra ta isha'q ce abadan da'iman don haka matu'kar dai babu wani dalilin personal acikin ranka to kawai a d'aura aurennan inyaso zahra taci gaba da samun kulawa daga maman ta wato *dr.ru'kayya*."
Abba ya gyd'a kai cike da gamsuwa,yana sake godiya ga Allah daya hada zahra da surukai na gari yanakuma fatan Allah ya tashi kafad'un zahra yabata ikon yima iyayen mijinta dama mjin shi kanshi biyayya.
Haka kuwa akayi take aka sanarma liman yakuwa dage ya tamke igiya uku ras tsakanin zahra da isha'q aurekam ya d'auru bisa sadaki mafi karanci don aure yafi albarka da karancin sadaki.
Umma tana cikin gida taji ana shafa fatiha sai lokacin wasu zafafan hawaye suka sauka akan kumatunta,wato dai shi tsautsayi baya wuce ranarshi.
Yanda isha'q ya kid'ime yasaka sadi'q binshi da mota yakara mashi motar yasha gaban isha'q duk suka fiffito daga cikin motar suna rokon isha'q yayi hakuri yabi komai a sannu,
Kasa motsawa yayi kamar wanda ya daskare haka yakejin jikinshi indai ba bayada rabon aure a duniya ba,mezaisa yarasa zahra akaron farko yad'auki dangana awannan karon yakuma sake rsa zahra?anya wannan kaddarar dake watangaliliya da rayuwwarshi kuwa.
Haka kawai yasakejin soyayyar zahra kamar ana ninka mashi ita,tabbas soyayya ba karya bace kuma amana ba wasa bace,
Abokanshi wajen biyar suka rufar mashi da rokon bude motar hakan ysakashi budewar kuwa,yanda yafito saika rantse yasha giyane saboda yanda jiri yake kwasarshi dakyar ya'iya furta"sad'iq zahra tazama tawa kokuwa ayauma nasake rasa zahra?"
Wani irin tausayin isha'q ya tsilga dukkan abokan nashi,
Dafa kafadarshi sadi'q yayi"haryanzu zahra adam ta isha'q ce,banga dalilin dazaisa afasa kulla auren da Allah yanufi saiya wanzu ba,isha'q bana tunanin akaf duniya akwai wanda yafi dacewa da zahra kamar ka.already zahra tana karkashin kulawarka isha'q".
Wata ajiyar zuciya isha'q yasaki,sai lojacin yasamu kwarin gwuiwar shiga motar da su sadiq suke sauran abokan suka shiga motar isha'q sukayi gaba suna sake kwantar da hankalin isha'q din.
.
Duk tarin yawan mutane gidan baihana dr.ru'kayya ficewa dag gidan ba, sakamakon kiran gaugawa data samu daga dr.haisam akan wata yarinya dawani yakad'e wadda take bukatar agajin gaugawa inma da haki sunason saka hannun dr.ru'kayya wajen fitar da yarinyar zuwa kasar cairo.
Jin yanayin matsalar yasaka dr.ru'kayya zura fara kal ta rigarta gami da saka hijabi tafice dasauri tana barma dr.aysha sallahun cigaba dakula da bakinta kafin ta'iso.
Rafiyar mintuna ashirin tasadata da babbar asibitin,dakanta take driving abinda harta mance rabon datayi kenan.
Parking tayi inda aka tanada domin hakan,tafito dasauri dai-dai lokacin da A'a yake mikama dr.haisam hannu don tafiya wajen cukuiniyar visa.
Dakatar dashi dr.ru'kayya tayi,tana tambayar koshine yakad'e yarinyar?
Dr.haisam ya amsa "shine hajiya"
Tayi d'akin da aka kwantar da zahra,tura dakin tayi cike da kwarewa takutsa kai dakin idanunta suka sauka akan zahra wadda take kwance batare datasan waye akanta ba.
Dasauri dr.ru'kayya ta karasa tana dudduba fuskar zahra,lokaci guda ta shaida atamfar jikin zahra wadda itace dakanta tabada d'inki iri d'ayane dana hanan.
Saikuma y'ar siririyar sarkar gold mai kwad'on da'akama designed da harafin Z wato farkon sunan zahra tabbas zahrace to why meyasamu zahra garin yaya hakan ta kasance?
Bata tsaya 'bata lojaci ba,ta fito a hanzarce tana shaidama dr.hisham yarinyarta ce ma ashe,yasha mamakin jin maganar don ayaranta babu wanda bai sani ba.
Sai dai basuda lokacin neman karin bayani ayanzu dasuke cikin hali na tunanin hanyar kubutar da rayuwar zahra daga halaka.
Kusan manyan likitoci hud'u suka nufi d'akin xahra da kayan gwaje2 don dr.ru'kayya tace sufara jaraba tasu sa'ar kafin ayi tunanin fitar da zahra kasar waje......
October 9,


Kuna tare da maman meenat, Aisha T. Fulani Insha Allah ��
4 comments 09078902304
[12:03, 24/11/2017] hm: *MIJIN 'KWAILA*
_jinjina ga masoya lbrn mijin kwaila'gsky bnsan yama zan fasalta matsayinku awajena ba_ =luv yhu guys=��
editing aisha T.fulani.


*by maman meenat*





Chapter 17.



Cikin abinda baishige mintuna goma ba dr.ru'kayya tagama had'a kayan aikinta tare da kwararrun likitoci sundu'kufa akan zahra don gano ko tasamu matsalane a brain d'inta,
Abinda suka binciko shine yad'anso daga hankalin dr.ru'kayyan bawai matsalar zata shafi lafiyar zahra dun-dun-din bane,saidai hakan zai iya haifar da barazana ga lafiyar kwakwalwarta amma kuma muddin tana samun kula akwai tendencies na zata iya warkewa cikin kankanin lokaci.
Dukkan wani abu daya kamata likitocin suyima zahra sungama cikin ikon Allah kan natane kawai yasamu matsala ayanayin nasu binciken zata iya farkawa akowanne lokaci so abu d'aya dai dasuke ganin mafitane gareta shine idan tafarka tafara kallon abu mafi soyuwa agareta,wanda akowanne lokaci takeson kallo.
Saikuma abu na 'karshe wanda takalla bawai kallo na razanarwa ba,watakila tahakanne zaisa ta'iya tunano abunda yafaru abaya,kenan bazata samu matsalar tunani ba.
Wannan kenan....
Isha'q kam dukkan bincikensu baikaisu ga gano ainahin inane zahra ta kurd'a ba,hakan yasaka shi kifa kanshi ajikin kujera zuciyarshi kamar zata tsage kirjinshi tafito don tashin hankali da damuwa,
Soyakeyi hawaye sufito daga idanunshi watakila zaisamu sassaucin tashin hankalin dayake ciki.
Abinda yafi daga hankalinshi baishige yanda zaisake rasa zahra akaro na biyu a rayuwarshi ba.
Yakira wayar mummy yafi a 'kirga tana ringing sai dai babu amsa,sosai suka shigarda report wa police don binciko zahra.
Acan gidansu zahran ma hankalin duka atashe yake,kusan kowa zakaga babu natsuwa a tattare dashi,duk shirmen zahra a irin wannan halin datake ciki yakamata kowanne mai imani da hankali ya tausayamata.
Abba kam da aminanshi basu samu zamaba,bazama sukayi neman amarya zahra dafatan komai zaizamo cikin sauki da salama.
Sai wajen uku na yammacine motar dr.ru'kayya tayi fakin cikin harabar katon gidan nasu maicike da jama'a yan biki,dayawa sunamata sannu dazuwa dakuma tambayar maijiki takan amsa kawai sai dai babu natsuwa ko d'igo a tattare da ita.
Dakin dady tanufa da telephone din dake kan dan teburin tsakiyar dakin tasamu damar lalabo lambar dady wanda harzuwa lokacin yana fama da ba'ki,
Ganin kiran matarshi yasakashi kebewa gefe guda yana amsa sallamar datakeyi,
Cikin damuwa dr.ru'kayya takecewa dashi"abban hanan kana inane?"
Yabata amsa"inatare da ba'ki ince dai lafiya?"
Tad'anyi kokarin kauda damuwar dake tattare da'ita tace"kalalaboman number isha'q yanzu inason magana dashi ne".
Dady yad'anyi jimm saikuma yace"akwai matsalane mummyn hanan,kidai bari in karaso gidan,don aurenma da har mahaifin yarinyar yace afashi kawai."
Itama abinda takeson sanar dasu din kenan tawatso mashi tambayar"anfasa kokuwa ya'ake ciki?"
"and'aura mana,mezaisa afasa".
Cikin raunanniyar murya tace"abban hanan matsala babba nahangowa isha'q,yanzu haka amaryar tana asibitina a kwance tasamu accident yuwuwar samun lafiyar kwakwalwarta shine abu mafi wahala,bana zato ko tsammanin cikin kankanin lokaci zata zama normal koda miliyan nawa aka barnatar don lafiyarta din,shikenan zamu zubama isha'q idanuwa yazama sakarai akan macene?inada tabbacin akwai zahra ko babu zahra isha'q dole zai iya rayuwa"
Tad'anyi jim tanason jin abinda maigidan nata zaiic Jin baitankaba yabata damar cigaba da maganarta"nikawai atawa shawarar a d'age bikinnan harzuwa lokacin da zahra zata samu lafiya,inyaso sai ayi auren shikuma isha'q yasakama zuciyarshi dangana tunda dama aurene kawai na jeka nayika bawani abu zai tsinta jikin yarinyar ba."
Dady ya katseta dacewar"to naji naki batun idan shawarace ko umarni duka ina tayaki jimamin rashin samun karbuwarsu don yanzu haka anrigaya da andaure aure tsakanin zahra da isha'q,sannan koda cikin mafarki banzaci bakinki zai iyafurta wannan maganar ba,mutanen dasuka yimaki hallacci saboda batashi sukayi aurar da yarinyar suba,ganin kima da mutunci dakuma halinda isha'q ka'iya fad'awa yasaka suka aminta da aurar mana da ita amma kisani idan za'akai zahra turu 'karewar hauka tofa bazamu dage dai-dai da second daya na biki ba.
Tunda har da lafiyarta iyayenta suka bashi ita,yakumace yaji yagani to lallai madamar ta warware zata tare d'akinta inyaso yayi jinyarta sannan banason nakuma jin bakinki akan maganar matsalar da isha'q zai shiga,idan yaro yadauki gatari rikemashi kota akeyi."
Bai saurari mai zatace ba yadatse wayar,
Tafi minti uku tana kallon kan telephone dib dake hannunta kamar shine yake mata maganar,tagyad'a kai ita sam dady bai fahimci manufarta ba,idan soyayya ce bazai nunamata kaunar zahra ba amma abu daya dabazata dauka ba shine fadawar danta cikin wahala haka kawa.
Tana niyyar fitowa daga d'akin dr.aysherh tana kutso kai atare suka kalli juna,aysherh tafara magana"nadad'e ina sauraron shigowarki ga baqi sunata zuwa sai akace kina dakin dady bayan naga fitarshi tun dazu,ince dai lafiya?"
Tayi tambayar idanunta sunakan dr.rukayya,
Sauke ajiyar zuciya rukayya tayi dacewa"matsalar isha'q bansan har tsawon lokacin da zata dauka kafin warwarewar taba,"
Aysherh tace"sanar dani komai qawata,abokin kuka ba'a boyemashi mutuwa."
"Hakane"
Dr.ru'kayya tafad'a lokaci guda tana warwarema aminiyar tata zare da abawa.
Wani mugun farin cikine ya ziyarci zuciyar asherh saitake ganin lokaci yayi dazata cilla kibiyarta wajen farauto ma tilon d'iyarta aneesa zuciyar isha'q wanda aneesan tayi matukar macewa akan kaunarshi.
Cikin kwarewa da hila dr.aysherh ta langwa'be kai dacewa"ayya gaskiya na tausayama zahra,sai dai kokusa isha'q yafi tsayamun araina yanda baligin mutum kamar isha'q zai tsaya a rayuwar kila wa kala don natabbatar matsalar zahra matsalace da take daukar lokaci kafin warakarta kobayaga haka abinda zaifi tayar da hankalina yanda kamalin mutum kamar isha'q wannan matsalar ka'iya kaishi ga aikata sabo na zina donshi ma lafiyayyene kamar kowa yanada feelings akan mace.sai dai na tabbatar matsalar zahra bazata ruguje komai ba Allah yabata lafiya ".
Shiru dr.ru'kayya tayi tana juya maganar aminiyar tata cikin kwanyarta,for how isha'q zai tsaya zaman jiran lafiyar zahra bayan jiran girmanta?
Anya tayi nazari wajen amincewa da zahra yarinyar da kwakwaran wayo baigama zama ajikin ta ba? Mafita daya dazata nemawa isha'q take tunani amma wacece mafitar,tadaisan ko hauka take bazata taba iya tunkarar iyayen zahra da maganar su rike zahra harsai tasamu lafiya ba,kuma shi kanshi isha'q din bazai lamunci rayuwa babu zahra ba.
Kenan menene mafita?
Mafita...mafita..abinda take nanatawa kenan tana kirga tsawon shekarun da kamilin yaro irin isha'q zai dauka na jiran gaibu,don zahra gaibu ce ayanzu adai wannan halin datake ciki.
Tafara matsar yatsun hannunta tana jeranta awanni zuwa sekonni kwana zuwa sati kai matsalar isha'q abin iyaye suyi nazari ce gaskiya.
Jin andafata yasata tunawa dacewar akwai kawarta dr.aysher tana kallonta suka sakarma juna murmushi lokacin da dr.ayshe take cewa"mafita akwai mafita,mafitar d'ayace amma wahalarta yafi ace kizagaye garin kaduna akafa,mafita itace auree".
"aure?"
Dr.ru'kayya ta tambaya fuskarta akwai alamun mamakin jin maganar kawar tata,
"of course,aure zaki karama isha'q shine hanya mafi sauki dazata bashi dama dakuma ikon kula da kanshi dama ita zahran gaba daya".
"nooo,ican't aysher"
Cewar dr ru'kayya"haryaushe xan'iya kallon idanun mahaifan zahra inmasu wannan butulcin?"
Aysherh tadage kafad'a"bazaki iyaba muddin bakya kaunar farin cikin danki isha'q......
turkashi!!!nayi nan...




*real mum meenat*��
[12/7, 1:01 PM] ‪+234 703 895 3431‬: [8:48AM, 11/17/2017] maman meenat😍: *MIJIN KWAILA🤦🏽‍♀*




   Chapter 18



*by maman meenat*



*edited by Aisha abdullahi t fulani (ummu farouq)*



*where are you my shamcy ? ur page is here gaisuwar Ki da bane, Allah ya bar so da kauna inayinki fa sister*💋




    *LANGWABE WUYA TAUSASA MURYA GAMI DA NARKE IDANU.MAGANAR TAUSAYI DUKA AGAREKU MASOYA STILL MUM MEENAT TASAKE NANATAWA "AM VERY SORRY MASU NEMANA TA WAYA MASU TEST KAI HARMA DA YAN BA RUWANMU DUKA ZAHRA NA GAISHEKU*

*~Nimadai bari na d'ana"P.D.P.......lol sister's ku 'karasa masu bin wannan novel ne kawai zasu gane me nake nufi~*"😜 lol....



chapter 18


"Bazaki iyaba matukar bakya bukatar walwalar ishaq,"
maganar dr.aysher tasake amsa kuwwa cikin kunnuwan dr.rukayya ahankali tasauke idanunta zuciyarta tamkar zata tarwatse tsabar damuwa saima kwata-kwata tarasa tudun dafawa.

kallonta aysher take irin kallonnan na bakida mafita kawata,
Afusace dr.rukayya tajuya tafice d'akin gaba daya shawarar kawar tata kemata kuwwa acikin kunnenta.

aysher bin bayanta tayi da kallo lokaci guda tasaki killer smile akan lips dinta,ahankali tafurta"this is the only way dazanbi naganin anee tasamu tagomashin shiga zuciyar isha'q.
tad'an dara kafin shu'umar zuciyarta tasoma kitsamata cewar"muddin zahra ta warke tabbas isha'q bqzai saurari aneesa ba.why not kimaida kula da zahra ta 'bangarenki tabbas tahakane kawai kikeda damar dawwamar da zahra acikin hauka har gaba da abada anee kam tasamu ragamar juya zuciyar ishaq duk ta yanda taso"

shekewa tayi da dariya kafin tabi bayan dr.rukayya kace cillata ake da kibiya.


            ***************
karshe hudu da mintuna ashirin cif suka sada ummq abba kai harma dasu anty lubnah zuwa cikin katafariyar asibitin;bayan kiran da dady yama abba ya sanar dashi komai game da zahra.

umma sosai take hawaye ganin duk rashin ji irinna zahra gata plate bata iya hassalama kanta komai,kai wallahi merai ba bakin komai yake ba.

Abba ma addu'a yake tofa mata,tabbas bayan numfashin dake fita ajikin zahra topha zaka iya rantsewa cewar batada rai.
gaba daya anyi rolling head dinta with bandage,inbanda sexy eyes dinta dake numshe eye lashes nata suna kwance kace anmata dashene dana kanti.

ad'akin babu wanda bai firgita da yanayin jikin na zahra ba.
[12:45PM, 11/17/2017] maman meenat😍: kusan awa daya suka dauka awajen kafin isha'q ya fado dakin,kallo daya zaka mashi ka tabbatar baya tattare da natsuwarshi,abayanshi sadiq ne dukkansu hankalinsu akan zahra yatafi.
ahankali yataka zuwa inda gadon nata yake hannunta yakamo yai twisting yatsunta danashi,ahankali oily eyes dinshi suka soma zirarar da hawaye saiyakejin kamar itama wannan zahran tafiya zatayi  ta barshi,
dora hannun nata yayi akan saitin inda zuciyarshi take harbawa da sauri da sauri.ahankali yasoma magana"zahra pls kada kitafi ki barni bazan taba iya rayuwa babu keba.meyasa kikeson barina bayan kin dawo gareni?
why zahra why,?wata irin rawa jikinshi yasoma kamar ana kad'a mazari .dasauri sadiq dake gefe yakaraso yakama isha'q yana dan bubbuga bayanshi"cal down mana ishaq be a man pls"
ishaq daya juyo yana kallon sadiq idanunshi sun cabja kala yace"tayaya kake ganin zan iya sakama raina natsuwa sadiq ? why? meyasa koda yaushe kaddarar rabuwa da zahra itace abu mafi saurin kusantoni?
meyasa why???? yasake nanatama sadiq tmbyar
[12:59PM, 11/17/2017] maman meenat😍: babu wanda ishaq baibama tausayi ba awajen ( *ciki har dani mum meenat*☹).

ahankali tasoma murza yatsunta dake cikin na ishaq,abinda yasakashi maida attension dinshi gaba daya akanta kenan..murza hannun take sosai kafin daga bisani ta fara bude idanuwa ahankali wanda suka kumbura sosai.

kafe ishaq din tayi da kallo yayinda su umma dasu anty lubnah duk suka mqtso da sauri,kusan 2mns tana kallon ishaq sannu ahankali tajuya kallonta akan abba..
ruwa..."shine kalmar data furta,
anty hafsa takarqso da sauri ta rike hannun ta wanda yake dqure da drip,"zahra"anty hafsa takirata ahankali.

kallon antin tayi saikuma tadafe kai dafadin"kaina anty zai cire,ciwo yake kid'auremun".
gaba daya dakin hamdala suke ishaq kam hugging dinta yayi baikoji nauyin su umma ba.

sadiq ma aguje yayi waje kiran likita.....


" *juma'at mubarak*🙏🏽


*kuyi haquri da wannan zanyi typing anjima insha Allah*

_taku Alaweeyya sani (mum meenat)_😘
[12/7, 1:01 PM] ‪+234 703 895 3431‬: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏻‍♀🤦🏻‍♀


chapter 19


*by maman meenat*



*kad'an daga cikin sakon masu karatu*..
*@ramlat kaduna cewa tayi*" *Assalamu Alaikum,maman meenat dafatan kina lafiya? agaskiya labarin MIJIN KWAILA labarine daba kasafai kakanci karo da irinshi a duniyar online novels ba*.
*gaskiya labarin yana saka zuciya nishad'i, alokacin dana fara karanta novel din sai in tsinci kaina cikin nishad'i mara misaltuwa.*
*nakanyi dariya nikad'ai,some times nakan maimaita wani act da zahra tayi.wlh sam bana gajiya da karanta labarin.ro'kona gareki kada kibama dr.aysha damar cutar da zahra don hakan bazaima zuciyoyi dayawa dad'i ba. up...up mum meenat muna godiya sosai muna jiran 19-20.*
#############
up.ramlat naga sakonki kuma naya ba;tnx so much dear wlh donku mukeyi.saidaku dakuma comments naku muke kara samun kwarin gwuiwar rubutun# i luv u sis .🙏🏽






Dasauri likitan yafado d'akin,shima ba 'karamin mamaki yasha ba ganin zahra tafarka cikin lokaci abinda basuyi zato ko tsammani ba.
'karasawa yayi inda suke ahankali yadafa kafadar ishaq dafadin"ka kwantar da hankalinka anything will b fne insha allah;"
shidai ishaq gani yake kamar daga yamatsa wani abu kan iya samun zahranshi don haka manne abarsa yayi kamar zai sake haifota.
agefe guda yanajin tamkar yacire ciwon dake jikin zahra yamaida anashi jikin.
Allurai likitan yasake yimata wanda tasaka bata wani d'au lokaciba tafara bacci.
sai gab da magrib dr rukayya tashigo asibitin bayanta dr.aysherh ce,da sallama suka kutsa kansu dakin dayake cike taf da jama'a.
umma tasaki murmushi tana masu sannu da zuwa itama dr.rukayya murmushin take tajuya tana kallon aysherh wadda gaba daya tqmaida hankalinta akan zahra dake kwance tana kwasar baccinta.
tabota rukayya tayi don haka tajuya adan razane tafara kame-kame,dr.rukayya tanuna umma da hannu tana fad'in"wannan ce maifiyar zahra kugaisa ko?"
'kasa-kasa ayahern ke kallon umma aranta tana kitsa abubuwa da dama ganin hakan yasaka umma fara gaisheta.
ad'an dakile ta amsa tamaida kallonta ga ishaq dake rike da hannun zahra har lokacin,dan gajeren smile tasaki tana fad'in "romeo baban soyayya bakaganmu bane?"
sai alokacin yad'ako idonshi cikinna dr .rukayya wacce tadansha kunu tana hararshi.
yagane zancen danhaka yamike ahankali saida yagaida aysher yakoma ga mummy,rike hannunta yayi ahankali yajata zuwa gaban gadon da zahra take kwance yqkamo hannayen zahran ya damka cikinna mummy yana kallonta yayi kalar tausayi"mummy ga amanar zahra nabaki,ke kadai na lamuncema kularmun da ita.
hatta kuda bana bukatar yasauka akan ta mummy.and kyakyawan albishir zqhra tafarka batare da wata matsala atattare da itaba,wannan kuma hukuncine daga allah but am fell hppy mummy."
yakarasa yana bayyana murmushi.
kowa awajen yana cikin farin ciki inka dauke dr.aysher dakejin kamar anamata ruwan barkono.
tunano alkawarin data daukarma anee takeyi adaren jiya;mekenan zahra tasamu lfy?kenan hkn yana nufin anee batada rabo ajikin ishaq kenan?
"inaaa sam".
tafurta aranta,dolene ma kota wanne hali aneesa ta mallaki ishaq zata aikata koma menene agame da hakan amma tayaya?
tambayar datafi tsaya mata arai kenan.
"gwaggo rabi"
sunan daya fad'o aranta kenan,kakar ishaq ta bangaren ubba tabbas itace kawai zata saka ishaq auren aneesa koda shida mahaifanshi basaso.
murmushi tasaki lokaci guda ta fice dakin da mugun sauri.....



real mum meenat.
[12/7, 1:01 PM] ‪+234 703 895 3431‬: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏻‍♀





  chapter 20







*written by maman meenat*😍




*edited aysha abdullahi(umman faruq)*





dukansu bin bayanta sukayi da kallo harta fice daga d'akin,asirrance umma ta sauke ajiyar zuciya itadai haka kawai saitakejin takasa samun natsuwa da dr.aysherh amma kuma babu wanda ta nunama hakan.

ishaq kam baibar hospital dinba sai wajen 11:pm shima dakyar umma ta lallabashi amma da fir yakafae shi zaoyi jinyar little zahranshi kamar yanda ya lanqayamata sunan.

********----***********-
Kwanan zahra goma a asibiti yazuwa wannan lokacin tawarke tangaran sai wata muguwar shakuwa data shiga tsakamininta da ishaq har takejin badadi idan yawuce tym din zuwanshi batare da yazo ba.
 to'aiba abun mamaki bane ga duk wanda yasan waye ishaq dakuma irin son dayakema zahra,dukkan abinda zahra take bukata ishaq yakan tanadar mata kai harma wanda bata bukatam ba.
itadai umma har kunyar yanda ishaq yake takeji amma shikam ko'ajikinshi.

dr.aysherh ma bata sarara ko sarewa akan kudurinta ba,matsala d'aya data samu shine gwaggo rabi bata 'kasar tatafi umara hakan ba karamin dagula lossafin ayshern yayi ba;sai dai yata iya alkawari da alwashi kam tashasu nahada auren aneesa da ishaq.
dayake makirace duk kwarewarka wajen bin diddigin abunda ke kunshe aranta bazaka taba ganewa ba.don azahiri kam tana nuna tsantsar kaunar zahra abinda kenan yake karamata kima acikin idanun ishaq dr.rukayya kai harma dasu umma inka dauke anty lubnah dake kallonta kar!.

ranar asabar wanda yayi dai-dai da zamowa sati biyu cif da kwanciyar zahra asiviti dr.rukayya dakanta tabasu sallama don dai amarya zahra ta warware tas bakace tataba samun wata matsala a tattare da itaba.
dama ta'kosa abasu sallama don jinta take kamar a prison,musamman dasu ummilolo sukazo gaisheta suke bata labarin gulmarta da lami takeyi wai ance ta haukace.
kaii ranar zahra tadanna mula-mulan zagi takuma ba ummilolo sallahun cewa tayima lami brush da kashin kaji kafin a sallamota.

ummilolo ta'amsa da to,
dayake lokacin dakin bakowa sunje sallah ,sukabar ummilolo ganin zata taya zahra zama.

ranar dasuka dawo gida ishaq jiyake kamar yayi kuka don ba karamin shakuwa yayi da zahra ba.

mummy yasama idanunnan sun canja kala tanan kawai zaka fahimci damuwarshi,

kallonshi take cikin kulawa yanda ya langwabe kai,ahankali ta rike hannunshi tace"akwai damuwane ishaq?"

tayi tambayar bayan ta tattara dukkan hankalimta gareshi
 sauke numfashi yayi yana shafa sumar kanshi a hankali,sai da yadan samu natsuwa yace"mummy shikenan yanzu idan zahra takoma gida sai yaushe?"
kafeshi da idanu tayi kafin tace"sai randa mahaifanta suka nememu mana."

dasauri ya kalleta saikuma yakoma kalar tausayi dafadin"haba mum pls kisaka baki kawai awuce da ita dakinta ".

baki sake dr.rukayya take kallonshi tana fadin"eh meko zaihana ayi hakan tunda nice kakar mashirmanta ba."

rike hannunta yayi yana rokonta"pls mum,banaso yarinyar nan tana nisa dani pls"

yakarasa maganar kamar zai saka mata kuka;

yunkurawa tayi danufin tashi"kaga sakemun hannu nisam ba'ahaka dani."

"kayi hkr idan takara samun karfin jikinta dakansu zasu nememu,ai sunada hankali ba yara bane."

tana gama fadin haka tayi gaba abinta batare datako sake waiwayar inda yake ba.

kifa kanshi yayi akan karamin teburin ofis din,Allah ne kawai yasan meyakeji dangane da zahranshi.

itako zahra murna hada tsalle aranta tana kissima saitaci uwar dije tabbas don ita bata barin kota kwana.

har suka gama shirinsu tsaf bataga gilmin ishaq ba,saikuma duk taji babu dad'i,takasa daurewa. takamo hannun dr.rukayya dake yima umma bayanin wasu magunguna.

juyowa dr.rkyn tayi,ganin zahra tasaki murmushi tace"yadai d'iyata zahra?"

zahra takasa daurewa idanunta sunyi kwalkwal da hawaye tace "mummy ina yake?"

dr.rky ta kalleta da rashin fahimta tace"wakenan?"

zahra ta amsa"wannan d'an gayunnan wanda yake bani chocolate da ice-cream;baki sanshi ba?"

tayi tmbyr tana kallonta"dariya dr.rky tayi tace"sunanshi yaya ishaq kinji haka zakike kiranshi".
 gyada kai tayi,alamar gamsuwa saikuma tasake maimaita question dinta"to yana ina?"

dr.rky tace kiyi hakuri zaizo kinji ko?

gyda kai tayi kawai takoma tazauna jiki ba kwari sam.

har suka isa bakin mota ishaq baizoba dr.rky ta kira number dinshi.
da sanyin jiki ya daga calling dinta tace"toka fito zasu wuce....






manage for this.

*mum meenat*✍🏼
[12/7, 1:02 PM] ‪+234 703 895 3431‬: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏻‍♀








chapter 21.






*written by maman meenat*😍


 *edited aysha abdullahu,*
(umman faruq).










*MODERN HAUSA NOVELS*



*MIJIN KWAILA FANS*


*M.MEENAT NOVELS*



*WANNAN SHAFI KYAUTANE GAREKU SISTERS"*😘




*Wallahi dashi ake samun natsuwa,yawaita yinshi yana kara imani,yana sanyaya zuciya.*
*wallahi kika/ka lazumceshi bakada kaico!wlh muddin ka lazumceshi zaibaka farin jini natsuwar ruhi,kwarjinin fuska ,zaisaka yawaitar arziqi duniya da lahira...*

*BAKOMAI BANE FACE SALATIN ANNABI(SALLALLAHU'ALAIHI WA SALLAM.)*🙏🏽




"Toka fito zasu wuce"
maganarta ta doki dodon kunnenshi,
"to"kawai ya'iya furtawa,saikuma yaji wani kwarin gwuiwa ya ziyarceshi.

mikewa yayi saida ya rufe mata office din yanufo harabar asubitin,
akoridon dazai sadashi da farfajiyar asibitin yacikaro da aneesa wadda ta tsuke cikin riga da sket nawani jan material,
asamansu tad'ora siririn gyale kalar flowers din kayan.
fuskarnan with full make up.
bayaga katon sun-glass daya mamaye rqbin fuskar tata,

tun daga nesa kamshin turarenta yagama bud'e hancin ishaq.
kallo d'aya yamata yasake tsuke fuska,tatako tamkar tarwada yanda take kada jiki.

gilashin fuskarta tacire ta kafe ishaq da shu'uman idanunta datake wana maza dasu,ganin yasake hade rai yasakata sakin karamin smile tare da tare hanyar dayake kokarin ratsewa ya wuce.

karyar da wuya tayi,cikin salonta namatan dasuka kwankwadi karatun yahudu tace"hada ya ishaq don allah yanzu da gaske saika wuceni bako gaisuwa"?


yanda tayi maganar a shagwabene yasakashi kallonta.

sarqa idanunta tayi cikin nashi kafin tace"waito miyene laifine,kawai donnace inasonka?": "haba ishaq,wlh inaji kamar bazan iya rayuwa ba idanna rasa ka."

tayi shiru don tuni muryarta tafara rawa,

ganin bai tankaba yatsareta da gold eyes dinshi yakara sakar mata da jijiyoyin jiki.
jitake kamar takamashi da karfin tsiya tayi hugging nashi,duk idan ta kalleshi takanyi imagining yanda zatayi luf a faffadan kiejinshi.

"ishaq,"

takirashi dai-dai lokacin data rungume hannayenta akan kirjinta.
kallon daya batane yasakata hadiye miyau bata shiryaba.

idanunta suka kawo ruwa cikin taushin murya tace"don Allah na rokeka katsakurarmun koda kankanin gurbine axikin zuciyarka.nasan kasan menene so,babu bukatar saina fayyacemaka menake ji dangane dakai.sonka azuxiyata natabbata jarabane don nakasa samun matsayi daga gareka.

jiyayi tabashi tausayi,amma daya tuna zahra saiyaji sam bama zaifara kwatanta sonta dana wata ya mace ba.

ya runtse idanu lokacin dayake tunano kalaman late zahranshi’’ _ya ishaq kasani zahra takace kai kad'ai inason kaima ka'ajiye aranka cewar kai kadaine  na Azahra don banajin zan iya sharing dinka dakowace mace.ina tsananin kishinka yayanah_.

sauke ajiyar zuciya yayi,yad'ora da fadin"kiyi hakuri aneesa natabbatar kinada masoya da yawa kibama wani dama acikinsu.ni amatsayin kanwata na daukeki."

kallonshi take kasa-kasa,acikin zuciyarta tana ayyana ishaq amatsayin mutum mara tausayi dakuma sanin darajar soyayya.

sam batayi auneba ta hangoshi ya wuce abinshi

bin bayanshi tayi da kallo;lokaci guda tajingina da vango don jirin datakeji yana barazanar kayar da ita.

juyawa tayi da sauri ta nufi ofis din aysherh wadda take zaune tana duba patients, cikin shagwaba da sangarta aneesa tafada ofiz din batare da tunani ko daukar izini ba.

bata damu da ganin mara lfyr da aysrh ke dubawa ba tafada kan cinyarta gami da sakin kuka me tsuma rai,harga Allah tanama ishaq so mai zafin gaske.

adaburce ayshen tagama duba mara lafiyan da bada iznin kada wanda yakuma shigowa tanada uzuri,

rungume aneesa tayi tanadan bubbuga bayanta ahankali tace"meyake faruwa ne baby?"

anee cikin muryar kuka take magana"haba mum sai yaushene zaki tabbatarma duniya cewa ishaq nawane? sai yaushene zaki nunama duniya cewar dani ishaq yafi dacewa, yaushene sunanshi na *mijin kwaila* zai dusashe yazamo mallakina",pls.mum inajin kamar lokacin mutuwa tane yazo muddin narasa ishaq,bqna zaton sake farin ciki arayuwata madamar bana tare da ishaq mum pls help..."

kuka yaci karfinta takifa akan teburin ofis din tana tsiyayar da hawaye sosai.

dr.aysher tamike tasoma zagaye ofis din cike da tashin hankali;saqawa take tana warwarewa dolene tacikama anee burinta koda shine abuna karshe dazata aikata aduniya, kai koda duk abinda ta mallaka zai kare saita nunma dr.rukayya karshenta don tasan inda rukayya ta'amince da auren ishaq da anee toda bai isa ya bijire ba.

komawa tayi ta zauna ahankali gami da dafa kan diyar tata xike da rarrashi.
: zahra kam harta shiga mota tana waiwayen ta'inda ishaq zai bullo,
can ta hangoshi yana doso motar dasuke.

dasaurinta ta balle marfin tafita kaitsaye runguneshi tayi,tsayinta baikokai a kirjin ishaq ba.

cikin dariya take fadin"shine kaje  ka 'boye ko? hmm damunyi tafiyarmu bazaka sakeee ganina ba."

tafada tana sakarmashi murmyshi,

kama hannayenta yayu,yasaita tsawonshi danata tahanyar durkusawa yace"kalleni zahra".

qura mashi idanu tayi batako kyafta ba.
ya sauke numfashi ahankali yace"i love yhu,i love yhu with all my hrt zahra, ican't life without you zahra,"

zahra ta kwashe da dariyarta da fad'in "hu'umn,kainifa ban iya turanci ba.mudai anty dinmu tana mana karatun reader ne kawai,barima kaji a father and his son...."

bata karasa ba ishaq yasake matse hannayenta yace"zahra kiyimun alkawari zaki rayu dani rayuwa ta har abada.zaki kasance abarin damana aduk matsayin dana kasance bazaki gujeni ba?"

zahra kwalalo idanuwa tayi saikuma tama'ke kafada tace"amma inka yarda zaka dinga goyani yanda  ummana takeyimun da banida lafiya?"

tafada hadi da tafa hannayenta dakuma birkicesu tahada gaban hannun da bayan,yanda yara sukeyi idan abu ya kayatar dasu.

ishaq dariya tabashi ya lakace hancinta dafadin"zangoyaki abayana zahra,zanmaki dukkan abinda kike bukata dangane dani,zan maki koda wankane da wank...."

bai karasa ba zahra ta katseshi ta hanyar cewa"kuma zamu dinga hawa bene inka yarda,"

ya gyada kai.

"hardama kwamfutar wasa zan siya maki."

yadai lura akan zahra babu komai sai tulin kuruxiya.

tsalle.tayi tadare bayanshi.

dai-dai lokaxinne anee da dr.ayaherh suka karaso wajen.


wani kallo aneesa ta watsama zahra mecike da zallar kishi da tsana....



*maman meenat*✍🏼

[10:36AM, 11/25/2017] maman meenat😍: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏻‍♀

Chapter 22.

*written by maman meenat*

*edited aysha abdullahi* (umman faruq)

*Hakika kalaman baki basu isa furta matsayi da girman kimarki a idanuna ba,aysha umman faruq kedin ta dabance.matsayinki da kwazonki gareni hakika sune suka taka muhimmiyar rawa wajen bani kwarin gwuiwar himmatuwa akan rubuta wannan labarin,kin nunama maman meenat kaunar da bazata taba mantawa dake ba.Allah yaraya maki yaranki yaahirya su ubangiji yabarki da abban hyidar aci gaba da soyewa*
*wolla sister ina kaunarki,wujiga-wujiga*😘😍.

*Anty hajjaris mtn*
*Anty badiyya*
*kuna ina?, this page is dedicated for u sisters.tnks for ur luv and care am really appreciate.*😍

wani kallo aneesa ta watsama zahra me cike da zallar kishi da tsana.
jitake kamar tamakure zahra don takaici,
kallo daya zaka mata ka tabbatar da ainahin abinda ke zuciyarta.

itadai umma ganin abinda zahra tayi yasata juya kaida sauri donkunyace ta rufeta.
dr.rukayya kam dariyq sosai take musamman ganin datayi damnata yashiga nishadi cikin kankanen lokaci.

hango dr. aysher datayine yasakata tsagaita dariya takarasa wajenta da sauri,kama hannun aneesa tayi wadda ke.kauda kai cikin daure fuska,duk da sanin da dr.rukayya tayi cewar tatsuniyar gizo bata wuce koki bai hanata sake tambayar aneesa damuwarta ba.

anee kam gani take dr.rukayya tama raina hankalinta don haka saita kauda kai gefe amma har lokacin tanajin zafin yanda zahra tawani dane bayan ishaq saitake ganin kamar da gayya.zahran ta aikata haka,itadai zahra ko ajikinta wai antsikari kakkausa.

dr.aysher da dabara tatake yatsun kafar anee dana hararta kasa-kasa,
daga bisani tasaki dariyar dabatakai ciki ba tana kallon rukayya"hm mummy kibar aneesa da rikici wai tana fushine na hanata zuwa abuja,nace tayi hakuri sainan gaba."

tayi maganar tana sake kyaftama aneesa ido,
aneesa kam gefe ta harara gami da kwace hannunta cikinna dr.rukayya tayi gaba abinta.

zata iya barkewa da kuka muddin zataci gaba da kallon salon tacewar da ishaq yakeyi da zahra agaban idanunta.

azuciye tagifta ishaq wanda baimasan tanayi ba,hankalinshi nakan zahra dake zubamashi surutu.

dr.rukayya kam bayan anee tabi da kallo,saikuma tasauke ajiyar zuciya tana kallon dr.aysher da idonta yasauya kala don tausayin tilon diyarta da Allah ya jarabta da *son maso wani*
[11:50AM, 11/25/2017] maman meenat😍: sauke ajiyar zuciya tayi,kafin tasakala hannunta cikinna rukayya tace"bazan sake maimaita kalmar rokona akan cewar ishaq ya auri aneesa agareki ba,amma zanyi kuka mai yawa dakuma rataya alhakin hakan akanki duk ranar da'akace yau gashi wata lalura takama aneesa akan son ishaq.

zankuma dora alhakin rasa aneesa akanki matukar tarasa ranta tadalilin ishaq."

tasharce hawayen dayake fita idanunta tadora dafadin"natabbata duk nagartar dan adam yanada makusa rukayya,taki makusar itace babu abinda kike fifitawa fiye da kanki.
kinason kanki dayawa,kinkasa nunamun cewar aneesa diyace awajenki,farin cikin ishaq yafi rayuwar aneesa muhimmanci agareki.

tadan tsaigaita kafin tadora dafadin"kitaimakeni kitallafi rayuwar tilon diyata aneesa, bana burin rasata kamar yanda narasa yan'uwanta kinsan komai rukayya."

tausayinta yacika zuciyar dr.rukayya tasake makale hannunta cikinna aysher tace"tursasa ishaq ya auri aneesa bashine zai kawo maslaha acikin lamarin ba.aneesa tasamu kwanciyar hankali agidan aurenta shine abu mafi girma daya kamata ki tunkara,bana zato ko tunanin idanna matsa ishaq ya auri aneesa tahakanne kawai zai kwantar da hankalinta."

jaye hannunta aysher tayi tana fadin"kizauna kiyi tunani yazakiji da'ace iyayen zahra sun hana ishaq aurenta,?
wanne kunci zakiji acikin zuciyrki,?

ki kwatanta hakan akan kaina,na tabbata zaki gane menake nufi."

tana kaiwa nan tayi gaba abinta batare datasake koda waiwayar inda dr.rukayya take ba,
mota tashiga inda aneesa take zaune takifa kai tsakanin cinyoyinta tana gunjin kuka,zafi sosai zuciyarta kemata.
watakila damarta ta karshe zatayi amfani da ita akan zahra,irin dai damar datayi amfani da ita akan late zahra.

tasauke ajiyar zuciya jin andafa bayanta kobata waigoba tasan kowacec;
dago jajayen idanunta tayi tadora akan fuskar mahaifiyar tata tace,"dole zan mai-maita abinda na aikata abaya mummy,duk da alkawarin danayi akan natuba bazan sake ba,amma kisani bazan yarda ingama niqa wata takwashen gari ba.

naso ishaq tunkafin insan menene so,
mezesa insake rasashi akaro na biyu?
bana zato ko tsammanin zan'iya hakan mum ican't."

tafada har lokacin idanunta basu bar zubar hawaye ba.

"bazamu sake maimaita kuskuren mu ba aneesa, cewar dr.aysherh.

"amma kisani damata takarshe da itane kawai zanyi amfani;."

gyada kai anee tayi,lokaci guda tabi motar su zahra data giftasu da idanuwa,ahankali tasaki gajeren murmushin daya fito tare da guntun hawaye ita kadai tasan abinda ta kudurta acikin zuxiyarta.

       *****************

Kwanci tashi asarar me rai,ahaka muketa cinye lokacin mu,guzurin mu nadada 'karewa yayinda tafiyar take dad'a nisa.

gaduk mai hankali idan yadubi yanda lokaci yake gangarawa yanzu zaigane lallai tabbas duniya tana gudu.

acikin murginawar lokacin muka tsinci kqnmu asati nabiyu cif da sallamo zahra daga asibiti,
abunfa saidai hamdala don zahra kam tayi natsuwar dole,to tadolece mana tunda umma tasakamata takunkumin bashiga ba fita.

akoda yaushe dai tana makale gida tana kamama umma wasu ayyukan gida.

duk da harga Allah jitake tamkar tana prison ne musamman idan tajiyo zazzakar muryar ummilolo tana rera wakensu dasukeyi idan za'ayi wasa"liyoooo y'an wargi liyoooo,ya wasan dare darana yake,ke uwande kizo muna kira,ke dije kizo muna kira,ke zahra kizo muna kira inkinqi kisha bugun jiya......"

ai tunkafin ummilolo tadasa aya jikin zahra zaifara kyarma,so dayawa takanyi attempting fita amma dataje zaure saitaga ansakama gidan sakata, wannan yasa tadena fita kwata-kwata takanjiyo su ummilolo suna buga gidan amma sai umma taleka ta wargadesu aguje zatajisu ridididi sun ruga.

akan zauna wani lokacin tamike kafafu tayita barza kuka,amma umma saitaba banza ajiyarta.

saukinta daya dayake ishaq koda yaushe yakan zo musamman idan yatashi aiki da wuri,wannan tasa tarage kewa don zaunawa yake yabiyemata suyita tafka shirme.

ahaka bakaramin sabo tayi dashi ba.

itama umma sosai take nata bakin kokarin wajen jawo zahra ajiki tanakara nuna mata abinda yadace dakuma yimata nasiha musamman akan yawan jarabar fadanta.

todai kusan nasihar umma zamuce wata tana samun shiga watakan tanabi tanan👂🏼tafita tanan din dai👂🏼😌...

Kwana biyu da dawowar alhj saifullahi mahaifin ishaq daga cairo ya tuntubi rukkayya da maganar tarewar zahra,
itadai cewa tayi batasan komai akai ba.
iyayen zahran basuce komai ba,
alhj saifullahi dakanshi ya tuntubi ishaq akan yakamata zahra tatare tunda ta warware,

ishaq jiyai kamar anmashi bushara da Aljanna don haka yabar wuka da nama a hannun dady din.

Dadare kuwa dady yasamu abba agida bayan sallar isha'i kamar yanda ya alkawarta.

Abba yaji dadin yanda suka nunamashi kulawarsu akan zahra don haka yace"Ai alhj da zahra da ishaq duka nakane don haka kayanke duk lokacin dakaga yakamata in Allah yaso zata tare."

Alhj saifullahi bakaramin dadi yaji ba yace"totunda abun yqzama haka nasaka nan da sati guda,aiba wani dogon sha'ani za'atsaya yiba."

Abba yace"kwaraima kuwa,kuma kasan aure yafi albarka idan aka takaita almubazzaranci aciki."

dady ya gyada kai yadora dafadin"duk meke kawo wannan fituntunun idan ba saka riya acikin aureba,kaga masu kudi basu kira malamai sunyi wa'azi a auremsu ba amma sunkira mawaka fiye da ashirin.da'anyi magana ace ai zamanine."

dariya abba yayi yace"to'ai gashi tun ba'aje ko'inaba anbama shedan lasisin zama na dundundun agidan ma'auratan karshe saikaga auren tun ba'aje ko'inaba anata samun matsala."

musamman dama angama shashanci awaje to abu kadan saikaga zargi yana shiga tsakanin ma'aurata.

tun ba'aje ko'inaba saikaga anfara marin juna dq nuna ma juna yatsa."

dady yayi tsaki yace"barta nunama juna yatsa yanzu gashi har anfara kisa,amma abin haushi mutanenmu sunma maida abun abun wasa da tsokalar juna dashi."

Allah ya kyauta"
cewar abba dayake mama kin abun.

(nimadai nace amin)

koda abba yadawo yasanar da umma yanda sukayi da dady fatan alheri tayi,sannan taroki abba daya sanarma sauran yayun zahra zuwa da safe.

hakan kuwa akai ranar juma'a takama ranar zahra zata tare but umma tahanata gayyar kawaye.

*mum meenat*✍🏼

*for any corrections;comments or complain about this buk you should contact me as 07014709470.pls wtsapp only*...😊


[8:02PM, 11/27/2017] maman meenat😍: ​MIJIN 'KWAILA​🤦🏻‍♀

chapter 23.

​written by maman meenat​😍

​A​wannan ranar kam inkaga zahra sam bazaka shaidata ba don kyawon datayi,
donma matsalar duk yanda su anty lubnah suka dage akan tabari sumata kwalliya mekyau amma fir zahra kin amicewa tayi.

shigewa daki tayi abinta tajawo tarkacen kwalliyar tazauna bakin gado tasoma dankarama fuskar tata foundation yakama fuskar yayi shanana dashi don bawai tayi blending dinshi bane.

powder ta dauko no 1.memakon number 3,matsayinta na baqa tadora saiya kasance kalar powder din yafita davan da kalar foundation.

kwallima data shafa hawayen masoyi tayi;wato tajawoshi har gefen kunnenta.

asannan tasoma tsara eyebrow dinta,dafarko tafarashi kamar abin arziki sai-dai mamadin tayi using eyepen wajen yin brow din saita dauki kwalli kajal tasoma zanawa akan girar tata data kasance mefadice datsayi bayaga yalwar gashi da Allah ya yalwanta mata.

Agaban giran tayishi mefadi sosai yazarce kima saikuma tayi tsakiyan dan siriri dashi karshen girarma sai tayishi kwalele,don haka shape din yafita kamar tabarya.

ja sosai na lipstick tasakama lips nata masu taushi,
bayan tagama zageye bakinnata da bakin kwalli
 tsuke bakin tayi tana karkata fuska aganinta babu yana biyunta wajen kyau.

dankareren leshin jikinta dayasha dinkin riga da sket yamatukar amsarta.
kalar flwers na less din shine kalar siririn mayafinta hakanan takalminta duk kala dayane cikas dinta kawai kwalliyar.

yanda tafito tana takawa das-das yajawo hankalin matan gidan,duk da kasancewar umma batayi gayya ba illa yan uwanta dana abba hakan baihana gidan xika da yan ganin kwakwaf ba.

wata daga cikin abokanan wasan zahrance ta rangada guda lokaxin da idonta yasauka akan zahra metahowa cikin tafiyar yanga.

sahura ta sake rangada guda dafadin"tofa ga amarya agidan ishaq nan tafito,barka dazuwa sarauniyar isiyaku.,"

zahra ta farfara mata idanu dazummar wucewa,amma sahura donta tsokaleta tace"wai wannan kwalloya haka saikace wata ba'indiya zahra."

zahra ta juya manyan idanunta dafadin"aidai nayi kyau ko?."

sahura tace kwarae ma kuwa,don wannan da angon zaiganki wata kila tun daga yau ali zaiga ali."

sauran mata suka kwashe da dariya,

wata daga cikinsu tace"aifa lallai,yaganta tu'bul-bul yazata wata gara zai kwasa;Allah sarki inama inzama sauro inmakale insha kallon gwagwarmaya."

sahura tacafe,"yo ni amaryar banmayi zaton tasan harkar ba ai."

umma tafito daga daki tanama sahura dakuwa tace"kinci gidanku sahura,yazaki sakamun yar auta agabane wai eye."

sahura tana dariya tace"allah umman zahra kibani ita insakata daki
 inmata yar nasihar nan tamu ta manya watakila ashawo kanta.

umma gaba tayi"kyaji dashi dai."

su anty hafsa ne suka shigarma zahra akayita caccakar juna.

hakan yabama zahra damar sulalewa tafita babu wanda yasani.

akofar gida tayi kacibis dasu ummilolo anrasa gwanin dazai ahiga gidansu zahra kowa yana tsoron unma.

dasauri zahra takarasa ta basu hannu suka kashe tadubi uwande datasaki baki tana kallonta tace"dalla lafiya kike kallona,konaci ban biya ba."

uwande ta washe hakora tace"uhm ganinai kinzama yar gayu wlh."

dariya zahra tasaka kafin tace"yara kuma bakuda wayo kuce aimuku aure irinnawa,yara gidan bene zankoma inta kwana acan."

ummilolo tadanyi sakale,saikuma tasaki dariya"su zahra yan gayu za'asha dadin bene."

zahra ta kyalkyale da dariyar jin dadi,

ummilolo tace"dama ace nice zahra yaseen indinga hayewa kan bene inayin sululu.indinga shan dadina."

sauran yaran suka dinga dariya dafadin"ahegiya zahra za'asha dadi🤣.

zahra jin ana zugata hadacewa"aidama d'arewa zanyi har abinci akan bene zandinga ci,idan yara sukaje shan dadi inkorosu yanda akeyi gidan alhaji canji."

duk yaran suka goya mata baya akan haka zatayi.

yar purse din hannunta tabude tafiddo dari biyar din da abba yabata da safe kafin yafita yace yaudai tasha shagalinta.

nunama su ummilolo tayi,nanfa uwande uwar shawara tace"taf danice zahra kasuwa zanje insiyo magarya da aduwa da kukar yin kwarbebe indingayi inashan abuna wlh."

aiko zahra tace efaaa.azo aje kasuwa asiyo hada farama."

hakan kuwace ta kasance,duk tarkacen dasuka lissafa seda suka siyo hada goruba,zahra jinta take kamar yau take sallah don yau tana watayawa son ranta.

gidan su uwande suka shige,gidan bakowa sunacan gidansu zahra.

dayake gidan ginin kasane katangar duk ta gwanbale hakan yasaka zahra d'arewa akan katangar tana gwaguyar goruba hankalinta kwance.

sauran kawayen suma suna tsaitsaye gefenta,tadaiyi abin kirki tabama duk mutum biyu daya su raba.

itakuma uwar gayya tadumtse ledar a hannunta.

acan gidansu umma kam hankali yatafi bawanda yafarga da zahra tafice daga gidan.

***"***bangaren ango ishaq kam yau farin ciki bqya misaltuwa kallo daya zakamashi ka tabbatar da hakan.

duk da ayyuka sun sakashi gaba yau yaso ace shine dakanshi zai dauko little zahranshi,amma bayanda ya iya dole yayi handling komai awajen sadiq dasauran friends dinshi.

Dr.rukayya ma gida yagama cika da baki,su aysher ne kan gaba wajen hidima.

gwaggo rabima kakar ishaq ta'iso tun jiya hakan ba karamin dadi yama dr.ayaher ba.
[8:18PM, 11/27/2017] maman meenat😍: wadda keta kaiwa da kawowa,

gwaggo rabi ancakare da wani leshi me dankaren kauri,

gwaggoro tayi da kallabin tadauko kujera tadasa kofar dazata sadaka da sashin da zahra zata zauna tahana koda yara su gifta.

duk wanda zaishiga zata soma sababi"kaga munafurci wato anga isiya zaiyi amarya shine akeso a'bata mashi dakin amarya to naga me wucewa nan."

yanda ta kwama gilas afuska kamar aku kuturu shine zaibaka dariya🤶🏼.

ganin hakan yasaka dr.aysher neman kujera tazauna gefenta dafadin"bari intayaki gadi gwaggo naga yara sunason bata dakin amaryar."

gwaggo rabi tace"kemadai kya fada yannan,ita waccan(tana nufin rukayya)dayake bata kishin danta aikinga tazuba masu ido,salon akawo amaryar tace dakin yayi dauda."

dr.aysherh tace "nimadai haka nagani gwaggo".

gwaggo rabi tawangale hakoran dawasu sunfara zubewa tace"ainakosa inga wannan amaryar nasam saitafi ta dan'uwanshi,dayaje yakwaso kafura gashinan jikokina sunzama kamar basu sanniba da anyi magana su turanci,ke ko sallah basayi fa.kinga yanzu ita wannan datazo ta haifomun nawa nasu ko kallo basu isheni ba."

dariya takama dr.aysher taguntse baki.

nima dai dariyar nayi nace " ​mata ku qame qam​🤣

​mum meenat​🌹

[12/12, 4:31 PM] ‪+234 814 483 2069‬: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏼‍♀





Chapter 24.





*written by maman meenat*😍







*edited by Aysha abdullahi (umman faruq*😘





*Inasake jaddada godiya gareku masoyana masu kaunar rubutuna hakika kunada gurbi na musamman acikin zuciyata.*

*inasonku fiye da ynda kuke sona,naga sakonninku masu tarin yawa akan tambayar maman meenat lafiya.masu kirana masu text messages damasu taboni ta watssapp hakika ina jindadin haka tare da dinbin godiya,Alhamdulillah meenat tasamu lafiya jazakumullah for the special prayers*😘








Wuraren 5:pm yan daukar amarya suka iso,zahra dakecan tana wasanta dasu ummilolo tahango anty lubnah ta nufosu a fusace.hakan yasakata dira daga kan guntuwar katamgar dasauri,karasawa tayi kusa da anty lubnah kafin tayi wata mgna anty ta tareta dacewa"da iznin wa kika fito daga gida?"

Idanun zahra dasukayi narai-narai tasoma kwabe baki danufin kuka,anty lubnah tamaka mata harara tace"kika yimun kuka a swear saina baki mari stupid din yarinya kawai."

Zahra ta kauda kai taji haushi anty taamata fada agaban kawayenta.

Tasa keyarta antin tayi,uwande tabiyota da sauran tarkacen data siyo tana cewa"zahra ga magaryarki".

Anti lubnah tace"ku'ajiyemata kwa taho dashi,aizakuzo ko?".

Dadi ya ishesu suka amsa da eh.

Zahra namasu kashedin kada suci mata ko guda dayane.

Asirrance anty lubnah tashiga da zahra gidan wanda yake makil da jama'a don ko zuga yan unguwa sukayo suma zasuje gidan zahra ganin kwaf.

Saida suka sake cudata tasille jikinta da wanka,wannan karon shigar tattausan voyal lace tayi,dinkin buba da single wrapper, tayi matukar kyau babu wani tarkacen make up dasuka bata damar tayi.

Sosai umma tayimata nasiha wanda duk rashin jinta saida jikinta yayi sanyi kalau.

Inna maryama ce yayar umma ta lillubo amarya da katon abaya anrufe fuskarta ruf dashi,

Sauran mata suka soma guda.

Dakin Abba akashiga da'ita da hikima da dabara iron tasu ta manya yayima zahran nasiha mai tsayawa arai.

Daganan yabama innan umarnin tafiya da zahra.

Sai alokacin hawaye masu zafi suka soma bin kuncin umma,bata taba tsammanin rabuwa da zahra a irin wannan lokacin ba.

Tanaji tana gani aka fice da autarta zahra zuwa gidan aure.

Da addu'ar dawwamammen zaman lafiya tabisu .

Shima Abba kewa ba kadan ba yakeji,bayan cijewa da auriya shima zai iya saka kuk Zahra dai ko'ajikinta wai an tsikari kakkaus.

Amotama wara idanunta tayi fes tana kallon hanya,aranta tanajin nishadi mara misaltuwa.

Tafiya menisa ta sadasu da malali quarters inda gidan dr.rukayya yake,kato n gida daya gji da haduwa.

Horn sukai me gadi ya bude masu get,daganan motocin suka fara sunna hancinsu cikin gidan.

Sashen mummy suka wuce da ita mum din dakanta takama hannun zahran tawuce da ita part dinta don batason jin kananun maganganun dake tashi nacewar ishaq ya auri *kwaila*.

Su anty hafsa sune suka tsaya da zahra suka hanata duk wani rawar gaban hantsi don kuwa burinta tana zuwa ta dare bene😝.

Sukam su ummilolo ai duniya sabuwa ankashe tsufa an daure mutuwa.
Baki suka saki suna mamakin gidan zahra aransu suna raya zahra anzama yan gayu.

Basu anty lubnah sukabar gidan ba sai wajajen karfe Tara na dare,sosai suka sake kimtsa dakin zahran dakuma sake jaddada mata kada tasake tayi wani abu dazaisa kowa ya tsaneta,takame takuma zama mai hakuri tarage rashin kunya da saurin fada.

Itadai da to kaewai take binsu.

Ba karamin kokari Abba yayi
Adakin zahra ba kam

Donkuwa komai yaji masha Allah.

Uwande saida xasu tafi tabama zahra tarkacenta dayimata saida safe.

Sai a lokacinne idanun zahra suka fara raina fata,bata zata haka abin yakeba saida su anty lubnah zasu tafi.

Kuka sosai tasaka tarikesu gam tana cewa ita su maidata wajen umma,

Bakaramin tausyi tabasu ba,amma kuma babu yanda suka iya.

Mummy dakanta tashiga dakin tana rarrashin zahra,

Takuma turamata hanan suyi wasa,amma ayake akwai rashin sabo itada hanan din kallon-kallo sukayita ma juna.

Gwaggo rabi dai ciwon kafarta ya matsamata shine yahanata zuwa ganin amarya tayi kwanciyarta tace saida sfe taganta .


Goma da mintuna ashirin ango ishaq yafaka motarshi a farfajiyar gidan,fitowa yayi cikin shigarshi ta manyan kaya dasuka dace da siffarshi ta hadadden namiji.

Kamshin turarenshi kadai ya isa ya tabbatar maka cewa angone.

Hannunshi yana rike da ledar kaza da yoghurt daya siyoma amarya zahra,kai harma da chocolate.

Da kuzarinshi yake tunkarar gidan kada kaso ka tona zallar farin ciki awajenshi.

Wai yau shine Allah ya mallakama zahra amatsyin mata,tabbas bayada abinyi sai godiy.....






Kuyi hakuri  da wannan zuwa gobe zamu juna ida. Allah mai kowa da komai ya aramana lokaci.


*for any correction, comments or complaint about this book u should contact me at 07014709470*...


*mum meenat*✍🏼
[12/12, 4:31 PM] ‪+234 814 483 2069‬: [06/12 12:40 pm] Maman Meenat: *MIJIN 'KWAILA*🤦🏼‍♀






Chapter 25.







*Written by maman meenat*😍






*Edited by Aysha Abdullahi T.Fulani(umman faruq)*😘





*SAKON MASOYA*😘


*Salam er uwa.... Sunana Maryam Muhammad* *Alameen... Amma ana kira na first lady... Asalina er* *garin Maiduguri ce... Amma yanzu ina aure a zaria*
*Wato hakika ina karanta novel dinki ne na MIJIN KWAILA* *gasky na dade banyi dariar da nasha da nake* *karanta novel din ba🤣🤣🤣*
*Allah ya kara baseera da zakin hannu*
 *Daga masoyiyar ki MARYAM FIRST LADY (maman deena)*.


*mum meenat*😍

Wa'alaikissalam


Nagode sosai da kulawa Maryam


Dafatan zakici gaba da bibiyar labarin mijin kwaila..😘





Da wannan tunanin ango ishaq yashiga cikin gidan nasu,

Tsayawa lissafa farin cikinshi awannan rana ganina bata bakine.

Sashen mummy yafara zuwa bai sameta ba tana bangaren Daddy saidai gwaggo rabi databi kujera ta bararraje kafafu tana matsasu don jitake kamar ana mata sukuwar dawakai acikinsu.

Dasallama ishaq tashiga falon,gwaggo rabi ta'amsa lokaci guda tana wangale hakora dafadin"Ango kasha kamshi,"

Ishaq ya sadda kai yana dariya kasa-kasa yace"kewai tsohuwarnan kardai har yanzu baki kwanta ba."

Gwaggo rabi ta tale baki,kafin tace"inanaga ta kwanciya,ai inanan nakasa natsare dama jiran dawowarka nake ai,Donna kafafu sun matsamun aida acan bangarenku zan kwana".

Ishaq ya bude ido sosai yace"kwana kuma gwaggo? "

Gwaggo rabi tace "kwarae kuwa,saboda banason amarya tabukaci wani taimako ba babba akusa,tunda aikai da ita suka sabon shigane,jirani dai ina zuwa."

Tamike tana dafa cinya tana tafiya a gwagwale,

Ishaq bin bayanta yayi da kallo harta shige dakin datake zama aduk lokacin datazo.

Azuciyarshi yana mai-maita kalmar sabon shiga'to mekenan?"

Juyawo da kallonshi yayi gareta jin tana tahowa.

Takaraso dakyar tana mayar da numfashi tazauna jagwab,tadora dafadin"tunda aka saka ranar aurenku nasiyo wadannan kayan na'ajiye inajiran lokaci."

Amma kafar nan bata tashi yimun rashin mutum ciba sai yau."

"Karbi nan".

Tafada tana mikama ishaq bakar ledar dake hannunta.

Amsa yayi fuskarshi cike fal da tarin tambayoyi,

" bude mana kagani"

Muryar gwaggo rabi ta katse tunaninshi.

Ahankali yasoma warware ledar,wani farin kyalle yafiddo saikuma wani sassake aciki.

Yatsura mata idanu,kafin yace"kyalle nagani dakuma icce namiye wannan?"

Gwaggo rabi da tuntsuro kallabi gaban goshi kana tace"kyalle ai shine zaka shimfada kafin kataki amaryar taka,shikuma wannan iccen ai sassaken kukane,kayi kokarin dafashi da jar kanwa yanzunnan kashashi.To inamai tabbatar maka duk taurin matarka saika hudata,don zaka kara karfi dakuma kuzari,
Aimu zamanin my maza basa shigar mace haka bawani dan tanadi yo ai rainaka zatayi."

Takare tana washe hakora,ganin ishaq ya kasa magana yasa race"kada kawani damu,wannan maganin kasadinne ai,karyar mace taga gazawarka.

Ko cikin darene kuka gama ka dawon da kyallenan anunama dangi,matarka takawo matancinta gidanka kajiko,jeka ango Allah yabada lafiyar jiki."

Tafada lokacin datake kama hannunshi da turashi zuwa waje.

Mamaki ya ishi ishaq, yace"yanzu gwaggo rabi don Allah kina nufin bakubar wannan banzar Al'adar ba har yanzu,"

Towaima cemaki nayi abinda yasakani yin auren kenan,haba gwaggo don Allah kima daina wannan kadasu mummy sujiki."

Kallaon banza tamashi tace"eh aifa.to saurareni dakyau,ko ita uwar taka saida naga shedar jinin matancinta bare matarka,kuma a al'ada ai yau dai daka shiga daki yaune zaka taki amaryarka,don haka inkasa iyashege wallahi dakaina zan shiga in shimfada kyallen."

Taci gaba da sababi"yo harni za'anunama boko,ba boko ba walla koma menene ayau dai saika taki yarinyar nan,don nakosa inga jikokina ehe."
[06/12 1:11 pm] Maman Meenat: Ishaq kasa magana yayi don tsananin mamaki,amma daya tuna jaraba irinta gwaggo rabi saiya saki murmushi yace"shikenan matar,ai duk abinda kikace shi za'ayi,
Bari inje kada amarya tagaji da jirana ko?"

Yakare maganar yana haramar wucewa.

Gwaggo rabi data rangada guda tace"jeka sabon ango Allah yabada sa'a,bance ka sasdauta mataba.
Don banson ta rainamun kai.
Bayanma bikin yazo ina umara ai naso ace dakaina namka hadin uban maza,".

Dariya kawai ishaq yayi yashige abinshi.

Gwaggo rabi ta bi bayanshi da addu'a harya bacema ganinta.

Komawa ciki tayi ranta fes,addu'arta daya daren yau tasamu jikoki.🤣

Zahra amarya tuni tasoma baccinta da kayan dake jikinta, ta takure akan kujerar datake zaune.

Hanan dama tana ganin zahra tfara bacci itama tayi dakinta abinta,don dama atakure take.

Da sallama yashiga dakin,
Ba'a amsaba,sai kamshin turaren wuta kawai dake tashi.

Yakarasa ciki ahankali,
Idanunshi sukayi tozali da zahra dake kudundune tana kwasar bacci abinta.

Ajiye ledar hannunshi yayi,ahankali yasaka yatsanshi ya zagaye round face dinta dake kara kyau intana bacci.

Tsuramata idanuwa kawai yayi,ahankali tunanin late zahra yasoma ziyrtar zuciyrshi,

Ya numshe idanunshi dasuka ciko da hawaye,

Baitaba ganin kamanni zallar kammani kalar na zahra da zahra ba.

Yanada tabbas dakuma yakinin Allah ne ya canja mashi little zahra da waccen late zahra din.

Wani mugun sontane yake ratsa dukkan sasan jikinshi,

Kama hannunta yayi ahankali yasaka cikin nashi yana murzawa ahankali.

Hakanne ya farkar da zahra dake bacci tabude idanunta tar akanshi.

Donma sa'arta daya batada magagin bacci.

Idanunta ya gauraya dana ishaq, tamike dasauri tana murmushi,tace"lah kadawo?.

Shima smile ya sakar mata yace"nadawo zahra,haka kike bacci da wuri dama".

Dariya tasaki kawai.

Kamo hannunta yayi yace "zokici abinci ko?"

Tadan langwabe tace "aina koshi."

Namaci wanda mummy takawo.

Kallonta yake cikin ido yace"nawa special one ne ai.oya zokici".

Bamusu tamike,dakanshi yakama hannu ta har toilet saida tawanke baki,

Shine ya yanka mata kazar,zahra wadda tasaki baki tana kallonshi sam bata tankaba.

Ganin ya nufi bakinta da naman yasa tace"tab!nidai kabani inci dakaina,saikace banda lafiyane zaka bani abaki."

Dariya kawai yayi yamika mata plate din,datake batajin yunwa bataci wani me yawaba ta ture.

Dakanshi ya hada mata ruwan wanka tawatsa tana korafin"nidai ummana batacewa sainayi wanka idan ina bacci."

Kayan baccinta yafito mata dasu,nanma bata musaba tatube riga agabanshi tasaka ta baccin.

Kirjin Kama's kamar siminti🙈 .

Bai damuba,shidai kallonta kawai yake.

Saida tagama tahaye gado takwanta abinta.

Shima wankan yayo yagama shirinshi dayake na al'ada,

Ahankali yahawo kan gadon,yajawo zahra jikinshi.babu komai aranshi kawai yanason jinta kusa dashi.

Zahra kam bigit tamike idanu waje tace"anan zata kwanta,"

Bai tankataba,illa smile daya sakarmata.

Mikewa tayi,tana yayimar batgo tace"tab!nidai wallahi bazan kwanta kusa dakai ba,niba 'yar iska bace."

Ishaq yarike wuya yana kallon zahra dake murguda baki.






*mum meenat✍🏼*







*for any correction,comments or complain you should contact me at 07014709470*😘

*MIJIN 'KWAILA*🤦🏼‍♀




*written by Maman meenat*😍




Chapter 26.





*Ina baku hakuri masoya akan jina dakukai shiru jiya,nayi typing har nayi post abun haushi WhatsApp din yasamu matsala wannan yasaka gaba daya nayi missing komai nawa saida nasake installing kuyi hakuri pls*.

*Wasu zasuga sunman magana banyi responds ba,tokuma kuyi hakuri matsalar tashafeku kuma,don gaba daya chats dina suka 'bace.I luv you guys'😘*.






Ishaq wanda yasake hannayenshi ya tallafo wuyanshi kallon zahra kawai yake yana smiling, wai ita ba yar iska bace.Chaii,shikam inbanda soyayyama mezai tsinta ajikin zahra wadda ko irin yar kirgan danginnan nayara ma bata fara ba.

Sakkowa yayi ahankali yatako zuwa inda zahran take kwance,gaba daya ta takure jikinta tasaka kafa duk ta tattake bargon datake ciki lullube aganinta babu tayanda ishaq zai iya budewa.

Acikin ranta kuwa tana ayyana ishaq amatsayin dan iska,to dan iska mana inba iskanci ba nameye zaice wai zai kwanta kusa da ita?"

Tai kwafa daga kwancen datake aranta taraya tadena sakar mashi fuska tunda d'an iskane dama,kai gobema zatayi tafiyarta gida tafasa shan dad'in bene.

Da tulin tunane tunane babban barawo bacci ya sureta,batayi aune ba.

Ishaq dake tsugune gabanta yanajin alamun tafara bacci yasauke ajiyar zuciya,aranshi yaraya "zahra hukumace saida lallashi.

Kacokam yadauketa itada bargon ya shimfide bisa gado,yagyara mata kwanciya yaja pillow yadora kanta akai,gashinta yasauka bisa pillon.

Yadan jima yana kallon fuskarta kafin yashafi tattausan gashintan yayi addu'a ya shafa mata gami da sumbatar goshinta.

Yajuya ahankali yarage hasken dakin daga full light zuwa dim light yafice daga dakin bayan yaja mata kofar.

Kai tsaye dakinshi ya nufa,yagama shirinshi yakwanta abinshi aranshi yana karajin kaunar zahranshi jini da tsoka.

Yadau tsayin lokaci kafin bacci yayi gaba dashi.

Washe gari karfe 4:30am yatashi kamar yanda yasaba koda yaushe,a'aldarshi yakan tashi ya gabatar da nafiloli yayi karatun Alqur'ani kafin kuma yayi sallar asubahi.

Hakance ta kasance kuwa don saida ya kamalla komai yayi shirin masallaci,dakin zahra yanufa danufin tayar da'ita tayi sallah.amma ga mamakinshi ya'isketa tana sallar.

Wucewa masallaci yayi abinshi aranshi yana raya uhm lallai zahra anfara hankali koda yake gaduk wanda yasan Abba dakuma tarbiyar gidanshi yasan wasa da ibada baya daya daga cikin dabi'unsu.
Abba mutum ne jajurtacce daka tsaya tsayin daka wajen gina rayuwar iyalinshi abisa koyarwar kitabu wassunah donma Allah yabashi zahra datake neman gagararsu.

Ishaq bud'e kofar part din nasu yayi danufin wucewa masallaci, amma kuma saime?

Gwaggo rabi yagani rakabe jikin glass din window takasa kunne bagalo,ko motsin kirki batayi gaba daya hankalinta yana kan abinda takeyi.

Gaban ishaq yafad'i,aranshi ya ayyana gwaggo rabi amatsayin jarababiyar tsohuwa,to jaraba mana,inba jaraba ba mezai kawota kofar taga da asalatun fari.?

Wato tana labene taji abinda yake wakana tsakaninshi da zahra.

Kwafa yayi kafin yakarasa inda take gami da dafa kafadarta.

Azabure tajuya tana cewa"wa'innahu min sulaimana....."

Sauran maganar tamakale afatar bakinta ganin ishaq ne,tasauke ajiyar zuciya cike da borin kunya tace"Amm,af...dama  cewa nayi bari inzo inji ko kuna bukatar wani taimako,kasan yaran yanzu badai raki ba.daga sun kwana da namiji saikaji sun langwabe wai basu da lafiya."

Takare maganar tana gyara daurin zanenta dayake kokarin kwancewa gami dajan majina sharab,tawaige gefe ta fyace feeet.ta durje hancinnata da tafin hannu,bayan tahad'e hannun na dama da hagu ta mutsuke kamar wacce ke shafa versiline.

Ishaq ya watsa mata harara cike da kallon yanda take kazanta yace"to ai saiki koma inda kika fito,dondai bawani taimako naki damuke bukata."

Wangale baki tayi tace"to ai shikenan ma,fitomun da kyallen ko."

Juyawa yayi yana tafiya jin anfara tada sallah yace"kije kiyi sallah abinda zan dawo ne."

Aiko bamusu tajuya itama tana sambatu dafadin"to Allah dai yasa Anfara asa'a ai haka muke bukata,kafi yayanka hankali me auren kafura.kaga da'ace yanajin maganata Aida tuni yasaki kafurar nan yazo nan gida yayi aurenshi abinshi.

Shidai ishaq gaba yayi baisake tanka taba,sai dai harga Allah bayason wannan sakarcin da tsohuwar takeyi,aganinshi  ragema kanta daraja take.
Yo danma zahra yarinyace,da'ace babbace taleko taga abinda Rabin takeyi aitsaf zata wanketa soso da sabulu.

Yaja tsaki shidaya yana takaicin halin kakar tashi.








*real mum meenat*

Maman muhamman Naseer ba😘

*MIJIN 'KWAILA*🤦🏼‍♀






Chapter 27.





*writing by Maman meenat*😍





Sai wajajen karfe bakwai yashigo gidan,bangaren amarya zahra yafara lekawa,kwance ya isketa ta kudundune cikin bargo.hakan yabashi tabbacin bacci takeyi,yaja mata kofar yanufi bangaren iyayen nashi.

Gwaggo rabi itace uwar zaman falo to yaudai bata falon don haka kanshi tsaye yanufi dakin mum din,tana gaban dressing mirror tana gyara zaman kallabin kanta lokacin dayayi sallama hadi da sawo kai cikin ni'imtaccen dakin nata dabai rabo da kamshi.

Murmushi tasaki tana amsa sallamar tashi, karasawa yayi inda take yadafa kafadunta hadi da d'an kwantar dakai bisa bayanta yace"morning momma."

Tasaki karamar dariya dacewa"haba ishaq kaiwai meyasa har yanzu sam kaki ka girmane,yanzufa kazama babba kafara aje zuri'a saika rage wannan shagwabar taka.haka yayanka zasu taso suganka gotai-gotai kana yimun shagwaba ko?.

Dariya yayi sosai yace"mummy niko yara d'ari na ajiye ai bazan dena yimaki shagwaba ba,kefa mumma dina ce.kuma wacce akoda yaushe Idan nakalleta nakanji dadi mara misaltuwa so why zandena langwabe wa momma alhalin har yanzu am still young. "

Gyada kai tayi tana dariya tace"to aikaga saika bada himma,ina d'iyata zahra baku shigo tare ba mu gaisa."

"Naleka na'iske tana bacci,inaga bayan tayi sallah ta kwanta."

Yabata amsa lokacin dayake goge mata takalmin data fiddo zata saka.

Mikewa tayi tace"to aibari intasaka gaba muje kugaisa da dady,saimuje mugaisheda gwaggo rabi,mumata bangajiyar biki ko?.

Ishaq kai yasoma sosawa yace'am haba,gwaggo ai tuni mun gaisa,sai dai ko dady din."

Itadai mummy gaba tayi,tana cewa"to aisaika bada himma,dafatan baka mance yau Saturday ba.kace kunada meeting appointed da shugaban NTA akan tafiyar ka ko.?"

Narke idanu yayi yakoma kalar tausayi,yace"ina sane mum but ina tunanin yanda zantafi inbar zahra banmasan iya adadin tym dazanyi a can kasar ba."

Kallonshi mum din tayi tace"wannan aiba abun damuwa bane ishaq, anawa ganin wannan riba biyu ce.natabbatar kafin kadawo zahra takara girma takumayi hankali,da ikon Allah.kaima zakafi son hakan ai."

Sadda kai kasa yayi kawai.
Har akasan zuciyarshi bayason tafiya yabar zahra,haba toma menene amfanin auren matukar baya tare da ita."?

Kai tsaye bangaren dady suka nufa,yana zaune bisa sallaya yana karatun Alqur'ani sukayi sallama.

Saida yakai karshen ayar dayake karantawa yadago kai yana kallonsu hadi da sakar masu mutmushi,

Suma murmushin sukeyi mai,musamman ishaq dayakejin tamkar an nunkamai farin cikin shine.

Mum tafara gaidashi,sannan ishaq shima yabada tashi gaisuwar.

Dady dake shafa kan ishaq yace"babana angirma,naga kwana guda harka kara kiba,me zahra y'ata dafa makane haka".

Mummy data kyalkyale da dariya tace"ah to tambayarshi dai."

Shidai ishaq dukar dakai yayi kawai yana smiling,

Kamar daga sama suka jiyo muryar gwaggo rabi,tana fadin ina mesunan malam din yakene.

Wato nizaka mayar shashasha ko,inzauna tsayin lokaci ina jiranka ashe kainan kataho wajen uwayenka kabarni baki sake,tunda ni ba uwarka bace ko?"
 Takare maganar tana shigowa dakin,

Ishaq aranshi banda Innalillahi babu abinda yake mai-maitawa.shikenan yau tsohuwar nan zata mashi fallasa kuwa iri-iri.

Gwaggo rabi data nemi waje tazauna tace"dakai nake,kayimun kasake,nace ina kyallena ko uwayen naka kafara kawomawa sugani.tunda naga ai kabanbanta tskanina dasu,todai kasani tushiya itace mafarin dawa.daban haifi ubannakmeida kaima bai haifeka ba.tomezaku boyemun,inma yarinya bata kawo matancinta gidan miji ba aigwara kufada tunda wuri tagane inda dare yayi mata."

Zufa sharkaf tagama rufe ishaq yace"haba iya,waike meyasa kike hakane don Allah? Nace ai kijirani ina zuwa ko?".

"Injiraka ina?.

Cewar gwaggo rabi dake runtse idanu saboda tsabagen masifa.

Taci gaba" kaga daka ganni nan,duk da banyi boko ba tofa bawata bariki dadan boko zaiyi inkasa ganewa.inma zaka fito da sheda kafito da'ita kowa yagani.nan dai dagani saiko iyayenka gasu,bawani bare acikinmu."

Dady daya kasa gane kan inda zancen yanufa yace"shin tsaya gwaggo, waidon Allah duka wannan tada jijiyar wuyan dakukeyi ta mecece,meke faruwa ne.?

"Ka tambayeshi,"

Cewar gwaggo rabi dake nuna ishaq da yatsa.

Dady yajuyo wajen ishaq dya dukar dakai kasa yace"babana ya'akayine,meke faruwa tsakaninka da mutiniyar taka kuma."

Ishaq ya sauke ajiyar zuciya yace"no dady,bawani Abu bane kawai dai...."


"Kawai dai me?.."
Gwaggo rabi ta katseshi,

Taci gaba"inma zaka fito fili ka sanar dasu gaskiyar zance kafito,donni ba'a munafurci dani kasani."

Dr.rukayya da tunda ake maganar sai yanzu tasa baki tace"gwaggo inaga idan yaki fadi kawai kirabu dashi kisanar damu abinda ke faruwa."

Zumbur ishaq yace"but Mumm."

Da hannu ta dakatar dashi,tace munajinki gwaggo.

Aiko gwaggo rabi kamar dama jira take,tasoma wassafa labarin yanda komai ya wakana AtoZ.ba dady da ishaq ba hatta mummy saida abin yabata kunya.

Tace"gwaggo inaga don-dai bakisan wacece amaryar ba yasa kike wannan maganar,amma duk meenat*a anawa ganin yanzu andena wannan al'adar ai tuni. "

"To gwanar na'iya."

Cewar gwaggon,"aiduk abinda yaronnan yakeyi da daurin gindinki yakeyinshi.amma bari inje wajen amarysr dakaina".

Tamike tana dafa kafa tayi gaba,bata saurari kiran dasukeyima taba.

Ishaq yamike zai bita,dady yace"barta taganota watakila idan tagantan zata dena maganar datakeyi."

Dole yakoma yazauna hadi da dafe kai kawai,yana tunanin rikici irinna wannan tsohuwar.

Da sababi tashiga sashen amma jin anyi tsit yasakata cewa"to lallai y'ar mai,kyaci ubanki kuwa.wato agidan jikana zaki kawomana lalata,to munfi karfinki munrigaki munce Allah kina ina fito algunguma."

Still dai shiru taji,don haka ta nufi dakin datake ktautata zaton na amaryar ne ,tana tijara.

Wayam dakin ba kowa,

Hakan yasakata rike baki dace"ah lallaifa,amaryar kinsamu sake ."

Bata karasa maganar ta ba,tajiyo  abu saman kanta racacau...

Tazabura dasauri tace"mun shiga uku,ruwa kuma adaki me rufi?.."

Sauran maganar ta makale afatar bakinta hango zahra datayi can koli bisa wardrobe tana tsotsar magarya.

Fuskarnan tasha shegiyar kwalliyar nan tata mekama data aljanu.

Goruba tadauko tafara gwaguya,bayan tafesoma gwaggo rabi yayan magaryar data tara abakinta.

Tanaci tana gwalo idanu,dayake barakumullah akwai manyan idanu saita kara tsorata gwaggo rabin.

Aiko aguje ta ufa,tana fadin wayyo ku agajeni, jama'a aljana a dakin amarya....

Zahra jin an ambaci aljana yasata durowa Dirk, kamar wacce aka jeho ta rufama gwaggo rabi baya....









*mum meenat*😍

Maman Nasirudden dinku💃🏼




*






*mum meenat

*MIJIN 'KWAILA🤦🏼‍♀*








Chapter 28.








*Writing by Maman meenat😍*








*Edited by Aisha Abdullahi T.Fulani (Umman farouq)*




*Wannan shafin d'ungurunhun na sadaukar dashi gareki Ameena Muhammad'meenat faxy novel😘.*
*Dakuma Ameenat shamsu,my meenat Ameena Abdullahi kai dama dukkan wata mesuna Amina,hakika mum meenat tana kaunarku sosai*.

*Khairat baffa,da Amshat Kuma ban mance daku ba,Nace kuji dadinku.😉*






Zahra jin an ambaci aljana yasakata wantsalowa tarufama gwaggo rabi baya,

Wasan tsere suka soma,gudun inbakayi bani wuri.

Gwaggo rabi banda ihu babu abinda take zabgawa.
Jin taku abayanta yasakata waigowa,wayyo na Allah na ai qamewa tayi qam.
Bakinta yana karkawar fad'in"qulu,hiya ilaiya,,kuke ganinmu bamu ke ganinku.
Kirufaman asiri natuba,wa'innahu min sulaimana."

Sai alokacin zahra ta fahimci abinda gwaggo rabin take nufi,wato tana zaton itace aljanar🤔.
Dayake abu yazo game nema,dama hausawa sunce wai meneman kuka bare anjefeshi da kashin awaki,don hka zahra ta takarkare tasoma gwagwaloma gwaggo rabi idanu tana tsomalo baki tana kanannade hannuwa.

Gwaggo rabi dai a'inda tayanke jiki tafadi saiga fitsari,sirrrrrrrr yana bin kafafunta yana gangarowa bisa tile's.
Zahra wacce dariya taso kwacemawa tadaure takama kafafun gwaggo rabi tanaja qiiiiii,har takaita bakin kofar falon.

Itadai gwaggo rabi idanu suna rufe,addu'a babu kalar wacce batayi,kai hatta addu,'ar saka tufafi saida gwaggo rabi ta karantota awannan lokaci duk da bama dai-dai take karantawa ba.

Ai zahra nakaita bakin kofa,takoma ciki aguje tana sheka dariya dacewa"y'ar tsohuwa me shegen tsoro,gobema kisake xagin abbana saina jefa maki qadangare ta windon daki.",

Tayi kwafa,tashige bayi tadau soso da sabili tawanke fuskarta fes,tamutsuka mai da powder kawai,tacanja kayanta daga bakar jalabiya zuwa Riga da wando yan Pakistan.

Hayewa gado tayi abinta tana kyalkyala dariya hada rike ciki,aranta ta'ayyana aiko gwaggo rabi tabani tunda haka take da shegen tsoro .

Gwaggo rabi dai tana zaune jagwab kofar daki,idanuwa arufe don duk zatonta Jan dataji anayimata aljanune suka saceta.
Tsoronta d'aya tabude idanuwa taganta fadar sarkin Aljanu.

Dr.aysherh daketa kwad'a sallama itada yar lelenta aneesa wadda takile cikin matsiyacin swiss,jikinta na aman kamshin turare,

Baki tasaki sororo tace"wanake gani haka kamar gwaggo rabi? ".

" Nice y'ar nan,don Allah wacce duniya nake,tamutane kota aljanu?"

Gwaggo rabi ta tambaya cikin rawar murya.

Dr.aysherh tajuya takalli anee wadda kema gwaggo rabin kallon raini,suka sakarma juna murmushi.

Dr.aysherh tace"bude idanunki gwaggo hajiya Aisha ce,nice bude,.ahankali tabude idanun aiko saita kankame hannun aysherh tanacewa wlh aljana nagani adakin amaryar isiyaku,
Har rywan sama tayomun.

Gara mugaggauta barin wurinnan tunkafin takaimu fadarsu."

Dan bubbuga kafarta aysherhn tayi ganin atsorace take tace"aljana kamar ya,ke a'ina kikaga aljanar,?"

Gwaggo rabi baki na rawa tace,",a dakin amarya mana.Nan dai takwashe komai tasanar ma aysha ."

Wani killer smile ayshan tasaki tana kallon aneesa dake smiling din itama.don sunsani babu wanda zai aikata wannan aikin sai zahra.

 kama  hannunta ayshan tayi tace"saurareni gwaggo, aiwato ita wannan aljanar dakika gani tofa amaryar ishaq ce take rikida tazama aljana.don haka kada kiyarda koda wasa yau ace wani yaji wannan labarin tofa zata biyo dare ta kasheki.
Shawarar dazan baki kija bakinki kiyi shiru karki sanarma kowa abinda kika gani."

Gwaggo rabi tace"aini yauma zanbar wannan jarababben gidan tunda abu yahada hadasu aljanu aikuma bani basake shigowa gidannan har abada."

Aysha ta guntse dariyarta tace"lahh,karki soma,aimaganinta d'aya dazamuyi shine mutursasa ishaq yaqara aure,tanuna anee dayatsa.Kinga yarinyata nan,tanada maganin iskokai,tokawai kiruntse idanuwa lalli idan ishaq bai aureta ba,tofa ko tsinuwace ki gifta akan mahaifinshi.
Tahakane kawai zamuyi maganin wannan bakar aljanar kuma shima jikanki ishaq yasamu magada tunda kindaisan su aljanu bakamar bil'adama Duke ba basa haihuwa."

Gwaggo rabi tayi tsuru,tana ayyana ishaq amatsayin mara hankali,to Mara hankali mana,tayaya zaka hada jini da mutanen 'boye.oh itadai taga takanta jikoki daga me auren kafura same auren aljanu.?"

Tamatse hawaye tana shima aysha albatka tace"wlh ko'ubanwa yatsaya mar agarinnan saiya auri wannan kyakywar  yarinyar yarabu da waccen aljanar muje.

Takama hannun aysherh, sukayi gaba aishan nakara zugata dayimata famfo.

Zahra dake labe tanajin duk abinda sukeyi tayi kwafa,dacewa dukanku zakuci ubanku yara.....








*real mum meenat*😍



*pls kuyi manage da wannan,yarona Nasser babu lafiya,shima kyanda takama munshi,kusashi a addu'a da bakunanku masu albarka.Allah yasa yagamata lafiya.*Ameen😭.

*MIJIN 'KWAILA🤦🏼‍♀*








Chapter 29.






HIKIMA WRITER'S ASSO...🕊

*Writing by Maman meenat😍*








*Edited by Aisha Abdullahi T.Fulani (Umman farouq)*











Zahra jin an ambaci aljana yasakata wantsalowa tarufama gwaggo rabi baya,

Wasan tsere suka soma,gudun inbakayi bani wuri.

Gwaggo rabi banda ihu babu abinda take zabgawa.
Jin taku abayanta yasakata waigowa,wayyo na Allah na ai qamewa tayi qam.
Bakinta yana karkawar fad'in"qulu,hiya ilaiya,,kuke ganinmu bamu ke ganinku.
Kirufaman asiri natuba,wa'innahu min sulaimana."

Sai alokacin zahra ta fahimci abinda gwaggo rabin take nufi,wato tana zaton itace aljanar🤔.
Dayake abu yazo game nema,dama hausawa sunce wai meneman kuka bare anjefeshi da kashin awaki,don hka zahra ta takarkare tasoma gwagwaloma gwaggo rabi idanu tana tsomalo baki tana kanannade hannuwa.

Gwaggo rabi dai a'inda tayanke jiki tafadi saiga fitsari,sirrrrrrrr yana bin kafafunta yana gangarowa bisa tile's.
Zahra wacce dariya taso kwacemawa tadaure takama kafafun gwaggo rabi tanaja qiiiiii,har takaita bakin kofar falon.

Itadai gwaggo rabi idanu suna rufe,addu'a babu kalar wacce batayi,kai hatta addu,'ar saka tufafi saida gwaggo rabi ta karantota awannan lokaci duk da bama dai-dai take karantawa ba.

Ai zahra nakaita bakin kofa,takoma ciki aguje tana sheka dariya dacewa"y'ar tsohuwa me shegen tsoro,gobema kisake xagin abbana saina jefa maki qadangare ta windon daki.",

Tayi kwafa,tashige bayi tadau soso da sabili tawanke fuskarta fes,tamutsuka mai da powder kawai,tacanja kayanta daga bakar jalabiya zuwa Riga da wando yan Pakistan.

Hayewa gado tayi abinta tana kyalkyala dariya hada rike ciki,aranta ta'ayyana aiko gwaggo rabi tabani tunda haka take da shegen tsoro .

Gwaggo rabi dai tana zaune jagwab kofar daki,idanuwa arufe don duk zatonta Jan dataji anayimata aljanune suka saceta.
Tsoronta d'aya tabude idanuwa taganta fadar sarkin Aljanu.

Dr.aysherh daketa kwad'a sallama itada yar lelenta aneesa wadda takile cikin matsiyacin swiss,jikinta na aman kamshin turare,

Baki tasaki sororo tace"wanake gani haka kamar gwaggo rabi? ".

" Nice y'ar nan,don Allah wacce duniya nake,tamutane kota aljanu?"

Gwaggo rabi ta tambaya cikin rawar murya.

Dr.aysherh tajuya takalli anee wadda kema gwaggo rabin kallon raini,suka sakarma juna murmushi.

Dr.aysherh tace"bude idanunki gwaggo hajiya Aisha ce,nice bude,.ahankali tabude idanun aiko saita kankame hannun aysherh tanacewa wlh aljana nagani adakin amaryar isiyaku,
Har rywan sama tayomun.

Gara mugaggauta barin wurinnan tunkafin takaimu fadarsu."

Dan bubbuga kafarta aysherhn tayi ganin atsorace take tace"aljana kamar ya,ke a'ina kikaga aljanar,?"

Gwaggo rabi baki na rawa tace,",a dakin amarya mana.Nan dai takwashe komai tasanar ma aysha ."

Wani killer smile ayshan tasaki tana kallon aneesa dake smiling din itama.don sunsani babu wanda zai aikata wannan aikin sai zahra.

 kama  hannunta ayshan tayi tace"saurareni gwaggo, aiwato ita wannan aljanar dakika gani tofa amaryar ishaq ce take rikida tazama aljana.don haka kada kiyarda koda wasa yau ace wani yaji wannan labarin tofa zata biyo dare ta kasheki.
Shawarar dazan baki kija bakinki kiyi shiru karki sanarma kowa abinda kika gani."

Gwaggo rabi tace"aini yauma zanbar wannan jarababben gidan tunda abu yahada hadasu aljanu aikuma bani basake shigowa gidannan har abada."

Aysha ta guntse dariyarta tace"lahh,karki soma,aimaganinta d'aya dazamuyi shine mutursasa ishaq yaqara aure,tanuna anee dayatsa.Kinga yarinyata nan,tanada maganin iskokai,tokawai kiruntse idanuwa lalli idan ishaq bai aureta ba,tofa ko tsinuwace ki gifta akan mahaifinshi.
Tahakane kawai zamuyi maganin wannan bakar aljanar kuma shima jikanki ishaq yasamu magada tunda kindaisan su aljanu bakamar bil'adama Duke ba basa haihuwa."

Gwaggo rabi tayi tsuru,tana ayyana ishaq amatsayin mara hankali,to Mara hankali mana,tayaya zaka hada jini da mutanen 'boye.oh itadai taga takanta jikoki daga me auren kafura same auren aljanu.?"

Tamatse hawaye tana shima aysha albatka tace"wlh ko'ubanwa yatsaya mar agarinnan saiya auri wannan kyakywar  yarinyar yarabu da waccen aljanar muje.

Takama hannun aysherh, sukayi gaba aishan nakara zugata dayimata famfo.

Zahra dake labe tanajin duk abinda sukeyi tayi kwafa,dacewa dukanku zakuci ubanku yara.....








*real mum meenat*😍



*pls kuyi manage da wannan,yarona Nasser babu lafiya,shima kyanda takama munshi,kusashi a addu'a da bakunanku masu albarka.Allah yasa yagamata lafiya.*Ameen😭.

0 Response to "Mijinki A Tafin Hannunki"

Post a Comment