A daren jiya ne aka fara biyan wasu daga cikin masu cin gajiyar shirin TVET IDEAS INITIATIVE, inda aka tura musu alawus na naira dubu arba’in da biyar (₦45,000).
Wannan mataki ya zo ne yayin da ake ƙoƙarin biya dukkanin basussukan alawus da ake bin shirin. Majiyoyi sun bayyana cewa gwamnati na ɗaukar wannan matakin ne domin tabbatar da cewa an biya kowa haƙƙinsa kafin a fara ɗaukar sabon rukunin (batch) masu amfana.
Haka kuma, an sanar da cewa za a fara ɗaukar sabbin masu shiga shirin daga ranar 13 ga watan Afrilu. Ana sa ran wannan rukunin zai ba wa matasa da dama damar samun horo da tallafin da zai taimaka musu wajen dogaro da kansu.
Zan sanar da ku da zaran an fara ɗaukar sabbin waɗanda za su amfana da shirin.
0 Response to "SABON BAYANI KAN SHIRIN TVET IDEAS INITIATIVE : A daren jiya ne aka fara biyan wasu daga cikin masu cin gajiyar shirin TVET IDEAS INITIATIVE"
Post a Comment