-->

SHAFIN HASKENEWS NA WHATSAPP

Duba Addu'ar Da Yadace Ayi Bayan Tabbatarda Ganin Jinjirin Watan Ramadan

Duba Addu'ar Da Yadace Ayi Bayan Tabbatarda Ganin Jinjirin Watan Ramadan

Duba Addu'ar Da Yadace Ayi Bayan Tabbatarda Ganin Jinjirin Watan Ramadan

Bismillahirrahmanirrahim. Dukkan godiya sun tabbata ga Allah madaukakin sarki, mai kowa mai komai, mamallakin kowa da komai, cikin rahamarsa yau muna kwanan wata 29 ga watan Sha’abaan. Hakan na nuna cewa bisa ga rahoto da aka tabbatar na ganin jinjirin wata, to gobe Insha Allahu zai kasance daya ga watan Ramadaan. Tsira da aminci su tabbata ga fiyayyen halitta, Manzon Allah Annabi Muhammad SAW.

Yaku ‘yan uwa, mu sani cewa watan Ramadaana wata ne mai falala da yawa, rubutun mu na gaba zai kawo mana su Insha Allah. Saboda haka, mu lizimci dukkan wani aiki na alkahairi don neman rahamar Ubangiji, kuma mu nesanci dukkan wani zunubi don gujewa fushin Ubangiji SWT a wannan wata mai dumbin falala.

Yazo a cikin Hadisi wanda Bukhari da Muslim suka ruwaito, Manzon Allah SAW yana cewa: “ku dau azumi da kallon jinjirin wata (Ramadaan), kuma ku ajiye azumi da kallon wata (Shawwaal)”. Wannan yasa babban sharadi na azumin Ramadaan shine ganin wata.

To a nan, menene musulmi yakamata yayi idan ya ga wata?

Ya tabbata a sunnah cewa idan aka ga wata akwai addu’a da ake yi. Wannan addu’ar kuwa ita ce “Allahumma ahillahu alaina bil Amni, wal Iman, wal Salaama, wal Islam, Wat Taufiq Lima tuhibbu wa tarda, Rabbuna wa Rabbuka-Llah”. [At-Tirmidhi]

Ma’anar sa, “Ya Allah Ka Sa (wannan wata ya kasance) na samun tsaro, da Imani, da zaman lafiya, da musulunci da dacewa ga abunda Kake So, Mahaliccin mu kuma Ubangijinka Allah.”

Daga karshe yaku ‘yan uwa mu daura damara sosai na ibadaa sosai tare da ikhlasi. Mu shirya karanta Al-Qur’ani, Tarawi, Sadaka, ciyarwa, da sauran ayyuka na neman yaddan Allah.

0 Response to "Duba Addu'ar Da Yadace Ayi Bayan Tabbatarda Ganin Jinjirin Watan Ramadan"

Post a Comment