-->

FOLLOW HASKE NEWS WHATSAPP CHANNEL

FOLLOW HASKE NEWS WHATSAPP CHANNEL
To continue receiving our daily updates on news, jobs, and opportunities, please follow our new channel above, Thank you for your continued support Haskenews Media & Publishing Services
Zamu sake fitar da ‘yan Nageriya mutun milyan ashirin da biyar 25m daga kangin talauci - Cewar Farfesa Osinbajo

Zamu sake fitar da ‘yan Nageriya mutun milyan ashirin da biyar 25m daga kangin talauci - Cewar Farfesa Osinbajo

Zamu sake fitar da ‘yan Nageriya mutun milyan ashirin da biyar 25m daga kangin talauci - Cewar Farfesa Osinbajo

Mataimakin shugaban Ƙasar Nageriya farfesa Yemi Osinbajo yace shirin Hukumar zuba hannun jari ta ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje wato- NDIS na ɗaya daga cikin wata hanya Mai mahimmanci da zata kawo zuba hannayen jari a Ƙasar.

Osinbajo ya bayyana haka a lokacin taron Hukumar cigaban ƴan Najeriya mazauna ƙasashen waje NDIS karo na 4 na wannan shekara ta 2021.

Mataimakin Shugaban Ƙasa yace hakan zaiyi sanadiyar a fitar da ‘ƴan Najeriya Miliyan 25 daga ƙangin Talauci a shekarar 2025. Taron Daya gudana ranar Talata a ɗakin taro na shugaban ƙasa dake Villa Abuja.

Osinbajo Wanda ya samu wakilcin Sakataren Gwamnatin Tarayya Boss Mustapha yayi nuni dacewar an ƙirƙiri NDIS domin samar da zuba hannun jari a Najeriya.

Osinbajo ya bayyana cewar manufar Gwamnatin Buhari shine a inganta kuɗaɗen shiga a ƙasar.

Yace gwamnatin a shirye take domin samar da ayyukan yi ga matasa Yan Nageriya.


Source: opportunitieshub

0 Response to "Zamu sake fitar da ‘yan Nageriya mutun milyan ashirin da biyar 25m daga kangin talauci - Cewar Farfesa Osinbajo"

Post a Comment